Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 9

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 9

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 9: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 9. "Biftu......tashi ki bishi" Morsa safiyya ta furta da…

3,372 words

"Biftu......tashi ki bishi" Morsa safiyya ta furta da muryarta data dakushe kadan saboda kukan dazu. Tana ankare da ita......kamar bata gaidashi ba,hakanan bata bashi attention din daya dace ta bashi ba. Tana tsoron yadda akhnan din zatayi zaman aure......irin zaman auren nan da ake cewa iya zama ya sanya mace ta kame zuciyar mijinta. Ta sani akwai tarin naqasu dama gyare gyare,amma abinda yake bata nutsuwa da kwanciyar hankali nau'in mijin data aura din.

A hankali take takawa,iskar da tun da yamma bata yankewa duniya ba tana ci gaba da kadawa cakude da qamshin qasa da kuma sanyin da hadarin ya bari,saidai sanyin ya yiwa halittu da dama dadi,saboda baiyi yawa sosai ba saima wani shiga jiki da yake yana sanyayar da zukata.

Kamar yadda hanyar take a baya,shuru don ba hanyar shigar kowa bace.....shimfide interlock da bishiyoyi hagu da dama dake sake bawa gurin yanayi me kyau.

Duk taku daya sai taji zuciyarta ta buga kafin a hankali ta soma jiyo wannan mayataccen qamshin. Cak ta tsaya,don idanuwanta dai basu gano mata shi ba,a hankali ta soma juyawa zuwa bayanta zuciyarta na wani motsawa da wani irin yanayi.

Yana tsaye tsaf daga bayanta. Dukkanin hannuwansa cikin aljihun kuftar jikinsa.

Lafiyayyen tsadajjen yadin kuftar da aka yiwa aikin sarauta wuya da hannu da bakin aljihu qasan wando harma da gefe da gefan rigar.

Yayi wani irin sassanyan kyau.....karon farko data ganshi cikin shigar da bata taba ganinsa da ita ba. Shigar ta wani amsheshi,tabi jikinsa.....zaka dauka ya hada jini da al'ummar nigeria......qasar hausa,bakano wanda cikin jerin jinsin mazan da sukafi mazan kowanne gari sanin haqqin wanka,saidai kuma kash.....wannan sassalkan gashin nasa dake kwance saman kansa.......wannan zubin nasa daya banbanta da qira da siffar kanawa ko qasar nigeria......shine abu daya da zai gaya maka wani qabila ne daban da bahaushe ba.

Inda zata iya buda baki tayi magana,abinda zatace masa shine.

"Kaci gaba da saka irin wadannan kayan.....suma sunayi maka kyau kamar yadda cloak thobe ke maka" Saidai bugawar da zuciyarta keyi ma bazai bari komai ya fita a bakinta ba.

Tana jin nauyin idanunsa a kanta sosai.....suna mata wani irin tasiri da taji kaman tana son daburcewa,ta rasa wanne irin idanu ya mallaka masu kaifi da kwarjini har haka?.

Wani abu yake gani cikin idanunta,wani abu da yaja ra'ayinsa kadan,ya sanyashi sake cusa hannuwansa a aljihun rigarsa. Kansa ya karkatar kadan yanason lalubo qwayar idanunta,amma kuma ya gaza yin hakan sam saboda yadda taqi daga fuskarta da kyau.

Ya kafeta da idanu....baice mata komai ba......bai kuma bata hanya ba,hakanan ya daureta sosai da wannan idanun nasa masu tsananin kwarjini.

Daburcewa ta soma ji sosai cikin jikinta......ta soma complain ita daya qasan ranta.

"Yasan kaifin idanunsa akan dan adam kuwa?" Ta tambayi kanta da kanta,tambayar da babu abinda ta qara mata sai rudewa.

Can qasan ranta kuma har yanzu da wannan feeling din,kwana biyar yayi maimakon hudu,a kwana biyar din bai nemi koda wayarta ba,bayan sun hadu kuma by incident sai ya sake bace mata?. Sai a yanzu ta ganshi a gaban kowa?. Kuma ko bayan ya gama zamanshi bataga ya kalli koda inda take ba?,hasalima sai ita aka yiwa tayin binsa?.

