L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 19
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 19: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 19. Murmushinnan ta qaqalo,sannan ta koma tana zama din,a…
3,342 words
Murmushinnan ta qaqalo,sannan ta koma tana zama din,a qasan ranta tana fatan wani abu ne ya taso wanda zai kuma daga darajarta.
"A daren shekaran jiya hukumarmu ta kama wasu mutane......wanda nasan labarin ya iso gareka?" Kai sultane ya gyada a nutse.
"Ma sha Allah.....munyi magana dasu,mu tuhumesu,mun kuma matsi bayanai muhimmai daga gurinsu,saidai ba yadda muka iya.....duk yadda mukaso mu kauce sunan iyalinka ya fito a ciki". Magana tasa ta qare da wani irin shuru......sannan kuma ta jona wani burkitaccen yanayi a zuciyar mammina da kwanyarta.
"Iyali waye a ciki kenan?" Tayi tambayar da sultane ya buda baki da zummar yi.
"Hajja zaituna,giwa". Ba wanda wuta bata daukewa a gurin ba,banda Ahmad da yake zaune abinsa yana gyarawa sultane rigar jikinsa.
" Ayi mana afuwa" Alhaji nasiruddeen ya fada yana sadda kansa qasa.
Shuru sultane ya sakeyi,mamaki kuma yana dan cikashi. Me ya hada iyalinsa dasu?,me ya hada zaituna kuma da Office Central de Répression du Trafic Illicite des Stupéfiants(hukumar hana fataucin miyagun qwayoyi).
Ajiyar zuciya ya sauke,yana maida idanunsa kan mammina.
"Kina da abinda zaki ce?". Kai ta juya kadan,tana qoqarin danne komai da komai da takeji. Ida aka ajiye komai ma.....ita giwa?....mace kamarta ace an shigo har masarauta bincike a kanta?.
" Bani da abinda zance.....kawai abinda zuciya da jikina suke gayamin shine......an shirya tozartani ne....ta yuwu an hada baki da abokan adawa don a bata sunanka dana masarautarmu gaba daya" Ta fadi tana fatan maganartata tayi tasiri a zuciyarsa.
"Ba haka bane Allah ya baki yawan rai...." Alhaji nasiruddeen ya fadi don kare zargin da takeson jifansu dashi,saidai kafin suce komai sultane ya dakatar dashi.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Duka wannan bata taso ba,basuce komai a kanki ba,hasalima basuce suna zargi ba,bincike kawai zasuyi don wankeki daga zargin da wadancan mutane suke jefa a kanki,so indai hakanne bana tunanin zai zama wata damuwa......."
"A shiga har gidana.....na aure da wasu garada....ayimin bincike har inda yake sirrina ne sannan na gaza damuwa?".
" Ba irin wannan binciken bane,amintattunmu ne guda hudu kawai " Alhaji nasiruddeen ya fadi da girmamawa.
Daga kanta tayi ta zube masa idanunta a kanshi. Taso ta ganeshi,koma tace ta ganeshi,kuma daga wannan aikin batajin zai sake gigin yin wani aiki daya shafi koda na qasanta ne ballantana ita.
"Na fahimta.....na fahimta da kyau,ba kuma laifi,kuna iyayi" Ta fada tana gyara zamanta sosai da yanayin saukar nutsuwa a zuciyarta.
"Mun gode" Shima ya fada yana rusunar da kansa.
"Zaki zabi da wanda zasu shiga cikin hadimanki?". Kai ta girgiza tana murmushi.
" Ba zabi.....suna iya shiga da duk wanda suka zaba".
"Ahmad......ka rakasu" Kiran sunan ahmad din kawai sai daya kada hantarta. Me yasa ahmad?,me yasa ba zaa saka wani ba ahmad ba?,ahmad daya rayu cikin wata rayuwa data bashi experience din da ko jami'an bata jin suna dashi?.
Da idanu ta bisu har suka kammala ficewa gaba dayansu,duk da wani sashe na zuciyarta yana cika da wani irin confidence.
