Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 16

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 16

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 16: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 16. Sam bata huta ba,kusan yini tayi cikin haram tana…

3,371 words

Sam bata huta ba,kusan yini tayi cikin haram tana addu'o'i. Har addu'ar da bata dauka cewa zata iya ba. Addu'o'in da bata taba kawowa a ranta wataran zata roqa ba. Shi take kalla a sanda yake zaune yake kuma dadewa saman abun sallah hannuwansa a sama. Wannan ya mata tasiri qwarai,ya kuma cire mata qyuya da ganda na dogon zama tana addu'a. Tayi zaman addu'ar da tunda take a rayuwarta bata taba irinsa ba. A hankali sai takejin wani tarin nutsuwa suna shigarta.

Bayan sallar la'asar ne birra ta iskota,tana zaune a lokacin tana hutawa kawai bayan ta shanye ruwan zam zam cup har biyu.

"Yallabai yace.....bayan sallar isha'i zaku qarasa sa'ayinku" Kadan ta daga kai ta kalleta,kaman ta tambayeta inda ta ganshi sai kuma ta fasa ta daga mata kai kawai.

Sai datayi sallar isha'i sannan ta wuce masaukinsu. Ta buda qofar ta tura,ba alamun akwai mutum cikin suit din nasu.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 29*

"Ki shiryamin komai ki wuce,zan qarasa shiryawa da kaina" Tace da birra tana zare qaramin hijab din data dora saman abayar jikinta. Karon farko da tayi ta'ammali da hijab har haka a rayuwarta,wadannan hijabs dinma data gani cikin kayanta batasan waye ya dinkosu ba. Haka kawai taji a yau din tanason shiryawa da kanta,kaman bai dace ba kuma birra ta wanzu a suit din nasu ba.

"Wai fa...." Ta fada tana duban birra dake shirin wucewa ciki.

"Hijabs dinnan fa?" Qasa birra ta danyi da kanta tana sake boyayyen murmushi.

"Ba iya su kadai ba.....duka kayan cikin luggage din......dama wanda na shigo miki dasu dazu,sheikh muhammad ne...."

"Ya isa" Akhnan ta fadi a nutse tana miqewa,sai birran bata sake cewa komai ba ta wuce ciki itama ta bita.

A baya bata damu da tsaiwa duba komai ba,amma a yanzun bayan ta fito a wankan saita samu kanta da bin komai da kallo.

Abayas din....hijabs.....bathsetdinta......set na mayukanta dama komai......ba asalin komai nata bane. Komai ya canza da wani irin tsari. Juya su take tana sake kallo,komai cikin wani tsari yake da burgewa,kaman yadda komai din yake nuna asalin tsadarsa.

Iska ta fesar a hankali,ta lura da banbance babancen,tayita mamaki ita kanta a karan kanta,amma ta dauka shirin birra ne,saidai ko data raya hakan a ranta ta danyi kokwanto,yaushe birra tasan abubuwa masu tsada irin haka?.

Yau cikin shigar fari ta shirya kanta. Farar baya ce me wani irin duwatsu masu sheqi da walqiya ruwan silver dake cancanza kaloli da duk abinda yayi reflecting nasu. Silver ash din snickers ta saka,sannan ta rufe kanta da Malaysian hijab shima daya kasance color din. Ita kanta data kalli kanta da kanta a madubi saida ta lumshe idanu,murmushi ya qwace mata,wani irin murmushi me sanyi. Bata taba sanin irin wannan shigar zata mata kyau ba sai yanxu,bata taba sanin zata zama daya daga cikin suturu da zasu dace da jikinta ba sai yanzu. Taja da baya tana duba lokaci,saita yanke ta fita ta living room din ta samu koda lemo ne tasha kafin su wuce.

Waya ce maqale a kunnensa saboda barin Bluetooth dinsa da yayi a daki,fitowarsa kenan daga wanka khansaaa ta kirashi. Ya daga wayar amma qishirwar da yakeji ta tilasta masa fitowa neman ruwa sannan ya koma ciki ya shirya.

