L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 2
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 2: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 2. Yatsunsa ya murxa kadan,baisan me zaice da bobbo da zai…
3,362 words
Yatsunsa ya murxa kadan,baisan me zaice da bobbo da zai gane.....baisan da wanne yare zaiwa bobbo bayani ba,bashi kadai ba harda su omar. Abu daya ya sani wani qatoton abune yake a tsaye a wuyansa a yanzu haka idan ya tuna shirin mammina mafi muni,shirin halasta haram tsakanin muharraman da tafi kowa sanin girma da nisan haramcin dake tsakanin AHMED da KHADEEJA.
"Akwai sauran bayanai" Bobbo ya fadi kansa tsaye yana duban haisam. Sai a sannan haisam din ya dawo da dubansa ga fuskar bobbo din,ya gyara zamansa da yanayin zamannan dake cike da qasaita wanda ya zame masa jiki,ko a office ko a taro koma a inane,wanda yawancin lokuta baimasan yana yinsa ba.
"Akwai" Ya amsawa bobbo a nutse da muryar nan tasa da nutsuwa kewa ado koda yaushe.
"Ina saurare" Bobbo ya fada shima yana tattarawa haisam dukka nutsuwarsa.
"Asalin sunan ZEENATU ne.....zaituna sunan aminiyarta data salwantar da ita ne bayan ta tabbatar a duniya itace kadai ta rage halittar datasan kaf sirrikanta.....ta taho da jaririn ajaani xuwa niger.......ta kuma dauki jinin sultane muhammad hammud ta maidashi tantirin dan shaye shaye bayan ta bayar da kyautarsa ga magajiyar karuwai.....kyautar da an shiryata ne da nufin za'a waiwayeta bayan wasu shekaru saboda cika wasu munanan qudure qudure da muradi na hada haramtaccen aure tsakanin 'yan uwan da aure tsakaninsu ya haramta har gaban abada.......khadeeja diyar sultane......da ahmed babban d'an sultane daya kamata ace yana rayuwa a fada yanzu kaman sarki,.......wanda ya kamata ya karbi sunan MAGAJIN SULTANE a yanzu haka" Ya qarashe maganan yana jin wani d'aci yana ratsashi tun daga zuciyarsa har izuwa harshensa.
Shuru ya sake wanzuwa,girma bayanan da haisam yaci gaba da bashi yana ratsa bobbo. Girman rashin imani.....zallar zalunci da BAQAR SHUKAR zaituna yana ratsa zuciyar abbo din.
"Lokaci yayi muhammad.....a yanzu ka lalata komai,ka kuma bata dukkan wani shaida makama ko hujja tata,......ka saare dukkan wani qarfi da takejin tana dashi,na baka dama a kanta a yanzu" Bobbo muhammad dawud ya fada shima yana jin wani irin abu me nauyi yana sake sauka a zuciyarsa.
Wani kalar murmushi ne ya subucewa haisam din yana murza tafin hannunsa da yatsunsa,wani kalan murmushi da baida alaqa da jin dadi ko walwala ko kadan.
"Taci bulus kenan bobbo" Ya furta calmly,saidai wutar dake ruruwa me girma ce.
"Zunubin zama a qasar AGADEZ,cakuduwa da mutane masu aminci,da kuma ha'intarsu kadai....iya wannan zunubin yafi qarfin a kama zaituna cikin girma......dole ta rasa wannan GIRMAN data dade tana tattalinsa.......dole kuma ta zama mutum ta farko da zata fara tonawa kanta da kanta asiri........inaso a gaban idanunta AHMED ya zama magajin sultane....... Inaso akan idanunta abinda take jayayyar hukuncin Allah a kansa ya faru alhalin bata da yadda zatayi....."
"Sultane fa?" Bobbo ya fadi yana duban tsakiyar idanun haisam,yana kuma karantar zurfin bacin ransa.
"Za'a yi komai yana nan......saidai zai dan kwanta ya huta da kalar hutun da zai zame masa sassauqa.....hutun da zai hanashi ganin wasu daga cikin tashin hankulan da suka durfafoshi suka durfafo iyalinsa,suka koma durfafo masarautarsa......na shirya kawai bobbo.......idanu da kunnuwanka kawai nakeso ka kulle......a yanzu na shirya kowa yasan waye sheikh muhammad haisam ibraheem aba jifar......"
