L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 18
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 18: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 18. Sosai ya fahimci abinda haisam ke magana…
3,367 words
Sosai ya fahimci abinda haisam ke magana akai,kishi.....kishi ne da bazai barshi ya shiga ciki ba,shima kuma bai yarda ya koma ba duk da matarsa tana ciki. Dole kuma yana buqatar wani,wanin da zai lallasar masa falaak din ya kuma bata taimako bayan wanda yayi iya yinsa.
Matsawa akhnan hanya maleek yayi yana fitowa,saidai bai yarda sun hada idanu ba,sai wani gaisuwar babbar yaya da yake mata.
"Barka da warhaka tanti.....ina fata kina lafiya" Ita bata ma fahimci wannan abun nasa ba,hankalinta dari bisa dari yana kan falaak,bata taba zaton ta damu da ita ba sai yau,yau din da taji batun kisa. Mamaki kuma ya kamata ganin maleek ya fito gabansu,ba alamun jini ko wani abu na kisa a tattare dashi,kawai tunda taji alamar haisam ya sake mata hannu saita zame da sauri ta wuce ciki.
"Fito munafuki" Haisam ya sake maimaitawa yana zubewa maleek idanu. Murmushi kawai maleek ya saki suna takawa zuwa lobby din dake daura da gurin,wanda aka qawatashi da kujerun zama daidai da yadda masu zama a gurin zasuji dadin zamansu.
Kai kawai maleek ke girgizawa,ya gaza amsawa haisam kalman munafukin daya kirashi.
"Kayyasa......wallahi mun dade a matsayin buhunhuna kuma bahuna......ashe naseeb ya fimu wayo?,me yasa duka shekarun nan muke zaune bamuyi aure ba?" Shuru kawai haisam yayi,da wannan kalar cikakkiyar nutsuwar tasa yake kallon maleek. Yanason gano abinda yaji ba'a kalamansa ba,a yanayinsa da yadda maganan ke fita daga can qasan zuciyarsa. Bazai qaryatashi ba,idan ya gwada da abinda ya faru dazu dashi baisan me ya sanya maleek wannan sambatun ba. Bayason jin komai,kamar yadda yasan maleek din shima ba fada zai ba,amma sambatun da yake masa yayi yawa,yana tsoron kuma amanar sultane a hannunsu,kada yaci gaba da tafi da falaak din a haka,shi yasan illar da irin hakan yake haifarwa a matakin farko tsakanin ma'aurata.
"Wanne irin rashin imani ka gwadawa d'iyar mutane?,kanason taci gaba da gudunka?" Sakin baki maleek yayi ya zubawa haisam ido.
"Captain......anya kuwa kaje inda naje?" Tambayar ta dan zowa haisam da nauyi,sai kawai ya lumshe idonsa ya budesu duka akan maleek,don ya sani,idan bai sauke masa nauyi me yawa ba daga cikin idanunsa ba yanzun sai ya sauka daga kan layi ko shi ya saukeshi.
"Ba wannan na tambayeka ko nace ka tambayeni ba.....ba huruminka bane" Idanun sunma maleek nauyi yadda aka saba,ya dauke kansa zuwa gefe saboda a yau dai yana jin bazai fasa yiwa haisam tsiya ba ko bata da yawa
"Allah ya sani ni bada niyya bane,bansan ma yadda akayi komai yazo a haka ba.....amma dai yadda kamin tambayar nan ne captain sai ake gayamin bakaje ko ina ba shi yasa ka tuhumeni,inda ka bude littafin kayi karatunsa da kyau Allah ba zaka tuhumeni ba,saboda kaima......" Saukar wani irin duka a gadon bayansa ya dakatar da jawabinsa,koda ya waiwayo sai yaga haisam ne,kuma sake mulmule hannunsa yakeyi,ba shiri ya matsa zuwa mazaunin gaba
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Fisabilillahi ina kan sharafina zaka tsugunnar dani....."
"Gwara ka tsugunna din ai......kaga sai kuyi jinyar,tare mara imani" Dariya maleek ya fashe sosai dashi
"Um....um fa captain.....kada lokaci yayi muzo muna wasan 'yar buya fa?".