Daure yake da farin towel,fari qal dashi me matuqar laushi. Daga qugunsa ya daureshi sosai,ya kuma tsaya masa iya qasan gwiwoyinsa.

Faffadan qirjinsa.......dogaye kuma tsayyayun qafafunsa.......yalwatacciyar kafadarsa......lallausar gargasar dake kwance saman qirjinsa dama duka sassan jikinsa sun bayyana suna zamewa fatarsa me cike da sulbi da wani haske na musamman ado. Shafaffen cikinsa ya taimaka wajen bayyanar qirjinsa dake cike da muscle,da wasu muscles din dake lullube da fatar saman shafaffen cikinsa.

Bai kula da ita ba kaman yadda bata kula dashi ba,don ba magana yakeyi ba yana dai sauraren khansaaa ne kawai kaman yadda al'adarsa take sauraro kafin yayi nasa bayanin,yana kammala zuba ruwan ya soma rufe gorar ruwan,daidai sannan ta daga idanunta daga latsa wayarta da takeyi cike da mitar ba wanda ya kirata tun daga jiyan zuwa yau?. Koda sultane kuwa?,koda aisa?,koda shehnaz?.

A hankali ta daga idanunta don ganin inda zata zauna,saidai maimakon ganin gurin zama sai idanunta sukayi wannan kyakkyawan ganin,daidai sanda shima ya aza idanunsa cikin nata.

Hannayenta ne suka dauki rawa,ta furta.

"Subhanallah" Da dan raunin murya muryartata tana shaking,sannan ta juya da sauri tana bashi baya,juyawar data sanya wayar hannunta sulalewa ta fadi a qasa.

Idanu ya zuba mata ta baya yana karantar yadda ta rude duka lokaci guda.

"Zan kiraki.....minti daya" Yace da khansaaa,sai ya zare wayar daga kunnensa ya kashe ya ajiye saman dan table din dake kusa dashi.

A nutse ya taka zuwa saman daya daga cikin kujerun,ya dauki bathrobe din dake ajiye gefanta ya zura ya kama igiyoyin ya daure ba tare da yace da ita komai ba.

Wata irin kunya cakude da wani nau'in tsoro ne suke dabaibayeta. Wani yanayin buguwa zuciyarta keyi tamkar wadda tayi tseren gudu na kilometers masu yawan gaske.

"Banyi tsammamin zaki fito ba" Ya furta a hankali don ya bata relief daga yanayin daya lura ta shiga,don har yanzu jikinta rawa yake idan ka lura sosai.

"N....nima b....ban sani ba" Ta amsa mata muryarta na rarrabewa saboda bugun da zuciyarta takeyi.

Taku kadan yayi ya isa bayanta don ya dauki daya towel din dake gefanta saboda tsane damshin sumarsa.

"Kina iya juyowa". Dab da ita ta jishi,dab da itan da takejin ko yaya ta juyo tabbas cikin jikinsa zata fada,saita kasa motsawa,qamshin shower gel dinsa yana buso mata a hankali,saita lumshe idanunta tana jin zuciyarta kamar tana shirin rikitowa daga qirjinta. Ya dauki towel din a nutse ya taka yana matsawa daga gurin. Wayarsa ya koma ya dauka sannan ya nufi qofar dakinsa yana shirin sake kiran khansaaa.

Ajiyar numfashi ta dinga saukewa a jejjere,ta saka tafin hannunta tana dafe qirjinta a hankali,sannan taja jikinta ta zauna saman kujerar.

"Wai Allah na..." Ta fada tana zare idanu,sai kuma murmushi ya qwace mata,kafin kuma a hankali idanunta ya sake dauko mata hoton yadda ta ganshi.

"lean, well-built body" Ta furta a hankali,sai kuma ta kama bakinta tana rarraba idanu.

"Me ya kaiki?,ina ruwan ki da jikinsa?,idan ya jiki kuma fa?"

