L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 15
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 15: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 15. Karon farko ya zuba mata ido da wani kallo na…
3,357 words
Karon farko ya zuba mata ido da wani kallo na daban.....tausayinta a karon farko ya soma ratsa zuciyarsa da qarfin gaske. Yaji zuciyarsa tana nauyi,yana rayawa a ransa,idan shine ya rasa nanay dinsa yaya zaiyi?. Inda ya rayu ba noorah......ba hussam.....ba rumaisa.....ba khansaa.....ba Aareef yaya rayuwa zata kasance masa?.
Tausayinta yakeji da gasken gaske.....dukka batasan dadin wadannan ba?. Batasan dadin uwa ba.....batasan dadin 'yan uwa ba. Ta rasa da yawa cikin rayuwarta ba tare data sani ba.....ta rasa wasu bangarori masu matuqar Muhimmanci bata gane ba. An kange mata rayuwa an tsaidata a wani muhalli guda daya,ta dauka iya haka ta morewa rayuwarta.
A yadda ta motsa ya fuskanci dauke idanu tayi daga kallon wani abu,kallon wani abu da ya tabbatar shine. Yaji a jikinsa a dazun,amma kuma yanason kamata a yansu da kansa......yanason kamata yadda ba zata iya musa masa ba,don haka yayi kaman ya dauke kai.....yayi kaman ba yaci gaba da abinda yake gabansa ne.
Karo na biyu ta sake waigowa,tana jin wannan haushin can qasan ranta. Me yasa yakeson maidata mayyar kallonsa?,me yake dashi me janye hankali har haka?. Ba haka take ba.....ta sani ba haka dabi'arta take ba. Komai kyau....komai isar d'a namiji baya da wannan muhimmancin a gareta.....me yake shirin canzata?.
Da wani irin zafin nama ya waiwayo,ya kuma kamata kaman yadda yayi timing. Ta dan razana don haka tayi saurin kauda kanta.
Murmushi ya saki....wani kalan murmushi me sanyi.
"Me yasa ba zaki bar wuyanki ya huta ba akhnan?" Har tsakiyar tafin qafarta taji yadda ya kira sunanta. Wani irin accent yayi amfani dashi daya sanya sunan ya sauya kamar ba sunanta ba....kamar ba sunan data saba ji daga bakunan mutane ba. Izzarta ta motsa kadan,saita hade ranta sosai,tana ji a ranta bai kamata haka taci gaba da kasancewa ba,bai kamata ya ganta tana kallonsa ba har haka.
"Da akayi me?". Wannan karon murmushin nasa sai daya bada sauti kadan,murmushin daya masa kyau ainun,har ya dauki hankalin wasu 'yammata dake zaune daf da inda zasu wuce,kuma akan idanunta,tana ganin yadda dayar ta tabo 'yar uwarta a dabarance,tabar danna wayar da takeyi ta xuba masa idanu kuwa. Idanunta ta dauke a kansu tana jin wani abu ya matse a qirjinta.
"Me yasa duka wannan?" Ta tambayi kanta,me yasa takejin kanta kamar ba ita ba?,kamar ba ita akhnan ba?,me yasa?.
Ya shirya shayar da ita mamaki,don haka ya miqa yatsunsa ya kama habarta ya juyo da fuskarta zuwa saitin tasa cikin ba zata. Tazarar dake tsakaninsu ya hade yana duban tsakiyar qwayar idanunta,a hankali ya motsa labbansa,tafiyar tasu dukka su biyun tana komawa very slow kamar wadanda qafafunsu sukayi sanyi.
"I'm your halal.....ki kalleni kai tsaye kaman zaifi your highness.....kina yawan kauda kai,kaman bakisan kina kallona bane"
Kasa cire idanunta tayi daga nasa,kaman yadda shima ya zabi ci gaba da karantarta ta cikin qwayar idanunta masu kalan blue da haske qwayayen haram ke sake haske masa su. Wani unique qwayan idanu da suka banbanta da irin wanda kowa yake dashi.
