L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 3
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 3: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 3. "Wanne littafi kike buqata ranki ya dade?" Mai hidimar…
3,347 words
"Wanne littafi kike buqata ranki ya dade?" Mai hidimar kula da dakin karatun ya tambaya cikin girmamawa. Cikin izzar nan tata ta numfasa kadan. Me zata ce masa tana buqata?,littafin da zai nuna mata inda sheikh muhammad haisam ke kwaikwayon dabi'unsa?,ko kuma zatace masa tana sha'awar karanta halaye da dabi'u manzo saboda yawaitar jin abubuwa daga bakin haisam?,ko kuma dai dukka a ture wannan.....dabi'un wani d'a namiji takeson haskawa da kyau cikin kanta.....d'a namiji......malamin addini....wanda ya karya komai da komai nata......ya rushe duk wani tsari nata da komai?.
"Tarihin rayuwar manzon Allah.......rayuwarsa da mu'amalarsa da kowa" Tayi maganan kaman wadda ta zabi jera kalaman kafin ta furtasu.
"An gama" Ya fadi yana juyawa da dan hanzarinsa zuwa inda tarin litattafan ke ajiye jimgim amma a tsare kwaba bayan kwaba.
Zamanta ta gyara sosai tana harde hannuwanta a qirjinta. A nutse da kuma wannan blue eyes din nata takebin dakin gaba daya da kallo. A hankali sai taji yadda littattafai suka cika dakin da wani irin tsari abun yana burgeta. Ba zatace ga abinda akeji a karance karance ba,idan ka dauke karatun daya wuce na magazines da newspaper da zataga sauka da tashin hannuwan jari ba.
"Ga wadannan Allah ya taimakeki" Ya furta yana ajiye mata books din a gabanta.
"Sunyi?" Ya tambayeta yana fatan zabin nasa ya burgeta.
"Kana iya tafiya,ka shaidawa birra ta zama a kusa" Ta fadi tana aza kyawawan blue eyes dinta saman cover din littafin farko.
"Le prophéte de I'Islam,sa vie d'aprés les sources les plus anciennes" Sunan marubucin ta duba
"Martin lings" Saita sauke zuwa littafi na biyu.
"Muhammad viedu prophéte" Ta sake duba author din.
"Taariq ramadan" Ta sake zameshi qasa tana duba na uku.
"La Vie du prophéte muhammad na ibn kathir" Guda daya ta zame a ciki,ta ajiyeshi gefe sannan ta gyara zamanta sosai ta fara duba wallafar taariq ramadan.
A nutse takebin littafin da aka wallafashi da yarenta na faransa,cikin qasa da mintuna ashirin tarihin ya fara shiga jikinta sosai. Komai na cikin tarihin ya soma daukan hankalinta,a hankali ta soma jin wani girma da karramawa na musamman da kima na manzo yana shigarta.
Sam sam komai da takeji cikin tarihinsa da mu'amalarsa bata taba saninsu ba,bata taba sanin da akwaisu ba. To yaushe ma ta zauna tayi wani karatu daya shafi wannan bangaren ballantana taci karo dashi?.
Batasan lokaci yaja haka ba,saida taji sallamar birra tana neman iznin qarasowa inda take zaune.
Ajiyar zuciya ta saki,tana zare idanunta daga kan littafin da takejin ba zata iya tashi a wajen ba saita kammalashi duk da yawansa,ta dora kan birra.
Tsaye birran take dauke da tea tray daya bawa cups da kayan saman kai daman zama sosai a samansa,wani irin tea tray da koda tsautsayi yasa wani abu ya zube bazai zuba a qasa ba ko a jikin me amfani dashi ba,wani abu dake maqale daga qasansa ya tare wannan.
Idanu ta zuba mata ba tare da tace komai ba,yayin da birra din ke dubanta da girmamawa
"Allah yasa ban katsekk ba......na kawo miki wani abune,bansan ko zaki buqata ba" Kanta ta daga mata a hankali da sign din daya bawa birra daman fahimtar tana nufin ta qaraso ne. Saita tako a hankali tana ajiye tray din saman table din da akhnan ta ajiye hannuwanta akai.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Fidda butar shayi daya da cup tayi tana qoqarin zubawa akhnan shayin,saidai kuma muryoyin da suke jiyowa daga wajen library din ya dauki hankulansu gaba dayansu.