"Al_saamit?.......the silent one?" Bobbo ya fada da wani kwantaccen kuma sauqaqqan murmushi kan fuskarsa. Ya sani,tsokanarsa bobbo yake,wata tsokana cikin girmamawa wadda haisam ya riga ya saba da ita.
"Na kulle muhammad.......na damqa maka dukkan wata dama kuma dari bisa dari.....na zare hannuna na baka wuqa da dama......ka qarashe wasan da dukkan salon da kaso" Idanunsa haisam ya lumshe yana kuma budesu dukka lokaci daya.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 03*
"Na gode" Ya furta yana kuma qoqarin shutting down system din.
"Salaana ya fito da mota" Haisam ya fadi yana qarashe kasheta ba tare daya dubi omar da yakeson yayi tambayoyi wa haisam din ba.
*M A M M I N A*
_"Kwanciya ba taki bace zaituna........ki tashi zaituna.......ki tashi ki nuna ma koma waye da yake wasa da rayuwarsa cewa yana kutsawa sansanin mutuwa ne yana yin wasa da ajalinsa......ki tashi zaituna kada ginin nan na shekaru masu yawa da kika jima kina yi ya fado ya danneki.....ki tashi zaituna!!!.....kada ki bari akhnan ta fahimci komai.....kada ki bata qofar da zatayi nisa dake da burikanki ba tare da sun kammala cika ba"_
Ire iren wadannan maganganun sune abinda taji zuciyarta na rad'a mata har cikin kunnenta a sanda take kwance da tarin zazzabin da ya dinga kadata kamar zata datse harshenta da haqoranta.
Wani irin wuf tayi ta tashi.......ta kuma buqaci maganin da zai warkar mata da zafin zazzabin cikin mintuna goma ko ashirin. Ta karba ta kuma sha,sannan kuma ya sauka kamar yadda tayi buri,ta shiga tayi wanka,sannan ta buqaci abinci wanda ta zauna ta cishi sosai ba tare da tana banbance d'and'anonsa ba. Tana cine kawai saboda tana buqatar energy sosai a tattare da ita,tana cine saboda tana buqatar aga confidence da cikakken karsashin nan da aka santa dashi,tanaso ta fito a giwarta sak,batasan komai nata ya nuna karaya ko rauni.
Ta sani......indai cimmawa ne an riga da an cimmata.....ta sani,jikinta kuma yana bata akwai tarin baqin fuskar dake rayuwa cikin gidan.....akwai tarin inuwoyin da suka saje da duhun katangun gidan,suke rayuwarsu suna kuma farautarta ba tare data san hakan ba,saidai koma waye.....koma meye tana bawa kanta tabbacin indai itace wannan zaituna din.......indai itace zeenatu to sai ta sanya nadama a zuciyar dukkan wanda yayi gigin ketawa ta cikin shirin ta......rayuwarta dama dadadden burinta.
SHIEKH MUHAMMAD HAISAM sunan da yake kwance a ranta......sunan daya zame mata tamkar wani jarrabawa. Dashi take kwana.....dashi take tashi.......tare da dukka tsare tsaren yadda zatayi dashi,ta yadda ba wani malami da zai sake mararin shigowar masarautar AGADEZ yace zai rayu ba tare da amincewarta da samun dama da dukkanin goyon baya daga gareta ba.
"Ki aika saima....ta duba cikin bangaren suturu mafi zama alfarma ta bani daya" Tayi maganar da d'aya daga cikin hadiman da ita ke biyewa yalwa a matsayi a gurinta. Har hadimar ta fice idanunta yana kallon sashe daya,lissafinta akan toshewar kowacce qofa da zata bada makama akan batan yalwa takeyi. Ba yalwa ba dalilinta,saidai ba wani abu da zai alamtawa kowa b'ata yalwan tayi,b'atan nata yabar tarin hujjojin da duk wanda ya kalla zaice yalwa ta zabi ta tafi da qafafunta bawai da sunan b'ata ba.
