Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 4

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 4

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 4: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 4. "Ina tamim qarami?" Ta jefawa tafisu tambayar tana jin…

3,360 words

"Ina tamim qarami?" Ta jefawa tafisu tambayar tana jin tashin hankalin da bata taba jin irinsa ba a kaf rayuwarta,bacewar tamim a karom farko tun bayan faruwarta taji ya zame mata barazana,irin barazanar nan me wawakeken gibin da ba wani abu da zai cikeshi. Sanda tafisu ta motsa da niyyar cewa wani abu takun da sukaji daga bayansu ya sanyasu waiwayawa gaba dayansu.

Idan akace mata anji qugin da cikinta ya debo tun daga qofar gate na farko na gurin ba zatayi yunqurin qaryatawa ba ko sau daya. Iya abinda take gani cikin fuskar tamim kawai qarami kawai ya gaya mata cewa yau tana fuskantar rana mafi muni cikin rayuwarta.

"Ranki ya dade......gidan villa ya qone......ba alamin burbushin me rai......ba babana.......ba kowa cikin mutanenmu" Ya fadi yana kecewa da wani irin kuka tamkar qaramin yaro.

"Gidan villa?,wanne gida ne a villa din dani kaina bansan dashi ba?" Tafisu ta tambayi kanta da kanta,saidai sanda tayi nufin maida dubanta kan mammina ko zata samu wani haske game da gidan........saita tsinciki miqewar mammina din da wani irin hanzari,miqewar kuma da tayi daidai da debeta da jiri yayi,ba zaton tafisu ba zaton tamim qarami ta tafi luuu gefan fuskarta ya daki kujerar. Banda tafisu tayi zafin naman tareta ba abinda zai hanata ta sake kifawa taci da baka. Cikin tashin hankali tafisu ta riqeta sosai tana kiran sunanta a jejjere hankalinta a matuqar tashe.

Duk da cewa ruhinta dama dukka hankalinta suna shirin yin qaura daga ainihin wannan duniyar da muke ciki amma hakan bai hanata tunawa da makomar abubuwa masu dama data binne cikin gidan ba.

"Tamim babba wanda da bayyanarsa gwara alqiyama ta tashi gaba daya......gwara a tattara a wuce zuwa filin hisabi zaifi mata sauqi......JINJIRI da har yanzu bata gama tsaida matsaya akan rayuwarsa ba......duk tana jagwalgwalawa gami da juya akalar rayuwarsa yadda taga dama.......gudaddun masu laifi daga kurkukun qasar Ethiopia masu tarin yawa.......masu muggan laifin da wasuma an rufe file dinsu da sunan sun mutu. Bakinta take son motsawa ta fadi abubuwa masu yawa da suke zuwa kanta a sannan,duk da ta sani wani binnannen abune da koda tafisu saninsa yayi nisa da tunaninta....... Cikin qanqanin lokaci ta sulale tayi relax sosai a jikin tafisu tana fita daga duniyar da muke ciki zuwa wata duniya ta daban.

Yadda tayi a jikin tafisun ya bawa tafisu tsoro,lamari ne na matar maimartaba gaba daya. Ta tabbatar inda cikin hayyacinta mammina take ko jingina da jikinta ba zatayi ba duk da yadda tayi imanin tana amfanarta ne kawai,dole tsoro ya shigeta,ta kurma ihun kawo dauki,cikin sakannin da basufi qiftawar ido ba gurin ya samu daukin hadiman dake da ikn yin zirga zirga a rea din

*A K H N A N*

Ko kadan bataji wani abuba wai don ta dakatar da mammina daga gurinta ba,hasalima karatun da takeyi sai ya mantar da ita komai da kowa.

Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke sanda ta kammala littafin,ta lumshe idanunta a hankali tana rungume littafin a qirjinta. Ba abinda ke mata yawo akai sai dabi'un ma'aiki masu ban sha'awa da qayatarwa. Dabi'un sanyin hali,kawaici haquri tausayi kyauta da martabawa mutum koda bawa ne. A hankali ta koma kan mu'amalarsa da iyalinsa,bata taba karanta labarin madaukakin mutum wanda bai dauki kansa komai ba a gurin iyalinsa ba irin annabin rahama. Ta saki murmushi kadan sanda ta tuna inda ta karanta,nana aisha tabi sahunsa sanda ya zame jikinsa daga makwancinsa don zuwa ziyara maqabartar baqee'a(yakanje nemawa al'ummarsa da suka rasu sassauci),ta dauka zaije dakin daya daga cikin kishiyoyinta ne,sanda yake dawowa ta dawo da gudu gudu don ta rigashi isowa daki,ta koma ta kwanta luf,saidai yana kallonta da yanayin yadda qirjinta yake dagawa ya fahimci komai,yayi murmushi. Sake murmusawa itama tayi tana shafa lallausar sumar saman kanta da dankwalin yadan zame kadan.

"Kishi?" Ta fada a hankali kamar tana tambayar kanta da kanta. Saita juya idanunta kadan,tana sake tambayar kanta......akan waye zataji irin wanna kishin?,ko akwai lokaci?,ko akwai wani da zata iya jin halittar kishi haka a kansa?.

"Muhammad haisam ne" Kai tsaye taji zuciyarta ta jefa mata amsar. Guri daya ta zubawa ido,tana jin shakka akan hakan.

Wanne matsayi ya taka a ranta da zuciyarta da zataji irin haka a kansa?,DABI'U ta yarda dabi'unsa nargartattu ne......musamman a yanzu data sake karanto daga inda yake koyinsu......suna masa kyau kuma.......ta yarda da haka,suna qara masa wata irin kamala.......amma shike nufin lallai zata soshi.

"Allah ya taimakeki" Taji an fadi daga gefanta. A nutse ta daga idanunta tana duban birra dake rusune daga gefanta.

"Inata magana......amma kin zurfafa a tunani.....ban taba ganin irin wannan zurfin tunanin daga gareki ba......Allah yasa lafiya" Idanu ta zubewa birra din,a tsakanin awannin nan......tsakanin awannin da komai ya wakana zuwa yanzu wasu irin sauye sauye take gani. Basarakiya ce ita.....wadda ta rayu cikin sarauta da mulki,tana iya karantar kowanne motsi hali da dabi'ar abinda ke kewaye da ita idan ya sauya.

Da yawan hadiman dake mata tattaki yayin fita wani guri ko cikin gida idan ka debe su birra basu bane yanzu. Yaushe aka canzasu?,waye yayi canjin ba tare da masaniyarta ba batasan wannan ba.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Yaushe kika koyi bin qwaqwqwafina?" Rusunawa birra tayi sosai.

"Tuba nake.......kawai ina qoqarin kiyaye amanar da sheikh yabar mana ne". Shuru ta sakeyi,kamar kowanne lokaci idan birran ta fadi wani abu daya dangaceshi.

Tafiyar kwana uku yace zaiyi......amma batasan ina zaije ba.....wa ya sani cikin qasarsu?.

"Yaushe kika fara damuwa da abubuwan da basu shefaki ba?" Taji zuciyarta tana mata tambayar data sanya komai nata tsaiwa cak. Siririn tsaki taja......ya akayi take dulmiya kanta a hankali akan lamarinsa?.

"Ki bawa barratu litattafan nan ta wuce dasu.......zamu qarasa sassan morsa safiyya" Ta furta tana jin ya kamata ta amsa kiran nata.

*M O R S A S A F I Y Y A*

Kusan komai ma da yake faruwa cikin gidan a yanzu ba damuwarta bane......kusan duk wani abu dake wanzuwa batajin yana cikin damuwarta. Damuwarta daya ce AKHNAN biftun safeena.......kuma ta tabbatar ta shiga hannun da koda ita daya ta rage a duniya ba zata wulaqanta ba muddin shine mijinta.

Ta kammala komai.......idan akace komai ciki harda rabon lafiyayyen invitation din gayyatar bikin da ta tsara yi na kwana biyu kacal. Bikin da tayi wani irin gayyatar girma da ba wanda yasan plan dinta na hidimar. Kowa ma tanason masa ba zata ne,wani irin bikin na zallar gargajiya da al'ada wanda aka haura shekaru hamsim ba'ayi irinsa ba.