*MAMMINA* Dukkanin idanuwanta ta zubewa hadimim tana kallonsa,kallo iri daya amma mai dauke da tarin ma'anoni da mamaki zallarsa.
Wayeshi cikin hadimai?,batasan fuskarsa ba sam........abu mafi muni da firgitarwa ita GIWA ita GIWAR AGADEZ?......GIWAR SULTANE?......yau ita akewa iyaka da shiga wani sashe na masarautar agadez?. Cikin yaye yayen Mafarki ne?,ko kuma zahiri ne idani biyu take?.
Wanne irin lalacewa tayi da har wani wulaqantaccen hadimi zai tsaya gabanta?,zai tsaya gabanta yana gaya mata.....yana bata labarin wani qasqantaccen malami dake ci qarqashin ALFARMARSU ya hana kowa zuwa gurin da akhnan din ke zaune har sai ta tashi?,ya hana kusantar inda take?. Akhnan din data raineta a tsakanin hannuwanta irin rainon da taga dama?. Akhnan din da ita keda alhakin yankewa komai da kuma sarrafawa cikin rayuwarta?,akhnan din da sai wanda taso ta girmama zata girmama?,sai wanda taso ta mutunta zata mutunta?,sai wanda ta lamuncewa sannan zatayi mu'amala dashi?.
"A kiramin me wada" Ta fada da wani irin zafi da mamakin da har yanzu kanta ya gaza daukan itace yau a tokare a hanya,an hanata qarasawa zuwa ga akhnan.
"Ranki ya dade.....koda me wada yazo ba abinda zai iya canzawa" Ya fada a tausashe yana qoqarin bata girmanta gami da rusunar da kansa qasa.
"Wanene kai!.....nace waye kai don ubanka?,waye ya tsaya maka?" Tayi maganan da hargagin daya zama sanadin isar tarwatsin ga kunnuwan akhnan da birra dake cikin dakin karatun.
"Gaba salamun baya salamun....Allah ya huci ranki,kibi komai a hankali karki tarwatsin da zai janyo hankulan wadanda basusan ma me yake faruwa ba.......yaduwar labarin kamar raguwar darajarki ne a idanun kowa". Tafisu ta fada da murya qasa qasa.
Waiwayowa tayi tana zubewa tafisu wani irin kallo,yadda tafisun tayi mata magana saiya mata kama da wanda ke mata gatse......sao takejin kamar akwai wani sauti cikin muryar tafisu,to amma kuma can cikin kalamanta akwai GASKIYA,ba zataso kowa yasan wannan tozarcin ba sam sam,don haka ta maida dubanta ga hadimin,saidai kafin tace wani abu me wada ya qaraso.
"Yaushe ni giwa na zama wulaqantacciyar da ganin d'iyata ma saida izinin wani maras darajan malami?" Maganan ta yiwa me wada zurfi da yawa,to amma ya sani,a halin da ake ciki yanzun ko sultane bazai zame mata tsanin da zataga akhnan kai tsaye ba yarjewar haisam ba.
"Kiyi haquri Allah ya baki yawan rai......ba wata hanya ta tayar da maganar sheikh muhammad haisam a cikin gidan nan" Idanu ta zubawa me wada cikin madaukakin mamaki,yaushe abubuwa suka girmama haka ita zaituna tana zaune?,yaushe zamanin da bawa da hadimai dama baqi zasu iya jayayya da umarninta gami da tayar da hukuncinta?.
"Karkice zakici gaba da jayayya dasu,ba tsaranki bane giwa......abu daya ya rage,kin isa da gimbiya,kisa a shaida mata zaki shigo gurinta,koda basuso idan ta aminta da haka dole su baki dama".
