L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 8
L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 8: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 8. Daidai lokacin da yake zaune shida sauran 'yan shidan.…
3,345 words
Daidai lokacin da yake zaune shida sauran 'yan shidan. Khadeem....mutallab.....amjad,omar,maleek,naseeb saishi na bakwai daya fita kadan daga da'irarsu yayi relaxing a wata kujera daban dake nesa kadan dasu.
Sosai ya narke cikin kujerar,dukka idanunsa suna zube saman mini system din dake girke a gabansa a kunne.
Tun jiya ba tare da sanin kowa ba,daga shi sai abeer ya sanya aka maqala na'urar tsaro a kowacce kusurwa ta gurin da za'a gabatar da taron. Yayi ne da nufin samar da cikakken tsaro.....yayi ne don ya tabbatar da cewa yau din gidan ya zamana cikin tsaro. Musamman yau din data kasance sultane ya zabeta,ya zabeta a matsayin ranar da haisam da kansa zai gabatar da ahmad cikin iyalinsa.
"Bansan ko akwai wani shirin ba,bansan ko akwai wani tsarin ba,amma inaso kayimin alfarmar gabatar da ahmad cikin iyalinsa a karo na biyu.....a daren ranar lahadi,inaso a gaban kowa,kowa ya shaida dawowarsa......koda kuwa ka boyemin,jikina yana bani batar Ahmad tana da sila......tana kuma da dalili ba haka siddan ta faru ba.....na kasa nutsuwa muhammad,idan na kwanta fuskar ahmad yana qanqani nake hangowa". Sosai wani abu ya narke a zuciyar haisam din,yasan wannan ciwon a murya da idanun Nanay dinsa.....wannan dalilin ya sanya yakejin lokaci kamar yayi tsaho.....lokacin da zai bata albishir din safeenarta tabar wani reshe.....reshen da gata a gabanta ya kawo mata.
Haka kawai yaji yana ra'ayin monitoring gurin da kansa,amma kaman bazai iya ba saboda gajiyar dake nuqurqusarsa kwanakin. Daga ahmad har Muhammad basason yayi nisa dasu,sukan kashe Lokaci sosai tare dashi,wannan ya sanya saboda ya fara shiga tsakaninsu sosai,suke wani mugun bash in respect tamkar babban wa da kowannensu ya rasa bai samu ba.
Ya zauna gaban masarrafin cameras din,ya kuma bude kowacce shiyya,amma sai ya samu kansa da kashe kowacce camera ya miqawa abeer dake kebance a daki shi dasu beeno,ya zabi fuskar camera qwaya daya......fuskar camera da ta nan ya hangi takowarta tana isowa gurin zaman da aka tanadar musu.
Lafiyayyar atamfa ce a jikinta me wani irin kwantaccen launi mara hayaniya ko saurin jan ra'ayi,saidai kuma yadda ta kwanta a fatarta shine abu na farko da zai fara fusgar hankalinka fiye da kima.
Wani irin sassanyan kyau da karon farko idanunsa suka fara sauka akai......wani sassanyan yanayi......basaraken jikin nan saye cikin atamfar hausawa.....atamfar data zama daya daga cikin suturun da yayi research akai na yankin africa da yaji yana burgeshi sama da komai.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Atamfar dai aka warware,aka dorata daga saman daurin dankwalin kanta wanda aka matse da clip don kada ta sauka,mayafin kuma ya watsu a gadon bayanta da sample din shigar suturar ALKYABBA.
Idanunta.....labbanta.....dama fatarta dukka sunyi wani fresh......blue eyes dinnan sunyi fayau,don ba wani makeup saman kyakkyawar fuskarta sai anihin zallar madarar kyan da duk motsawar da zatayi yake magana akan kansa da madaukakin sauti.
