L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 27
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 27: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 27. "Sheikh muhammad" Ta fadi da murmushi. Yakanyi murmushi…
3,357 words
"Sheikh muhammad" Ta fadi da murmushi. Yakanyi murmushi a duk sanda ta kirashi irin hakan,sai yaji sunan kaman yafi dadi a bakinta.
"A duniya.....wanne buri ne kike fatan cikarsa kafin ki koma ga mahaliccinki?". Tayi shuru tambayar tana ratsawa cikin kanta. Tana da wasu burika na daban......amma ta sani inde ta riga muhammad rasuwa to zai iya cika mata su,koda bata gani da idanuwanta ba,amma a yanzun burin da take dashi shine taga 'yan uwanta.
"Muhammad......burina bana jin me cika ne" Ta fada a raunane. Matsawa gabanta yayi sosai,ya kama hannuwanta ya riqe cikin nasa.
"Kija numfashi sosai nanay,ki fadi duk wani burinki,a gaban muhammad dinki kike" Murmushi ya subuce mata dake hade da ruwan hawayen da baikai ga zuba mata ba.
"Na sani.....wannan jan gwarzon namijin,zakin d'ana" Maganan ya sashi qaramar dariya,duk da ba yau ya fara jin ta fadi haka a kanshi ba,amma murmushinta kawai ya sanya wani farinciki a zuciyarsa.
"Burina naga safiyya da safeena,duk da nasan zai wahala rayuwa ta bamu wannan damar" Ta fadi cikin alamun karaya da yanke tsammani.
"Idan na sadaki da koda wani abune daya shafesu......wannan burin naki ya cika?" Samun kanta tayi da qanqame hannunsa sosai har yaji hakan cikin jikinsa,idanunta cikin nasa sosai.
"Koda abinda ya shafesu ka hadani dashi muhammad inaji a jikina zai zamana kamar ka hadani dasu ne kai tsaye......amma anya...."
"Kisa a ranki a nan kurkusa wannan burin naki zai cika" Har cikin tsakiyar kanta sai da taji wani abu,mamaki ya hanata cewa komai da wata irin shakka data cika zuciyarta.
Tafi kowa sani.....ba maqaryaci bane......idan ya fada koda da wasa ne sai ya cika. Wannan ya sanya yake kiyaye harshensa akan fadin abubuwa sosai don baya fadin abinda bazai aikata ba. To amma idan ta gamsu da abinda ya fada fa?. Ta ina zai nemo mutanen da ko burbushinsu ba wanda ya sake gani ko ya sake jin labari shekaru kusan talatin?. Amma kuma gaskiyarsa wata abace da ko yaushe take sake nuna zahirin waye shi.
_ki yarda kawai nanay.....mu lu'u lu'u followers muna tayaki murna da haifar jarumi kuma nagartacce,ya rabbi kasa mun haifi sanyin idaniyarmu muma_🙏🏽🙏🏽
★★★Kwananta daya tak ta soma karbar wasu darussa na sabuwar rayuwar data dinke tunaninta tsaf. Wasu irin al'adu na girmamawa,sutura,yanayin magana da yanayin kula da miji da bata taba ganin irinsu ba.
Komai da ake qoqrin azata akai da koya mata mamaki yake bata. Tanason karanta da fahimtar dukka dalilan yin hakan. SARAUTA ta tabbatar gidan wani sarautar ya shigo......gidan sarautar dake da wani irin tsare tsare da tarbiyyar da a tunaninta bata dauka wani gidan sarauta zai kasance irin haka ba. Abu daya da bata gane ba shine......waye shi a masarautar tasu?. A rannan yace mata shi BAWA ne......amma tako ina maganarsa ta gaza shiga zuciyarta da ranta tayi tasiri. Ba wata alama ta bauta a tattare dashi......horon da ake bata kuma baiyi kama da koyarwar da za'a zauna ana yiwa matar bawa ba.