"SU BAKI DAMA" maganar ta maimaitu cikin kanta ta kuma sanyata hadi wani abu me tauri cikin maqoshinta. Yau ita ke neman DAMA cikin masarautar?,damar da ita ke rarrabata ga wanda takeso?,ta kuma karbeta daga hannun duk wanda hakan yayi mata?.
"Ku shaida mata inason ganawa da ita" Tayi maganan tana jim alwashin cewa.......yadda ya soma da qoqarin maidata maqasqanciya bayan ya fara karbe ikon zartarwa da fada aji daga hannunta......lallai ba shakka saita sanya ya dandani radadin tozarci......saita sakashi yabar agadez a mafi qasqancin halitta......barin da bazai sake koda marmarin rubuta sunan yankin ba ballantana ya kalla ko yayi mararin shigarsa.
Bai musa ba,ya kuwa aika daya daga cikin masu tsaron gurin. Daidai lokacin da akhnan din ta maida labulen ta rufe... Labulen daya zama iyaka tsakaninta da gano fuskar mammina.
Haka kawai takejin ta fice fit daga rayuwarta,haka kawao takejin bata buqatar karbar hanyar rayuwa daga hannun kowa.....haka kawai takejin bata buqatar shawarwari masu dogon sharhi ko fashin baqi......haka kawai takejin ta jefata rami ta goga mata tabon da har ta tsufa bazai shafe daga rayuwarta ba. Saki....sakinma irin na wulaqanci......sakin aure cikin kwanaki uku kacal da daura auren?.
"Bana buqatar ganawa da kowa a yanzun......ina da abubuwa masu muhimmanci da nakeyi" Abinda ta fadawa birra kenan,ita kuma birra ta juya ta isar masa da saqon......shi kuma ya juya yana shaidawa zaituna bisa tarin qwarin zuciya da sauyin dabi'u da aka musu na FADIN GASKIYA YADDA TAKE daga rainon sheikh Muhammad haisam.
Tamkar gunki haka ta tsaya a gurin cak,idanunta suna qanqancewa zuwa ciki ciki,tana jin wani tarin qasqanci da tozarci yana baibayeta.
*Akhnasaim tales*🤍
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 05*
Lokaci na farko mahaukaciyar tsanar da takewa yarinyar ta taso mata. Karom farko da wannan tsumammiyar tsanar ta yunquro daga muhallin da taketa ajiyarta ta kafa sabbin rassa da sansani......saidai wani qaqqarfan sashe na zuciyarta yana sake jaddada mata.
"BA YANZU BA......DA SAURAN LOKACI" Da gaske ne......ta yadda da sauran lokaci......don ba zata taba yadda yarinyar taci bulus ba.......FANSAR SAFEENA da kuma rainon data yiwa MAQIYIYA na wadannan shekaru dukka saita fanshe......komai runtsi,komai tsanani......kuma komai wahala.
"Basai kin biyo ni ba" Tace da tafisu kai tsaye tana juyawa zuwa hanyar da zata sadata da sassan sultane.
A nutse ta shanye tea din da takejin d'an d'anonsa ya canza sama da wanda ta saba sha. Ya mata wani irin dadi da har sai datace da birra dake shirin juyawa ta bata guri.
"Wanne irin kaya kukayi amfani dashi a coffee dinnan?" Murmushi kadan birra ta sauke,sannan ta rusunar da idanunta.
"Yaukam bazan iya amsa tambayarki ba.....saboda komai ya fito daga hannun sheikh muhammad ne,yasa an kwashe komai an zuba nasa,bansan sunan coffee din ba". Shuru ta danyi kadan tana kuma karantar yanayin birra qasa qasa.
"Shugaba ne.....me kulawa da dukka wani nauyin dake kansa" Wata zuciyar ta rada mata maganar.
"Amma hakan shine tabbacin ya cancanci samun kusanci da zuciyarki da rayuwarki?" Ta yiwa kanta tambayar da amsarta ta tsaya cak cikin iska tana lilo.
Tana jin ficewa birra,a hankali ta bude littafin tana ci gaba da karantawa,wanda dukkan wani sakin layi da zatazo sai ya aje mata points da abubuwa masu tarin yawa.