Komai da komai cikin gidan ta tsara za'a yishi ba tare da an fita ko ina ba. Ta gama tanadarwa akhnan komai.......idan akace komai komai da uwa ke tanadarwa d'iyarta da zata aurar auren ma irin auren farko dinnan.

Lokacin da suka tattauna da sultane kuma akan falaak,akan maleek dakeson a yarje masa auren falaak sai taji hawaye yana taruwa cikin idanunta. Wane irin karamci wannan daga ubangijinta?......irin karamcin da bata taba zato ko tunani ba?. Aminin sheikh haisam ta tabbata sheikh haisam dinne,banbancin da zai zama a tsakaninsu d'an qanqani ne.

"Me zamu jira Allah ya taimakeka?.......me zai hana a daura auren ayi hidimar dukka lokaci daya?" Ta fada tana jin nutsuwa da gamsuwa har cikin ruhinta. Ko ba komai ta sani.....aminin haisam komai nasu zai iya zama daya kaman yadda qasarsu take daya.......kasancewar falaak tare da maleek zai zama tamkar kasancewar falaak din da akhnan ne. Wannan kadai zai sassauta zai kuma ragewa akhnan kewar gida......zai kuma sake bata daman tattara hankalinta gami da rage qiyayyar auren a ranta.

Murmushi sultane ya saki yana jin wani farinciki shima......farincikin da ya tabbatar ya haura wanda morsa safiyya keji.

"Da sauri haka safiyya?". Qasa tayi da kanta tana murmushi.

" Ba domin ita ba......sai don jin dadin d'iyata.....saidon diyata taji cewa ba ita kadai bace tabar gida" Murmushi ya sake kubce masa,yana mamakin yadda a komai morsa safiyya ke fifita masalahar akhnan sama data kowa......koda kuwa d'iyan cikinta ne......anya akwai qanwar uwa a zamin nan irinta?.

"Wato harda ke hairaan.......aka hadu aka yiwa diyata fashin miji.......sheikh ta gani takeso......amma kuka mata taron dangi kuka hadata da abokin sheikh?". Murmushi da yafi kama da dariya dukkansu sukayi,morsa safiyya na mamakin yadda yaji zancan. Duk da tasani,shi din aminin 'ya'yansa ne,mulki ko wani abu makamancinsa bai hanashi jan yaransa a jiki ba.

"A duk sanda bawa yabar wani abu saboda girman zatin Allah.........a duk sanda wani bawa yabar wani abu saboda maslahar dan uwansa........saboda danuwansa ya samu.......to lallai Allah zai musanya masa da abinda yafi zama alkhairi" Kai sultane yake jinjinawa. Wannan hankali da nutsuwa ta hairaan ya sanya ko yaushe yake jin kamar daga jikinsa ta fito itama.

"Haka yake.......munyi magana da Muhammad........kuma na samu gamsuwar shida maleek duk daya ne.......a ranar juma'ar nan,iyayen maleek zasu iso daga masarautar gera,inda mahaifin maleek ke sarautar yankin.......abokina bobbo muhammad dawud ya sake bani tabbaci a kansa......ranar juma'ar zai d'aurawa falaak aure da maleek......kwana shida suka rage kacal a yanzu......amma kuma.......inason suma saudiyya ya zamana guri na farko da zasu fara zuwa itama don su nemawa kansu da kansu albarkar aurensu.......zan bude ticket na sheikh da akhnan da qarin kwanaki daban......zan baki dama ki gudanar da bikinki don nasan kina da buqatar hakan......zan hada tafiyarsu tare kwana biyu da gama bikinki". Wasu irin hawaye morsa safiyya taji......wani hawaye me yawa da wani irin d'umi yana bin kuncinta. Ba zatace sultane baida wani alkhairi a tattare da ita ba......ba zatace sultane bai mata kowanne alkhairi ba iya zamansu.......amma dai wannan......wannan damar da wannan abun da yayi mata yana cikin manyan abubuwan da idan zata lissafa zasu kasance cikin sahu da list na gaba gaba.

A ranta takejin dukkanin burikanta sun fara cika.........burikanta burikan safeena......tana jin kamar ta fara cikawa safeena wani sashe na burinta.......idan har ta kammala da wannan........ranta zai zama fansa ne gurin bankado inda AHMED da jaririn safeena na ajani suka bace......koda hakan shine zai zama fansa kuma sanadin ranta.