"Sun narke dukkansu......amma inda zakace wani abu yanzu kowannensu saiya qaryataka" Maleek dake tsaye daga nesa kadan dasu ya fada yana riqe da falaak sosai cikin jikinsa kamar wani zai qwace masa ita,saidai kuma akhnan da haisam din dukkansu sun dauki hankulansu fiye da yanayin da suke ciki.
Duk da yanayin kunyar da maleek keta saka falaak adan tsukin......amma a yanzu....a daidai lokacin saita hango wani boyayyen abu....wani boyayyen abu da yafi qarfin kansu ita da maleek din gaba daya. Wani abu da yasa taji kamar zata narke.....kamar bata taba ganin abun burgewa a rayuwarta ba irin tsaiwar akhnan da haisam a gurin......duk da basajin maganan me suke.....amma ko daga nesa duk wanda zai wuce sai ya kallesu,sai kuma ya sake waiwayowa ya sake kallonsu,saboda wani irin perfect match da aka tasa a gurin.
A hankali ya sake mata habarta,taja baya da sauri tana sunkuyar da kanta qasa. Me yasa ta tsaya?,me yasa taci gaba da kallonsa?.
"Yaaa akhnan" Muyar falaak ta fusgi kunnuwanta,falaak din data kasa jurewa sai data kira akhnan din,duk da yadda maleek yaso ta bari su mamayesu kawai.
Tunda yaji muyar falaak ya tabbatar tare suke da maleek. Sauke hannuwansa yayi ya soma laluben nata hannayen cikin nasa ba tare daya waiwaya ya kalli inda suke ba.
Sosai ya matsesu cikin nata,dumin dake jikin tafin hannun kowannensu yana zagayawa sassan jikin kowannensu. Idan yace bayason tafukan hannayen ta yayi qarya......idan yace dumin da yakeji a ciki basa burgeshi yayi qarya......idan yace siraran dogayen yatsansa da suke shigewa cikin nasa basa burgeshi yayi qaerya. Karon farko a rayuwarsa daya tsaya karantar yanayin hannun wata diya mace.....kaman yadda ta zama mutum ta farko daya fara saka hannuwanta cikin nasa irin haka.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Banaso ki kalli kowa......shi yasa nace ni ki kalleni kai tsaye a duk sanda hakan yayi miki" Ya qarashe maganan yana duban idanunta,can qasan ransa kuma yana jin kamar maganar tayi nauyi.....kaman bai furta maganan daidai ba.
"Maleek na tahoha......boundaries please" Ya fada muryarsa can qasa kamar wanda kejin bacci,abinda ya tayar da duk wata tsiga kenan ta jikinta,saboda sai daya kawo bakinsa saitin kunnenta sannna ya qarashe maganan.
Ta rasa wannan boundaries da yake saka mata na meye......ta rasa me yasa yake yawan nanata mata kalmar a duk sanda zasuyi wata hulda data hada da maza a gurin.
Sakin hannunta qwaya daya yayi,sannan ya maidata a gefan kafadarsa daya suka fara takawa a hankali suna tunkarar su maleek dake tsaye a gurbinsu.
Idanunsa akan fuskar maleek kawai suka tsaya,yana kallon yadda maleek din ya sunkuya a hankali yayi magana da falaak. Bai kalleta ba.....amma in blurry vision yake ganin kamar ta saka tafin hannunta ta lullube fuskarta. Baisan me yace da ita ba.....amma yayi imanin gulmarsu sukayi.
Sakin hannunta yayi a hankali ya miqawa maleek sukayi musabaha,yana jin falaak na gaidashi.
"Barka da warhaka Aman-nin"
"Barkanki kina lafiya?"
"Alhamdulillah".
"Aman-nin......me kenan habibty?" Duka sai falaak din taji ya aza mata nauyi. Tun daga saukarsu zuwa yanzu a yau din ita kadai tasan nauyin da maleek yake sakawa takeji.
"Yaren Tuareg ne.....yana nufin yaaya"
"Zaa koyamin?" Ya tambayeta yana narke murya idanunsa dukka a kanta kamar ya cinyeta. Kai ta daga a hankali.
"Kun kammala umrar?". Haisam ya katse tattaunawar tasu,saboda lura da yadda maleek yake neman sauka daga layi.