"Baiji ba bazai kuma ji ba in sha Allah" Ta fada tana qoqarin ture tunanin ta hanyar kiran shehnaz,saidai kuma hoton ya kasa barin idanunta.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Haka jikinsa yake?" Taci gaba da fada cikin ranta. Favorite qirar da tasha kwatanta son samu jikin namiji,saidai abinda ya fara sare mata shine.....yawan mazan da muke dasu a qasashenmu basu maida motsa jiki a bakin komai ba. Kusan dukkaninsu qirar jikinsu irin na matansu ne.....damtsen miji da mata duka baka banbancewa kusan iri daya ne. A nata tsarin.....a nata ra'ayin komai na mijin da takeso ya zamana yasha banban dana mace.....asalin qira da siffar jarumta sosai,jarumi takeso....zakin gaske.....amma kuma" Saita dakata da tunanin a ranta kadan.

"Akwai wasu siffofi kaman....." Nanma ta katse tunanin kamar me tsoron tattaunawar yau da zuciyartata ma.

Jin muryar sultane ya yanke kowanne tunani daga ranta. Cikin doki kewa da qauna ta soma gaidashi. Daga nasa bangaren ya fita farinciki da jinta.

"Komai lafiya ko?,duk da muhammad ya tabbatar min" Kai ta daga tana murmushi.

"Lafiya alhmdlh....bappi ka manta dani,baka nemeni ba" murmushi yadan saka me sauti kadan.

"Inde muhammad ya kirani muka gama waya lafiya dashi,to na tabbatar kema lafiya kike".

"Amma bappi....kana lafiya?,muryarka si faible(so weak)" Murmushi ya sakeyi,tabbas idan yaje yana jinsa lafiya lau a kwanakin to yayi qarya,amma kuma ba buqatar ya gaya mata hakan. Nutsuwarsu da sake gamsuwa da zama da junansu yafi buqata a yanzu,ba wani buri da yake dashi sama da wannan a yanzu.

"Lafiya qalau nake,ina hutawa ne kawai" Kai ta daga a hankali. Hira kadan sukayi ahmad almaz ya karba.

Taji dadin magana dashi sosai,yayi magana da ita kaman yadda yaya zaiyi da qanwarsa,wani feeling wani yanayi data rasa a yanzun data sameshi sai takejin kamar ta fara zama completed.

Daga nan shehnaz ta kira,tana kira din kuwa ta daga kamar zaman jiranta takeyi.

"Ina da niyyar nemanki kenan kiranki ya riga nawa shigowa".

"Me ya faru?" Tambayi shehnaz din daidai sanda qofar dakinsa ta bude ya fito.

Da sauri ta yiwa kanta linzami ta hanyar zare idanunta daga inda yake takowa. Ta yiwa kanta alqawari ba za'a sake maimaita abun jiya ba duk yadda zaikai gayi mata kyau,saita tattara hankalinta akan shehnaz.

"Kwana aisa tayi tana kuka.....ta iso cikin wani yanayi daya daga hankalina. Sahel couture ya samu matsala biftu......dole ne na gaya miki wannan saboda kina gurin da ake amsar kowacce addu'a ta alkhairi. Anyi asarar maquden kudaden da idan ba wani ikon Allahn ba sahel ya tsaya da aiki har abada......tace batasan ya akayi ba,amma dukka kudaden sun fita dasa hannunta ne da sahalewarta,batasan kuma ya akayi haka ta faru ba......mammina ta yanke hukunci.......ta dakatar da aisa.......ta kuma ce zata kafa committee na bincike a kanta......kuma zata fuskanci duk hukuncin da aka tanada akan wanda irin haka ta faru ta sanadinsa". Wani irin sanyi hannu da qafafuwan akhnan sukayi.....wani irin yanayi da ta gaza tantance ame take?.

Aisa kuma?......aisa dai?. To me zatace?,me zatayi?. Sahel couture din daya zama alfaharin sultane?,sahel couture din data dauki alqawarin saita kaishi matakin da sultane sai yayi alfahari da mallaka mata shi din da yayi?,to me yake faruwa haka?.