Duk inda suka gilma cikin gidan sai idanu sun bisu. Baqon abune ganin ma'aikatan Office Central de Répression du Trafic Illicite des Stupéfiants tsakiyar masarautar haka suna tafiya kansu tsaye,tafiyar ma kuma bisa jagorancin yarima ahmad muhammad hammud. Ba wannan ba.......yadda suke dosar sashen mammina kai tsaye sai abun ya zama wani daban,abun kuma yaja hankulan duk wani hadimi dake kusa,wanda ke nesa ma labari ya fara tsalluwar masa.
Wasunsu suka fake da ayyukansu,wasu kuma suka nemi guraren da suke da tabbacin duk abinda ya faru zasu iya samu masaniya.
Duk da yawan securiy dake kula da kowacce qofa da zaka sanya qafarta ta sassan mammina,amma babu ta inda suka samu tuhuma tambaya ko kuma tsaiko saboda yarima ahmad dake tare dasu.
Alhaji nasiruddeen ya gyada kansa a hankali.
"Me yasa girma yawan adadin masu tsaro na sashen nan ya ninka na ko ina?" Yayi tambayar yana duban fuskar ahmad. Kafadarsa ya daga kadan
"Bazan ce ga dalili ba,don kusan nima har yanzu baqo ne cikin gidan" Ya bashi amsa akan salo da tsarin da aka dorashi tun farko yayin magana da baqin fuska.
A katafaren parlor dinta suka fara aikinsu,mutum hudun nan gaba daya Ahmad na biye dasu cikin qwarewa. Suka kammala da parlor din farko,suka wuce na gaba,daki bayan daki....parlor bayan parlor har suka dangane da dakin baccinta na qarshe wanda ya zama na musamman a gurinta.
Komai sai da suka bincike,suka kuma kara masa na'aura,saidai ba wani abu daya basu haske akan abinda suke tuhuma ko kuma nema.
"Muje kawai" Alhaji nasiruddeen ya fadi cikin sarewa da rashin qwarin gwiwa.
Taku biyu Ahmad yayi yana shirin sanya qafarsa waje idanunsa suka sauka kan wata waya data shigo ta window din dakin. Tsawa yayi cak yana qare mata kallo,wani abu daya taba faruwa a rayuwarsa ta baya yana dawo masa.
"Kai!....zo nan" Ya kira tamim,wanda shi ahamd ya zaba aka hadosu dashi. daurewa kawai yakeyi......amma kowanne sashe na jikin tamim rawa yake.
"Gani"
"Wannan wayar mece?"
"Ta panel ce...."
"Panel wanne iri?"
"Na Sola"
"Meye dalilin biyo da ita ta nan?" Ahmad yayi tambayar yana zubawa tamim idanu.
"Panel na solar din gidannan dukka a jimlace suke guri daya....baya ga haka ba wata waya da wani yake iya ganinta da idanu koda ta wuta ballantana solar.......meye dalilin sakawa daki guda daya wayar panel?" Ahmad ya qarashe tambayar yana duban Alhaji nasiruddeen wanda kiran da Ahmad ya yiwa tamim ya jawo hankulansu suka dawo dukkansu.
"Ku duba waccar wayar" Ahmad din ya fada yana ratsewa ya wucesu su da tamim din,saboda ganin wayar ya tuna masa wata rayuwa da yayi a baya,hawaye ne cikin idanunsa kuma bayaso kowa ya gani. Yana kan koyarwar haisam koda yaushe.
"Namiji duk inda yake jarumi ne,jarumtarka tana ninkuwa sama data saura a sanda aka haifeka shugaba....kuma a gidan sarauta....ko sau daya hawaye bai kamata ya fita a idanun NAMIJIN DUNIYA BA,idan ma ya kama zasu fita din ba'a kan idanun kowa ba". Wannan maganar ya riqe,kuma ta dasa jarumta da yawa cikin ransa.