Idanunsa ya lumshe a hankali yana jin wasu abubuwa suna spark cikin kansa,yaja boyayyen numfashi ya aje yana sake ware idanunsa daidai sanda take dab da abun zamanta. Idan har ya gani daidai kamar wadannan siraran labban sun furta
"Bismillah" Ne,sai yaji wani dadi yana sauka har qasan ransa da zuciyarsa. Siraran zara zaran fararen yatsunta da wani lalle me azabar ja ya yiwa ado me fusgar hankali ta sanya tana tattara lullubin saman kanta zuwa gaban rigarta da dinkin ya rufe komai ruf,saidai hakan bai hana bayyanar tudun qirjinta ba daya zauna dasss kaman zanashi akayi ba halitta ce cikin qirjinta ba.
Wani abu me qarfi yaji ya sauka masa.
"Me yasa ba hijab ba?" Ya yana motsa labbansa da qarfi,omar da yadanfi kusa dashi ya waiwayo da hanzari.
"Captain.......magana kakeyi?". Wadannan tsumammun idanun nasa ya daga a nutse ya zubewa omar su,kallon da ya sa ya omar janye dubansa daga kansa,bai kuma sake tankashi ba ya koma cikin hirarsu dasu naseeb.
Sake janye idon nasa yayi,yana sane ya yiwa omar irin wannan kallon,ya fuskanci tun dazun akwai wani magana ne cikin bakinsa.....ko a dazun bai shirya doguwar magana ba bare yanzun da yakejin komai yana sauka daga ainihin saitinsa daga kwanyarsa.
"Halal.....halal ce" Zuciyarsa ta fada masa a sanda yayi zooming fuskarta dab da dab. Daga nan inda yake yana iya hangen wani abu me nauyi cikin idanunta.....kamar kawai qarancin walwala saman fuskarta ta,kamar akwai abinda ke damunta can qasan ranta,hasalima wayarta na tsakanin yatsunta tana jujjuyata tana wasa da ita kawai,bata iya daga kai ta kalli mutane yadda ya kamata.
Haka kawai yaji sha'awar yayi magana da ita......a kwanakin nan aduk sanda zai tunata yana tunata ne da TAUSAYI. Ya yadda cikakkiyar marainiya ce ita gaba da baya ba tare da ita tasan marainiyar bace a karan kanta.
_smile.....its a sunnah_ abinda ya rubuta kenan ya kuma aike mata ya saqon karta kwana,sannan ya maida wayar gefansa ya ajiye yana maida kallonsa ga allon system din.
Akan idonsa saqon ya shiga. Yayi qara kadan,tayi kaman ta share,sai kuma yaga ta bude.
Reaction nata ya nuna sosai......wani irin reaction daya nuna zallar mamakinta a fili. Wadannan blue eyes din tadan bude kadan kafin ta maidasu daidai,ta sake dago wayar daidai fuskarta da alama tanason tantance number waye?.
Murmushi kawai ya subuce masa ba tare daya shirya hakan ba,yanayin sai yaji ya masa dadi. Tsokana......a tsakaninsa kawai dasu maleek irin haka take faruwa.....yau ne karon farko da tsokana ta hadashi da wani jinsi daban ba nasa ba. Wayar ya sake dauka,ya sake rubutawa a gajarce.
_smile mana please_ a wannan karon murmushinsa me sauti ne,saboda yadda yaga gaba daya ta diririce tana waige waige tana kuma sake kallon fuskar wayar tata,kafin ta tabo birra dake gefanta ta qaraso ta kuma rusuna ita kuma ta shiga nuna mata wayar birra tana kalla tana saurare.
Ya fahimci me takeson sanyata tayi sanda ta damqa mata wayar,ta koma ta zauna,saidai duk da wayar tabar hannunta yaga alamar bata nutsu ba,tanata rarraba blue eyes dinta kawai tsakanin jama'a,sai ya sake sauke murmushi yana jawo wayar ya danna Stwiched off ya kasheta gaba daya.
Sai a sannan yaji yadda parlor din ya dauki shuru,ya aro nutsuwa ya azawa fuskarsa kafin ya daga idanunsa ya bisu da kallo daya bayan daya.
Kowa kawai idanunsa yana kanshi,daga sanda yayi wannan murmushin me sauti sai ya dauki hankulansu,yadda yaci gaba da murmushi kadan kadan kuma ya qarasa kashesu gaba daya.
Yana da kirki sakewa da abokansa......amma ba kasafai zakaga yayi murmushi a jere har sau biyu haka ba.
