Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 20

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 20

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 20: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 20. Tunda suka zo baya gajiya da tsaiwa a gurin......baya…

3,299 words

Tunda suka zo baya gajiya da tsaiwa a gurin......baya gajiya da kallon gurin da yake fata ruhinsa da gangar jikinsa watarana su dawwama a gurin. Koda zai mutu kuma ya zamana yana da rabon qasarsa ta kasance cikin garin me tsarki.

Links na jubah dinsa yake sakawa a nutse yana sake qarewa haram din kallo. Yammaci ne sosai,wanda duka duka zuwa sallar magariba bazai haura awa biyu da rabi zuwa uku ba,a awannin kuma yakeso su qarasa ziyararsu saboda kwanaki biyu kawai ya rage su wuce Ethiopia.

Wani haske me laushi ke gilmawa ta haram din,tunda yake bai taba ganin garin dake da wani irin shuru me dadin sauraro ba irin madeena,duk da tarin baqi maziyarta ma'aiki S A W da kullum suke cikinsa.

Ya kammala sanya links din,ya dafe hannuwansa jikin glass din yana sauke wata ajiyar zuciya me nauyi,ajiyar zuciyar dake tafe da wata irin nutsuwa daga ruhinsa har zuwa gangar jikinsa.

Bayan tsaiwar da tayi na kusan mintuna biyar bakin qofar bedroom dinnata tana shaqar daddadan qamshinsa cikin fargabar yadda yau zasuyi face to face bayan wannan damar datayanke masa. Tun a makka tun ranar data dawo daga gurin falaak takejin wani irin tsoronsa yana shigarta. Gani take ko yaya suka kebe zai iyayi mata wani abu,saita maida duk wani ziyara da zasuje ko ibada lallai saita jajibo falaak da maleek,haka suka dinga tafiyar bibbiyu bibbiyu. Ta kuma zabi lokutan dawowarta daidai sanda yake haram ko ya kwanta bacci,kwanaki kadan sukaga juna ita dashi har suka taho madeena.

Ko a yanzun wani dan qaramin ciwon kai takeji da mura da tasan bata rasa nasaba da yawan zamzam me sanyi data dinga sha ba adadi.

Kwarjini yake mata sosai bayan wannan tsoron,kwarjinin daya sake daduwa tun bayan guraren da suka ziyarta. Gurare ne da tunda take zuwa saudiyya bata taba sanin akwaisu ba ballanta taje. Gurare na tarihi sosai daya shafi annabi Muhammad S A W da sahabbansa. Ba ziyarar kawai ba.....wani abu qwaya daya daya dinga narkar mata da zuciya.....wani abu guda daya daya tilastata ta dinga satar kallonsa har batasan adadin awannin data dauka ba.....wani abu qwaya daya daya sanyata zubewa lips dinsa idanunta tana kallon yadda yake motsa bakinsa,abinda ya dinga tayar mata da tsigar jiki shine. Duk wani guri da zasuje a tausashe da muryar nan tasa da sau tari idan ta kwanta take jinta cikin kanta.....cikin mafarkinta dama duk wani motsinsa.....da wannan muryar yake basu tarihin kowanne guri idan suka tsaya a gurin,da abubuwan da suka afku a gurin zamanin annabi Mohammad S A W. Idan akwai ayar data sauka zai karantata da kyakkyawan sauti da kuma daddadar qira'ar nan tasa. Bata manta ba.....qira'ar ta sanya mutane da yawa waiwayowa suna dubansa,sannan ta qara yawan mutanen da suka bi tawagarsu,dole ya koma bayani da harshe biyu English da arabic saboda mutanen dake biye dasu.

Sai kuma taji wani abu yana matse qirjinta sanda taga 'yammata na sake qaruwa,suna biye dasu har xuwa sanda suka kammala ziyaran.

Ko a shekaran jiya sunje mazr'a Al'Aaliyah inda nana mariyatul kibdiyya ta haifi sayyadina ibraheem dan manzan Allah S A w. Sunje Daar almadeena museum.... Acan din taga abubuwa masu yawa da aka surantasu cikin killataccen glass da suka shafi ma'aiki matansa da sahabbansa.