Sabuwar rayuwa take shiga......wata irin sabuwar rayuwa da bata taba sanin da zamanta a duniya ba. Sai a sannan ta tuna da zancan aisa.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Duk yadda kike ganin kinsan duniya da yawa,qasashe masu tarin yawa,kin cakuda da mutane qabila kala daban daban......amma akwai inda zaki shiga kiga kin koma kamar wadda batasan komai ba.....rayuwa gaba da gabanta ne.....kafi an fika,Allah ne kawai a sama" Tayi maganan ne tun farko farkon fara zuwan manemanta da sultane ke sahale musu ganinta. Ta raina daya daga cikinsu daya kasance d'an sarkin Cameroon,duk da tarin dukiyarsa da wayewarsa. A lokacin aisa taso ta aureshi......amma ta gaya mata ba'a halicci d'a namijin daya hada dukka qualities din da take buqata daga gurin namiji ba,auren wanda bai hada wadannan nargartar ba tabbas zai zama tozarci ne da qasqanci a tattare da ita,koma baya da rasa martabarta.
Wata irin kulawa ake bata.....wata irin girmamawa da tattalin da hatta su birra saida suka raina yadda suke kula da ita a agadez. Komai nata ya canza,daidai da fatarta tasan akwai wani abu daban dake faruwa a rayuwarta.
Qamshin jikinta ya zame mata qamshi na biyu dake debe mata kewa bayan qamshinsa.......qamshin turaruka na SHUWA INCENSE AND MORE( +234 704 229 3387) wani qamshi da yake sanyata dadewa cikin duvet duk safiya idan ta farka tana shaqar qamshin yana kai mata har cikin kwanyarta,yana kuma qoqarin kwashe mahaukaciyar kewarsa da takeji tana qoqarin hanata dukkan walwala. Ta dauka a kowacce rana zai shigo ya ganta......ta dauka kowacce rana zata zame masa ta ziyara,saidai abun mamaki babu shi ba dalilinsa. Ba kiransa a cikin kwana biyar din data dauka cikin gidan.
Amma a kowacce rana hasnaa da rumaisa da wasu mata da batasan su waye ba suna ziyartar gidan. Cikin kulawa take ta kowacce fuska,cikin kulawa da tattali take da wani irin gata daya sanya ta soma tambayar kanta,wacce irin rayuwa tayi a baya ne?,gata ne da kulawa ta samu?,ko kuma copy ne kawai na gatan ba original ba?.
Abun mamakin yadda kwanyarta ke kwashe komai......ita kanta me dora mata tsarin tana ganin mamaki qarara kwance saman fuskarta.
Bawai suna da wani qarfin ikon sauya mata rayuwa bane.....aah ta yarda tabi komai yadda aka tsara saboda tana buqatar fita daga gidan. Tana buqatar sanin WAYE SHI?,tana da buqatar ganin anihin rayuwarsa,hakan kuma dukka ba zata samu ba sai tayi qoqarin maida kanta yadda sukeso.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 49*
Suna waya da shehnaz,aisa da morsa lokaci lokaci......amma har yanzu ta gaza samun sultane sai sau daya tak. Shima maganarsu dashi gajeriya ce......ya mata wata magana a qarshe data sanyata fashewa da kuka.
"Gida nakeso na dawo bappi......gida nakeso nazo na ganka" Murmushi ya sake mata.
"Nace miki ko bayan na mutu kike kuka ko biftu?" Ya fada da murmushi
"To ko mutuwa nayi indai haisam bai lamunce kizo ki ganni ba ban yarda kizo ba.....idan kika bishi hakanne zai samawa ruhina salama koda cikin kabarina......duk da ina lafiya cikin qoshin lafiya,muna kan wani aiki ne da yake janyemin lokaci,duk sanda kika nemeni baki sameni ba....karki saka a ranki wani abu ne mara kyau,cikin aminci nake da kiyayewar Allah".