Maido dubansa maleek yayi ga haisam din,dama kuma abinda yakeso kenan,sai haisam din ya watsa masa harara. Dariyarsa ya danne,ya sani muddin idanun haisam suna kanka baka isa kayi abun arziqi ba.
"Habibty ta gaji......gobe zamu qarasa sa'ayi" Kafada haisam ya daga dukka biyun.
Kallon akhnan falaak tayi,wannan qaunar.....wannan 'yan uwantakar,sai taji ta kasa jurewa duk da dariyar da take boyewa. Ta taka da sauri yana rungume akhnan din don ta sani ba lallai ta fara samun hakan daga akhnan din ba.
"Yaa biftu.....Essaghlegh-kem(nayi kewarki).Temegded temhust(kinyi kyau)". A karon farko taji wani 'yan uwantaka na ainihi yana ratsata sanda falaak ta rungumeta,sai ta samu kanta itama da zagaya hannu ta rungume falaak din cikin jikinta,sannan ta amsa mata itama cikin yaren Tuareg din,don suna ganin shine kadai safest yare da zasuyi maganansu cikin sirri.
"Kice wani abu daban mana falaak?,ta ina kikayi kewata?,ina kuka bace?". Baya kadan falaak taja tana dariya a kunyace,amma kafin tace komai taga haisam din riqe da hannun maleek suka qara taku kadan gaba dasu suka basu tazara.
" Ya biftu......man dinki....man dinki shine ya koremu,yace bazai hada masauki da habeeb ba.....ina jins......"
"Habeeb?" Akhnan ta samu kanta da maimaitawa tana zubawa falaak ido. Kunya ta saukarwa falaak,tasa tafin hannunta tana toshe bakinta gami da sakin dariya.
"Afwan ya biftu......amma shine ya koremu seriously fa........basan wanne irin hot love zaa baza ba haka da ba'a gayyatarmu" Ta qarasa fada qasa qasa tana raba idanu.
Fuska akhnan din tadan hade tana hararan falaak
"Baki da kunya sosai ashe falaak ?.kin manta?Nekk a weltma-kem tameqqart.(ni yayarki ce?" Ta fada tana komawa ainihin akhnan dinta.
Murmushi ta sake saki a kunyace,sai suka taka suna zama saman tiles din gurin. Idanu kawai akhnan ta zubawa falaak,yadda take magana yake bata mamaki. Me maleek ya bata haka kaman ta zauce a kanshi?.
"Ya isa" Akhnan ta fada a hankali tana dagawa falaak hannu. Wani irin soyayya ne me zafi take gani a idanun falaak din,koda suna tare amma idanunta yana tare da maleek din,kamar yadda ta karanci kaman shike tsokanota daga inda yake.
"Zamu wuce yaa biftu" Falaak ta fadi bayan ta miqe.
"Byee" Akhnan ta fada tana daga mata yatsu,itama saita maida mata ta soma takawa tana nufar inda maleek din yake.
Qasa ta danyi da kanta tana murza yatsunta. So take ta fayyace.....laifi falaak tayi?,ko kuma akan daidai take?. Wanne irin so ne wannan?,baiyi zurfi da yawa ba?. Tadan yi taku biyu baya don daidaita tsaiwarta,sai taji kaman ta dunguri wani abu,ta juya da sauri.....saurin daya bawa fuskarta daman shiga cikin nasa,sukayi musayar numfashi sannan tataka baya da sauri,saidai tuni ya saka hannunsa ya riqo qugunta. Da sauri ta daga ido ta kalleshi sanda take riqe cikin hannunsa,sai ya mata nuni da bayanta da idanu.
Takalmi ne a gurin na mutane,wanda tabbas data taka koda bata fadi ba saita kusa faduwa,saita maida dubanta kansa,a hankali ya zame hannunsa yana sakinta amma still idanunsa cikin nata.
Kallon nan yana mata nauyi da yawa,ko a yanzun sai taji idanunsa suna neman sanyata ta diririce,saita soma gyara zaman hijab dinta ko zata samu chance na lalubo nutsuwarta.
"Coffee?" Ya motsa labbansa ya fadi a hankali idanunsa suna kan kwantaccen gashin gefan fuskarta daya fito.