*_S U L T A N E_*
Cikin kasala ya sauke numfashi cikin qawataccen dakin hutawar tasa,ya lumshe idanunsa sannan ya budesu duka lokaci guda. Ya rasa dalilin daya sanya yakejin irin wannan kasalar me qarfin gaske haka a jikinsa cikin satin gaba daya. Kamar dai yanzu,fita yakeso yayi,yana da zaman fada da kuma tattaunawa da wazeer dama yayan kakan morsa safiyya akan auren falaak da yace masa anje nema ta hannunsa,amma tunda ya kammala cin abincin rana komai yayi masa nauyi.
A nutse ya daga kansa da fuskarsa dake kwance da mamakin wanda ya fado masa daki haka,ba neman iso ko izini,mamakinsa ya sake fadada sanda idanunsa suka sauka akan fuskar zaituna.
Cikin qarfin hali ya tashi daga kashingidar da yayi ya zauna sosai yana dubanta,kallon da yake matan ya sanya gargadi me qarfin gaske qwacewa zuwa gareta.
Kuka kawai ta saki,kukan da take da tabbacin yana da tasiri matuqa ga sultane din,kukan data tabbatar yana daya daga cikin abinda ke saurin karya mata shi.
"Subhanallah......zaituna....ke da kanki?" Ya fadi yana daga mata hannu yana kiranta cike da mamakin abinda ya sanyata kuka.
Batayi qasa a gwiwa ba ta qaraso gabansa tana zubewa,hannunta saman fuskarta kaman qaramar yarinyar tana danne hawayen dake zuba mata.
Wannan hawayen ba fake bane......wannan hawayen bana qarya bane,hawaye ne na gaske,baqinciki da d'acin da taji a sanda ake shaida mata Akhnan bata da lokacin ganinta da saurararta da kuma ganawa da ita......shi ya cushe mata mafitar numfashinta.
"Bansan bani da kima daraja ko martaba ba sai yanxu......bansan cewa bankai naci darajar kasancewata matarka ba......bansan wanne tozarci aka shiryayimin ba ba tare da kunya da kuma tuna cewa ni dimma UWA ce ba koda ban haifa ba.....ni din MATARKA ce ba sai a yau" Ta fada tana sake narkewa da kuka. Ba bakinsa kawai ba,shi idanunsa ma a yanzu nauyinsu yakeji,baida wani sauran energy da zai dogon jayayya ko magana da zaituna. Ya sani wasu lokutan tana da rigimar da bata da tushe,don haka ko a yanzu sai yayi saving energy dinsa ya zuba mata idanu yana jiran ta bashi cikakken bayanin abinda ya faru daya sanyata zubda hawaye haka kamar qaramar yarinya.
"Yanzu lalacewata da tozartar da aka shirya yimin har takai ni da kaina saina nemi izinin ganin biftu?,har takai bani da ikon ganinta?" Ta fada tana nuna kanta da yatsarta wasu sabbin hawayen suna zuba mata.
Da zaki daina kukan da nafi fahimtarki zaituna" Sultane ya fadi yana jin yadda qafafunsa da hannayensa suke sake yin sanyi.
Ta fahimci da gaske fuskantarta yakeson yi din,kuma tana fatan fahimtar tasa ta zame.mata tsani da zata soma girgiza iko da isar da sheikh muhammad yake hangen ya samu. Gyara zama tayi sosai gabansa,saidai har yanzu bata har hawaye ba,duk da yadda takejin zazzabin dake jikinta yana shirin dawo mata.
"Naje da zummae duba lafiyar akhnan cikin dakin karatunka......amma hadiman da aka sauya dake kula da muhimman sashe dama biftu suka gayamin sheikh haisam bai bada wannan damar ga kowa ba sai mutum biyu......ashe bana cikin mutane masu muhimmancin da sune zasu fadi wadanda ke da ikon ganin biftu ma bawai iya kadai ganinta ba?" Ta fadi muryarta tana rawa sosai.
Idanu sosai sultane ya zuba mata,yana kallon yadda take hawaye daya bayan daya. Baice da ita komai ba,sai daya bata tazarar lokaci sannan ya sake daidaita zamansa.