Tayita kiran aisa sa shehnaz ko zataji wani abu,amma ba wata alama data nuna akwai damuwa ko matsala cikin masarautar,haka ahmad data kira shima abinda ta gani kenan,wannan ne ya sanya mata nutsuwa a ranta,ta maida hankali ta kammala wancan training din ta fito,tunda duk binciken da tasa a mata sunce basu gano komai a kansa ba,wannan karon ita zata nuna masa adadin nata ikon.
Batasan me yake faruwa ba,tasan dai kawai ta tsinci kanta tsundum da yawan duba wayarta. Duk bayan shudewar wasu mintuna saita duba screen din wayarta,daga haka saita fara zarcewa zuwa gurin kira.
Takan jima da wayar a kusa da ita,takan jima tana juya wayar a hannunta,batasan me take jira ba,batasan me take nema ba. Sannu a hankali sai wadannan hotunan data fuskanci da yawa an daukesu ba tare daya sani ba......a mabanbantan lokuta a kuma mabanbantan gurare suka zame mata qawaye.....suka zame mata abubuwan da duk rana ranar ba zata fito ta fadi ba bata buda ta kalla ba.
Daga qarshe ta sani.....ta bari zuciyarta tayi mummunan sabo da al'amuransa......sabon da batasan meye dalili ba.....sabon da batasan meye ya kawoshi ba......ta sani ta saba ta saba ta saba......amma duk da haka akwai abu daya dataqi yarda a karan kanta cewa SOYAYYA CE.
Yarda da cewa tana sonshi tana jin shine qarya ta qarshe da zata qara yarda zuciyarta ta qulla mata. Ta sani tadade da kashe duk wani gurbi na taso wani d'a namiji a zuciyarta. Ko meye takeji ta yarda ta sallama da cewa SABO NE SILA.
Tasha kallon number daya kira a wancan ranar......amma kuma ta dade da yiwa zuciyarta bore wadda ke shawartarta ta gwada kiransa. Yasan inda zai ganta......yasan number da zai kira ya sameta,bai nemeta ba......ta yaya dalilin sabo zata bari alfaharinta na diya mace yayi qasa?.
Tana tsoron sabo ya karya wannan alfarmar don haka a wani yammaci ta dannawa number delete,amma batasan me ya sanya wani abu ya tsaye mata a wuya ba bayan ta goge number.
Ranar farko da hawaye suka cika mata idanu ranar da kewarsa ta hanata bacci. Tayita juyi,tayi alwala tayi sallah duka wannan kewar data rasa wacce iri ce ta hanata sakat.
Me yasa duk yadda na dade da sultane da kowa da kowa dake cikin masarauta bana jin girman kewarsu haka a raina?. Me yasa banquntata da yawa ba daga rashinsu a kusa dani?,saishi?.....WAYE SHI?,meye na musamman a tattare dashi da kewarsa ta dara ta kowa nauyi cikin zuciyarta?.
D'isar qwallar kawai taji saman cinyarta,sai wani irin mamaki ya kasheta.
"Qwalla akhnan?,qwalla saboda kewar D'A NAMIJI?" Ta jima jikinta a sanyaye tana jin zafin abun. Me yasa ta sake masa haka da yawa?,me yasa ta bari suka saba da ganin juna da jin motsin juna?,wanne irin sakarci tayi haka?. Hannu tasa ta dauke qwallar tana gayawa kanta,har yanzu itace dai akhnan muhammad hammud.....bai kamata ta bari wani abu ya karyata ba,amma dai daga qarshe sautinsa.....qira'arsa.....karatun qur'aninsa ta kunna da qaramin sauti can qasa,shine abinda ya sama mata nutsuwar data samu yin bacci a wannan daren.
★★Duk zirga zirgar daya yini cikinta tsakanin gidan prime minister da gidan governor na jimma a yinin ranar data zama ta qarshe tun daga safiya zuwa yanzun da sararin samaniyar jimma ke bada wata lallausar iskar hadari hakan bai ture tunaninta ko sau daya daga ransa ba.
