Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 10

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 10

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 10: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 10. "Ya isa falaak.....ya isa ha...." Sai muryar morsa…

3,364 words

"Ya isa falaak.....ya isa ha...." Sai muryar morsa safiyya din ta maqale,salin alin kuma ta hadiye sauran maganganunta gudun kada hawaye ya balle mata,ta karya musu qwarin gwiwar da take musu tattalinta.

"Momma......sultane fa" Muryar ahmad dake takowa cikin dakin ta sauka a kunnuwansu gaba daya. Murmushi ta qaqalo,ta soma qoqarin zame hannuwanta da take zaton falaak ce kawai zatayi gardama,saidai ga mamakinta tsam taji akhnan ta riqe yatsunta cikin nata.

A hankali ta daga idanunta tana duban morsa safiyya din,sai a sannan taga damshin hawayen daya jiqa zara zaran eye lashes dinta.

"Kiyi haquri" Akhnan din ta furta a hankali labbanta suna motsawa. Kai morsa safiyya ta soma girgiza mata,akwai tarin abubuwan data karanta tattare da ita,saidai a yanzun a wannan lokacin ba muhallinsu bane gaba daya.

"Biftu" Ahmad ya fada a nutse yana tsugunnawa a tsakiyarsu yana sanya hannunsa cikin dabara yana raba tsakanin hannuwansu dana morsa safiyya

"Ya isa.....muje sultane yana son ganinku" Ya fada da wani irin yanayi da yasa ba wadda ta masa musu a ciki,ya bude musu nashi tafin hannuwan suka saka hannunsu a ciki ya miqe tare dasu gaba daya.

*_HAISAM/SULTANE_*

"Ina kyautata maka zato fiye da yadda kake tunani" Sultane ya sake fadi bayan gajeran kallon kallon daya ratsa tsakaninsu shida sultane din.

Sallamar ahmad itace ta katse ragowan dukka tattaunawar data rage tsakaninsu.

"Wa'alaikumussalam" Sultane ya amsa sallamar murmushi yana subuce masa daga saman fuskarsa. Idanunsa akan ahmad din wanda ke riqe da hannuwan akhnan da falaak.

Cikin girmamawa ya isa gaban sultane dasu,ya ajiye masa su,a daidai lokacin kuma haisam ya miqe a nutse ya taka yana fita daga dakin. Basai sultane ya fada masa ba,a yanzu a wannan lokacin,baya buqatar izinin sultane waje fita a gurin,lokaci ne na uba da 'ya'yansa,lokaci ne na ganawar mahaifi da yaransa cikin sirrin da su kadai ya shafa.

"Allah yayi muku albarka,Allah ya albarkaci rayuwarku da aurenku gaba daya......bakuyimin komai ba tsahon zamanku tare dani,idanma kunyimin din na yafe......saidai kuma akwai abu guda daya da zaku iyayimin wanda ba lallai na iya yafeshi ba". Dukkaninsu......daga falaak har akhnan sai da suka daga kai a gigice suna dubansa. Da murmushi a fuskarsa yake jinjina kansa.

"Eh,kuqi zaman aure,kuqi biyayya wa mazajenku......ku bijire musu,kuqi binsu cikin abinda Allah da manzonsa suka shard'anta....inde ba cutarwa ba zalunci ba tauye haqqi......ku zauna a gidajenku,kuyi biyayyawa mazajenku,wannan shine abu guda daya da nake buri,nake kuma buqata daga gareku" Ya qarasa fada da wani irin sanyi a muryarsa.

"In sha Allah bappi.....in sha Allah zakayi alfahari damu" Falaak ta fada muryarta na rawa tana kama tafin hannun akhnan tana riqewa cikin nata,kamar tanason ta bata tabbacin maganan data gayawa sultane.

"Allah yayi muku albarka,yasa aljanna ce makomarku"

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Ameen" Labban akhnan suka motsa da qyar ta amsa,kafin muryarta can qasa tace.

"Bappi......ka yafemin" Kalmar ta fito tare da silalowar hawaye daga cikin idanunta. Murmushi ya sake saki,yana jin yadda jikinsa a kowacce rana yakeyin weak.