"Kaman girmana ya tabu" Taji can qasan ranta wata zuciyar tana gaya mata,hakan yasan ranta yadan tabu kadan.

"Ko zan iya komawa?" Ta fada da muryar nan tata me wani irin laushi.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Iska sosai yaja,wata irin iska data zuqo masa dukkan qamshin dake fita a sanyaye tun daga gashin kanta zuwa sassan jikinta. Ya fesar da iskar a hankali yana lumshe idanunsa gami da budesu.

Yadda take avoiding kallonshi tun a wancan ranar.....akwai wani abu cikin idanunta da yake karantarsa tas. Yana da wannan baiwar......baiwar iya karantar dan adam da tunaninsa ta cikin ido.

Sosai take sake jin yana aza mata nauyi,tana jin kamar ta daga idanunta ta kalleshi......kamar ta daga kanta taga meye ya tsaidashi?......bai amsa mata ba,kuma bai tafi ba,bai kuma barta ta samu daman tafiya ba.

Tarin da taji yadan fara yi kaman ya qwarene ya sakata daga kanta da sauri,saurin daya haifar da shigar qwayar idanunta cikin nasa,fuskarta a dan yamutse da alamun tsoro na tarin daya sarqeshi,saidai suna hada idanun saita sameshi qyam a tsaye,ba wani alamun jigata ko kuma sarqewar tarin kamar yadda taji sautin.

Wani irin riqe qwayar idanunta yayi cikin nasa. Sosai ya nutsa qwayar idanunsa cikin nata,ya lumshesu sau uku yana budesu duka cikin nata da wani irin yanayi na qwarewa wajen sarrafa dan adam ta cikin idanuwa kadai.

"Duka fushin na meye?" Ya furta da wani irin soft and cool voice,ba taushi da sanyin muryar ba kawai.......can cikin sound dinsa akwai wani irin deep abu dake ajiye magana sosai cikin kunnuwa da qirjin me sauraro.

Ji tayi kaman qafafunta suna lanqwashewa,kallon yayi mata nauyi da zurfi da yawa,inda ace tana kusa da wani abunne tabbas da zai taimaka mata qwarai,don zata dafashi don ta samu daidaito gurin tsaiwa.

"Ehmmmm?" Ya fada still yana hana idanunta motsawa daga cikin nasa. Kallon kallo ne ya sake wanzuwa tsakaninsu,kallon da ita daya tasan me yake ajiye mata a gangar jikinta da zuciyarta,sawa yake kowacce gaba ta jikinta tana laushi.

"Akhnan ce fa?,princess akhnan" Wani sashe na zuciyarta ya tunasar da ita. Wannan shine ya bata wani qwarin gwiwa,qwarin gwiwar zame idanunta sannan taja da baya kafin ta juya da nufin saka nisan tazara tsakaninsu. Saidai kuma kyawawan taku uku kawai ya cike tazarar,ya kuma sha gabanta da kyau,har yana mamaye tsahonta gaba daya,yana kuma lullubeta da faffadan kafada da qirjinsa.

Haka kawai sassanyan qamshinta ya masa....haka kawai yaji kaman yayi sauri ace ta koma ciki yanzu.....kamar akwai ragowar mintuna.....kamar akwai abinda yakeson ya fada.

"Gaisuwa.......gaisuwa sai ance kiyi?" Ya fadi yana dubanta har yanzun.

"Barka da dare" Ta samu kanta da hanzarin fada. Ba don maganansa ba,sai don tana buqatar ya tallafeta ya bata hanya kafin ta gagara mallakar kanta. Koda wasa bata bari ta sake kallonsa ba,hanya kawai take nema,bata kuma ganta ba muddin bai matsa mata hanya ba.

A hankali ya sauke idanunta kan yatsunta,karo na farko daya sake ganinsu a zahiri ba a allon computer ba irin jiya. Sosai ya zube musu idanunsa. Ya sani,tun ranar daya karanta cikar sunna ga jan lalle,umarnin ma'aiki ga mata dasu zama masuyin lalle,tun daga wannan rana son abun ya shiga ransa,musamman daya tashi ya samu Nanay dinsa ma'abociyar yinsa ce,ta kuma koyawa kowa cikinsu rumaisa Anaani noorah yinsu,hatta da khansaa'u dake gidan aure.