Gurare ne da suka dinga saukar da wani sanyi da taushi a zuciyarta. Ashe a baya suna zuwa ne kawai ibada ba tare da sun qarawa ibadar armashi ba?. Bata taba umara irin wannan ba a rayuwarta,bata da tabbacin ibadarta,amma zata iya cewa wannan ce umararta ta farko data karbu dari bisa dari.

Da wani irin yanayi take takowa zuwa living room din,kamar wata qasaitaccen dawisu. Yanayinta haka me sanyi a wasu lokuta,takun tafiyarta da izza da nutsuwa suka yiwa ado,wannan yana sanyawa idan yana tafiya take jan hakalin mutane sosai,bawai maza kawai ba,harda mata 'yan uwanta.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Abaya ce me sulbi a jikinta midnight blue,asalin silk blend me wani irin yauqi da daukan hankali. Wani irin zaunannen kyau tayi,color na rigar yayi masifar fita da kalan fatarta. Dan Malaysian hijabs da ya zame mata abokin sawa tun zuwansu qasar ya fidda kyan fuskarta tare da qara bayyanar da quruciyarta.

Ko a yanzun da yake tsaye,motsinta yaja hankalinsa,motsin daya sanyashi waiwayowa a nutse. Wadannan narkkakkun idanun nasa suka sauka saman fuskarta,sai wani abu ya haska cikin idanunsa.

Quruciya.....qananun shekarun nan da yayi masifar rainasu,a yanzun yana sake ganin qarancinsu qwarai da gaske. Can qasan zuciyarsa ya samu kansa da irge hasashe da laluben ainihin shekarunta.

Ya lumshe idanunsa kadan yana budesu a kan fuskarta,yanayin kallon daya qara mata fargaba ya kuma aza mata nauyi me yawa,sai tayi qoqarin kauda kanta kadan tana nufar inda ta ajiye wayarta dazun bayan shigowarta.

"Barka da warhaka" Ta fada da wannan muryartata me wani irin taushi,wadda ko sau nawa zata buda baki tayi magana sai yaji wani abu daban da baisan meye ba a cikin muryar.

Maimakon ya amsata,sai ya gyara tsaiwarsa sosai,ya zube hannuwansa cikin aljihun jubah dinsa yana qare mata kallon dashi kansa baisan dalili ba.

Yadda fararen qafafunta ke sauka saman tattausan carpet din kamar me tausayin qasa......yadda abayar ke budewa sosai ta bayanta tana bada wasu kaloli kaman ba kalar midnight blue ne kawai a jikinta ba......a hankali duka yanayin suka hadu suka saukar masa da wata irin nannauyan kasala. Yana karance da duk wani takunta tun daga wancan ranar.....wani lokaci siririn murmushi kawai yakeyi. Idan da yaso.....idan da yaga dama ba zata kawo wannan gurin ba. Idan da wani abu daban yake buqata daga gurinta yasan duk ta hanyar da zai karba,bazai ma bata daman da zata iya guduwa daga gareshi ba,to amma ba wannan lissafin yakeyi ba a yanxu.

Yana buqatar ta gama sanin wacece ita?,wacce rayuwa tayi a baya?,wacce kalar rayuwa kuma zatayi a yanzu?. Yanaso kuma yaga iya gudun ruwanta gurin qwarewarta wajen guduwa. (Hmmmm Captain.....wata qaddarar tana bada zabi ne?).

Har ta qarasa gurin,ta zare wayarta daga charge tana jin nauyin dukka idanunsa a kanta.

A hankali takejin wani kusanci a tsakaninsu.....cikin jikinta takejin tabbas yana kusantowa gareta. Ta basar ta danne tana mazewa gami da zarcewa da danna wayarta,duk da yadda zuciyarta ke wani irin bugawa a hargitse,tana kuma bata shawarar ta daga qafarta zuwa waje ya sameta a can,amma ta kasa koda motsin kirki.