Ta sani......ta kuma tabbatar da cewa. Bata yadda za'ayi yalwa ta zabi tafiya daga gareta,bata yadda za'a yi yalwa ta zabi tafiya daga masarautar agadez. Tafiyar yalwa din wani SHIRYAYYEN ABU NE da mutane irinta ne kadai zasu gane hakan.
Tsaf ta shirya cikin ire iren shigar dake nuna zallar alfarma alfahari da kuma izzar da takejin tana da ita. Ba kwanaki ko shekaru qalilan ba........a dukka tsahon shekarun data kwashe qasar agadez ta samu wani irin girma da ba wata halittar diya mace data sameta. Girmamawa da tarin darajtawar da ita ta nemeta.......ita ta siyeta.......ita kuma take tattalinta har kawo yanzun da takejin ba wani.....ba kuma wani abu daya isa ya rabata da wannan izzar tata,izzar da itace MAKAMINTA izzar da takejin zatayi dukkanin me yuwuwa gurin adanata da kyau har zuwa sanda numfashinta zaibar gangar jikinta.
"Ina fatan akhnan na cikin gida?". Kai ta gyada mata cikin maqurar ban girman nan da suka saba bata.
" Eh tabbas.......ance ta fita zuwa dakin karatun me martaba"
"Dakin karatu kuma?" Mammina tayi tambayar tana zubewa hadimar tata idanu.
"Eh Allah ya baki yawan rai" Shuru ya ratsa kadan,mammina din tana juya zoben dake yatsar hannunta. Wani abu ne yake harbawa cikin kanta da saurin gaske yana sake nauyayawa da kuma zurfafa tunaninta.
Zuwa dakin karatu baya cikin dabi'a ko al'adar akhnan din kaf tsahon rayuwar data raineta a kai,idan dan zamanta dashi ne fa?......idan dan kebancewar da tayi dashi ne wanda duka duka idan aka lissafesu guri daya ba zasu haura kwanaki biyar ba fa?. Hakan na nufin zai zamemata wani sabon aikin kenan wajen kawo qarshen alaqarsu da aurensu?. Ya kamata ta bari irin hakan yaci gaba da wanzuwa?,har takai sun fara musayar wasu dabi'u a tsakaninsu ita dashi?.
"Inason magana da ita.....zan isa zuwa dakin karatun inaso kuma kowa ya sani"
"An gama" Ta fada cikin girmamawa ta juya ta ficewa.
A yau fitar tata ta zama cikin salon da takanyi amfani dashi lokuta da dama. Wata irin tafiya tsakanin sassanta zuwa dakin karatun sultane din. A kowanne taku da zata gamu da bayi ko hadiman gidan kyauta ce take yinta. Kyautar kudade ga duk wanda suka hadu a hanya dashi. Wannan salon yana daya daga cikin wani hanya data bata daman mallakar zuciyar mutane da yawa dake rayuwa cikin masarautar,alkhairinta kuma ya danne na kowa........sai d'ai d'aikun da har a lokacin alkhairin nata ya gaza saya mata matsugunni a ransu ba tare da suma sunsan dalili ba.
*_SHEIKH MUHAMMAD HAISAM_*
Cikin lafiyayyar motar Mercedes Maybach S_class suke tafiya zuwa killataccen gidan dake cike da tarin tsaro. Killataccen gidan da almaz ya dade a cikinsa.......JINJIRI da har yanzu baida cikakken suna kuma D'A ga ajani ya zama cikon na biyun.
Yana zaune d'ai d'ai saman lausassar kujerun alfarmar da motar ta mallaka,yayi relaxing sosai cikin kujerar,dukkanin idanunsa a lumshe suke qasa qasa,zaka iya dauka bacci ne yake shirin saceshi. Sau uku omar yana daga idanu yana dubansa,sai ya bari ba tare da yace dashi komai ba. Iya yanayinsa kadai ya gaya masa 'yan miskilancinne suka motsa,dukkan alamu sun nuna bayason magana me zurfi....kaman yadda yake ganin alamun akwai wani kwantaccen fushi qasan ranshi.
Tafiyar kusan awa daya ce cif ta kaisu unguwar,unguwar dake a wani muhalli da ba kowa yake samun sukunin zama a gurin ba. Unguwa ce ta masu hannu da shuni dake cikin garin agadez qwarai da gaske,wannan ya sanya unguwar keda wani irin security sosai.