Motsa yatsun tayi kadan,kamar tasan su yake kalla,hakan sai ya sake daukan hankalinsa,yabi yatsun da kallo yana jin kamar ya miqa hannu ya shafa yaji yaya suke?,yaya lallen yake a hannunta?.

"Zan iya samun hanya?" Ta sake fada still ba tare data kalleshi ba.

A hankali ya janye gefe yana bata isashiyar hanyar da zata wuce din. Ta qasa......ta qasan da idanunta ke zube saman rufaffun takalman qafarsa taga yaja bayan,wani abune yayi mata tsaye a rai,don tace zata tafi?,sai kawai ya bata hanya ta sauqi irin haka?.

"Kina lafiya?,ba wani matsala?" Ya sake fadi da muryar da tafi ta dazu laushi. Kai kawai ta gyada masa a hankali taci gaba takawa tana wucewa.

Baisan me ya tsaidashi a gurin ba,yaci gaba da bin takunta da kallo,abinda a yau karon farko ya fara noticing. Wani irin cat walking,kowacce qafa kaman akwai qa'dar ajiyeta.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 16*

*_A K H N A N_*

Tun daga wankanta zuwa kammala shirin baccinta komai ne yake dawo mata cikin kanta daki daki. Wannan kusancin......wannan kallon......wannan qamshin nasa da yake sake mannewa cikin zuciyarta da rayuwarta gaba daya.

"Me yasa yake da izza har haka?" Ta sake nanata tambayar da har yanzu ta gagara samun amsarta.

Tunda take a rayuwarta,ba zata iya tuna wani namiji da izza ke nunawa cikin komai nasa ba irin haisam din,haka malaman suke?,ko kuma daga shi dinne?.

Sake qanqame jikinta tayi guri guda gami da cusa pillow tsakanin qirjinta kamar zata maidashi cikinta.

"Me yasa yake saurin surrender?......me yasa idan nace abu baya kafewa akai?" Ta sake tambayar kanta tana jin wani rashin dadi. Kaman dazu,ta dauka zaice ba zata tafi ba,ta dauka zai gaya mata uzurinsa na qarin kwanakin da yayi akan wadanda yace zayayi din,amma babu ko daya a ciki. Hasalima sai daga qarshen qarshe yake tambayarta lafiyarta......wannan shine MIJIN?.

Tambayar data yiwa kanta na qarshe ya karyar mata da zuciya,sai taji wani dumi cikin idanunta kamar hawaye yana son taruwa. Ta lura da sauye sauye kan komai na sassanta,kama daga cima,yanayin tsaro da sauransu,koda bata tambaya ba tasan daga shine.......amma kuma sai taji duka kamar wannan bai gamsar ba.

"Me yasa kike damuwa.....miji ne fa kawai da aka aura miki ba amincewarki" Wani sashe na zuciyarta ya rada mata hakan a hankali,abinda ya sanyata ware dukkanin idanunta tana kallon bangon dakinta duk da duhun daya mamayeshi,kamar meson tuna wani abun na daban. Kuma kamar jira akeyi tayi hakan wayarta dake silent ta fara haske.

Idanu ta zubawa wayar,zuciyarta na bugawa a hankali a hankali. Haka kawai takejin wani fata yana shigarta game da kiran wayar......haka kurum take raya wani abu kan kiran daya shigo mata wayar a daidai wannan lokacin,wannan fatan da saka ran ya sanya ta miqa hannunta da hanzari tana daukan wayar,saidai kuma sunan aisa ta gani baro baro saman wayar.

Mamaki kadan ya kamata........tadan ware idanunta,aisa a irin wannan lokacin?. Ta sani sam ba dabi'arta bace kira late da dare haka,idanma zata nemeta irin haka inde dare yayi saidai ta shaidawa barratu ko birra su sanar da ita ta duba watsapp dinta.

Dab da kiran zai katse ta dauka,ta saka wayar a kunnenta ba tare da tace komai ba.