*_Tabdijan.......rugiji gabji.....AIKE NE DAGA ME GAYYA ME AIKI ko kuma ARASHI NE?.....SHIN ME SUKE NEMA?,zasuci nasara su kama abun harinsu?,ko GIWA zatayi nata aikin na tabbatar da faduwarsu?_*
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 35*
Idan ya tuna a baya shi din tantirin dan shaye shaye ne.....idan ya tuna a baya yadda ya rayu cikin maye,buguwa da shan kowanne irin nau'in kayan maye sai yaji kaman ya dawo da baya ya goge komai. Denawarsa wani abune da ko iya shi kadai haisam yayi masa bazai manta dashi ba. Wani irin dainawa ta farat daya cikin taimakon wasu addu'o'i daya bashi da wanda yake masa da wanda yake bashi yasha. Cikin sauqi komai ya dinga zarewa daga ransa bayan uban amai da yayi kwanaki uku yana yinsu a jere. Wannan shine ya bashi experience na iya gane gurin da ake ajiyar kayan maye da qwayoyo,yake iya kuma sansanosu. Ya sauke ajiyar zuciya yana furta
"Alhamdulillah"
(Dama ita rayuwa haka take,duk wanda ya shuka tsiya wallahi wallahi wallahi sai ya girba,ruwanka ka shuka alkhairi ruwanka ka shuka sharri,ta cutar da rayuwarsa da plan din ta ruguzashi......gashi a qarshe shine ya zama silar tonuwar wani birnannen sirrinta da ba wanda ya sani,tayi jifa ya dawo mata).
Hand glove Alhaji nasiruddeen ya bawa daya daga cikin yaran bayan dukansu suma sun sakashi a hannunsu. Wata siriryar wuqa yaran ya bude,suka isa gaban igiyar dukkaninsu.
Daga qasa suka fara farketa suna fedeta,saidai basuga komai ba. Suna dab da isa rabin wayar wasu fararen abubuwa suka fara bayyana.
"Ci gaba da tsinkesu" Alhaji nasiruddeen ya fada.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Kawai yake maimaitawa. Ba ita ba,darajar sultane yake kallo. Da wanne idanu mutanensa zasu kalli gidan da masarautar gaba daya?. Giwa.....matar sarki guda?.
*S U L T A N E*
Wani irin shuru ne ya ratsa gurin tun bayan fitarsu Alhaji nasiruddeen zuwa ga binciken,shurun da morsa safiyya taji ita ba zata iya ba,ta sauko gaban sultane sosai ta zauna tana sake masa murmushi.
"Ranka ya dade......munyi waya da amarya jiya fa" Kansa ya daga yana jin kalamanta suna sauke masa wani abu.
"Amarya?,wacce a ciki?" Murmushi itama ta maida masa.
"Yata......'yata akhnan mana"
"Sonkai safiyya?" Yadda yayi maganan ya sanyata sakin murmushi.
"Falaak dai nabar muku,amma akhnan har abada tawa ce.....kuma tamu ce" Tayi maganan da manufa biyu.
Manufar kuwa takai,ta isa inda takeal taje. Daga kai tayi tana duban morsa safiyya,duk da yanayin jira da dako irga mintunan da suke shudewa da takeyi amma hankalinta yana kai. Har akhnan tayi kira?,tayi waya amma ita bata kirata ba?,bata nemeta ba?.
Anya batasan waye almaz a gurinta ba kuwa?,banbance babancen suna qara yawa......sauyawar yarinyar haka da sauri yana bata tsoro. Idan har shine yake hure mata kunne.....saita sanyasu dukkaninsu sunyi dana sani. Akan ta kasa nasara a rayuwarta......gwara ta rasa rayuwarta. Bata shiryawa tsaiwa don ta fadi ba.....bata shirya kallon toxarta da idanuwan data tanadesu domin kallon nasararta ba.
Da ita dake tunanin,da sultane dake hira a hankali cikin taushi da morsa safiyya magana ta neman iso daga me wada ne ya dakatar dasu.
"Sun kammala sun dawo,suna neman izinin shigowa"
"A gaya musu su qaraso" Sultane ya fada yana gyara zamansa,morsa safiyya ma tana sake gyara lullubinta.