A hankali omar ya dafe Bluetooth din dake kunnensa sanda suke fitowa daga cikin motar suna dosar ainihin cikin gidan.
"Ina captain?,na gaza samunsa a waya" Maleek ya fada cikin yaren oromo. Saida omar ya saci kallon haisam kadan,yadda yake takawa d'ai da wannan ginshirar tasa sannan ya maida dubansa
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Kabi captain a hankali,abubuwanne yau suka motsa......da alama kaman a kusa yake,na kasa gane meye haka me girma da nauyi daya taba ransa".
"Please omar.......ka fada masa"
"Nooo maleek......ba'a irin wannan lokacin ba"
"When?" Maleek ya tambaya cikin sarewa. Kaman omar zai saki dariya sai ya daure.
"Inde falaak ce na tabbatar haisam bazai bari ka rasata ba,tunda ya tabbatar kana sonta"
"I trust you......"
"Kaman yadda nayi trusting Captain namu....." Omar ya amsawa maleek yana yanke kiran da dan hanzari ganin suna dab da shiga ainihin qofar farko da zata sadaka da sassannin gidan
Gaba kadan omar ya qara yana daidaita tafiyarsa data haisam din,sannan ya sanya key din hannunsa ya murza ya bude qofar.
Qawataccen parlor ne da aka yiwa wani sassanyan tsari me daukan hankali. Daga cikin parlor din ba kowa sai mutum uku,sheikh Ousmane ahmad(almaz),sai jinjiri dake zaune saman daya daga cikin lausasan darduman dake shimfide a qasan gurin.
Idanun haisam a kansu su dukkaninsu,yayi sallama da muryarnan tasa ma'abociyar kwarjini,sallamar data ratsasu dukkaninsu suka kuma daga kai suna kallonsa.
Da murmushinsa ya taso,Ahmad almaz,wanda dukkanin kamanninsa suka juye zuwa na wani kamilin matashi wanda ainihin kamanninsa na ba'abzine mallakin qasar agadez ta fara tsatsowa. Wani irin kamala da bata da alaqa kota kusa kota nesa da wancan ALMAZ din,wancan almaz din da zaituna ta sassaqashi da kalar tunaninta da cutatarwarta.
Yana sanye cikin ainihin kayan gargajiya na agadez,wanda hakan ya taimaka qwarai wajen sake bayyana kamanninsa da mahaifin sultane wato kakansa. Wata irin boyayyar kama da me nazari zai saurin daukota daga fuskar almaz din.
Cikin girmamawa da nutsuwa ya rusuna yakewa sheikh haisam barka da zuwa. Haisam din ya amsa yana duban fuskar almaz din. Ba abinda yake dawo masa sai wahalar da sukaci kafin su maida almaz din cikin hayyacinsa. Ba abinda yake tunawa sai ranar da sakamakon gwajin DNA na almaz ya fito,wanda ya sake wanke masa kokwanton da yayi saura a ransa na kasancewarsa jinin SULTANE MUHAMMAD HAMMUD. Ba abinda yake sake tunawa sai yadda almaz din ya birkice a sannan,kuka wiwi.....yana iya tuna kalaman daya gaya masa a sannan.
"Ba ragontaka sam a tattare da d'a namiji......d'a namijin ma daya amsa sunan YARIMA kuma sarkin gobe.......idan wannan yariman yayi kuka yau.....a gobe mai zai gayawa mutanensa game da JARUMTA?" Yanayin yadda maganan tayi tasiri nan da nan a zuciyar ahmad ya sanya haisam lumshe idanunsa a hankali,ba shakka akwai wani burbushi ko kuma ace jinin sarauta sosai dake zagayawa cikin jikinsa.
Idanunsa ya daga yana dorawa akan JINJIRI da yaketa tunanin bashi suna. Ba nasabarsa kawai suka datse ba......ba rabashi da mahaifiyarsa kawai sukayi ba......ba nonon dake kasancewa abinci ga kowacce sabuwar haihuwa suka haramta masa ba. Aah......daidai da SUNA sun kasa bashi.....RAI kawai suka bar masa,amma sun kashe dukkanin rayuwarsa gaba daya.