"Biftu" Taji muryar aisa da tayi wani irin mugun sanyi ta kira sunanta.

"Aisa?" Ta maimaita sunanta itama tana jin wani yanayi.

"Kiyi haquri biftu.....na kasa.....na gaza riqe wannan amanar,komai yafi qarfina biftu bazan iya ba,zan ajiye zan dawo agadez" Tayi maganan muryarta wani iri. Shuru akhnan tayi,zuciyarta na faffasa yadda taji sautin muryar aisa. Muryar aisa ba haka take ba.....ba haka yanayin aisa yake ba,bata da wannan raunin,tana da taurin zuciya da kafiya shigen nata,duk da cewa ita ta fita sauqin sarrafuwa da sassauci.

"Mene ne aisa?"

"Komai ma biftu,komai ma,amma kiyi haquri ki yafemin,zanzo zamu zauna,komai nawa yana gayamin KIN GAZA AISA.....komai nawa yana gayamin kaman naci amanarki ne,kamar ban kyauta ba,kamar zunubina bazai wanku ba,kamar na zama sanadi.....kamar nice sila" Dukka tayi maganan muryarta tana sake raunana sosai.

Maganganun sunwa akhnan nauyi da girma da yawa,tana qoqarin magana taji alamun aisa ta datse kiran,ta kalli screen din,saita soma yunqurin kiranta amma na'ura ta shaida mata wayar a kashe take gaba daya.

Bata natsu ba,ta miqe ta zauna ta fara kiran shehnaz. Kaman dama wayar na hannunta ne tana jiran kiran akhnan din ta daga.

"Shehi....Qu'est-ce qui se passe avec Aïsa?(me yake faruwa da aisa?" Ta tambayeta da french.

"Je ne sais pas.mmmmc'est étrange,je me demande pourquoi elle pleaurait(Ban sani ba nima,baqon abune wannan.....inata mamakin me yasata kuka)" Ta fada da alamun damuwa sosai cikin muryar shehnaz din.

Shuru akhnan tayi,tana sauraren bayanan shehnaz.

"Tun kwanakin can nake jin yanayinta kamar ba'a daidai ba,bata fadamin ba bata kuma nuna tanaso naji ba shi yasa ban matsa mata ba,amma koma meye gobe ko jibi tace zata taho,ko bata sameki ba ni zan jirata naji" Kai ta gyada a hankali

"Allah ya kaimu". Ta katse wayar sannan ta koma a hankali ta kwanta,saidai har zuwa sanda bacci ya dauketa aisa ce a ranta.

*M A M M I N A*

Bata taba jin tana so tayi kuka a rayuwarta ba irin yau........ta jima kuma bataji kuka yana neman hallaka numfashinta ba irin yau din.

Duk wani hadimi da hadima dake kusa kusa da dakunan baccinta ta sallamesu,ta kuma kulle kanta a daki tayi wani irin kuka harda ihu daidai da yadda take jin baqincikinta zai ragu.

Batasan adadin tsahon lokutan data dauka ba a haka ba,har sai data tabbatar ta samu sassaucin abinda takeji qasan ranta,sannan ta shiga bandaki tayi wanka da ruwan sanyi waiko zata samu sassaucin abinda takeji cikin jikinta.

Dawowa tayi dakin,tayi zaman dirshan,zaman 'yan bori tana qoqarin farfasa tunaninta daya bayan daya.

Ayau,ta samu dukkan tabbaci da yaqinin sheikh muhammad haisam yana cikin jerin sahun mutanen da suka shigo agadez don farmakarta

"Idan ba haka bane?,me ya hadashi da almaz?......kenan dama can almaz din yana hannunsa?,idan haka ne dukka al'ummar villa street suna hannunsa kenan". Wani irin zazzafan gumi taji ya karyo mata,haka kawai takejinta kamar ita kadai ce.....haka kawai takeji kamar ita kadai ta rage a wannan sansanin,......a wannan filin. Batasan me yake damun tafsu ba,cikin kwanaki gaba daya wani nesa takeyi da ita wanda ta bada uzuri da juyawar ciki da har yanzu ta kasa saurara mata. Da waye zatayi shawara?,waye zai hango wata mafitar da ba lallai ita din ta hangota ba?.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Tambayar da tayi mata tsaiwar mashi aka,bata kuma samo amsarta ba......sai wani courage daban da takeji daga wani sashe na zuciyarta.