Manyan blue eyes dinta ta daga tadan kalleshi,haka kawai wannan karon yaji kamar an qarawa qwayar idanun nata haske,sai kuma ta zame a hankali ta motsa bakinta tana fadin.
"Okay".
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽
💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 28*
A nutse take qarewa gurin kallo,shima ko ba'a gaya mata ba vip ne......ta sani vip ne gurin,don komai nasa a tsare yake. Hatta da butoci da cups da tray na tea din daban suke.
Daya daga cikin ma'aikatan gurinne ya qaraso cikin girmamawa ya gaida haisam. Sai yayi magana dashi da yaren da bata fahimceshi ba. Juyawa yayi ba dadewa ya dawo da kalolin tea da coffee din ya ajiye musu ya juya.
Kallonta yayi kadan sannan ya kalli tray din,ya dauki buta daya ya tsiyaya mata cikin madaidaicin cup din ya tura mata zuwa gabanta.
"Akwai wani abu daban da kike da buqata?" Ya tambayeta yana kai nasa cup din bakinsa. Original oromo coffee......tea din daya jima dayin missing dinsa tun bayan shigarsa agadez. Kai ta girgiza a hankali,ta miqa hannu ta dauki cup din,amma kuma ta kasa kaiwa bakinta. Wani irin rashin sakewa da rashin sabo takeji,cin abinci a gabansa wani sabo kuma baqon abune a gurinta. Saita dinga juya cup din kawai cikin hannunta a hankali har sai daya lura da hakan.
"Kina iya sha bayan ya huce?" Ya tambayeta yana sauke idanunsa daga kanta. Shuru ta danyi kafin a hankali ta dauki cup din takai bakinta.
A yangance da nutsuwar izzarta tayi sipping sannan ta sauke cup din tana jin dadin coffee din yana ratsata. Idanunta ta maida cikin cup din tana kallon abinda yake ciki sosai abinda batayi ba a dazu,sai ta sake daga idonta tana dubansa.
Girarsa ya daga mata dukka biyun yana aje cup dinsa.
"Oromian coffee" Ya furta a taqaice,ta danbi lips dinsa da kallon wanda dumin coffee dinsa ya sake sanyawa yayi wani irin jaja jaja me kyau,saita dauke idonta a hakali zuciyarta na raya mata wani abu.
Minti talatin kawai sukayi koma koma raffles don su sake hutawa sosai. Birra ta shigo har dakinta ta tayata rage kayan jikinta,tayi wanka ta fito ta sake shiryawa cikin kayan baccin guda daya data dauko mata.
"Me yake damunki ne birra?....me kike sanda kika hadamin kaya ne?" Qasa tayi da kanta cikin Girmamawa
"Tuba nake.....sheikh yace komai daya danganci gida a barshi a nan....umarnin dana karba kenan". Shuru akhnan din tayi tana kallon birra,tana kuma son gano dalilin daya sanyashi ya bada wannan umarnin. Bata gane komai ba,don haka kawai tace da ita.
"Jeki"
"Ki huta lafiya" Ta fada tana juyawa sannan ta fita.
Duk da duhu daya mamaye dakin,amma hakan bai hana shigowar haske daga gurare daban daban na waje ba. Wani irin sukuni takeji a duk sanda ta bude lumsassun idanunta ta hangi hasken harami daga nan inda take kwance da kuma ginin ka'aba.
"Astgafirullahal azeem" Ta samu kanta da maimaitawa tana tuna wannan kalmar.....wannan kalmar ita ta dinga ji haisam din yana yawan maimaitawa,wannan kalmar a yau batasan adadin sau nawa ta jita a bakinsa ba.
Ta sake lumshe idanunta komai yana dawo mata sabo. Tun daga tasowarsu daga agadez,Niamey,jidda zuwa cikin haram.
Dawafinsu da komai daya gudana a tsakaninsu yau din. Gyara kwanciyarta tayi zuwa rigingine tana zurfafa tunaninta.