Ba kasafai ta fiya son a gane lagonta ko faduwarta ba. Batason a gane meye rauninta shi yasa take iya iyawarta ta boye masa tsoronta,saidai abinda bata sani ba.......tana auren wani mutum ne na daban......wani mutum da yake iya karantarka ta cikin qwayar idanunka kadai ba tare daka furta masa komai ba. Motsinka kadai ya isheshi amsa.....motsi kawai wata fassara take bashi me tarin ma'anoni.

Jinsa dab da ita da wannan sassanyan qamshin nasa da kowacce rana idan zata jishi sake dilmiyata yakeyi cikin wani yanayi me wahalar fassara. Ta daga fuskarta da sauri,saidai irin kusancin da ta gani a tsakaninsu yafi firgitata sama da komai. Taku daya tak tayi da nufin janyewa baya amma sai ya saka dogon hannunsa ya riqo tsintsiyar hannunta da kyau,bai kuma bata dama kota second daya ba ya janyota jikinsa,saidai kuma bai bari ta fada faffadan qirjinsa ba ya tareta ya tsaidata dab dashi yana riqe qugunta da dukka hannayensa biyun.

Kallon kallo suka fara yiwa junansu,nata idanun cike da tsoronsa da wani irin shakka.......zuciyarta na bugawa da gudun da ta sani tabbas idan shuru ya sake wanzuwa tsakaninsu zai iya jin qarar bugun.......yayin da nasa idanun ke cike da wani abu dashi kansa baisan meye ba. Wani abu da yake zama kamar wani dan aike daga idanunsa zuwa na akhnan din.....wani abu da ya yiwa zuciya da qirjin akhnan nauyin gaske.....wani abu daya fara ratsata tun daga qwayar idanunsa yana bin kowacce hanya da jini yake iya wucewa yana sauka kai tsaye a zuciyarta.

KAIFI......wani irin kaifi idanunsa ke dashi.....bata taba ganin d'a namiji da yake zarra irin tasa ba. Ba wani namiji data taba kafewa da idanu irin haka bai rusunar da nasa idanun ba.....amma shifa?.

Ko yaushe qwayar idanunsu suka gauraya qoqari yake ya dakushe tata. Qoqari yake ya kashe duk wani kwarjini nata ya mamayeta da nasa.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 37*

"Kina zaton idan naso kamaki kina da wani sauran dabaran guduwa ne a hannuna princess akhnan?" Yayi maganar da wani coolness daya daki zuciyarta. Halittar BURGEWA taji tana kafa sansani cikin ruhinta. Burgewa......yadda yayi maganan ya wani burgeta,ya wafci idanu da hankalinta,har ya sanya zuciyarta ta wani irin motsawa da kalar qarfin daya sanyata taji kamar iska dake dakin ta mata kadan,ko kuma shi ya zuqeta tas.

Idonta ta kalmashe kawai tana sauraren kalmominsa dake fita a jejjere da wani irin isa da izza.

"Kin gama wasan buyan?.....ko na qara miki lokaci biftu?" Ya sake kiran sunanta a qarshe da wani yanayin data tabbatar inda qwayoyin idanunta a bude suke......tabbas da ya gama cutarta......inda qwayoyin idanunta a bude suke........tabbas......ba iya zuciyarta kadai ba.....zai iya karanta rayuwarta ta baya ma gaba daya.

"Ki sassauta........bana nufin abinda ke kike tunani" Ya fada yana sassauta riqon da yayi mata.

Wani dummm taji....kalamansa na qarshe daya kamata taji farinciki.....kalmarsa ta qarshe daya kamata ta faranta mata rai.......amma saitaji batayi mata ba.

Abinda take gudu don shi.......a fakaice ya gaya mata baya gabansa kenan?.

Batasan me ya sanyata dora hannunta saman nasa hannun dake qugunta ba,ta kuwa xameshi a hankali don ya sassauta riqon da yake mata din.

"Abinda kake tunani ba shine a raina ba.....ai ibada mukazo yi.....ita sultane yace muyi...." Sake matse qugunta yayi fiye da dazu,har tana jin yatsunsa sosai cikin fatar cikinta.