A hankali taji an zare wayar daga hannunta,don dama a handfree take amma da lower volume bame qarfi ba. Daga idanunta tayi a hankali sai ta bishi da kallo,yana tsaye a gabanta,ya kuma sanya wayar a kunnensa. Tana jin sallamarsa da yadda shehnaz ta amsa da sauri ta fara gaidashi.

"Ki sanar da aisa.....ni nace ta koma Niamey yau.....ta bude office taci gaba da aiki,duk wanda ya tambayi dalili kome yasa......kice ta fada masa CEO tace ta koma......ki fada mata.....zan nemeta qasa da awa shirin da hudu zamu tattauna" Daga akhnan din har shehnaz mamaki ne ya kamasu.

Shehnaz dai ta sani......ba wanda keda qarfin ikon tada hukuncin mammina duk fadin niger ma ballantana agardez......agadez dinma cikin masarautar da kowa ya sani tana da cikakken iko a kanta?.

Ta dauka zai miqa mata wayarta ne......amma maimakon haka sai taga ya kasheta ya jefata cikin aljihunsa.

"Muje" Ya fada da wata nutsuwa yana dubanta,sai ta miqe tsam ta soma takawa tana wucewa ta gabansa zuwa waje.

Duk da zuciyarta a nauyaye take sosai da tarin tunane tunane,amma hakan bai hanata ganin idanuwan mata sosai akan haisam din ba. Jifa jifa idanunta suna gane mata,saidai abinda bata sani ba shima yana gani?,ko ita kadai take gani?. Still idanunta basu gaza gane mata wannan soyayyar ba.....wannan soyayyar da kake iya ganinta ko ina a sararin masallacin dama gurare daban daban. Ma'aurata cikin shauqin soyayya,wasu da yara wasu babu sai iya su kadai. Wannan yanayin ya dinga debe mata kewa yana ware mata zuciyarta a hankali,musamman da taji lallausan sautin nan nasa yana fadin.

"Allahu akhbar.....Allahu akhbar....subhanallahi wabihamdih......subhanallahil azeem" A sanda suke tattakawa saboda gabatar da sa'ayinsu.

Akan safa suka tsaya kaman yadda tsarin yake,suka fuskanci ka'aba ita dashi. Sukayi dukkan kabarbari da addu'o'in da akeyi sannan suka soma nasu personal.

Ta kammala nata addu'o'in amma tsaiwarsa da irin nutsuwa da take hanga a tattare dashi ya zama wani abu daban.......dukka tsarinta na hanawa kanta satar kallonsa a wannan lokacin ya wargaje. Wani irin kushu'i take hanga da zallar qanqan dakai gaban ubangiji,yanayin daya qara mata qaimi,takejin kamar akwai tarin addu'o'in daya kamata tayi batayisu ba.....kaman tana da sauran buqatu daya kamata ta roqa,kawai sai taji zuciyarta tana narkewa sosai a gurin.

Sake maimaita addu'o'inta take,sai taji wasu suna shiga cikin kanta suna kutsowa ta bakinta. Aisa lamarin sahel duk sai taji kaman ya kamata takai lamarin gaban sarkin sarakuna. Ko meye ya kasance da sauqi.....sahel couture nada matuqar muhimmanci a gurinta.....kamar yadda aisa keda nata tarin muhimmancin.

Da wani irin taushi ya sauke hannuwansa,maimakin ya barsu a qasa a hankali kamar jiya.....da wani sanyi taji ya kusa tafin hannunsa tsakiyar nata. Ta sauke wata irin ajiyar zuciya tana jin nutsuwa na saukar mata. Wani irin yanayi da ta kanji a duk sanda ya riqe hannunta ya fara bin jikinta,suka fara takawa suna gangarawa zuwa marwa da tarin addu'o'i da cikakken koyi da yadda ibadar take.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 30*

A yau da suke sa'ayi tsakanin safa da marwa din,wani mutum take gani na daban......wani muhammad haisam take gani ba wanda take gani ba. Wata siffa tasa....other side nashi da bataga komai ba a baya sai yanzu. Batasan adadin sau nawa ta saci kallonsa ba,a sanda ta lura zuciyarsa tayi wani irin zurfi da nisa gurin ibada. Hatta da kamanninsa a yau sai take ganin na dabanne. Bai bata qafarsa ta taka kama jiya ba......amma yau dinma hannuwasa suna zagaye da kafadunta dako ta ina. Ko sau daya bai bari wani d'a namiji ya gogi kafadarta ba.....ko sau daya bai bari ta shiga inda za'a matseta ba.