"Zaituna" Ya kirata dakasalalliyar murya da kasalar da yake jinta har jininsa.
"A yau a kuma yanzu haisam ya fimu iko da biftu.......a musulunce haisam yana da ikon iyakance adadin mutanen da yakeso biftu tayi hulda dasu suma suyi hulda da ita.....bai sabawa addini ba......"
"Hardani uwarta?.yatsa ni uwarta dana raineta?" Tayi tambayar cike da zallar mamaki tana nuna kanta da yatsa.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Koda ni da nake mahaifinta a yanzu ya fini iko da ita" Sultane ya fada cikin nutsatsen muryar nan tasa mai cike da kamala. Saidai maimakon kamalar ta sanyata fahimtar ainihin gaskiyar maganar sultane......sai maganan ya zame mata tamkar wani baqar magana ce daban sultane yake gaya mata.
"Kanason gayamin ni ba mahaifiyarta bace ta asali?,kanaso ka tunamin abinda na riga dana sanshi?.......burin morsa safiyya na dab da cika kenan?" Ta fada cikin yanayin son tada hankali,domin kuwa dama take nema....qofa take nema da zata ja hankalin sultane ya rusa wannan tsarin,ta kuma samu daman isa ga akhnan kaman yadda ta saba don ida ginin tsari da manufarta. Shuru sultane din yayi yana dubanta jikinsa na sake mutuwa da kasala,shurun da yayi ya bata daman gama fadin abinda take da niyyar fada sannan ya soma magana a nutse
"Jahiltar maganata bazai qareki da komai ba zaituna sai bacin rai.....da kyakkyawar niyya da manufa me kyau ya kamata ki kalli maganata.......ina miki bayanin nan ne badon na amintar dake ba,sai don na baki haske. A irin abinda akhnan ta fuskanta..........farmaki daga mutum mafi kusanci da aminci daga cikin masarautar mahaifinta......bazai zama abun mamaki ba don mijinta ya killaceta daga kowa ciki harda ke,ba kuma da manufar yana tuhumarki bane ko zarginki.......aah.....qilan yayi hakanne don ya sama mata nutsuwa da dawowa hayyacinta daga firgicin data fada" Ya qarasa maganar yana nazarinta. Shuru tayi,shurun kuma da bai masa kama da shurun wanda ya gamsu da maganar da aka gaya masa ba.
"Me ya tashi hankalinki haka zaituna?" Sultane ya samu kansa da qare mata kallo gami da jefa mata tambayar,tambayar data zowa mammina da wani irin bazata,bazatar data sanyata daga kanta da sauri ta kalleshi,sai kuma ta buge da sharar qwalla.
"Abubuwa da yawa sultane,ina tsoron kada a gina qauracewa juna tsakanin ni da ita.....diyatace......ina jinta a matsayin diyar da ni Allah bai bani ba,sai ya wanken zuciya.......ya kuma bani madadi da biftu din". Kai ya gyada a hankali.
"Inde hakanne ki kwantar da hankalinki,akhnan zata cimmaki har sassanki ba tare da kin daga hankalinki ba"
Kai take kadawa a hankali,yadda take kada kan a zahiri zaka dauka ta gamsu ne,zaka sauka fahimta tayi,saidai abinda yake zuciyarta......abinda ke cikin SAQAR RANTA daban yake da abinda kai kake hangowa.
"Na fahimta,Allah ya saka da alkhairi" Kawai ta fadi,ta kuma zabi ta miqe.
Idanunsa ya lumshe yana furta.
"Madalla" Ba tare daya iya dubanta da kyau ba saboda yadda jikinsa yake sakeyin rauni.
"Lokaci yayi......abubuwa sunata tabarbarewa.......abubuwa suna sake lalacewa........lokaci yayi sultane..........ya kamata na samu sarari......ya kamata komai ya qare" Abinda take fada kenan cikin ranta. Tana jin zuwa yanzu ya kamata yasan makomarsa shima.......tana jin zuwa yanzu tayi shekarun da ba wani d'a namiji data taba yi dashi.....komai izzarsa.....komai kudinsa.....kuma komai sarautarsa.......tana jin an kawo gaba.....an kuma kawo gargarar da shima ya kamata ya soma fuskantar makomarsa.