"Kisa a ranki baki taba batamin ba akhnan......baki tabamin laifi ba......amma nan gaba zaki iya yimin matuqar baki tsaya kin yiwa Muhammad biyayya ba......a yanzu duk wani hasashe naki na ido bazai iya gaya miki waye muhammad haisam ba......amma zan fada miki wayeshi,qila a nan gaba idan kin tuna da kalmata koda bana raye zaki ga ta hau daidai da mizanin dana fada miki......muhammad haisam LU'U LU'U ne......LU'U LU'U n da ke lullube cikin wani guri da hankulan mutane da iyaye baikai kanshi ba.....amma hakan yayimin.....inda hankula sunkai kansa da wurwuri.......qila a yau da banyi nasarar zama surukinsa kamar haka ba" Ya qarasa fadar maganan murmushi yana balle masa. Dukkan alamunsa sun nuna sosai yakejin dadin yanayin......sosai abun yake masa dadi har qasan zuciyarsa.

"Ko bayan bana raye....ko bayan na mutu ki tuna wannan" Kalmar mutuwar daya ambata saita zame mata kaman wani babban abun barazana daya birkitata,ya kuma sanyata fashewa da kukan da tun dazu take neman control dinshi dama,ta fada jikin sultane ta riqeshi da kyau kaman ba gobe.

"Ba zaka mutu ba bappi na......ba zaka mutu ba......zan fasa tafiya na zauna da kai" Riqeta yayi sosai yana share mata hawayen da hannuwansa,Shima tana sake kashe masa zuciya da gangar jiki bayan kasalar dake sake mamayarsa a kowacce rana.

"Kin manta na fada miki farinciki na?,......farincikina shine zamanki gidan aurenki,kibi umarnin mijinki ki samu aljanna khadeejatu"

Kusan a cike farfajiyar gidan take da jama'an da suke da kusanci da ahalin sultane muhammad hammud,yan uwa bayi da hadimai da suka zama tamkar 'yan uwa na jini ga iyalin me martaba.

Motoci ne na alfarma guda goma aka ware don tafiya daga agadez zuwa Niamey,cike da hadimai da zasuyi masu rakiya har zuwa sanda zasu tashi daha babban filin sauka da tashin jiragen sama na Niamey Diori hamani international airport,wanda daga can suka tsara yadda zasu tashi zuwa jedda

Sultane ne da kansa riqe da hannuwansu yana takawa ta jerin mutanen dake tsaitsayi hagu da dama suna bankwana dasu cikin nuna kulawa da soyayyar da ta samo asali daga adalin mahaifinsu.

Haisam da maleek din dukkaninsu suna bayan sultane din,cikin kamala da shigar dake sake nuna zallar haibarsu.

Motocinsu ya banbanta,kamar yadda sultane ya sanya kowacce cikin motar da aka tanada don tafiya da ita ita da mijinta.

Janyewar sultane baya ya soma takawa don barin gurin gudun tsinkewar zuciya shi ya bawa mammina daman matsowa. Cikin wannan shigar dake nuna alfahari fariya da izzarta.....cikin suturar da kowanne lokaci take zabar mafi qyalqyali da jan hankalin sutura don nuna tarin girman isarta.

Idanunta cak saman fuskar haisam......saman fuskar haisam din da ko sashen da take bai kalla ba,hasalima ya maida hankalinsa wajen tura saqo ga dukka ayarin ta hanyar na'urar dake cikin wayarsa na cewa airport din agadez zasu nufa maimakon bin kwalta zuwa Niamey kamar yadda aka shirya da farko.

"Yata......ba shakka zanyi kewarki......irin kewar da ban taba irinta ba,banda aure ba wani abu da zai iya yimin wannan yankar qaunar tsakanina dake,saidai na godewa Allah daya sanya komai zai zamana na gajeran lokaci ne........kada wani yanayi ya rudeki ki manta da mafarkanki......jajirtacciyar mace bata yin barcin da zai kaita ga mantawa da mafarkanta dama burikanta........ka tsaya tsayin daka,ka gina mafarkinka......ka gina burinka......karka bari wannan mafarkin ya rushe.....wannan shine cikar jajirtacciyar mace........kina da dama.....kina da fili.....kina da gurbi.....kuma kina da sarari na gina mafarkanki,koda hakan yana nufin zaki canza hanya da mutane masu yawa". Tayi maganan tana runtse hannunta cikin na akhnan.