A jere suke shigowa,Alhaji nasiruddeen da kansa yana riqe da babbar baqar leda......babbar baqar ledar da kallo daya tak mammina tayi mata taji wani abu ya karta a mararta jini me dumi taji yana tsinke mata.
"Wannan alamace ta tashin hankali.......amma ni zaituna bana taba yarda na fadi" Ta fadawa kanta da kanta,
"Bana ja da baya,bana bada kai.....giwa ko ta fadi tafi qarfin wawa" Ta sake jaddadawa kanta tana hadiye wasu abubuwa masu tsananin tauri razani da firgici zuwa cikin cikinta.
Gaban sultane ya matsa kansa tsaye ya zubesu yana zazzage ledar. Idanu sultane yabi kayan dashi zuciyarsa tana bugawa,Alhaji nasiruddeen ya koma da baya a nutse ya zauna yana fuskantar sultane.
"Bincike ya kammala......kuma zarginmu ya tabbata......ga irin nau'in kayan da muka samu cikin dakin". Zuciyar sultane tayi wani irin nauyi,ba jiya yau ko dazu dazu yasan Alhaji nasiruddeen ba. Mutumne daya qware gurin aikinsa,cikin tarin gaskiya da amana. Uwa uba qasarsa ta niger qasace da take da tsauri akan sha'anin cin hanci da rashawa. Babu ta inda za'a shirya komai saboda cin hanci ko toxarci. To amma abin yazo mata wani iri,ta wata sigar daya kasa yarda dashi.
"Ayimin afuwa Allah ya taimakeka......inaso a bani daman yi mata wasu tambayoyi a nan....idan kuma hali yayi zamu wuce da ita zuwa office dinmu" Maganan ta zowa mammina a bazata,wanne office?,ita din zasu dauka don tuhuma?
"Na baka nasiruddeen" Sultane ya fada kansa tsaye a sanyaye. Bashi kadai ba,hatta da morsa safiyya a sanyaye take kallon komai. Tafi kowa sanin wacece zaituna kaf fadin agadez,bata tunanin akwai wani wanda zai gaya mata wacece ita......amma wannan lokacin abun ya girme mata itama.
"Ranki ya dade......wadannan qwayoyin da hodar iblis......"
"Ba nawa bane" Ta amsa kai tsaye tun kafin yakai qarshen tambayar tana qoqarin cusa nutsuwa cikin maganganunta da reaction dinta. Shuru ya ratsa bayan amsar data bayar. Shurun ya zarce na wasu sakanni,sannan ya sake magana.
"Amma an samesu cikin dakinki".
"Eh ba nawa bane" Ta sake maimaita amsa daya dai. Dole akwai wani yanayi na aiki,da muddin ya biyo ko ta kan waye a danne sanayya,banda ita dince.....ba wanda za'a kama red handed da wadannan kayan a tsaya masa tambaya cikin gida.
"Bedroom dinki......dakin kwananki,waye yake amfani dashi?" Yayi tambayar yanayinsa yana nuna mode na aiki ya shigeshi. Idany ta zuba masa itama sosai,tamkar tana gargadarsa,tamkar tana gaya masa cewa.
"Kabi a hankali.....ina da hadari sosai".
"Nice" Ta amsa kai tsaye.
"To me yasa suke cikin dakin?" Ya maimaita. Shuru ya ratsa na sakanni,sannan ta amsa
"Ta iya yuwuwa wani ya saka saboda ya batamin suna kamar dai haka"
"Wani?.....kamar wa kenan?" Ya sake tambaya yana dubanta ta tsakiyar idanunta. Duk amsar data kamo sai taji ta subuce,akwai sunaye da yawa da takeso ta furta amma sai koda qwaya daya yaqi fita a bakinta,wannan ya sake bada shuru me nauyi,har sai daya sake magana.
"Sun kasance cikin wani irin boyo na sirri,da dukkan alamu dake nuna ba'a son kowa yasan dasu,da dukka wata kalar dabara dame laifi yake iya boye kayan laifinsa...."