"Karki yadda ki fadi.....karki yadda kaikai qasa......koda yanzu kina tunani motsinki zai iya zama barazana.......ki bashi lokaci,sanda zai tashi daga agadez zuwa qasarsa......wannan futar ki tabbatar ta zame masa fita ta qarshe daga qasar......daga yankin nan. Fitar da zata sama nisa na har abada tsakaninsa da agadez da kuma sultane.

"Ki daure......a qarasa komai dashi......ya fita yabar qasar,komai zaizo da sauqi" Wani murmushi ta saki,murmushin dake da alaqa da sassaucin data samu da 'yan qanqanuwar mafitar da zuciyarta ta bata.

Burinta a yanzu ba control bane......babban burinta a yanzu shine ta qarasa aikinta na ture kaza daga kan qwai ta kwashe qwan.....kauda sultane me gaba daya,ta kuma tumbuke bishiya daga tushenta,tayi rantsuwa........ta kuma lashi takobin tabbatar da wannan aikin,a kusa ko kuma a nesa.

Wayarta dake gefe ta dauki qara da tsuwwa,ta waiwaya ta zuba mata ido kamar ma ta manta da ita. Kamar ta shareta,kaman kada ta dauka,amma sai sunan dake harbawa saman screen din yaja hankalinta,ta miqa hannu ya daga ta saka a kunne.

Batace komai ba,amma maganan da ake mata daga wancan bangaren ya sanya wani shu'umin murmushi subuce mata.

"Ko a iya nan kun kammala aikinku......inaso kowacce hujja ta bata ta salwanta kamar komai bai taba faruwa ba.....burina akan sahel couture ya gama cika........aiki ya kammala.......ku jira sakamakonku........ina alfahari dakai" Takai qarshe tana cije labbanta da haqorinta irin na zallar muguntar nan,sannan ta zare wayar a kunnenta har yanzu murmushi yana sauka saman fuskarta.

"Kafin na tafi......ya kamata kowa ma ace anbar masa wani babban tabo.....babbar barakar da bazata taba gyaruwa ba" Ta fada a bayyane tana jin alamun nasara na tare da ita kena,tunda har a sanda take zaton faduwa babban labarin nasara yazo mata.

*_RANA BATA QARYA_*

Cikin wani irin tarin nutsuwa yake zaune gaban sultane,wanda ya kebe ne daga shi saishi,duk da cewa shi da maleek ya fara yin magana dasu.

Sanye yake cikin wata qayatacciyar jallabiyya da asalin kudinta ita da cloak thobe din jikinsa yake isa babban jari da tarin al'umma marasa qarfi. Wasu irin thobe da a idanu kawai idan ka kallesu kasan an nunawa kudi iyakarsa wajen mallakarsu.

"Na aura maka biftu ne......saboda fadin manzan Allah.......mu aurar da diyoyinmu ga maza irinka,idan ka sota zaka mutuntata ka mutunta ahalinta,idan ka qyamaceta kuma ba zaka wulaqantata ba........haisam,bazan boye maka ba,ba kuma don ban aminta dakai ba aah......ina sake jaddada maka ne kaji tsoron Allah akan khadeeja.....bazan boye maka ba,inason khadeeja sama da kowa cikin 'ya'yana.....amma hakan........" Sai zuciyar sultane dake kashingide saboda rashin qwarin jiki da yake fama dashi ta raunana. Ya yunqura ya miqe ya kuma zauna sosai,rabon da yaji alamun taruwar hawaye cikin idanunsa tun rasuwar mahaifiyarsa.