Haka kawai akhnan takejin bataji wannan kewar ba......haka kawai takejin bataji wannan yanayin ba da taji a tare da morsa safiyya sanda hannunta yake cikin nata.

Ba komai da takeji illa burin zame hannunta cikin nata,haduwar hannuwansu guri guda baya tuna mata da komai sai alqawuranta......wadannan alqawuran da sukaso rudar da ita.....suka jefata wani mummunan yanayin da har yanzu bata da tabbacin ta fita ko tana ciki?. Banda nutsuwar da take samu a yanzun batasan wanne suna zata kira kanta ba,batasan wanne suna zata kira rayuwarta dama dukka sauran burikanta ba.

"Sheikh muhammad haisam" Ta kira sunan haisam kai tsaye. A nutse cikin wani irin yanayi da kallon dake dauke da ma'anar BAKI DA MUHIMMANCI ya zube idanuwa fes saman fuskar mammina din. Fuskar daya tabbatar shi yaga dama ya barta har zuwa yanzu......harma takejin tana da zarra da qarfin halin furta wadannan kalaman.......amma ya tabbatar yayi imani abinda ya tanadar mata saita gwammace bata taba walqawa cikin rayuwarsa shi muhammad haisam ba.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 18*

"Ina fatan dai ka sani.....duk da cewa komai temporary ne......buzuwar mace......tana da cikakken 'yanci,mata ne masu 'yanci,masu son 'yanci.....masuson walwala da barinsu suyi rayuwarsu cikin sakewa,basusan wahala ba ko wasu dokoki da zasu taqaita musu jin dadinsu ko walwalarsu ba.....saboda haka nake cewa,ka kula da ajiyarmu zuwa lokacin da zamu karba.........inaso kayiwa agadez kallon qarshe....don ba lallai ka sake samun dama kwatankwacin wannan a rayuwarka har abada" Ta qarashe maganar da wani irin kallo cikin idanunta.

Nasa kallon ya zurfafa a kanta,kallon da duka duka na sakanni biyar ne,saidai qasa da second biyar din wani abu me qarfin gaske ya nemi rusunar da nata kaifin ganin.

Abu na qarshe daya daketa sosai har cikin jijiyoyinta murmushi ne.....murmushi daga fuskar haisam......murmushin da bata buqatar fashin baqi ko qarin bayani daga gurin kowa. Da baya take ja a hankali amma idanunta suna kan motocin da suka fara hawa saiti don fita daga masarautar.....motar dake dauke da lamba shidda casss.....motar da haisam da akhnan suke ciki,motar da takejin tana dauke wasu abubuwa da suke da nauyi a mizanin Rayuwarta. Saidai kuma murmushi ya subuce mata,murmushi ya kubce mata saboda hangen nasara......samun sarari da kuma samun cikakkiyar dama na sarrafa SULTANE da masarauta gaba daya.

Saidai wani abu guda da bata sani ba......sanda take kwance a lokacin haisam ya tsere mata da wani irin matakin nisa a gudu......sanda take fara tunani......a sannan haisam ya kammala nasa har ma ya rufe babin yana jiran chapter ta gaba.

Sanda motocinsu ke kammala fita daga gidan......sanda ta juya tana komawa ciki cikin murmushin nasara......a daidai wannan lokacin 'yan press(yan jarida) motarsu ke kutso kai,daga babban gidan tv da radio na qasa.

*_Tofa.......😄,me kuma zai faru?_*

Wani irin shuru ne ya ziyarci cikin motar,shurun da haisam yayishine yana qoqarin controlling fushinsa. A yanzu babu muhallin yin fushi,sarari ne da fara shimfida girbi bayan baqar shukar da aka dade ana yinta. Shurunsa yana zarcewa ne da maimaita kalaman zaituna cikin kansa. Mara kunya duk a inda yake mara kunya ne. Bai taba zato zata iya ci gaba da duban idanun wani daya shafi ahmad ba balle ta nuna fake love din da take masa,ciki kuwa harda akhnan din. Akhnan din daya gama fahimtar wasan data shiryayi da Rayuwarta ba qarami bane,CETONTA ko shine ya zama silar tsoma qafafunsa kenan cikin agadez?.