"Me kika yanke?,wane mataki kike nufin dauka akan wannan abun?" Tafisu dake biye da ita a baya ta fadi qasa qasa hankalinta gaba daya yana kan mammina.
Wani murmushi tayi,bawai don ta daina jin dacin abun a bakinta da zuciyarta ba.....bawai don abun ya bata farinciki ba,aah......saidon ta tabbatar ita zaituna tafi qarfin kasancewa cikin qasqantaccen yanayi irin wannan jar abada.
"Lokaci yayi tafisu da sultane shima zai d'an d'ani WACE ZAITUNA kamar yadda sauran na baya wuka dandana......ya isa haka,na masa kara da yawa tafisu,lokacina ne yanzun tunda har ya fara aza matsayi da isar wasu gaba da tawa". Wani irin shuru me kaifi ya gifta kafin tafisu tace.
"Me kenan ranki ya dade....?"
"Ya kamata sultane ya kwanta.....ya kwanta ya huta,ya kwanta kwanciyar da zata zarce dashi har makwancin nasa na gaskiya". Maganar saita qare da wani irin shuru me wani irin kaifin gaske,tafisu ta motsa bakinta zatayi magana,amma sautin muryar hadiman dake zaune cikin wata rumfar da aka katange da bamboo wood ya ratso har inda suke.
"A villa road ne.......nima dana taho daga kasuwa tun daga nesa na hangi hayaqi"
"Kai kaga wutar da takeci kuwa?......me martaba bai sani ba,an jima ba'ayi mummunar gobara irin wannan ba a agadez,kuma abun mamakin gida daya ne yakeci da wutar"
"Wutar nan anya haka kawai ta sauka?,lokaci guda gidan ya koma kamar burbusashen biscuit?" Dayan ya sake fadi.
*Akhnasaim tales*🤍
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 06*
Wata irin mummunar faduwa gabanta yayi,a hankali sai yanayin karsashin da take da yadda take daga qafafunta sukayi low a hankali. A haka ta qaraso dab da karan bamboo din,ta dakata da wani irin sanyi,sannan ta daga idanunta tana duban tafisu.
"Kina jin abinda suke cewa?" Tayi tambayar kamar wadda keda hope kan tafisu tace mata bataji komai ba.
"Kaman villa road ranki ya dade........"
"Nan ne......jikina yana bani wani abu tafisu.......maza kiyimin magana dasu" Ta fada tana jin qafafunta kamar ba zasu iya daukarta ba,don haka ta sauqaqawa kanta,ta sulale ta zauna saman concrete chair din dake girke a gurin.
A razane da jin kira daga gurin giwa suka iso,suka zube dukkaninsu kansu a qasa,zuciyoyinsu kamar zasu tsinke da fatan ba wani laifi suka aikata ba.
"Ku bani labari.....me yake faruwa a villa road?" Tayi tambayar a sabule duk da tana qoqarin tattala qwarin gwiwarta.
"Gobara ce.......mafi munin gobarar da aka dauki shekaru ba'ayi irinta ba......"
"Ina buqatar ganin video din gurin don asan yadda za'a tari komai da biyan diyyan asara" Ta fada tana jin wani gumi yana yanko mata,can qasan zuciyarta tana sake tsananta takatatsantsan a dukka maganarta,kada ta furta wani abu da zai tona binnnan sirrinta.
"Yanzun in sha Allahu zamu cika umarninki uwar gijiyarmu". Sanda suka tashi suna barin gurin bayansu tabi da kallo,tana jin kamar taje tare dasu ta gani. Gidan nan ne ya cinye da wuta kamar yadda zuciyarta ke raya mata?.....gidan nan ne daya qunshi babban sirrin da bata dashi a duniya gaba daya kamar yadda jikinta da zuciyarta suke bata?,ko kuwa hasashe ne kawai na zuciya.