Baisan meye me qarfi da girma haka dake maqale da ita a zuciyarsa ba. Kwanaki ne da suka zame masa cikamakin kwanika masu muhimmanci wajen cika alqawari kan aikinsa. Yayi handling muhammad jinjiri ga ahalin ajani a sirrance bisa sharadin ba zasu bayyana dawowarsa cikin ahalin ba har sai ya kammala nasa aikin......ya rufe file na case din mutuwar ajani,ya miqawa gwamnatin qasar Ethiopia tamim babba tamim qarami da dukka qasurgumayen masu laifin da ake ci dasu cikin haramtaccen gidan villa street da ya salwantar dashi. Abu guda daya ya nema su daga masa qafa suyi masa alfarma shine,gurfanar da zaituna cikin asalin qasarta tushenta,wanda ya buqaci su bashi wasu watanni don komai yazo daidai da yadda ya tsara.
A yanzun aikin da ya yiwa qasar ba wata alfarma da tafi qarfin ayi masa ita.......bama wannan lokacin ba.....tun a bayan,yana da wani irin girma kima da martabar da gaba yake da alfarma kowacce iri ce,ballantana a yanzun. Ya sake samun wani girman na musamman,darajarsa ta sake ninkuwa,hakanan ya sake shiga cikin abubuwa masu tsada da darajar da qasar Ethiopia din ta mallaka.
Ya dauka ya kammala aikin a kwana biyun kawai,saidai ahalin ajani sun dora masa nauyin daya hada da moti na zuwa kebantaccen gurin da moti dinne kawai ya sanshi inda sauran kaso me girma na dukiyar ajani take.
Tafiyar tazo masa da wahala sosai,bai sani ba gajiya jikinsa ya fara yi ko kuwa?. Shi kansa ya sani,a wannan karon yayi aikin daya kamata ya daukarwa kansa da kansa hutu,ya bawa gangar jikinsa dama ta huta sosai. Kwanansu uku a gurin suka kammala komai,aka fidda dukiyar data bawa moti lambar yabo daya iya dauke wannan sirri na tsahon shekarun da amininsa ya buqata. Yawan adadin dukiyar daya gigita kowa,saidai moti ya shaida musu,akwai reshe daya daya rage da ajani ya fadawa wani cikin aminansu.
Sun zabi killace muhammad a tare dasu,ya saba dasu zuwa sanda haisam zai bada umarnin sadashi da dangin mahaifan safeena kakanninsa kenan.
A wannan yammacin da motocin alfarmar da suke zama tambarin prince sheikh muhammad haisam suke tafiya cikin wata irin nutsuwa saman kwaltar......idanunsa can qasa qasa cike da tarin gajiya......idanun da suke zube saman kwalta yana ganin yadda yanayin ya fara juyewa irin yanayin da yakeso......irin yanayin da tsirrai ke wani irin kyau,yanayin da tsirran ke fidda sabbin ganye masu daukan hankali,su kwantar da duk wata qura da ka iya damun dan adam da walwalarsa.
Lafiyayyen agogon fatar da yayi luf saman kyakkyawar fatarsa dake lullube da nu'imtacciyar gargasa ya kalla. Yamma tayi sosai.....amma zuciyarsa yaji tana karkata wani guri na daban a maimakon gida.
Wani guri ya dan danna daga seat din gabansa
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Mu wuce palace training home" Ya furta da wani nutsuwa da jan aji,jan aji da ginshirar data dadu saboda gajiya da kasalar da yakeji. Daga ta cikin abinda ya danna din aka dawo masa da amsa cikin girmamawa,da alama ya tura saqo ne zuwa ga driver din motar.
Maida idanunsa yayi kan kwaltar yana kallonta,kafin a hankali murmushi ya subuce masa,wani tattausan murmushi daya qarawa fuskarsa ajiyayyen kyau.