Dab da isarsu airport din ya waiwaya a hankali zuwa sashen da take zaune. Kowacce rana tana sake tabbata ITA DIN MALLAKINSA CE......a yanzun gata sukutum da guda gaba dayanta sultane ya damqa ragamar Rayuwarta a hannunsa da dukkan yarda. Zai iya tsallakewa kuwa?,zai iya cinye wannan jarabawar?.

Baya iya ganin fuskarta......amma yana iya ganin zara zaran yatsunta data gamesu guri daya tana murza zoben dake tsakiyar yatsan nata. Koda baya ganin fuskarta yana jin akwai hawaye me yawa kwance cikin fuskarta. Idan tayi kuka yanzu......idan a yanzu tana kuka kadai saboda barin agadez.......me zataji?,yaya zatayi a sanda tasan wacece mammina?.

Wani radadi takeji da zugi cikin ranta....wannan tsohuwar aqidar wannan tsohon ra'ayin yanason yunquro mata. Ya rabata da mahaifarta......ya rabata da kowa nata......ya dauketa cancakat zai kaita qasarsa garinsa ba tare da tasan wayeshi ba....zai kaita inda ba idanuwan sultane babu kulawarsa......dukka don kawai buqatar kansa?,duk kawai don shi yazo a NAMIJI?. Tun daga mataki na farko.....tun a yanzun da mintuna da awannin kasancewarsu tare suka fara harbawa,ta fara lissafawa da qididdige yadda abubuwa masu tarin yawa nata suka fara juyewa zuwa MALLAKINSA ciki harda nasabarta da sunanta.

Iya wannan abun tunanin dake zukatansu ya wanzar da wani irin shuru,wanda bai yanke ba sai sanda suka isa airport din bangaren private parking lot na airport din.

Dukka motocin suka tsaya,sai a sannan ta daga blue eyes dinta a hankali tana duban airport din. Mamaki kadan ya kamata,kaman idan taji daidai zasu wuce Niamey ne a mota saboda ba jirgin da zai tashi a daidai wannan lokacin,amma me sukeyi cikin airport din.

Bata kalleshi ba,amma tana jin sanda driver ya fice daga motar daga can bangarensa,motar ya zamana daga shi sai ita kadai.

Wani shurun ya sake ratsawa tsakani,tana jin kamar wani sabonshi ne,ya kuma zame masa jiki. Jinkirin fita a duk sanda sukazo wani guri,har sai kusan wanda ke dakon fitowarsu hankalinsa yakau. A baya yana bata haushi da hakan da yakeyi,amma a yanzun saita tsinci kanta da lalubar dalili?.

Izza ce ko kuwa?. Qasaita ce ta masa yawa?,wanne irin izza ne wai a jininsa?. Tambayar data fusgeta har takai ga daga idanunta da har yanzu taketa ririta hawayen cikinsu ta kalleshi.

Kaman ko yaushe,kaman yadda ya saba mata,wannam attitude din nashi dake bata haushi. Ba ita yake.kalla ba......wayarsa yake kalla. Ba ita yake kalla ba,hankalinsa ba'a kanta yake ba. Me yasa sai ita zata dinga kallonsa?,me yasa sai ita zata dinga satar kallonsa?. Hasalima ai sultane tasan ya basa amanarta. Me yasa bazai damu da ita ba?. Irin duk motsinta dinnan idanunsa yana kai?,irin duk wani tari nata ko qanqani ne ya tamabaya.

Wuf tayi ta zare idanunta daga kansa sanda yake motsa manyan idanunsa yana dagasu xuwa kanta. Kafeta yayi da kallo sanda take dauke idanunta cikin basarwa. Ya jita.....yaji duk wani kallonta a kansa,har iya tsahon mintunan data dauka din.

Bata zata ba batayi tsammani ba taji hannuwansa saman kanta.....dukka hannuwansa guda biyu inda yasa yatsunsa yana jan bannan veil da tayi rolling dashi saman kanta.