"Lafiyanku?" Ya maze yana jefa musu tambayar
"Kai zamu tambaya captain,ko yau ka fito daga daki a daren farkonka iyakar murmushin da zaka yita yi kenan" Amjad dan kai tsaye ya fadi yana miqewa ya dauki wayarsa,don ya tabbatar tunda ya fadi wannan maganar akwai case ci gaba da zamansa a gurin.
Wani nauyi yaji ya kamashi,saidai bai bari sun fahimta ba ya bisu da tsaki,ya maida hankalinsa ga system din,yana jin kamar bayaso amma haka ya kasheta yana fadin.
"Yana daga cikin kyawun musuluncin mutum,yabar abinda babu ruwansa".
*_KOMAI NISAN DARE_*
*_KOMAI NISAN JIFA_*
*_KOMAI GIRMAN GONA........_*
*AGADEZ PALACE*
*sultane muhammad hammud meeting room*
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 14*
Saman kujerun da aka tanada cikin kebantaccen dakin ganawar na musamman. Dauke yake da Wazeer,babban alqali na jaha,wali,galadima,shugaban limamai,da shugaban malamai. Ta daya bangaren kuma tsoho ne me ran qarfe wato kakan safeena wanda shine kan zuri'ar diory hammani family a yanzu gaba daya wato mamman hamza,da 'ya'yan 'yan uwansa da a yanzu suke taka matsayin iyayensu ne a wajen mamman hamza din.
Daga bangaren sultane kuwa,yakumbo ce,sai qannanesa guda biyu da suke zaune a diffa da zinder,sai nannie sai kuma morsa safiyya da mammina dake zaune gaba kadan da morsa din cikin jin izza tare da mamakin dalilin wannan hadin da wannan kiran da sultane din yayi musu.
Kusan duk wani gaishe gaishe an kammalashi,sarkin malamai ya gabatar da addu'o'i sosai,sai shuru daya biyo baya kowa yana tattara hankalinsa ga sultane.
"Alhamdulillah......Alhamdulillah......alqawarin Allah baya tashi.....alqawarin Allah baya sauya ba,haka rabon bawa baya wuceshi,ban taba zaton wannan rana zata zo,ban taba tunanin zata riskeni ba......amma cikin hukuncin Allah bayan shekaru masu yawa da fidda rai sai gashi rabona ya dawo zuwa gareni...........muhammad,ku qaraso kaida ahmad" Sultane yayi maganan yana kallon wani guri.
Labulen dake wajen ya yaye kadan,ahmad ya fara yowa gaba,haisam na biye dashi,dukkaninsu cikin nutsuwa da kamalar data qara musu kwarjini. Shigar dake jikin almaz a yau din ta sake saka wani irin kwarjini a fuskarsa da kamala cikin halittarsa......irin wannan kwarjinin da duk wani ahalin sarauta ke dashi,a yau kamar an sauya fuskar almaz din,kamar yaune ranar farko da aka masa wanka da ruwan kwarjini irin na ainihin jini da 'yan gidan sarautar AGADEZ,kwarjinin haisam kuma sai ya sake haskashi da wani irin yanayi da ya sanya kowa zuba masa idanu.
Kamar an dauko babbar mota an jibga mata tsakiyar kanta.....kamar wadda jirgin sama ya daki tsakiyar qirjinta.....kamar wadda akayi dauka aka wujijjiga aka jefo daga saman wani dutse ko tsauni me tsananin tsaho haka taji yanayinta ya koma.
Batasan ta miqe tsaye ba har sai da suka hada idanu da haisam. Wani irin miqewa ta tsananin razana da firgici........amma kuma saita maye gurbin hakan da nuna alamun farinciki da tsananin mamaki.
"Almaz......ahmad" Tayi hanzarin gyara sunan tana soma takawa tana nufarsa.
Cak ya tsaya yana dubanta......abubuwa da yawa suna dawo masa saman kansa. Banda haisam yace kada yayi komai.....kada ya sake ya aikata komai wanda yake ba daidai ba,ba shakka ba abinda zai hanashi kwasheta da mari sannan ya kwasheta ya watsar guri guda.