Ya sassauta wannan tsahon nasa yana sunkuyowa daidai bakinta,abinda ya bata wata babbar dama na qarewa idanunsa kallo fiye da kullum. Idanun nan dake dauke da wadattatun eye lashes,farare qal kamar ba idanun namiji ba.

"Ibada?......ai ibadar ma nau'i nau'i ce......ba umra bace kawai ibada......shima wancan abun ibadar ne". Kamar ya kada mata sassanyar iska cikin hunturu haka matsananciyar kunya ta sanya ta fara ji cikin jikinta. Neman inda zata cure ta cukuikuye takeyi amma babu,sai jikinsa kawai dake tsaye a gabanta.

Yanzun me ya kawo wannan maganar fisabilillahi?. Shima haka yake?,shima d'aya yake da sauran?.

"Kina tsoro?........bai kamata ki dinga tsoro kan abinda yake da nisan tazara tsakaninki dashi ba" Ya fada yana zare yatsunsa daga qugunta a hankali.

"Idan naso......numfashinki me zai zama ba naki bane......a duk sanda zai fita daga qirjinki zai fita ne yana ambaton sunan muhammad haisam......zan sace baccinki......zan gudu da nutsuwarki.......tunaninki gaba daya zan mallakeshi.......ta yadda zaki zama baki da wani sauran xabi.....bakya gane komai sai abinda haisam ya shirya ya kuma tsara miki". Wani irin ego nata ya motsa......wanda yake cakude da tsoro.

Anya batayi wani abu na ba daidai ba kuwa da yasa yake ganin yana da dukkan wadannan damarmakin.

"Allah ya sawwaqe" Ta fada da wata karyayyar murya. Batason yasan me take struggling dashi.....bata shirya bashi kowacce qofa ba.....saboda bai dace ya fara fitowa daga sashenta ba......bai kamata ace daga bangarenta bane komai ya fara.

"Allah ya sawwaqe?,really?" Ya fada fuskarsa tana fadada da wani abu da yafi kama da murmushi,ya dage dukka girarsa sama da alama yanason samun amsa ta gaskiya.

"Eh......Allah ya tsareni......har yanzu......ba wani namiji daya cika wadannan sharuddan da qa'idojin" Wani sassanyan murmushi daya sanya har fararen haqoransa a jere reras ya saki,ya sake taku biyar baya yana bada tazara a tsakaninsu,idanunsa kuma still cikin nata,ya riqe qugunsa da hannayensa gaba daya kamar me nazarin wani abu daga gareta.

"Au.....eh fa.....na manta wannan din me tsada ce,princess of agadez.....bai kamata almajiiri irina yayi tunanin samun komai haka da sauqi bafa ko?" Ya qarashe da sigar tambaya.

"Basai ka yaudarar dani ba bayan yaudarar da sultane da kayi......na sani.....wanda yake magana kamar yana da ikon mallakar zuciya da numfashin mutum… ba almajiri bane.” samun kansa yayi da harde hannayensa a qirjinsa da wani kalar murmushi dashi kansa yasan yakan jima adane a fuska da qirjinsa kafin irinsa ya fita. Sai abu na matuqar burgeshi da daukan hankalinsa tukunna.

"Amma kuma......idan kana ganin zaka mallaki tunanina......to har yanzu baka sanni ba tukunna. Don kana magana ne kamar wanda ya riga ya samu nasara......amma kuma har yanzu ban baka wannan damar ba"

Wannan karon murmushinsa yafi na dazu fadada. Ya zare hannunsa yana tafashi a hankali.

"Bravo princess......." Ya fada da murmushin nan akan fuskarsa.

"Shi yasa kika dinga bincike a kaina a boye?" Ya dan matsa gabanta kadan

"Kina tunanin na yaudareki harda sultane?" Ya sakeyin shuru na second biyu.

"Kinason sanin wanene ni?...." Ya qara fada da wani softness cikin sound dinsa.