A nutse ya ajiye idanunsa gaban goshinta,inda wani sashe gashinta me santsi da baqi ke kwance luf gaban goshinta. Irin sumar nan ta cikakkiyar buzuwa da tayi gadon suma ta kowanne bangare.

Bugun zuciyarta ya tsaya na wucin gadi,ta dauke numfashinta dif tana jin yadda zuciyarta ta dawo aiki da wani irin gudun wuce sa'a sanda ya sanya yatsansa a hankali kamar me tsoron taba qirjinta yana sakin tattara tattarar da mayafin yayi saman qirjinta.

"Bazan iya jure wannan shigar ba......material na abayar nan yana showing........" Sai kuma ya dakata yana jan jikinsa baya.

Ko da ba gaya mata ba,tana jin yadda kalmomin da haruffan suka fito a rarrabe,kamar bugun zuciyarsa keson hana sautinsa fita daidai.

"Subhanallahil azeem" Yake fadi idanunsa a lumshe,yana jin yadda bugun zuciyarsa ke rarraba numfashinsa. Tsahon wasu sakanni,sannan ya bude idanunsa a hankali. Abubuwa da yawa,abubuwa da yawa ya gani saman fuskarta saboda wani irin kusanci daya wanzu tsakaninsu sanda yake qoqarin daidaita komai nata kada wani sashe na Jikinta ya bayyana.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

Wata irin glowing skin dake shimfide saman fuskarta,wasu irin eye lashes da eye brows da suka kusa hadewa da junansu. Wata irin lobawa daga tsakiyar habarta harma da gefan kuncinta guda daya.....ga kwantaccen sumar data yiwa goshinta ado daya tabbatar ta sauka har kusa da kunnenta.

A nutse ya bude murfin motar,ya fice,ta bude idanunta a sace tana kallonsa. Takunsa na dabanne......wani irin taku da tunda take ganin nau'in isassun maza bata taba katarin ganin wani da irinsa ba. Tayi gaggawar kauda kanta sanda ya iso bakin qofar da take zaune,ya saka hannu ya bude mata murfin motar kamar yadda ya saba yana ja da baya don bata hanya.

Ta gefe ta sake satar kallonsa,still ba ita yake kalla ba,ya tsaya kawai daga bayan qofar da wannan wayar dai a hannunsa. Saita dauke kanta ta hadiyi wani yawu da haka kawai taji ya mata tauri da d'aci.

Ranta taji ya dan jagule,ta motsa a nutse tana sako qafafunta waje,daidai nan ya matso da sauri,ya sanya hannunsa da nufin ja mata rigarta ta sauka ga qafafunta,idanunsa suka sauka saman fararen qafafunta masu dogayen yatsu wadanda jan lalle ya yiwa wani irin ado me daukan hankali..

*M A M M I N A*

Bayan juyawarta zuwa cikin gidan sai takejin iskar gidan yau kawai ta dabance,kaman yadda ta tabbatar nishadinta zai zama na dabanne.

Almaz yana maqale a ranta,saidai tana ganin abune me sauqi bazai zame mata matsala ba. Ta sanshi tun yana qanqaninsa,duk wata tarbiyya da raino nasa itace ta bada wannan horon,ta yaya dabbar daka raineta da hannunka ta isa ta zame maka barazana?.

Ta tabbata ta kuma yi imani haisam baisan me yakeyi ba.....kodai lissafi ya kwance masa,ko kuma tsananin murnar samun akhnan......akhnan din da yake kalla kamar banza ta samu sama taka ya sanya ya soma daburcewa a lissafinsa. Wanda ita hakan yayi mata daidai,akhnan zata zama tamkar fatsar da zata kamashi a hannunta tayi wasa sa rayuwarsa har sai yayi nadamar ajiye malinta ya dauki bangaren bin diddiqinta.

"Allah yaja da ran giwa.....Allah shi riqa miki" Maher.....maher d'aya daga cikin irin da haisam ya bari agadez......maher din da a yanzu mammina ke hasashen sakashi a gaba ya maye wasu gurabe na mutanen data rasa ya furta maganan cikin tsananin girmamawa.