Kanta tsaye ta rungumeshi tana sakin qirqirarren kukan da a zahiri yake cike da tsoro da kuma fargaba. Tsoron tonuwar asirinta......tsoron kada wani abu daban ya biyo baya......tsoron faruwar wani mummunan abu na yayewar sirrinta.
Idanu kawai morsa safiyya ta zuba musu shida mammina din,zuciyarta na wani irin tsalle a qirjinta,wani yanayi takeji da yake sake bata tabbacin lallai shi din jinin safeena ne. Sai ta miqe tsaye cak,tana jin qafafunta suna rawa ta qarasa gabansa. Ta yarda da sheikh haisam har fiye da yadda ta yarda da kanta,tunda ta gansu tare ta tabbatar akwai wani abu,to amma tanason ta bawa zuciyarta tabbacin da babu shakka ko kokwanto a kansa.
A hankali yayi taku biyu yaja baya yana raba jikinsa dana mammina.......sannan kuma ya juya kansa gefansa yana duban morsa safiyya dake tsaye tana kallonsa da idanunta da suka cika taf da qwalla.
Haka kawai yake ganin wasu abubuwa tattare da ita,haka kurum duk dabai shaida wace ba yakejin wani strong connection daga idanunta zuwa nasa. Wani nutsuwa da kuma wani kalar aminci yana baibayeshi.
Taku uku ta qara,ta iso gabansa,ta miqa masa hannunta,saiya bi hannun nata da kallo
"Hannunka" Ta fada tana sakin murmushin dake cakude da qwalla. Bai musa ba ya miqa mata hannun nasa,ta riqe cikin nata ta soma janye hannun rigar dake jikinsa.
Hannunsa ta soma jujjuya tana neman abinda takeson gani. Ta sake juya hannun zuwa saya b'angaren,take idanunta suka gano mata abinda takeson gani din.
Wata runguma me qarfin gaske takai masa tana sauke wani nutsatsen kuka me taba zuciya,sai kawai ya samu kansa da riqeta sosai cikin jikinsa. Wani abu yaji yana motsawa har qasan zuciyarsa.....wani irin motsawar zuciya da zaije bai taba jin emotion irin wannan ba. Karyewar zuciya ya dinga ji kamar shima ya saki kukan,saidai tuni ya horu ya kuma karantu akan dabi'un basarake......ya kuma haddace kusan dukkan al'adu da dabi'ar masarauta.
"D'ana ne......ahmad ne.....ebba na.....ebba masoyi" Sunan yaji ya harba cikin kansa.....sai yaji wata wuta ta kawo cikin kansa,ya daga idanunsa yana saukewa a kanta still duk da tana jikinsa. Kamar yana tuna sunan.....kamar yasan sunan a wani mafarki daya taba yi.....kamar yasan sunan a wata rayuwa daya taba yi a baya.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
"Ki zauna safiyya,kiyi haquri" Nannie itama da idanunta suka cika da hawaye ta fada bayan ta miqe tana kaman morsa safiyya ganin yadda kukanta yake qara yawa ainunn,har dukka jikinta yana amsawa.
Wani irin sanyi takeji suna bin dukka gabbanta.....wani irin yanayi da ba zata tantance wanne bane. Dan uwanta ahmad dai?,ahmad da aketa fadi wanda batayi wayon da zata ganeshi ba a sanda ya bace?. Amma wannan fuskar kamar tana mata kama da wata fuskar.......duk da ta rasa ganowa inda ta taba ganinta,koma a inane tasan bataga fuskar da yawa bane da babu abinda zai hanata tunawa.
A hankali ya qaraso gaban sultane,sultane din dake zaune saman doguwar kujera shi da akhnan da falaak da suke zaune dama da hagunsa.
Sulalewa yayi saman gwiwarsa cikin tsananin girmamawa yana soma gaidashi da yaren Tuareg,abinda ya saka tsananin farinciki a zuciyar sultane,don bai taba tunani ko kawowa zaiji yaren ba.
Daga gaban sultane sai ya isa gaban manyan da suke nan gaba daya ya fara gaidasu,suna girmamashi yana girmamasu,yanayin daya sanya taruwar qwalla cikin idanunsa.