"Wayeshi......wannan rayuwar batayi kama da wanda aka yiwa alfarma ba" Ta motsa labbanta a hankali tana fadi. Tuna komai take in details,tuna yadda yake gudanar da komai da yanayin sabo na mu'amala da komai da komai ma. Akwai yanayi sosai daya bayyana sabo da rayuwa me tsada a tattare dashi.....akwai yanayi daya bayyana gogewa da iya mu'amala da mutane.....akwai yanayin da yake haska wani abu a tare da dukka motsinsa......yanayin dake bayyanawa idanu kaman ya saba hulda da manyan mutane.
Ta yaya zai iya ganin manyan malaman harami haka idan har shi din ba wani bane?. Tambayar data sanyata miqewa sosai ta zauna tana rungume da pillow a qirjinta. Idanunta suna juyawa tsakanin dan haske da duhun dake gauraye a dakin.
Wani irin shuru taji cikin kanta,ta juya qwayar idanunta tana jin sautin muryarsa yana dawowa cikin kunnenta.
Ta lumshe idanun tana sake bibiyar kowanne sauti.... Kowacce magana da yayi mata a yau din.
Yana da wata irin murya me taushi.... Mai sanyi sannan kuma me zurfin gaske da idan ya maka magana kakejin saukarta kai tsaye saman zuciyarka. Wata irin murya da idan ta jita koda da kalma daya take ne sai taji zuciyarta ta buga. A hankali ta sake lumshe idanunta tana wassafa fuskarsa cikin gizanniyar idanunta.
Giant ne.....ta dade da lura da wannan....wani irin giant da tsaiwarsa kawai tana iya daukan hankalin diya mace,saboda murjajjen jikin da yake dashi,wanda ta dade tana kyautata zaton ma'abocin motsa jiki ne da daga qarfe daga yanayin structure din jikinsa duk da bata taba ganinta a sarari ba.
Tana iya tunawa da dogayen hannayensa masu dogon yatsu da suka sha tareta daga shan kayi daga dawakinta. Wani irin dogayen yatsu da suke mata kama dana mutumin daya saba da iko. Motsinsa bame sauri bane......amma kuma yana da wani irin control da zafin nama idan yaso.
Idanunsa sune mafi daukan hankali,manya ne ita kanta shaida ne akan wannan,amma ta lura wani lokacin daga shine?,ko halittarsu ce a haka?,sukan rage girma su lumshe sosai,har sai kayi zaton bacci yakeji,akwai wani irin calm intensity a tattare dasu me yawa. Sau tari idan ya kalleta,sai taji kaman yana ganin fiye da abinda ke saman fuskarta,har cikin jininta da jikinta tana jin yana da wani kebantaccen baiwa na iya karantar yanayin mutum ta cikin idanunsa,wannan yana daga cikin dalilin daya sanya take kaucewa dogon kallo daga gareshi.
Eyebrows dinsa da suka kusa hadewa da juna......hancinsa daya zauna sosai saman fuskarsa.....shi ba siriri ba kuma shi bame fadi ba,ya hade duka siffofin guri guda.
Ta lura dashi.....baya da yawan murmushi,amma aduk sanda yayin sai fuskarsa ta sauya da wani sirrin boyeyyen kyau da a iya lokacin murmushin kawai yake bayyana. Kawai komai nasa yana sake fadi da wani irin murya me nauyi da qarfi cewa he's not an ordinary man........amma me yasa ta gaza gane komai a kansa?,ta gaza gane ainihin wayeshi?.
Lips dinsa data tuna saida dukka tsigar jikinta ta tashi,wani abu ya motsa mata sosai cikin jikinta wanda batasan dashi ba,saita samu kanta da curewa guri daya,ta matse pillow din cikin qirjinta sosai tana tuna yadda dumin hannunsa ke bibiyar kowacce jijiya ta jikinta da wani irin sauri ya sauke mata kasala da gajiya.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Wani irin mirginawa tayi tana girgiza kanta.
"Why akhnan?.....me yasa?....me yasa?" Ta tambayi kanta tana girgiza kai.
Ko sau daya a farke ko a sarari bata taba zama irin haka tana wassafa wani d'a namiji ba tunda take. Ba wani d'a namiji data taba zama tama tuna da cikakken sunansa bama nasabarsa ballanta siffofinsa. Ba wanda yayi wannan isar.....ba wanda matsayinsa yakai...me yasa saishi?.