Murmushin jin dadi ta saki,yaron yana ranta tana jin kuma wani aminci a kansa,saidai duk da haka ta dakata ne ta gama karantarsa. Sau da dama yana cikin wadanda ba'a gulmarta idan an ganshi,saboda yadda yake girmama sunanta ma kadai da duk wani abu daya rabeta ballantana ita kanta.

"Me yake tafe dakai?" Tafisu ta tambayi maher.

"Yan jarida ne.....daga gidan talabijin da radio na qasa.....sukeson tattaunawa dake" Ta danyi jim tana duban maher din.

"Tattaunawa?" Ta tambaya cikin son qarin bayani. Kai ya gyada.

"Itafa Allah ya baki yawan rai......qoqarinki da jajircewarki akan mutanen qasarki da yankinki.....labarin alkhairanki daya karade ko ina shine silar zuwa su tattauna dake,sunce ki musu afuwa basu sanar ba basu nemi izni ba kafin yanzu.....amma a yanzun ma idan kina ganin saidai suje su dawo a basu lokaci zasu aikata hakan" Ya qarasa fada yana karantar yanayinta. Shuru tayi na daqiqu,shurun da tafisu ta katseshi ta hanyar fadin.

"Ba girmanki bane....karamci ne a tare dake ki karbi baqin da suka zabeki ke kadai,duk da ba ke kadai bace matar sultane amma sukace dake sukeson ganawa". Murmushi ta sake saki a hankali,tafisu tazo da magana. Wannan dalilin ya sanya takeson tafisu sama da kowa cikin mutanenta. Tana da wani irin hasashe da hangen nesa me zurfi.

"A basu guri mafi kyawun dauka.....zan shiga ciki na canza saina fito".

"An gama Allah ya taimakeki sarkin karamci" Maher ya fadi yana miqewa sa gaggawa.

A yau sai ta sakejin kanta yana fasuwa.....bawai don bata taba hira a kafar yada labarai ba.....aah,saidai wannan din tazo mata akan gabobi masu yawa,tazo mata da wata babbar dama da zata isar da wani saqo cikin sanyin rai.

Sutura ta alfarma tasa aka sake ware mata,tasa kuma akayi aiken kabakin arziqi ga tarin masu daukan rahoto da labarai daga gidajen tv da radio masu yawa bisa jagorancin babban gidan jarida na qasa. Tasa a shaidawa sultane zatayi ganawa da 'yan jarida,bai kuma hanata ba tunda kusan lokaci lokaci tana yi din.

*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*

*Lambar asusu:- 6019473875* *Safiya musa abdullahi* *Keystone bank*

*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*

08187255862

*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*

*2349166221261* *Safiya musa abdullahi* *NITA* *CFA 1,000*

*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*

08187255862

*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*

*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA* 09166221261

*SHAIDAR BIYA* 08187255862

*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*

*QASAITA👑*

*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*💎

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 19*

Bata dauka haka yawan adadinsu yake ba sai data fito zuwa gurin,fitowartata kamar waa shugabar qasa hasken camera ya fara haskawa tako ina na masu qoqarin daukan hotonta.

Har qasan ranta taji dadi.....har qasan ranta kuma taji ta sake fashewa da wani irin taqama izza da alfarma,sai data zauna sannan kowa ya zauna suka sake miqa gaisuwa bisa wakilcin mutum daya.

Ta amsa musu da salon amsawarta dake dauke da izza da kuma son nuna ita din macece me kirki,kuma ita ta kowa ce,daga bisani ta basu dama,wanda kuma ya kasance shine me wakiltarsu gurin mata tamabayoyi ya matso ya soma gabatar da kansa.

Tambayoyi ne daya bayan daya suia fara mata kan irin ayyukan da ita kanta take gudanarwa al'ummarta. Daya bayan daya take zaqulo dukka ayykan da tayi,manyan ayyukan da dukkaninsu tana yinsu ne saboda ta sake kafa kanta......tana kuma yinsu ne saboda biyan wata buqata ta qashin kanta.

Sai da suka shafe sama da sa'a guda kowanne gidan jarida yana nadar hirar,bayan data dakata alamun da suke nuna takai aya,sai ya saki murmushi.

Readers Also Read

More by Huguma