"Wasan 'yar bacewa zamuyi" Ya fada yana danna masa harara,dole maleek ya sake sakin dariya sosai yana duban haisam.
Qafafunta har rawa suke sanda ta isa bakin gadon dake a yamutse kamar na 'yan dambe.
"Falaak" Ta kira sunanta muryarta tana rawa ta kuma haura gadon da sauri tana rarumar falaak din.
Rungumeta tayi sosai a jikinta,ita kuma falaak din ta saki kuka sosai tana riqe akhnan din itama.
"Me yayi miki falaak.....me yayi miki?" Tambayar kawai da akhnan din ke iya maimaitawa kenan a rude tana sake riqe falaak sosai cikin jikinta. Idanunta akan fuskarta da taga ta wani rame lokaci daya ta fada sosai.
"Ba komai" Amsar da falaak ta iya bata kenan. Batasan yadda zata mata bayani ba,batasan me zatace mata ba,saida tazo sannan takejin wata kunyarta tana danneta,damuwa da rudewar kuma data gani tattare da akhnan din saita qara mata qaunarta sosai.
Tambayar duniya amma amsar falaak itace ba komai,dole akhnan ta saketa a hankali tana fadin.
"Na baki ruwa?,bakinki kaman ya bushe....jikinki da zazzabi sosai".
"Wanka nakeso na sakeyi,ruwan dumi nakeso sosai" Kai akhnan ta daga mata jikinta har yanzu rawa yake,don bata gamsu da abinda falaak ta fadinba,bata taba ganinta cikin wannan yanayin ba duk da ba wata doguwar alaqa bace a tsakaninsu.
Hannunta ta dauke da dan sauri jin ta dorashi saman wani danshi danshi..
"Jini?!" Ta fada a rude tana duban falaak,saita sake maida idanunta akan bedsheet din. Nan gurinne kawai keda jinin,amma akwai wasu gurare da ya danyi staining kadan kadan.
"Falaak......ki fadamin ne yayi miki....jini fa nake gani,ki fadamin ko na kira sultane yanzun nan"
"Ba komai.....ba komai tanti" Falaak ta fadi idanunta suna rau rau da hawaye. Ido ta zubawa falaak ranta yana baci,da alama yarinyar soyayya ta rufe mata idanu ne har bata ganin laifinsa,ita kuwa ba zata bari ba.....ba zata bari kowa a cikin su ya cutar dasu ba don suna ganin ba qasarsu suke ba,kawai saita sauka daga saman gadon da hanzarinta,don ta tuna wayar haisam din ya zameta a hannunta sanda zasu shiga elevator.
A nutse ya daga idonsa daga kan waya ya maida kanta sanda take fitowa daga dakin,ya zuba mata idanu ganin tana waige waige. Miqewa yayi tsam,don shi kadai ne a gurin,maleek ya sauka can first reception zaya karbi saqo.
"Wayata zaka bani" Ta fada tana miqa masa hannunta. Hannun yabi da kallo,gefan hannun rigar tata ya danyi stain na jini kadan. A nutse ya sauke kallonsa cikin qwayar idanunta. Yana karantar wani fushi da zafi sosai cikin idanunta
"Kiyi me da ita?" Ya tambaya calmly.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 33*
"Na kira sultane.....na fada masa jini har a kwancinta amma taqi gayamin abinda yayi mata....bayan dazun zai kasheta tacemin" Tayi maganan tana sauke numfashi da alamun fushi sosai a fuska da muryarta.
Wani irin kyau tayi masa.....wani irin kyau daya sanyashi lumshe idonsa sannan ya budesu dukka akan fuskarta. Bai taba ganin fushinta na gasken gaske ba sai yau.....wani irin kyau fuskar tayi yadda ta tsuketa.
"Ba zata gaya miki ba.....kema ba zaki kira sultane ba....kije ki taimaka mata kawai ya isa".