Murmushi kadan ya saki,Shima ya taso a nutse zuwa gurin haisam din. Cikin nutsuwar da yake gani tun ranar farko tattare dashi ya soma gaidashi. Shi din SAK jinin AJANI.....yana diban kamanni qwarai da wasu daga cikin 'yan uwansa wadanda kamannin ajani suka dauko. Baida shakka tantama ko kokwanto akan sahihancin zamansa halastaccen dan ajani saboda komai nasa ya nuna hakan.
Hannu ya miqa masa kai tsaye,miqa hannun daya lura cewa ya yiwa jinjiri nauyi har sai daya kalli tattausan farin tafin hannun haisam sannan ya maida dubansa ga idanunsa.
"Karbi mu gaisa......muhammad......daga yau zaka amsa sunan muhammad" Wani abu ya gani sosai cikin idanunsa,wani irin rauni da laushi,kaman ma hawaye ne kwance cikin idanun nasa. Sanda tafukan hannunsa suka hadu dana haisam sai ya kasa boye abinda ke cikin ransa.
"Tunda na tashi a jikina nakejin wannan rayuwar ba tawa bace,tunda na tashi na tabbatar akwai wani boyayyen abu cikin rayuwata,a jikina nakejin ni dinnan bani bane,ina dadewa cikin tunani,ina jimawa cikin nazarin da bansan wanda zai fahimtar dani ba,bansan fuskar kowa ba sai ta matar da tamim dana kwashe shekaru ina ganinsu tare tun tasowata......tun daga ranar dana fada hannunka na fara jin kamar sabon ruhi dama gangar jiki ka bani.....muhammad.....sunan yayimin dadi.....kaman wani suna ne me girma ko?" Ya qarasa maganan yana danyin murmushin da yafi kama da yaqe,idanunsa akan fuskar haisam.
Har cikin jininsa yaji wani abu ya zarta masa,sunan annabi guda......annabin da sunansa......jarumtarsa......shahararsa da mu'ujizarsa ta zagaya ko ina,amma yau sai ga wani diyan da aka Haifa cikin musulunci da sunnar annabin baida koda labarin sunan annabinsa?.
Sai da yaja iska sosai yakaita har hunhunsa sannan ya fesar,yayi qoqarin daidaita nutsuwarsa yana dafa jinjiri da ya zama muhammad ajani a yanzu.
"Ba rayuwarka bace wannan.......ka kuma fita kenan a cikinta" Yayi maganan yana jin shima tasa zuciyar tana wani irin tsagewa. Wato har gwara ahmad almaz kenan?,wato har gwara gwara shi?. Shi sun barshi yaci gaba da shaqar iskar rayuwa da cakuda da mutane,duk kuwa da cewa iskar gurbatacciya ce......gurbayacciyar iska ce dake cutarwa gami da naqasa dukkanin wani gaba ta dan adam......amma muhammad fa?,sun kasheshi ne ba tare da sun zare numfashinsa daga ruhinsa ba,amma dukkanin wani kisa na ma'ana sunyi masa shi. Sun watsar dashi ne kawai yana rayuwa irin rayuwar dabba,wadda batasan komai ba sai abincinta. Ba asali......ba suna.....ba makomar rayuwa......ibada da addini duka babu ko daya.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261 KO 08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 04*
A nutse dukkaninsu suka zauna,ya kuma maida hankali ga oustaz Ousmane suka gaisa,sannan ya fara bibiyar yanayin karantarwar da ya dauki nauyin ya dinga yiwa ahmad da Muhammad(almaz da jinjiri).
A nutse yake sauraren bayanan Ousmane,yana gyada kai a hankali. Wato lamarin ubangiji girma gareshi,duk da sun datse dukkan rayuwa daga gun muhammad amma hakan bai sanya ya tashi a wata fandararriyar halitta ba. Yanayin yadda Ousmane ke masa bayani sai ya dinga duban fuskokinsu a hankali. Dukkaninsu suna da wata baiwa ta kaifin basira saurin fahimta da daukan abu,abinda ya yiwa haisam dadi kenan,ya kuma tabbatar masa komai zaizo musu da sauqi har fiye da yadda yake zato.