Wannan malamin?,wannan mutumin daya fara karya kusancinta da sultane,ya canja mata table na rayuwarta ya mallaketa da dukkan mugunta?.
Ada idan ta tuna hakan ciwo takeji.....baqinsa take gani,amma a yanzun duk da zuciyarta ta maimaita mata sai taji bataji komai ba,bataji komai ba sai wani irin yanayi dake mamayarta.....bataji komai ba sai wani abu me kama da kewar idanunsa.....kewar muryarsa da wannan miskilancin nasa.
Ta tabbatar a yanzun dare ya soma nisa,yadda kuma suka kwaso gajiya dole shima ya kwanta ya huta. Wani bushewa maqogoronta taji yayi,ruwa taji tana da buqatar sha,wani yanayi ya saukar mata da wata irin matsananciyar kasala a jikinta,saita zare pillow din,ta jawo jiki ta sauko daga saman gadon,ta saka hannunta tana tattare gashinta ta daure cikin scarf mahadin kayan baccin,sannan ta fara takawa zuwa living room din.
A nutse ta bude qofan ta soma fitowa tana mamakin labulen fuskar ka'aba dake a bude,wannan yasa living room din baiyi duhu sosai ba,don haka bata buqaci kunna haske ko daya ba taci gaba da takawa tana duban sashen da yake tarwai da fitilun haram da basa dusashewa ko daukewa.
Sai a sannan ta lura dashi,shine a zaune saman daddumar dake shimfide gaban gurin wadda ke dauke da tambarin hotel din. Cikin sujjada yake,wata doguwar sujjada da har ta dauko ruwan ta dawo tazo ta wuce bai dago ba. Haka ta dinga satar kallonsa har ta koma cikin dakin.
Zama tayi gefan gadon,ta bude ruwan ta riqe a hannunta. Baya gajiya?,shikam baya gajiya ne?. Haka kawai takejin kamar ya mata wayo,tana nan zata kwanta tayi bacci amma shi ya gagara baccin.
"To amma.....na gaji" Ta fada can qasan ranta.
"Kisha ruwan ki kwanta,saiki tashi da wuri kafin asuba tayi" Zuciyarta ta bata shawara. Saidai koda tasha ruwan ta koma ta kwanta baccin kasa zuwa yayi. Tsintar kanta tayi da tashi a hankali,ta jawo qofar baya ta soma leqensa ta tsakanin space din.
A yanzun a zaune yake,qur'ani ne kuma a hannunsa sautin karatunsa yana fita can qasa da wannan sautin nasa dake kusan narkar da zuciya. A hankali ta maida qofar ta rufe sanda yakai qarshen surar da yake karantawa,ta koma da baya a hankali har zuwa saman gadonta.
Pillow ta sake riqewa sosai tana sauke ajiyar zuciya,kafin ta tashi a hankali ta bude jakarta. Littafinta na tarihi ta dauko,tarihin fiyayyen halitta,littafin data kammala na farko ta dauko wallafar ibn taimiyya,sai kawai ta kunna fitilar gefan gadonta ta matsa rub da ciki ta bude ta dora karatu.
Batasan adadin awannin data kwashe ba a zaune,don ko bacci cikakke bata ji,tasan dai ta fada wata duniya daban da wadda take ciki. Zata iya cewa karatun a yau ya mata amfani fiye da kullum,saboda gata a gurin,gata a kusa da inda komai ya wakana na tarihin rayuwarsa. Taga abubuwa masu yawa,taga gurare masu muhimmanci gurin amsa addu'a,ta sake fahimtar abinda ya sanya haisam din bai yarda ya kwanta yayi cikakken barci ba. Sai taji gaba daya ta sake daura tata damarar,sai taji kaman duk zuwan da takeyi umra a baya kaman wasa ne,wannan zuwan.....wannan lokacin shine sahihin lokacin zuwa na gasken gaske.
*_W A S H E G A R I_*
Duka washegarin basu hadu dashi ba,tun daga asuba har zuwa dare,don ita dimma washegarin saita zamar mata kamar an mata allura an kuma sake qara mata qaimi akan ibada.