"Jini fa a jikinta?,sannan kace kada na kirashi?" Ta qarashe fada tana kallon yadda yake takowa inda take yana rage tazarar dake tsakaninsu. Bata matsa baya ba,saboda ranta a bace yake da gaske,wannan ya basu daman tsaiwa sosai gab da junan da cikakken motsi dayansu yayi yana iya cike gap din.
"Sun cika aurensu ne.....zaki fallasa sirrin first night din wasu ne?" Dummm taji kanta yayi mata,hannunta dake pointing wani guri ya tsaya cak ya qame a gurin. Wani irin yanayi me nauyin gaske ya saukar mata,shin me yasa ma ta tsaya bata ja baya ba sanda yazo dab da ita,gashi yanzu ya fada mata wasu kalmomi da nauyinsu ya sanya takejin kamar ba zata iya daga qafanta ba.
"Uhmmm.....tell me....me zakice da sultane din idan kin kirashi,I’ll help you call him." Ya fada yana latsa wayarsa kamar me nema mata number sultane din.
Kaf energy dinta aka kwashe,idea dinta kuma ta bace. Shi baida kunya fisabilillahi?,meye na gaya mata haka kai tsaye?,saita samu kanta da kallonsa kawai bakinta ya gaza cewa komai.
Sanda ya dago idanunsa sai suka hadu da nata,ya dage giransa dukka biyun.
"You keep staring......uhmmm tell me me zaki gaya masa?" Idanunta ta sauke da wani irin sanyi,sai tayi taku uku baya cikin dabara,sannan ta juya da wani zafin nama tana arcewa cikin dakin.
Da kallo yabi bayanta,yadda take saurin kawai zai gaya maka akwai abinda ya tilastata,akwai abinda kuma take gujewa,amma sam saurin baiyi matching character dinta ba.
Baisan ya akayi murmushi ya subuce masa ba,ya ciji gefan lips dinsa na qasa,ya koma da baya a hankali ya zauna bayan ya ajiye wayar a gefansa.
Ta dade tsaye tana kallon falaak sannan ta tattaka tana mata sannu. Tsoro sosai ya dinga mamayarta sanda taga falaak din na takawa da dabara zuwa toilet. Abinda bata taba ba,yau itace da yaye bedsheet da kanta,bedsheet din data ji qwalla da tsoro sun kamata da taga ragowar jinin da yayi staining a jiki.
"Maza basu da imani" Ta samu kanta da fadi itakam ta yaya ma zata bari akai wannan abun bare har ayi mata irin wannan aika aikar?.
"Kina da tabbaci?" Zuciyarta tayi mata tambayar data kusa tsayar da bugun numfashinta saboda tsoro.
Ita ta taimaka mata da iya abinda zata iya ta gasa jikinta,saidai ko gurin gyara gurin falaak din ta lallaba tayi. Koda akhnan batayi mata komai ba zuwanta ya bata relief sosai. Kallon falaak kawai take jikinta a sanyaye tsoro yana kamata,to amma sai take samun sassauci idan ta tuna ba wani soyayya bane a tsakaninsu da zai kaisu ga wannan,uwa uba ma daki daban daban suke kwana,ba kaman falaak ba data lura suna sharing daki daya ne.
"Ke kinsan haka yake,me ya kaikai sharing daki dashi?" Tambayar ta bawa falaak mamaki da dariya can qasan ranta,da gaske akhnan batasan haka abun hake yake ba?,inde haka ne kuwa akwai qura,sai ta yanke tayi mata gwari gwari kawai.
"Haka abun yake tanti....haka kowacce mace takeyi"
"Take uban me falaak?,kinsan me kike fada kuwa?" Ta fadi har batasan tayi spark ba saboda wani tsoro da falaak din ta qara mata. Qasa tayi da kanta dariya nason qwace mata amma tana dannewa. Da gaske koda akhnan tasan da wannan abun amma sam bata taba kawoshi a lissafinta ba sam a cikin aure.
"Da gaske nake....ki kira tanti hairaaan kiji"
"Akanme?.....ni bazai faru dani ba bare na nemi sani,kema Allah ya baki lafiya ke kika jama kanki" Ta fada tana yamutsa fuska. A yadda taga falaak din a yamutse saboda abu qwaya daya tak ita saita bari ya faru da ita?.