Ashe wannan shine tushensa?,ashe wannan shine asalinsa?,ashe wannan ne dalilin da yasa kullum kuma kowacce rana yakeji a ransa rayuwarsa ba tasa bace?,ashe shi yasa yaqi gamsuwa rayuwar da yake gudanarwa itace rayuwarsa?.
Komawa yayi ya gaida yakumbo nannie da morsa data iya amsawa da qyar saboda kuka,sanda ya iso kan mammina ji yayi zazzafan mari ya kamata ya sauke mata ba gaisuwa ba,amma koda tuna da kalaman haisam sai ya basarwa yana gaidata da wani irin yanayi daya sanya gabanta tsananta faduwa.
Irin kallon da take gani a idanunsa suna tabbatar mata da gaske almaz dinne,irin kallon da take gani tattare dashi yana gaya mata cikin hayyacinsa yake......cikin kuma hankalinsa yake. Ba wani abu daga tunaninsa daya bace.....ba wani abu daga tunaninsa daya sauya ko ya samu naqasu.
"Almaz ne" Ya fada yana kallon tsakiyar idanunta bayan ya miqe da sautin da ba wanda yaji daga shi sai ita.
Wani abu taji ya daki qirjinta......abun daya taho da tsananin qarfinsa ya kuma dunqule mata a qirjin ya sanyata jin jiri tana daga zaunen,sai gashi ta gagara zama tana neman sulalewa.
Nannie ce ta tarota tana salati,wani irin numfashi mamminan ke fiddawa gumi kuma yana yanko mata saboda yadda take kokawa da numfashin nata,da alama iskar gurin bata isarta.
"Akwai taimakon da za'a bata?" Sultane ya fadi yana duban haisam adan rude,kai haisam ya gyada,sannan a nutse yace.
"Daki kawai za'a kaita.....sannan a kunna mata wadatacciyar iska a bata guri ita kadai". Da sauri sultane yasa aka kira tafisu da sauran manyan hadimanta suka dauketa bayan sultane ya taka har zuwa bakin dakin taron.
"Yanzu zamu kammala zaman,idan akwai wani rashin ci gaba a yanayinta a kira likita kafin mu fito" Ya fadi sannan ya juyo yana dawowa ciki.
Dukkanin takardun gwaje gwajen qwayar halitta nashi dana ahmad DNA test ya gabatar musu,bawai kuma don kowa bai yarda ba,aah saboda sake samun tabbaci da nutsuwar zuciya.
Duk wanda yake zaune a gurin girmama lamarin ubangiji yakeyi,sunata juya abun tare da taya sultane murna.
Saidai ba wanda yasan ta yadda ahmad ya bayyana.....ko ta yaya aka ganshi,duk da kowa akwai wadannan tambayoyin a ransa,amma rashin bayyanarwa ya sanya ba wanda ya nemi ba'asin jin hakan.
Wazeer,babban alqali na jaha,wali,galadima,shugaban limamai,da shugaban malamai dama ahalin diory hammani sunka wuce bisa rakiyar sultane gami da sake yiwa junansu barka da arziqin dawowar ahmad din cikin ahalinsa,sai dakin ya kasance daga sultane falaak da akhnan,sai morsa safiyya da nannie. Sai haisam dake zaune cikin kujera. Ya motsa zai fita tun sanda tsohon mamman hamza zai tafi amma sultane yace ya zauna. Akwai maganganu da yawa daya gani tattare da tsohon,wanda basu taba haduwa shi dashi ba sai a ranar.
"Gobe hammud inason ganinka,kai da abokin takarata daya kayar dani" Ya fada yana duban haisam. Koda wasan kaka da jika yasha banban a ayaren Oromo da yaren Tuareg amma ya fahimci tsokanarsa yake,sai yayi murmushi sultane yana fadin.
"Zanzo da kaina....zamu riskeka gida in sha Allah".
Ko a yanzun yana zaune cikin kujera,waya ce a hannunsa yana sake tattara wasu bayanai. Idanunsa basa kan kowa amma cikin jikinsa yakejin Kamar akwai wasu idanu a kansa. Zaifi so sultane ya sallameshi don gurin ya sake zama na ahali sosai wato yasu yasu.
