Kenza eBookz

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 83

L u'u l u'u book 3 complete by huguma - Chapter 83

L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 83: L u'u l u'u book 3 complete by huguma Chapter 83. "That I was already in trouble." Ta hade gira.

3,373 words

"That I was already in trouble." Ta hade gira.

"Wane irin trouble?" Sai ya dan matsa yatsunsa dake cikin nata.

"The kind where a man stops thinking about himself."

Akhnan ta ji wani irin abu ya taba zuciyarta. Inde zai magana da ita irin haka,sai ya sake matsa zuciyarta da soyayyarsa.

Ko yanzu.....a irin wannan lokacin......har yanzu yana qoqarin rage mata tsoro,bai barta da firgici ko damuwa ba.

Sai kuma wani motsi ya sauya yanayin dakin.

Likitocinne suka fara magana da juna cikin farinciki a muryarsu.

Akhnan ta juya kanta kadan,bata fahimci komai ba tukuna. Saidai a take qaramin sauti ya cika dakin. Rauni sosai a muryar dake son nuna jarumta da qwazo......sabon sauti ne.....mma ya isa ya sauya komai.

Hawaye taji sun cika idanunta kafin ma ta sani. Ta sake juya kai zuwa ga haisam.

Fuskarsa ta sauya gaba daya,kamar mutumin da aka cire masa duniya aka ba shi wata sabuwa.

Bata taba ganin irin wannan fuskar tasa ba. Fuskar dake shimfide da wani sabon farin ciki tsantsarsa.

Sai ya lumshe idanunsa na dan lokaci,kamar yana godewa Allah a ransa.

Da ya sake bude su....suka hadu da na akhnan.

Kasa magana yayi,don yaji kawai ba'a buqatar kalmomi. Sai ya daga hannunta ya sumbaci bayan tafin hannun a hankali,sannan cikin murya mai rauni da ba ta taba ji daga gare shi ba yace

"Thank you,akhnan." Hawayen da take qoqarin hanawa suka zubo jin wani sabon kukan bayan wancan daidai sanda haisam ya gama kissing hannun ta yabar mata wani abu me taba zuciya.

Ta yi murmushi a hankali a lokaci guda,saboda a wannan lokacin....ta san cewa ko bayan shekaru masu yawa ne.....idan ta tuna wannan rana. Abin da zata fi tunawa ba tsoro ba ne. Sai yadda haisam ya kalleta.....kamar ita ce kyauta mafi girma da Allah ya taba yi masa a kaf rayuwarsa.

"Wait." Muryar likitar ta ratsa dakin. Dukkansu suka tsaya kafin a hankali daya daga cikinsu ya kalli monitor.

"Doctor..." Ya kirata Wani irin shiru ya ratsa dakin. Kamar ita kanta ba ta yarda ba likitar dake duba cikin akhnan din.

"I think..."

"...there's another baby." Miqewa tsaye kawai haisam yayi,har yanzun dai bai saki hannun akhnan ba,amma mamakin da yaji yana juyashi sam sai yaji bazai iya zama ba.

"There's another baby." Ta sake maimaitawa sanda ta tabbatar.

Zaro ido akhnan tayi "Another baby?!"

"We were told twins." Haisam ya fada yana jin yau duka kaman jarumtarsa ta qare.

"So were we." Likitan ta fadi itama.

Har yanzu yana tsaye,kamar an dakatar da tunaninsa,har zuwa sanda daya daga cikin nurses ta zagayo ta kawo masa daya daga cikin jariran da aka gama gyarawa.

A hankali ya karbe shi......ya karbeshi da hannayen nan nasa. Hannayen da suke riqe na'urori domin binciken tabbatar da gaskiya. Hannayen da suka rattaba manyan yarjejeniyoyi. Yanzu kuma... Sune suke riqe da jariri.

"All yours." Nurse din ta fada tana nuna masa bangaren da guda biyun ke kwance ana gyarasu suna sake rikita dakin da kuka.