Ya sani.....kuma jikinsa yana bashi,zaije ya tarar da wani yanayi tabbas saman fuskarta. Abinda ita kanta bata sani ba.....abinda ya jima shi kuma da kara tarsa da kuma lura dashi shine. Ita din wata iri macace me son kulawa.....macace meson a damu da ita,wanda hakan qila ya samo asali ne daga fake love da fake caring na mammina. Wadda ta kadaita a dukkan komai,ta tattara kulawarta da damuwarta a kanta a zahiri ba tare data hadata komai da kowa ba. Ta tashi da wannan yanayin,ta saba dashi,shi yasa komai yake zuwa mata a baqo a duk sanda aka dauke kai daga lamarinta.
Da gaske yayi busy din da dukka wayoyinsa ma basa hannunsa,ya ajiyesu a killataccen guri. Amma behind hakan akwai wani TARKO da yakeso ya d'ana,akwai wani ANALYSIS da yakeso yayi.
Daga ranar da hannuwansa suka kai gangar jikinta,daga ranar da hannuwansa sukakai muhalli da guraben da bai taba zaton zasu je ba.....daga ranar ya tabbatar MUTUWA ce kadai zata iya sanyawa ya zare igiyoyin aurenshi daga kanta,koda mutuwar ma baya tunanin ta isa ta sanyashi yayi hakan. Daga ranar daya qetare iyakar da bai taba qetarewa wata mace ba sai a kanta,....daga ranar daya shiga wani yanayi da babu wata diya mace data taba ganinsa a cikin sa,koda kuwa nanay dinsa......daga wannan ranar ya dasawa kansa MALLAKA......ita din mallakinsa ce.....koda da kallo na idanu zaiyi bakin qoqarin hana kowacce halitta isa gareta ta hanyarsa.
Yana da kishi......yana da kishi sosai ya sani,wannan kishin bazai taba bari ya barwa wani ita ba. Koda baiji mafi girman soyayya a ransa ba.....amma ya raba wani sirri nasa da ita,ta ganshi cikin wani yanayi na fitar hayyaci,shi kuma bazai taba bawa wani d'a namiji hannuwansa sukai kan inda nashi hannun suka kai ba.
Idanunsa ya lumshe yana jin tunaninsa kawai na qarshe kaman an dora masa wuta saman zuciyarsa,sai kawai ya miqa hannu yana sassauta necktie din dake daure a wuyansa cikin lafiyayyar luxury suit din jikinsa da kalarta ta fidda anihin ma'anar kalmar KYAU a tattare dashi,ya maida idanunsa ga hanya sanda suka fada titin da zai sadasu kai tsaye da qofar killataccen gidan.
~Da wannan miskilar fuskartata take zaune birra na qarasa daure mata dogon gashinta a tsakiyar kanta. Fuskarta tayi wani fayau,wani irin ajiyayyen kyau na samun ninkin kulawa da wani sirrantattun abubuwa da batasan amfaninsu ba da suka ratsata. Da farko batasha saboda bai mata kama da abun al'adarta ba,amma daga qarshe zenabu ta zauna ta amintar da ita tasha cikin hikima. Kuma koda tasha din ya mata dadi a baki,ya mata kama da wani abunsha da sukanyi na al'adar buzaye,tun daga ranar bata sake musun sha ba.
A girmame aka nemi izinin shigowa sannan aka turo qofar,bata damu ta waiwaya ba,ta zubawa kanta idanu ta ciki madubi tana kallon yadda shigar kayan sukuwar dokin suka mata kyau.
Qoqarin kokawa takeyi da tunaninta da dukkanin iyakacin qarfinta......qoqarin koyawa kanta rayuwa takeyi dashi ko ya nemeta ko bai nemeta ba,shi yasa yau da yammar nan ta buqaci a shirya mata doki zata hau cikin gidan tayi sukuwa a faffadan filin wasannin ball dake cikin gidan.
Alitash ce,daya daga cikin hadimanta na cikin gidan,wanda sosai takejin dadin zama dasu kamar yadda suke dasu birra. Wasu irin bayi ne data rasa wanne irin horo aka musu haka na iya faranta ran ubangidansu da duk abinda yakeso a sanda ya dace?.