"Duk fa wayon amarya sai ansha man ta.....kin manta?"
"Falaak.....ki kama kanki" Ta fada tana tsumewa
"Inacan tausayinki kamar zai hallakani,amma ke alfahari ma kike da abun?". Ta fada a qufule
"Dole nayi alfahari mana....nakai mutuncina gidan mijina,mijina na sunnah ne ya karbu budurcina abun alfahari ne yaa biftu,ina fata kema ya faru a kanki zakifi fahimta" Ta fada a ranta amma a fili sai tayi qasa da kanta tana cewa.
"Kiyi haquri na daina"
Knocking akayi aka turo ana shigowa,maleek ne,sai a sannan akhnan taga basarwar da yaketayi,sai yanzu ta fahimta
"Mugu" Ta fada qasan ranta tana jin haushinsa yana saukar mata. Wayarta ya ajiye mata a gefe yana cewa.
"Captain yace ki duba akwai saqo".
"Captain?" Ta maimaita tana daukan wayar,don sunan baqo ne a kunnuwanta,bata ma kuma gane wanene ba.
Procedures ne na yadda falaak zata samu relief a rubuce cikin wayar ya rubuta ya ajiye a notebook dinta. Kunya taji ta kamata sosai gauraye da haushi,har shima wai yasan meye ya faru ne?,kawa saita dan kai idanunta kansu maleek.
Yadda ya gwaggwafe gaban falaak din riqe da yatsunta yana murzawa,har ita dake gurin bata iyajin abinda yake gaya mata ya aza mata nauyi da yawa,kawai sai taji ba zata iya zama ba,ta miqe tsam,daidai sanda yake fadin.
"Tanti....ki zauna fita zanyi"
"No" Tace a taqaice kawai tana takawa gami da ficewa a dakin.
*_A G A D E Z_*
*_SULTANE PALACE_*
Zaune take a gabansa cikin nannauyar kwalliyar na dake cike da alfahari da kuma nuna isa,kwalliyar data qara adadin nauyinta don ta boye ramar data fara yi wadda ta bayyana kadan har a qasusuwan wuyanta.
Tun daga watannin baya,ranar da gobara ta tashi a gidan. Bacewar tamim.....bacewar yalwa,gobarar villa dama dauki daidai din da akewa hadimanta,har xuwa ranar qarshe da 'yan jarida suka dirar mata bata sake baccin kirki ba.
Kaman zatayi sanyi,kaman zatayi collapse,kaman zata saddaqar amma kuma zuciyarta ta gaya mata KI TASHI ZAITUNA!.
Wani irin salo take gani tattare da yaron da dawowarsa yafi haihuwarsa zame mata barazana a rayuwarta. AHMAD yaron data kowacce fuska baka isa ga qaryata jinin sultane bane a jikinsa.
Bai rayu dasu ba....bai rayu cikin masarautar ba......amma yasan kowanne nau'in salon sarautarsu.....lungu da saqo na cikin gidan.....adadin ma'aikata dama komai dake wanzuwa a cikin gidan. Batayi mamaki ba.....kasancewar ALSAAMIT tattare dashi zai iya zama mafi girman hatsari fiye da haka.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Wani irin takawa d'ai d'ai taga kaman morsa safiyya tanayi.....wani irin girma ta fuskanci kanta yanayi......abinda ya hanata bacci darare da yawa.....saidai kuma ta samu babban makama sanda ta soma lura da rade radin da kuma gani da tayi da idanunta SULTANE bashi da wani cikakken qwari da lafiya.
Murmushi tayi sanda ta lura da wannan
"Wataqila ina da sauran dama ne.....daman da zata zamemin ta qarshe" Ta kama damar da kyau kuwa,ta fara kusanta kanta da sultane matuqar kusantawa. Abinda ya bata mamaki yadda take samun cikakken dama da access da komai,saidai cikas kadan kadan da take samu daga ahmad din.