"Da gaske?" Ya mata tambayar kaman da gaske amsarta yakeson ji,sai kuma ya dora yana maida mode dinsa na farko,miskilanci da izza

"Ki kula da abinda kike bincike sosai a kai"....

Wannan karon tsoron dake ranta ya ninka wanda takeji a kansa a baya.

" Ta yaya?,ta yaya ya sani?,ta yaya yasan ta fara bincike a kansa?,saidai izzarta ba zata bari yaci nasara a kanta ba.

"Bincike?" Ta fada tana jan numfashi a boye,saidai duk yadda takai ga boyewar ya ji kaman yadda yake da kaifin jin abu komai qanqantarsa.

"Ba kowanne abu bane ake kira bincike....." Ta furta da confidence tana qoqarin kaucewa haduwar idanunsu.

"Wani lokaci mutum yana qoqarin fahimtar abinda yake gabansa ne kawai......idan hakan ya sanyaka kaji kamar ana leqenka....." Saita dan dakata tana tattara courage dinta.

"To wataqila akwai abinda kake boyewa fiye da yadda kakeso a gani".

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Wow" Wani bangare na zuciyarsa ya amsa a nutse ba tare daya furta ba da dukkan qarfin da suka amsa cikin bangwayen zuciyarsa. Tsakiyar idanunta kawai yake kalla. Wannan qwarin gwiwar......wannan zarrar......wannan tsaiwar kafiya da taurin kan......dukkansu.....dukkansu wasu abubuwa ne daya karanta tattare da ita,wasu halaye da yaji sunyi masa.

Taurin kai.....zarra kafiya da tsaiwa kan ra'ayi.....ba'a samunsa tattare da lusarin mutum da baisan yau dinsa ba ballantana gobensa. Wasu alamomi ne dake nuna CIKAR MUTUM na sani da ikon zabar meye ya dace dashi.

"Okay.....na baki daman ci gaba da bincikata....saidai na miki alqawari........ina miki albishir ba zaki samo komai tattare da wannan muhammad din ba.....kince Allah ya sawwaqe ko?" Yayi maganan duka lokaci daya.

"Let's play a game mana......ni dake.....duk wanda yayi winning........i mean,duk wanda yayi nasarar hana dan uwansa satar zuciyarsa......ko ni nayi nasarar saceta.... Akwai wata sadaukarwa da daya zaiwa daya,zai.bashi abinda bai taba tsammani ba....agreed?"

Cikin jikinta takejin kamar akwai wani abu daban.....kamar akwai wani abu da bazata iya daukarsa ba.....

"Ni ban iya satar zuciya ba.....amma nasan yadda zan kare tawa" Ta furta ba tare data shiryawa fadin hakan ba. Dariya ce taso qwace masa saboda yadda tayin......dariyar daya manta rabonsa da yayita,saidai wannan ginshirar da izzar ta danneta ta maidata qasaitaccen murmushi.

"Kina tsoro ne?"

"Ni.....tsoro?....."

"Yes.....kada ayi nasara a kanki".

"Ba'a nasara a kaina....koda yaushe nice nake nasara a rayuwata"

"Har a hippodrome?" Ya jefa mata tambayar a bazata,ta kuma sauka a kunnuwanta a bazata din data tilastata waigowa da wani irin zafin nama.

Fes idanunta suka samu kyakkyawan matsugunni cikin nasa. Idanun da suka soma narke mata a hankali.....a hankali suna dawo mata da komai yadda ya faru. A wancan ranar.....a wancan lokacin.

"Boyayyen mutumin Niamey?,hippodrome?" Labbanta suka motsa a hankali ta furta da wani irin low tone. Zare nasa idanun yayi a hankali,sasaauqan murmushi yake saki,bai kuma bata amsa ba ya fara takawa a hankali yana zura tattausan takalminsa cikin qafafunsa. Takalmin da yayi wani kyau yayi ladabi sosai cikin qafarsa....asalin takalmin gidajen sarauta na oromo.

"Game started" Kawai ya fada a hankali yana nufar qofa. Har yakai qofa bata motsa ba,sai daya bude ya sanya qafafunsa a waje sannan yace

"Dates farm zamu in sha Allah" Maganan ya bata qaimin data iya cira qafafunta da qyar.