Wani double peace takeji.....wata irin nutsuwa.....wani kusanci......kusancin daya sanyata ta bishi da kallo a sanda sukazo daidai green light,inda maza ya wajaba suyi tafiya da sassarfa. Ya soma zame hannunsa cikin nata......ya soma takawa da sassarfa da wani irin energy kamar jarumin da zai shiga fagen yaqi tsakiyar abokan adawa.

Mazane daruruwa ke tafiya cikin sassarfa a gurin,amma sai nata idanun suka tsinceshi shi kadai a cikinsu. Ya qetare maza da yawa,amma duk wanda ya gifta sai taga banbanci me yawa tsakaninsa dashi. Tsaho cikar jiki da murjewa dama yanayin kuzari. A duk sanda ya wuce da sassarfa kafin su sake hadewa sai taji wani irin loneliness ya sauka a hankali ya lullubeta. A duk sanda ya zame hannunsa daga nata sai taji kamar ta koma wani empty.....kamar ita daya tayi saura a duniya.

"Subhanallah" Ta fada tana sauke idanunta qasa a hankali tana qoqarin maida kanta ga ibada.

Wata irin ibada tayi da iyakacin imaninta bata taba irinta ba duk zuwanta gurin. Daren ranar gaba dayansa cikin harami suka qarar dashi,ya mata tayin tafiya masauki amma sam sai taji tafi qaunar zama a nan din.

Har kashi uku yana cewa ta tafi,amma bata tafin ba sai bayan an idar da sallar asuba,bacci ya soma fusgarta da gasken gaske sannan ta wuce zuwa masaukin ba tare data nema inda yake ba.

Doguwar rigar bacci kawai ta sauya ta zube saman gadonta,bata dauki dogon lokaci ba kuwa bacci yayi awon gaba da ita.

Baccin da knocking din da taji ana mata shine ya tasheta. Da qyar ta bude idanunta tana jin kanta ya mata nauyi. Ta buda bakinta don tambayar waye ma taji ba zata iya ba,don tana kyautata zaton birra ce,don haka kanta tsaye kawai ba tare da tunanin komai ba ta sauka qasa sa hargitsatsen gashinta da rigar baccin data lafe mata a jikinta da ko brazier babu ta doshi qofar.

A kasalance ta bude qofar tana murza idanunta tana shirin fara yiwa birra qorafi.

Narkakkun idanuwansa ya zube saman fuskarta a farko....fuskar da tayi wani yanayi daya qara mata kyau saboda qananun gashin gaban goshinta zuwa kunnuwanta da suka kwanta sosai suka qawata baby face dinta. Uwa uba kuma gashin kanta daya hargitse yana rufe wani sashe na fuskarta wanda taketa qoqarin janyeshi kada ya shigar mata baki,bakin da taketa qoqarin son budeshi tayi masifar daya lura ta iya ta musamman akan birra idan ta mata ba daidai ba.

Ba tare daya shirya ba.....cikin wani irin yanayi idanunsa suka zarce a hankali suna sauka saman qirjinta. Kallon daya zama guda daya tak amma me wani irin qarfin da yaji kamar an saka wani abu me matuqar qarfin magnet an zuqi kowanne jini dake zagaye da jijiyoyinsa.....kamar an mannashi da wata na'ura dake bada sinadarin shocking dake iya girgiza kowacce gaba ta jikin dan adam. Suna tsaye kyam tamkar an haliccesu ne saboda su tsaya a gabansa a wannan rana. Sun bayyana kansu tun daga shape dinsu da yadda suka tsaya cas a qirjinta kaman an daidaitasu. Komai na siffa da kamanninsu sun fito.....abinda kawai ya zama hijabi a tsakaninsa dasu shine yaloluwar rigar baccin data manne jikin fatarsu.