Yaron da idan hanya ta hadasu yake mata wani irin kallo,kallon data tabbatar idan har yana da dama.....idan har zai yuwu zai iya daukan wuqa ya kaita lahira.
"Ta yaro kyau take bata qarko..... Ka daina dariya wasa yayi kyau.....wannan zaqin mulkin......wannan darajar da wannan matsayin gaba daya na 'yan kwanaki zuwa watanni ne....zaka sake bacewa bacewar da har abada ba zaka dawo ba" Haka takan fadi cikin ranta,amma a fili saita bishi da murmushi.
Kamar yanzu da take zaune gaban sultane din,tana yanka masa fruit din tana bashi yana sha,tana kuma jansa da hira a nutse.
Tun daga nesa ta hangesu,morsa safiyya ce cikin wata irin shigar kamala dake bayyanar da darajarta da wani irin Kwarjini. Ahmad yana biye da ita a baya da wani kalan girmamawa tamkar yana fadawa duniya ITADIN MAKWAFIN MAHAIFIYATA CE.
Ta zuba musu idanu da gaske,har cikin tsakiyar zuciyarta tana jin wani irin zugi a duk sanda ta gansu a haka. Dawowarsa ta sake qarawa morsa safiyya wani irin girma da martaba da bata zata ba,saboda kowa kiranta yake UWAR YARIMA ME JIRAN GADO.
Duk kuwa da yadda taso sunan ya zamana nata ne.....ko ta hana tasirin sunan,amma ko daya a ciki bata samu nasara ba.
Akwai tarin mutane masu yawan gaske dake neman kusanci da Ahmed din,wanda kusancin yana da muhimmancin da dole kowa ya buqaci wannan gurbin a kusa dashi.
A zahiri saita saki fuskarta,tana maida dubanta ga sultane da bai lura da tahowarsu ba.
"Ga magaji nan zuwa shida mamarsa". Kansa ya daga zuwa sashen,yana duban Ahmad yana jin wani abu me girma yana motsawa cikin zuciyarsa. Baisan dame zai yiwa haisam sakayya ba....duk da har yanzu baisan yadda komai ya kasa ce ba har yanzu.
Murmushi kawai yake saki har suka iso,murmushin da mammina take jinsa kamar tsiruwar allura saman naman zuciyarta.
"Barka da hutawa" Morsa safiyya ta fada tana cire takalmanta a girmame tana qarasowa gabansa.
"Bakanki uwar yarima" Murmushi ya subuce mata tayi qas da kanta,yanayin da ya masa kama sosai da safeena.
"Da kanka me martaba?"
"Sunan ya dace da wadda aka bawa ai......ga maman gimbiya....ke kuma ta yarima ce" Ya fada yana nuna mammina data qaqalo murmushin dole. Idanu morsa safiyya ta daga ta kalli mammina,cikin sa'a ita ita take kalla,sai kawai safiyyan ta ajewa mamminan murmushi tana dauke kanta. A yanzun bataga komai tattare da mammina ba sai wata kwantacciyar damuwa,damuwar da duk dare saita tsaya saman abun sallah ta kaiwa Allah sunanta. Allah ya hanawa rayuwarta sukuni muddin da haqqin safeena saman wuyanta.
"Zamankin nan a gabana.....sai naga kaman safeena ce" Ya fada zuciyarsa tana masa nauyi.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 34*
"Allah ya tsinewa safeena da kabarinta dama dukkan abinda ya fito ta tsatsonta dama ahalinta gaba daya" Mammina ta fada har bakinta yana motsawa,wani abu me masifar nauyi takeji yana sauka saman zuciyarta. Ta tsanu safeena tsana mafi girma,tsanar da ko a lahira batajin zata daina mata wato bayan an mutu an gama kwanciyar kabari an tashi,dukkansu basu kai su goge wannan tsanar ba.
Ba wani dan adam a duniya daya taba kawo ma komai nata cikas sai ita.....ba wani wanda ta taba saka plan a gabanta ya zama silar wargajewarsa bayan baqar wahala datasha akai irinta. Daga ita sai IBRAHEEM,sauqinta daya.....IBRAHEEM har yanzu yana cin darajar taba sonshi da zuciyarta tayi,amma duk da haka shima saida ta barwa rayuwarsa tabo ta hanyar daukar rayuwa d'a na farki daya soma haifa a rayuwarsa.