Ko a yau da tace tanason hawan dokin,ta dauka a yadda tsare tsarensu yake zasu hana,amma sai gashi tana cikin bathroom tana wanka suka shaida mata an gama shirya komai.
Zenabu ce kawai taso tadan mata gyara kan shigar da tayi. Wando ne skinny daya kama jikinta sosai,ya fidda kowanne lungu da saqo da tudu na jikinta,kamar yadda fingilalliyar rigar itama ta fidda dukiyar fulaninta kamar ka saka hannu ka cirosu,suka kuma fidda plate tummy dinta kamar bata taba sanya masa abinci ba tunda Allah ya halicceshi,saidai kuma daga baya ta sanya aka yiwa gurin tsarin da daga ita sai hadiman data zaba su shiga harta gama hawan nata,basu kuma sake cewa komai ba.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 50*
"Allah ya qara daukaka darajarki.....an kammala" Ta fada da girmamawa. Tadan juya ta kalli alitash,sai kawai suka burgeta.
"Na gode......"
"Amhara tace ko zaki fara cin wani abu?" Alitash ta fada da kulawa. Kai ta gyada a hankali,ba shakka zata iya bawa hadimai da bayin agadez maki casa'in ta cikashewa wadannan zuwa dari bisa dari. Ta fahimci zataje din,saita miqe suna mara mata baya zuwa parlor din da tafi zama cin abinci.
Falon yana cikin falukanta da tafiso a 'yan kwanakinta cikin gidan. Komai ya kasance da tsarin gargajiyar dake nuna al'adar oromia. Wasu abubuwan nasu suna burgeta,amma yadda ba wanda yace mata komai,ba wanda ya taba mata bayani,itama bata damu ta daga kanta ta tambaya ba.
Kafin ta qaraso sun saita mata takalman da zata sanya ta cire wadanda ta fito dasu a qafarta kamar yadda suka saba,ta zare wadancan ta saka wadanda suka batan,ta fara takawa a nutse tana nufar traditional royal dining table din.
Ta san abinda tafi buqata a yammacin,abinci mara nauyi,koda ta makara bataci abincin rana ba,don haka bata takurata da tambayarta me zataci ba,ta soma serving dinta.
Wani lafiyayyen farfesu ne me romo sosai data lura akhnan din tana matuqar so cikin irin abinciccikansu. Yana tattare da wani sirri sosai a cikinsa,ta zuba mata oromian black tea daya kasance royal black tea ne saboda tsadar ganyayyakin da ake dafashi dasu,ba gidan kowa kake samunsa ba,kamar yadda ba kasafai ake samunsa ba duk da sune suke nomashi,ta saka mata spoon da fork,sannan dukkaninsu suka tattara suka bar mata parlor din saboda sun karanci bata fiyason cin abinci cikin mutane ba.
Tun daga gate din farko da motocinsu suka tsaya aka soma bude dukkanin qofofin gidan da wani iri salo na karramawa da girma. Motocinsa daban suke.....cikin fadin Ethiopia dama qasashen dake maqwabtaka dasu,cikin qanqanin lokaci hadiman dake gidan gaba daya suka zagayeshi cikin marabta ta girma,ya kuma gaisa da kowa cikin mutuntawa da sanin daraja da kimar da Allah ya yiwa dan adam,kafin kowa ya qyaleshi,ya juya ya soma takawa zuwa cikin gidan a nutse.
Duk wani setting room ko parlor da zai wuce cikin matuqar girmakawa hadiman dake gurin suke zubewa su gaidashi,sannan kuna su zare jikinsu su fita don sun tabbatar yau yazo ganin gimbiya ne. Baya da dabi'ar son a zube a gaidashi,amma duk yadda yayi dasu sun gaza dainawa. Sunajin ba zasu iya daina gaidashi ta hakan ba,girma da kimarsa da mutuntakar dake tsakaninsu tafi qarfin su iya gaidashi daga tsaye.