*Akhnasaim tales*🤍

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 07*

A yanzun da akhnan ke takowa zuwa babban parlor din daya zamana kusan a yanzu morsa ke yini saboda shiryen da suka zame mata linki biyu,na akhnan din dana falaak,falaak din da a gobe juma'a ne zai zamana cikar ranar daurin aurenta da maleek,sai akhnan din ke dubansu tun daga nesa ba tare da sunsan da shigowarta gurin ba.

Cikin tsakiyar suke da wasu irin akwatina da ba zatace ga abinda yake ciki ba. Tarin Invitation da tana iya ganin qyallinsu daga inda take takowa,da wasu suturu a gefe da amintattun hadimanta ke ninkesu suna shiryasu.

Ta maida dubanta kan hairaan da falaak,sai takejin kamar ita daya ce bare a cikinsu. Farinciki ne kwance saman fuskokinsu,hairaan din ta kaiwa falaak duka tana fadin.

"Mara kunyar amarya kawai" Sai falaak ta saki dariya tana boye fuskarta.

Ko alama bata taba kawowa zataso wani a kusa irin son da taji tana yiwa sheikh Muhammad haisam ba,amma daga randa ya zama mallakin bifttunta sai duka ya koma mata kamar bai taba tsugunnawa a wani gurbi na zuciyarta ba.

Komai da morsa safiyya keyi ta saki tana tattara hankalinta akan akhnan. Fuskarta da wani kalan murmushi da taji wani abu ya tsarga mata a yau ta nuna mata gefanta.

"Zauna a nan" Tana zama kuma dukka hadiman dake gurin suka zube suna gaidata da girmamawa. Amsawa daya tayi musu,kowacce ta ajiye aikin hannunta suka jera layi suka fice.

"Barka da warhaka tanti" Falaak ta fadi da muryarta da tayi wani irin wasai kuma tarwai. Kai ya gyada a hankali

"Barka" Ta amsa mata,saita maida idonta kan hairaan.

"Barka da wannan lokaci". Abun ya yiwa kowa dadi,wani abu ne da falaak din bata taba yi ba tsakaninta da hairaan din ba.

"Barka kade qanwata......momma mufa fita zamuyi mu baki guri" Hairaan din ta fada tana miqewa,daidai sanda anwaar ke shigowa parlor din. Akhnan yaketa kallo yana rungume da qatuwar ball dinsa. Tun rabar data bashi wasu chocolate manya shikenan bai manta fuskarta ba,duk da batace masa komai ba batayi magana dashi ba amma shi bai manta ba,saita saki murmushi ta miqa masa hannu,take ya tajo da saurinsa,ta kama hannun nasa tana zaunar dashi saman cinyarta. Kai morsa safiyya ta dauke tana jin wani farinciki yana ratsaya,zuciyarta ta karye kaman kuka zai kubce mata. Sannu a sannu dai Allah yanata jefa soyayyar yaran a zuciyarta,wanda tana da yaqinin zamowa sa zasu yi da falaak a qasa daya zai sake kawo kusanci a tsakaninsu,tunda dukkaninsu basu da kowa basu da wanda yakai junansu.

"Zai bata miki fa wannan kyakkyawan farar doguwar rigar.....yaje sumayya tayi masa wanka" Kai ta girgizawa hairaan alamun ta barshi,saita daga idanunta take kuma suka hada ido da morsa safiyya alamun ita take kallo tun dazun.

"Barka da yamma,kin yini lafiya?" Morsa safiyya ta fada kai tsaye sanda dakin ya dauki shuru bayan kowa ya fice ya barsu.

Karo na farko.......lokaci na farko da taji wani nauyinta ya kamata. Karo na farko da taji kaman hakan bai dace ba..... Murmushi morsa din ta saki,boyayyen murmushi dake fassara farincikin da takeji,ta gama karantar me takeji,kunya da rashin sakewa......yau ita akhnan kejin kunya?,yau ita akhnan ke qin sakewa a gabanta don ita ta fara gaidata?.