Kwanakin barinsa agadez ne kawai yakejin zasu haura,wasu kwanaki bakwai din yana zaton suna iya qaruwa,don yanason kafin yabar agadez ya kafa harsashi......ya kafa nakiyar da zata tarwatse da mammina dama dukkan wanda yake rab'e da ita.
"Dr Na'eem ya qaraso fa" Omar yace da haisam wanda dukka hankalinsa yake kan bayanan Ousmane. Idanunsa da sukayi wani irin laushi ya daga kadan.
"Ka qaraso dashi" Ya amsa yana maida dubansa ga oustaz Ousmane.
"Zanga baqo,kuna iya ci gaba,bayan nan zan gansu daya bayan daya"
"Mintuna goma ma suka rage mana lokacin tashi yayi......sai kuma karatun dare" Oustaz Ousmane ya fadi.
A nutse haisam din yake bin wata qofa da zata sadashi da wani parlor din na daban,ya sake zube hannuwansa a aljihun wandonsa yanajin yadda jikinsa yake amsawa. Results ne na DNA test da ya bayarwa Dr Na'eem din don qara rufe dukkan sauran hojjin da kuma sake tabbatar da nasabar almaz da sultane.....muhammad kuma da ajani.
A tsaye ya samu likitan,baqi kakkaura kuma giant ba'abzine sosai wanda yake da kyakkyawar alaqa da hukumomin sirri na tsaro na qasar Ethiopia. Hannu suka bawa juna kafin kowannensu ya nemi gurin zama,sannan Dr Na'eem din ya miqawa haisam wasu takardu.
Baice komai ba ya sanya hannu ya karba,ya bude ta farko yana duba bayanan. Bayanan dai da zuciyarsa keta gaya masa ne na za'a samu.....su dinne kuwa rubuce saman takardar. Dukkanin qwayoyin halittar muhammad na ajani ne......komai na gwajin yazo sak da sak da ajani dama duk wani yaro daya fito daga tsatsonsa.
Ta baya ya miqawa omar takardar,ya bude sakamakon ahmad almaz.
Wannan karon wani huci ya sauke,ya ajiye takardar a gefe yana daga risunannun idanunsa yana duban Dr Na'eem
"Na gode qwarai da qoqarinka na kawo gwajin haka da wurwuri,ina fata nan gaba idan wata buqatar ta sake tasowa zan samu goyon baya". Murmushi Dr Na'eem yayi yana duban haisam
"Aiki dakai wata babbar alfarma ce ga mutum........a shirye nake koda yaushe da amsa kiranka". Sai suka sake bawa juna hannu,Dr Na'eem ya miqe yana daukan briefcase dinsa.
Zagayowa omar yayi wani rudani yana bayyana saman fuskar sa,ya zauna sosai gaba haisam yana shafa sumarsa yana jin kwanyarsa na rikicewa.
"Ya akayi dukka zatonka da hasashenka suka zamo daidai?.....wacce irin matace wannan mara imani?,wannan aikin......koda namiji ne ya sarqa wannan qullin lallai ya cika baqin azzalumi.....waye yake raba uwa da 'ya'yanta idan ba Allah ba?......wanne irin zalunci ta yiwa wannan baiwar Allahn?"
"Ka dauka a banza Allah ya jarabceta itama ya hanata haihuwa?" Haisam ya furta da wani laushi yana qoqarin controlling kansa. Ya sani inde wannan fushin yaci gaba da masa jagora......tabbas zuciyarsa ba zata bashi goyon baya ya yiwa mammina yanayin kamun daya shirya zai mata ba.
*A K H N A N*
Karo na farko a rayuwarta data fara lura da irin girma da tsaruwar da dakin litattafan mahaifin nata ke dashi,duk kuwa da cewa tunda ta taso a gidan tasan da zaman gurin,amma ko sau daya bata taba mararin shiga don buqatar karatu ta qashin kanta irin wannan ba.
Yau sai gata kace kace cikin dakin karatun sultane din,da wai kuma buqatar yin karatu......karatun da a yanzun takejin ra'ayinta ya karkata sosai a kansa.