"Kana zargina kenan yanzu?" Ta fada fushi yana nunawa saman fuskarta. Idanu ya zuba mata,yana karantar muddin akaci gaba a nan,muddin yaci gaba da biye mata zata nannade tabarmar kunya da hauka ne,kuma ya tuna,wannan umarnin da aka ruba masa shi da manyan baqi BA'A GABAN SULTANE KOMAI ZAI KASANCE BA. sai ya tausa muryarsa
"Ba tuhumarki nake ba.....tambaya ce kawai". Kalmar tasa ta qarshe ta danneta,shurun da yayi mata nauyi da yawa ya biyo baya,kamar an daure harshenta,kamar an daure kowacce kalma daga bakinta,tana jin sanda ya juya ga sultane.
" Ayimin aikin gafara ranka ya dade,a bani dama mu wuce da giwa zuwa hukuma mu qarasa bincikenmu a can,idan komai ya daidaita zamu dawo da ita har gida in sha Allah". Tayi zaton zataji muryar sultane yana fadin bai yarda ba,ta dauka zaice sam sam,amma ga tarin mamakinta sai taji muryarsa cikin rauni yana cewa.
"An baku izini".
" Muhammad?" Ta kira sunan sultane kai tsaye idanunta kafe cikin nasa. Yadda ta kirashi gatsal din ya jawo hankalin kowa da kowa a gurin hatta dashi sultane din. Zare idanunta tayi ta maida kan ma'aikatan daidai sanda sultane yake cewa Alhaji nasiruddeen su dan basu mintuna biyar. Ba musu dukka suka juya suka fice,gurin ya rage daga ita sai morsa safiyya sai sultane din,morsan da sam mammina ta manta da wanzuwarta a gurin saboda tsananin rudewar da taketa pretending tana boyeta.
"Kai da kanka ka miqa matarka inda za'a wulaqantata?,da kanka ka amince wasu jami'ai su tafi dani?". Idanunsa ya lumshe sannan ya bude lokaci guda.
" Ba tozarci ko wulaqanci bane.....haka tsarin yake,dokar ce a haka,muke gyara doka da bayar da ita.....ba zamu taba zama masu karyata ba.....idan na hana su tafi dake ashe bamu da gaskiya kenan?, a duk inda kake gaskiyarka ce take fidda ka,ita take kunceka ta dawo dakai mataki da matsayinka" Maganan ya mata kama da jirwaye me kama da wanka. Har ta bude bakinta zata sake magana sai idanunta suka sauka kan morsa safiyya,abinda ya sanyata shanye duk abinda take da niyyar fada,ta maye gurbin abinda yake kan fuskarta da murmushi
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Na yarda dakai,na amince ba zaka taba sakin hannuna ba a sanda nafi buqatarka. Ko waye ya qulla wannan abun zai warware in sha Allah.......rabuwarmu ko toxartata saidai a jira" Idanu morsa safiyya ta kawar kawai,can qasan ranta abubuwa da yawa suna kai kawo. Ta sani.....zaituna nada wani irin hatsari.....ta sani,zaituna din wata halitta ce da komai akace zata aikata zai farun,sai abinda Allah ya tsare kawai,wadannan maganganun duka ta sani tana yinsu ne saboda ita.
Ita da sultane din duka sukabi zaitunan da kallo sanda take ficewa gurinsu Alhaji nasiruddeen.
Motarsu suka bude mata,don baya cikin doka mutum ya tafi a motarsa kaman yadda zaituna taso tayi da farko. Inda tuhuma ce kawai ba'a kamata da komai ba ana iya bata wannan damar. Da farko ta tsaya kai da fata bata shiga motarsu saidai ta taho a tata motar,duk da tasan cewa doka bata bata dama ba. Amma sai tawagar 'yan jaridar da sukayo kansu.....'yan jaridar da basusan waye ya kirasu ba suka sanyata da qafafunta ta shige motar,musamman da idanunta suka sauka kan biyu daga cikinsu. Suna cikin 'yan jaridar wancan ranar......suna cikin 'yan jaridar da suka yada labarin takardunta na wancan ranar,har abun yake neman zame mata barazanar da a yanzu ake d'ari d'arin karbar taimako daga gurinta daga kowanne asibiti ko gidajen marayu da sauransu.