"Kada kiji wata kunyata......hakan ba mummunan abu bane.....uwa tana iya gaida diyarta ta kyakkyawan hanyar tambayar lafiyarta irin haka.......yanzu ba wannan ba....." Morsa ta fada tana jawo wani qaramin akwati. Sai data saka hannu ta dauke anwaar tana dubansa.

"Kaje gurin sumayya ta karbi madara" Batama qarasa ba yayi jifa da ball din nasa yana nufar qofa,sai akhnan din ta bishi da kallo har ya bace kafin ta dawo da dubanta ga morsa.

Saman cinyarta ta aza mata akwatin.

"Ina me fatan sauke wannan nauyin da amanar dake wuyana shekara da shekaru....." Morsa ta fada muryarta tana rawa.

Haka kawai tunda ta kalli akwatin taji ta dokanta ta budeta,bawai don kyanta ba,aah hasalima kana kallonta kasan tsohuwar akwati ce. Ta danyi kiciniya kadan da ita sannan ta gano gurin budeta ta bude,don daga maganan farko morsa safiyya bata iya sake cewa komai ba,hasalima hawaye take daukewa a dabarance da tissue din hannunta.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Bracelet ne na danyan gold......(dan uwan wannan bracelet din dake hannun mammina da haisam ya sauya mata da fake dinsa). Abun wuya da dan kunnaye da sauran kayan tarkacen kwalliya na gold data tabbatar na mahaifiyarta ne,don koda ba'a gaya mata ba tasan tsohon gold ne don dukka tsaffin design aka masa. Haka ta dinga fita dasu daga qarshe kuma taci karo da wata takarda da littafi.

Littafi ne na addu'o me shafuka kusan hamsin,wanda aka rubuta da yaruka uku,oromo da yaren Tuareg wato yarensu na buzaye sai yaren larabci da shine asalin rubutun. Ta sauka zuwa ga mawallafin sai sunan safeena din baro baro ya bayyana. Mamaki ya sanyata daga kai kadan ta kalli morsa safiyya,alamun tambayoyine fal cikin idanunta.

"Mahaifiyarki macace me Tarin ilimin addini.....ilimin addinin daya zame mata jagora gurin karbar dukka qaddarar rayuwarta.......wannan littafin shine abu na qarshe data wallafa sanda ya rage mata kwana casa'in kacal tabar duniya". Wani nauyi ya sauka a zuciyar akhnan,ta aza idanunta akan takardar dake da gajeran rubutu cikin yaren Tuareg.

_Wadannan sune kadai abinda na mallaka yake 'yata,kuma sune abinda nabar miki,ina fata su isa gareka sanda kike shirin tafiya dakin mijinki.......ZAMANKI MACE TA GARI SHINE CIKAR BURIN RUHINA da salamar gangar jikina_. Damqe takardun tayi a hannunta tanajin hawaye yanason taruwa cikin idanunta.

"Alfarma nakeso kiyimin......ki kafa tarihin zama kusa da safiyya......ki kafa tarihin kin rayu cikin gidan safiyya koda na iya kwanakin nan ne......inason ki qarasa kwanakin a nan sashe na cikin 'yan uwanki,hairaan da falaak da zata amsa sunan matar aure juma'ar nan itama......wannan ta zama alfarma guda daya da zan dinga tunawa da cewa kinyimin ita a rayuwarki". Idanunta dukka ta bude a hankali tana duban morsa safiyya,idanunta da a yau sai take ganin suna hango wani abu daban da dukka shekarun baya bata taba ganinsu a fuska da idanun morsa safiyya din ba. Ta yaya ma zata iya cewa a'ah.....matar data sake kusantata da wani abu daya shafi mahaifiyarta?.

★★★

"Bansan wacce irin sa'a ce dakai ba har da mukayi nasarar samun hayyacinta ka tatsi dukka wadannan bayanan daga gareta ba" Dr na'eem ya fadi yana share gumin goshinsa da qaramin lallausan handkerchief na towel din dake hannunsa. Kujera yaja ya zauna,ya sake daga idanunsa yana duban haisam dake tsaye qiqam gaban gadon da yalwa ke kwance akai kamar sojan da aka bugawa kugen yaqi. Gadon da a dazu ya dinga jijjiga da jijjigar da gangar jikin yalwa keyi.