"Amma hakan bazai hana na aurar da ita ba,saboda hakan shine cikar kamalar mace.........ina sake baka amanarta......ba don ina kokwanto kan cikar kamalarka ba,a yanzun duk duniya,ba wani d'an adam dana aminta dashi sama dakai" Wani irin nauyi yakeji sultane yana sake aza masa.......wani irin sanyi dukka yake ji yana bin jikinsa. Yana jin kamar bazai iya ba.....kamar bazai kai labari ba. Ya sani,idan ana maganar amana wata abace me girman gaske......abace da idan ba ita tsallake siradi kansa baya yiwuwa a gurin bawa. Zata kasance abu mafi santsi a tafin hannun bawa ranar qiyama,ita zaa aza maka a hannunka ka tsallake wannan siririn zaren da ko kaurin gashi baikai ba.....siririn zaren dake tsakanin wutar jahannama,ka tsallaketa da ita,tana santsi kamar tarwada a hannunka. Duk sanda ta subuce ta fada to zaka bita ne ka daukota don ba zaka wuce ba sai da ita,idan kaci amana zaka yita sintirin daukota daga wuta Allah ya tsaremu,idan kuwa ka kiyayeta lafiya qalau shikenan zaka wuce,wucewar da babu wani bawa da yake da tabbas a kanta. (Ya Allah,ka bamu ikon kiyaye amana....Allah ka tsallakar damu siradi lafiya).

"Muhammad" Sultane ya kira sunan haisam da yanayin daya sanyashi daga manyan idanunsa kadan ya kalleshi.

"Akwai wasu abubuwa a wancan ranar dana gani......akwai abubuwa da yawa dana saka musu ayar tambaya.....akwai abubuwa masu yawan gaske daya kamata ace na sani inaji a jikina hakanan......inason nasan gaskiya muhammad......inaji a jikina akwai wani boyayyen abu......shin zaka iya riqo da hannayena na sauka daga mulkina na damqawa ahmad?......zaka iya dafawa raunina ka fiddani daga cikin duhu zuwa haske?" Maganan ta zowa haisam a bazata,magana data sake tilastashi daga kansa a hankali yana duban sultane,yana masa wani kallo ne dake bayyana gaskiyar magana manufa da abinda yake fadi daga tsakiyar zuciyarsa ne

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 17*

*M O R S A S A F I Y Y A*

Zaune suka a gabanta dukka su biyun,sanye kowaccensu da abaya data banbamta gurin launi da design din ma gaba daya.

Falaaq na sanye da dark mint green,wadda aka saqata da ainihin satin material me kyau da tsada. Yayin da akhnan ke sanye da baqar abaya,Japanese nida da aka saqata daga asalin yadin silk me yauqi dake shaking yana sake qawata farar fatarta dama ainihin kalar baqi wul din da abayar ke dashi.

Zaune suke gaban morsa safiyya,a kebantaccen dakin kwananta da babu kowa a cikinsa,daga ita sai 'ya'yan nata guda biyu.

Dukkaninsu tafukan hannuwansu suna cikin nata,na tsahon wani lokaci suka dauka a hakan,duk wani magana da zata musu koda kalma daya bata bari ta fadeta suna nesa da ita ba,ta damqesu sosai cikin nata hannuwan,tana jin kamar ba zata iya zame hannun nasu daga cikin nata ba.

Wani emotion ne me nauyi tun daga idanunta zuwa zuciyarta,irin wannan yanayin da UWA data aurar da d'iyarta ne kawai ta sanshi a ranar da za'a karbe diyar daga hannunta zuwa gidan wani.

Sheshsheqar kukan falaak ita ta haifar da wani irin shuru a tsakaninsu,wani irin shuru dake dauke da nauyin da zuciya ce kadai tasan iya adadin mizaninsa.

Komai akhnan tana jinsa ne kamar almara,komai tana kallonsa ne kamar wani shirin film ko a littafi. Yau ita akhnan?,itace wani d'a namiji zai dauketa cancakat?,daga mahaifarta?,daga masarautarta?,daga cikin iyali da ahalin data taso a ciki?. Ba Niamey kawai zata bari ba.....ba agadez kawai zata bari ba.....aah,zatabar qasarta da nahiyarta ne gaba daya.

Karon farko da taji kukan falaak ya sanya wani rauni cikin zuciyarta,lokaci na farko da riqon da morsa safiyya ta yiwa hannuwanta take jinsu har cikin qasusuwanta da zuciyarta.

Readers Also Read

More by Huguma