Taimakonta daya sautin maganan da tayi baikai ga fita ba,saidai ahmad da idanunsa suke kanta ya tabbatar akwai wani abu data fada. Murmushi morsa ta sake.
"Allah yayi mata rahama"
"Ameen amee" Ahmad da sultane suka hada baki gurin amsawa.
"Ya qarfin jikin?" Ta sake tambayarsa
"Mun godewa Allah dai" Yadda yayi maganan sai morsa safiyya taji zuciyarta ta tsinke. Yanayin yadda safeena ke gaya mata kenan a kullum rana har ranar data bar duniya.
"Allah ya baka lafiya madawwamiya kai da sauran marasa lafiya"
"Ameen" Dukkansu suka amsa harda mammina a wannan karon wadda zuwansu gurin ya sanya taji kaman ta zama bare,kaman an wareta.
"Yarimanmu" Mammina ta fada tana murmushi. A nutse ahmad din ya juya yana dubanta,ya aje mata wani kallo da yanayin izzar data taba mammina din sosai.
"Wai duka yaushe ya iya wadannan abubuwan gaba daya?" Ta tambayi kanta da kanta.
"Idan kina fada,kaman kina qarawa zuciyarki nauyi ne,inda kin haqura da furtawar kiji da abu daya". Ya fada da yaren oromo daya tabbatar ba wanda zaiji abinda yace,don ko morsa safiyya ya fahimci ba yaren kowanne bangaren takeji ba,tsahon barinta qasar kuma yasa ta manta wasu abubuwa da yawa.
Murmushi kawai ta maida masa kaman yadda ta saba,har yau ko kalma daya bata taba furta masa ba,amma kuma shi ya sani,hakan ba yana nufin komai lafiya ba.
Gaban sultane ya qarasa cikin girmamawa ya tsugunna.
"Muna da baqi ranka ya dade cikin gidannan"
"Baqi?,wadanne iri?" Sultane ya fadi,don yadda yakejin jikinsa a yanzun bacci kawai yake da buqata.
"Eh baqi.....amma kamar ba gurinka kai tsaye sukazo ba.....daga babbar hukuma,alhaji nasiruddeen bahago" Jin sunan kawai ya sanya sultane tashi ya zauna sosai.
"Ba baqi bane ahmad....akwai sanayya me girma,duk sanda kuma kaga sunxo babban dalili ne ya kawosu,a shigo dasu" Ya fada yana duban Ahmad din. Kai ya jinjina a nutse,ya miqe wani sirrintaccen murmushi yana fita daga fuskarsa......ya taka a hankali xuwa qofa don bawa me wada umarni.
Tunda suka shigo gurin idanun mammina yake kansu. Haka kawai takejin akwai wani baqon al'amari a tattare dasu. Yadda suke dan kallonta daya bayan daya lokaci taji bata nutsu dasu ba. Bata duba yadda morsa safiyya ta kame daga gefe ba,suka gaisa cike da kima da dattako,suka kuma duba jikin sultane sannan suka mata barka da dawowar Ahmad ba tace.
"Kaman buqatar kwanciya sultane yake....don Allah idan ba matsala,ko zaku iya gama komai da wuri ya samu ya huta" Ta fada tana miqewa.
"Zaki zauna ne ai hajja zaituna,zuwan naki ne" Alhaji nasiruddeen ya fada a girmame.
Cak ta dakata tana dubansa,saidai kafin tace komai ya maida dubansa ga sultane.
"Allah ya baki yawan rai,ayimin afuwa nayi magana da iyali kai tsaye ba tare dana nema izini ba" Murmushi kadan sultane yayi,ba jiya ba yau ba,shekaru masu dama ne suka bada sanayyarsa da sabonsa da Alhaji nasiruddeen da kuma yanayin aikinsu.
"Ba komai......zaituna....zauna" Ya fadi yana dubanta.