Tsakanin ahmad da haisam batasan sau nawa ta raba idanunta a kansu ba. A duk sanda ta kalli ahmad din,sai ta dinga ji wani yanayi yana shigarta. Kaifi da qarfin jini.....wani yanayi na yau itama tana da yaya?,tana da wani jigo namiji dan uwa?.
Idan ta kalli haisam sai taga bataga komai ba,bata hangi komai ba sai wani basarwa da shariya daga gareshi. Tunda ya shigo ba zata iya tuna ko sau daya da taga ya daga kai ya kalleta ba. Har gwara falaak data gaidashi taga yayi kamar ya kalli sashen da take yana amsa mata da wannan kamewar tasa.
Ta sake zare dubanta daga kansa a hankali
"Meye alaqarsa da bayyanar ahmad?......mene alaqarsa da nemoshi?" Ta tambayi kanta kokwanton data kasa warwarewa kanta shi. Daga idanunta ta sakeyi tana saukewa akan ahmad dake tsugunne gabansu ita da falaak.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261
*SHAIDAR BIYA* 08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 15*
"Ni sunana ahmad,kefa kefa?" Ya fada yana dubansu dukka su biyun.
Murmushi ya kubcewa falaak sosai da yafi kama da qaramar dariya.
"Yaya ahmad.......ni sunana falaak.....ita kuma khadeeja,akhnan ko biftu,daa itace babba,amma yanzu tunda ka dawo kaine babban" Saida sukayi murmushi dukkansu harda ahmad din. Ya maida dubansa akan akhnan,har yanzu batayi magana ba. Da gaske dai haka dabi'arta take.....haka yanayinta yake,ba wani abu bane daban da a baya ya dauka. Ya hadiye wani yawu mai tauri da quna......ya dinga maimaita furta.
"Alhamdulillah" Da tuni qanwarsa yake aure?,da tuni zuwa yanzu alaqa da mu'amala tsakaninsu tayi nisa?. Da mummunan nufin wancan shaidaniyar ya cika da yanzu me kenan?.
Hannunsa ya miqa musu dukka sun biyun son suyi musabaha,sai falaak ta dora nata akai,amma akhnan saita noqe.
"Ehemmm......ko har yanzu ban shiga cikin ahali ba?" Ya tambayi akhnan yana dubanta. A hankali ta sauke idanunta akan hannun nasa,wani abu ya narka zuciyarta sosai tashin farko.
Yatsun sultane take gane a nasa hannun,tsahonsu da yanayin zubinsu,hatta da girman babban yatsansa na sultane ne,sai ta miqa masa nata hannun a hankali dukka ya hadesu guri guda nashi dana falaak da akhnan din.
"Duk da zaku tafi a sanda ni nazo,ina fatan zan zame muku kamar sultane ko?,babban yaya naji kuna cewa shine madadin uba" Wani sanyi taji yana ratsa zuciyarta a hankali.
A baya inda yana nan?,inda yana rayuwar ta qila shine zai dinga bata shawara?,shine zata dinga kaiwa kokenta?,shine zai duba daidai daba daidai ba qilan sama da yadda sultane yayi?.
Idanunsa basa kansu,amna kunnuwansa suna gurin,musamman sanda ya isa gabansu......musamman sanda ta sanya hannunta cikin nasa sai yaji wani abu ya masa tsaye a wuya. Halal ce......ba haramun ba,dan uwnata ne na jini,uwa daya uba daya,to amma haka kawai wani wutar kishi ta d'isa saman ransa.
"Na tsaidaka muhammad.......bari na barka haka sai gobe?" Sultane ya fadi wani girma yana fita daga idanunsa zuwa ga haisam. Wata irin qaunar haisam din yakeji sama da yadda yakejin ta yaransa,bai sani ba ko a nan gaba zai qaunaci ahmad kamar irin haka ko sama da haka?.
Miqewa yayi fuskarsa adan sake,yana bawa sultane hannu sannan ya juya a nutse ya fara takawa don ficewa daga gurin.