Sai da ta samu nasarar maida gashin nata kafadar hagunta yabi dogo fari tas din wuyanta sannan ta daga idanunta taga kuma waye tsaye a gabanta. Wata iri mahaukaciyar razana tayi,taja baya da sauri da siraran qafafunta dake rawa,ta saka hannu da nufin maida murfin qofar ta rufe.

Saidai kuma hannu daya kawai ya saka ya tokare qofar ta gaza rufeta. Da hannu daya ya dakatar da motsin qofar,sannan a wahalce cikin wani yanayi me wahala ya daga wayarsa yana miqa mata,yana kallon qwayar idanunta da idanunsa da suka canza kala cikin qasa da minti daya,don bazai kuma gangancin kallon qirjinta ba duk da ta saka hannayenta dukka biyun ta cukuikuye gaban rigar.

"Magana akeson yi dake" Ya fada muryarsa tana harhadewa. Hannu daya ta saka ta karbi wayar kamar walqiya sannan ta koma bayan qofar tana qoqqarin turata. Ta turata din kuwa ta rufeta bam alamun yabar bakin qofar kenan.

Ta jima tana maida numfashi,hannayenta dukka suna kakkarwa kamar wadda aka yiwa wanka da ruwan qanqara cikin tsakanin hunturun sanyi.

Wani dogon numfashi ta aikewa hunhunta sannan ta fesar a waje,abinda ya dawo mata da wani sashe kadan na nutsuwarta.

Wanne tsautsayi ne ya kaita rayawa birra ce tayi mata knocking?,wanne tsautsayi ne ya kaita buda qofa a haka?,abinda sam ba halinta bane?.

Tunaninta ya katse sanda wayar ta dauki wani daddadan sauti,ta maida dubanta kan wayar da bata gane wacce irin waya bace ballantana kamfanin data fito. Abu daya ta iya ganewa inda zata daga kiran,saita daga din kai tsaye saidai da dan mamaki tattare da ita ganin sunan maleek ne akai.

"Tantiii...." Taji muryar falaak can qasa kamar sautinta baya fita. Gaban akhnan yadam fadi,saboda yanayi ne da bata taba jinsa tattare da falaak ba.

"Tanti......don Allah kizo......mutuwa zanyi wallahi.....maleek ya kasheni". Sai kuka ya ballewa falaak din.

Dukkanin ilahirin jikin akhnan ne ya dauki rawa,wani irin tashin hankali ya rufto mata.

"Falaak" Ta kira sunanta da wani irin tsoro da kuma nauyi a muryarta.

"Kisa falaak?.....kina ina?".

"Haisam zai kawoki" Taji muryar maleek a raunane maimakon ta falaak da suke magana. Abinda ya sake rudata kenan,duk jikinta ya sake daukan rawa,batasan sanda ta bude qofar da hannunta ba cikin sassarfa ta nufi dakin haisam din ba tare data tuna yanayin rigar dake jikinta ba,tana jin zuciyarta kamar zata ballo qirjinta ta fado,tsoro da tashin hankali suna mamayeta.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Bai taba jin yanayi irin na yau ba tunda yake a rayuwarsa dangane da mace. Bai taba tsintar kansa a mawuyacin yanayin da yakeji a yanzu cikin jikinsa ba game da d'iya mace.

Ya sani basai an gaya masa ba,tun daga farkon balagarsa ya fahimci irin nau'in halittarsa,tun daga sanda ya fara fama da wani matsanancin ciwon ciki daya danganashi da asibiti. Bai fahimci bayanan da aka yiwa nanay ba,amma tun sannan yake samun wani irin kulawa daga wajen nanay. Ja a jiki,yawan gaya masa yaji tsoron Allah,yadda zai kare mutuncinsa dana mahaifansa. Sannu a hankali ya fahimci nanay ta sanshi.....ta sanshi sani irin na kar da kar.....ta sanshi irin sanin da uwar da tasan kanta ne kawai takewa yaronta.

Readers Also Read

More by Huguma