Range Rover Autobiography ita ga ya nufa a nutse. Ba yadda ya doshi motar kai tsaye kawai ba.....asalin tsada da darajar motar......yadda ya buda motar da muqullin dake hannunsa kai tsaye ya sake d'aureta kaman yadda ya saba. Ya taka a hankali ya zagaya seat me zaman banza,ya bude mata murfin.

Kallonsa tayi kadan,har yanzu kokwanto a kansa yana sake nuqurqusar zuciyarta,amma saita dake ta taka tana shiga motar. Hannunsa ya saka ya tattare mata rigarta cikin nutsuwa,sannan ya rufe murfin motar softly.

Yadda yake zagayawa ta gaban motar zuwa nasa seat din cikin karsashi da wani irin kuzari yaja hankalinta. Da idanu ta bishi,maganganunsa suna dawo mata.

"Yana da zarra.....yana da zarra irin ta isashen namiji" Ta gayawa kanta da kanta tana lumshe idanunta a hankali. Tako ta ina nema yake ya qure mata,salon iya maganarshi daban ne,kaman sai ya zabi kalmomi yake amfani dasu,kamar kuma yana da iyakacin kalmomin da dasu kadai yake amfani idan zaiyi magana.

Qamshinsa ya mamayeta,kusancin dake tsakaninsu ya mata girma,mamakin kuma yadda zai tuqasu da kanshi ya sanyata kasa motsi.

"Bismillah" Ya fada yana qoqarin tayar da motar. Kasa jurewa tayi jin ya kunna motar,cikin tsoro takai hannunta saman nasa ta riqe sosai.

A nutse yadan daga idanunsa yana dubanta,idon nata ya masa wani irin kala da wani irin haske sanda ta juyashi tana dorashi saman dashboard din motar,tsoro fal cike da blue eyes dinnan nata.

"Ka tsaya!" Ta fada adan rude da muryarta data fara rawa.

"Me ya faru?" Yayi tambayar a nutse ba tare daya zame hannunsa daga cikin nata ba,saidai ya taka motar da kyau ta fara gangarawa da wani kyakkyawan tuqi.

Zuciyarta tadan tsaya cak,ta soma bin gabanta da kallon,yadda yake sarrafa steering cikin wani irin qwarewa kadai ya isa ya bata amsar abinda take kokwanto.

A kunyace ta zame hannunta daga cikin nasa,ta danyi qasa da kanta,yadda yayi shuru yana saurarenta nauyi yake sake mata akai,saita yanke kawai kawo qarshen shurun.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 38*

"Na tsorata ne,ban dauka ka iya tuqi ba" Maganan ya sanya murmushi me yawan saman fuskarsa,wannan karon har ya gaza boyewa

"Kina rainani ne?" Tambayar ta sake sakata jin kunya,sai kawai tayi kamar bata jishi ba.

"Yana da kyau ki koyi tambaya kafin ki yanke hukunci" Ya fada calmly. Har cikin ranta taji maganansa yana kan gaskiya,to amma ta yaya zata iya controlling kanta da dukka wadannan baqin abubuwan da take gani tattare dashi?,ta yaya zata aminta dashi?,ya zata bari ta yarda dashi?.

Tana yarda su kasance a muhalli daya ne kawai don suna amintaccen gurin da babu cutarwa a cikinsa. Amma bayan nan gurin.....wannan gurbin....wannan muhallin.....zata sanya idanu da lura sosai a kansa......zata taqaita wanzuwa dashi a muhalli daya har sai ta gano anihi da gaskiyar WAYE SHI?.

Shuru motar ta sakeyi,shurun da sam baiyi mata dadi ba. Kaman yasan me yake kai kawo cikin zuciyarta,sai yasa hannu yana daidaita iskan Ac din dake motar. Wani abu data lura dashi,kwata kwata shi ba ma'abocin son sanyin Ac da yawa bane.

Readers Also Read

More by Huguma