"Da gaske ne an samu qwayoyi a tare dake......da gaske ne tafiya zakuyi don tuhuma?" Tambayoyin da suka ratso glass din window din da take zaune suka isa ga kunnuwanta,tambayoyin da suka tilasta mata runtse idanunta tana jin zuciyarta da idanunta suna zugi.
"Ina tafisu da nace zamu tafi tare?"
"Ba'a ganta ba......amma ko daga baya ne zata iskemu a can" Driver din motar ya bata amsa yana tayar da motar.
*S U L T A N E*
Idanu morsa safiyya ta zubawa sultane,wanda tun bayan tafiyarsu mammina bai sake cewa komai ba banda shurun. Koda ba'a gaya mata ba tasan yanayinsa,tasan kuma halinsa,alamu ne na zurfafa cikin tunani,tunanin data tabbatar baida fa'ida gareshi da lafiyarsa,musamman yanzun da yake yawan qorafi akan yanayin qarfi da lafiyar jikinsa.
"Bappin akhnan" Ta kirashi da sunan da tasan yana masa dadi sosai. Kansa ya daga yana dan sake mata murmushin qarfin hali.
"Nace ko zaka tafi ka kwanta ne?,zuwa anjima qilan idan ka samu kayi bacci zakaji dadin jikin naka?" Kai ya daga mata a hankali,shi kansa baya marmarin ci gaba da zaman. Wani irin abu yakeji yana taso masa game da mammina. Wani irin yanayi da yafi kama da zargi rashin yarda da rashin aminci. Ya sani,gidansa cike yake da tsaron da ba wanda ya isa ya keta sassan matansa ta sauqi haka har yayi ajiya makamanciyar wannan,ballantana sassan mammina din,da kusan ko sashensa bazai nuna masa tsari tsaro da kulawa ba.
"Muje" Ya fada yana yunqurin miqewa. Koda ya miqe sai yaji kamar ana jijjiga jikinsa da qafafuwansa. Sai yaji kamar komai yana shirin bace masa a lissafinsa,kafin ya iya yin komai wani jiri ya debeshi.
Salatin morsa safiyya da hailalarta kawai ya iyaji,yana jin sanda ta tareshi amma bata da wannan qarfin,dole ita dashi din duka suka zube a qasa.
Da wani irin tashin hankali take kiran sunansa tana tattaba fuskarsa ganin idanunsa suna komawa gami da rufewa ruf. Iyakar yadda zatayi ya gagara,sai ta miqe a birkice tana kama sunayen duk wani hadimi da tasan za'a sameshi a kusa dasu.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 36*
"Ba numfashi a jikinsa kwata kwata" Daya daga cikinsu ya fada yana duban morsa safiyya gumi yana yanko masa.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Ta samu kanta da maimaitawa sau babu adadi,ya sulale tana zama dab dashi tana riqe hannayensa sosai cikin nata.
Safeena ce take dawo mata cikin kanta....wancan ranar da ba zata taba gogewa cikin kanta ba,har sai ranar da tata ta sameta.
"Karka tafi ka barni kaman yadda safeena tayimin" Ta motsa labbanta tana fada a hankali tana jin kamar hankalinta yana neman gushewa daga jikinta.
"Likita ya iso Allah ya baki nasara" Taji muryar daya daga cikin hadiman,kai ta daga tana dubansa kamar bata ganewa,sai kuma ta sake matsawa kusa da sultane din da har yanzu ba wani abu nasa daya motsa,kamar tana gaya musu bazan iya tashi daga nan ba.
★★★
*M A D E E N A* _ALMUNAWWARA_
*_InterContinental Dar Al Iman Madinah(presidential suit)_*
Cikin lallausar jubah yake sanye wadda aka samar da ita da zare da auduga me darajan gaske. Fara ce tas me wani irin daukan idanu saboda tsadajajjen silk material me asalin tsada da aka maida audugar zuwa ga saqarsa.
Yana tsaye bakin babban glass window din,wanda kai tsaye idanunsa suke kafe akan haram na masallacin ma'aiki S A W.