"Sun riga sun ciyar da ita wani abu da zai dinga kashe mata organs dinta,kowacce rana zatayita mutuwa ne ba tare da tasan mutuwa takeyi ba.......idan da ta dauki wani lokaci a haka,za'a je ne kawai a tsinci gawarta ba tare da ansan meye yayi ajalinta ba" Dr na'eem ya qarasa bayanin yana bude gorar ruwa yakai bakinsa.

Da wannan nutsuwar tasa dai ya sauke dukka hannuwansa biyu qasa. Da wannan nutsuwar tasa yayi tattaki ya jawo kujera ya zauna,da wannan zaman nasa dake nuna izzar mulkinsa.

A dukka bayanan daya qarqare samunsu......ya fahimci wasan da mammina tayi da hankula masu tarin yawa.....ciki kuwa harda hankulansu yalwa din. A iya saninsu da abinda suke iya gani,a iya mu'amalar da takeyi dasu suna zaton sune na gaba gaba abokan sirrinta,tunda sune sukafi kusanci da ita,saidai wani abu da basu sani ba......wadannan wulaqantattun bayin......wadannan hadiman da ko kusa da ita basu isa suzo ba sune mafi kusanci da ita. Ya gane hakanne bayan ya qwamushe mutumin dake kula da duk wani kwandunan shara na sassan nata,ya wankesu bayan an yasar da sharar,ya kuma maidasu muhallinsu.

Miqewa dr na'eem yayi,suka bawa juna hannu shida haisam kafin su rankaya tare da haisam din su fice suna sake tattaunawa.

Tafiya me dan tazara sukayi kafin su kawo ainihin muhallin ajiyar motoci inda Dr na'eem yayi parking motarsa,ya bude ya shiga sukayi sallama,sannan shima yayi taku biyu baya yana duba agogon hannunsa.

Juma'a ce......juma'ar daya kamata ace yana masallacin masarauta......ya samu jam'i kamar yadda ya saba. Juma'ar ita ya tsara zai koma masarauta.....juma'ar a ita ya lissafa aikinsa ya kammala. Eh aikinsa ya kammala.....saidai yanason budewa mammina qofa daya tal cikin tarin dubban qofofinta daya bude kowacce ya zare maqullin kuma ya yasar........don haka yana buqayar ranar LAHADI.

A ranar lahadin ta sace Ahmad din ta rabashi da tsatsonsa ta kuma batar dashi......a wannan ranar.....a daidai lokacin yakeso ya maido mata da saqonta.

"Zamu iya tafiya?" Salana ya tambayi haisam cikin girmamawa. Dauke idanunsa yayi daga kan agogon,bayan ya duba lokaci harda kwanan wata ya duba yana lissafin watannin daya share a agadez......yana lissafa watannin daya diba baiga nanay dinsa ba.

Yana kewarta.....yana tsananin kewarta sosai,wannan aikin na kwanakin nan daya sakashi a gaba ma ya sanya ko waya basuyi ba kwata kwata,saidai time to time yana ganin saqonnin noorah rumaisa da Anaani,musamman noorah dimma,kamar ita da taufeeq sunfi damuwa da nisan da yayi dasu,duk da yasan kowa a cikinsu ma hakan ya keji,sun fisu dauriyar boyewa ne kawai.

"Su khadeem fa?" Ya tambayi salana a nutse.

"Yau daurin aure,dukkaninsu suna cikin agadez......sunce na barka ka kammala uzurinka".

"Ya salam" Ya furta yana nutsa yatsunsa cikin sassalkan gashinsa.

Bai taba hango daurin auren maleek ba babu shi a gurin......bai taba hango maleek zaiyi aure bai halacci daurin auren ba.

Wayarsa ya soma laluba,me yasa zasu masa haka?,suce kada a tuna masa?. Duk yadda aikin yake da muhimmanci nasu muhimmancin na dabanne,bayajin akwai wani abu da zai shiga cikin wannan alaqar......ya kuma tabbatar kowa da kowa cikin team 7 din yaje banda shi.

Bai kira maleek kai tsaye ba,don bayason raba masa hankali a irin yanayin nan daya tabbatar zumudi ne fal cikin maleek,sai ya kira omar

*Akhnasaim tales*🤍

Readers Also Read

More by Huguma