A nutse idanunsa suka koma kansu. Na farko. Na biyu. Na uku. Sai ya yi wata irin murmushi me sauti qasa-qasa. Wannan murmushin da akhnan bata taba ji daga gare shi ba.

Idanunsa ya maida kan yaron a hankali. Kyakkyawar halittar me wani irin kyau da shiga zuciya. Komai nasa qanana masu kyau da daukan hankali,da kamannin da baisan da baisan na waye ba shimfide saman fuskarsa. Shi ko akhnan. Wata irin qaunarsa ta farat daya ta soma shiga zuciyarsa,qaunar daya tabbatar ashe sanda yana cikin akhnan qaunar bogi ce yayi musu,yanzunne yake ta haqiqa da gasken gaske take shiga.

Da kansa ya taka ya kawo matashi saitin fuskarta.

"Twins ko?" Ta fada tana son samun tabbaci. Haisam ya sauke idanunsa a kanta,sai ya girgiza kai a hankali.

"Apparently not." Ta yi dariya cikin hawaye tana jin yadda zuciyarta ke bugawa da qaunarsa shi da abinda yake riqe dashi da sauran 'yan uwan da bata gani ba.

Shi ma yayi murmushi. Sai ya matsa kusa da ita,ya sumbaci goshinta,sannan ya rada mata

"Akhnan..."

"Mm?"

"Next time..." Ta daga gira,sai ya kalli jariran uku.

"...we're discussing this with Allah first." A wannan karon har likitocin suka yi dariya. Yadda komai nasa ke cike da nutsuwa.....komai nasa ke cike da addinin nan da kowa ya sanshi dashi. Wani miji na daban suma suke gani,wanda ya sanya sukayi wata irin tiyata me sauqin da basu taba irinta ba.πŸ’Ž *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*πŸ’Ž

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 152*

Ya tayasu sun mantar da matarsa a inda take ba tare da allurar bacci ba. Kallo kulawasa kaffa kaffa dake cikin idanunsa a kanta na dabanne,ba irin wanda suka saba gani a idanun kowanne magidanci bane.

A gurin....sun sake ganin wata fuska tashi ta daban,da duniya bata san da ita ba. Wani sassauqan yarima.....wanda farincikin iyalinsa.....kulawa dasu ya sanyasu sama da komai nasa.

Akhnan kuwa ta kasa daina murmushi,idan ta tuna ba twins ba ne. Ba kuma daya ba ne......Allah ya ba su fiye da abin da suka yi tsammani,sai taji kamar sa'arta ta kere ta kiwa a rayuwa.

A wajen theatre dukkaninsu sultane jira sukeyi. Sanda qofar ta bude nurse din ta fito don ta musu albishir dukkaninsu sukayo kanta.

"Ya suke?" Dariya tayi cikin nishadi.

"They're fine."

"They?" Hussam ya fada yana matsowa kusa da imda nurse din take tsaye.

"All three of them.."

"Three?" Morsa safiyya ta fadi da wani irin tarin mamaki a fuskarta.

"Three?!" Noorah itama ta sake fadi tana sakin qaramin ihu.

"THREE?!" Hussam ya sake fada yana qara fidda ido sosai.

"Three healthy boys" Nurse din ta sake jaddada musu albishir dinta na farko.

Morsa safiyya ta fashe da kuka. A wannan karon ba ta iya tsayawa ba.

"Alhamdulillah..." Kusan dukka bakunansu ke furtawa.

Sultane ne ya janyeta yana lallashinta,kafin ta nutsu ta zauna. Tana kuka tana dariya lokaci guda,wanda bata taba sanin ana hakan ba sai a kanta.....a kanta a yanzun.

A cikin dakin kuwa an gama komai. An shirya akhnan da duka yaran zuwa dakin hutu. Sannan aka kawo yaran kusa da ita.

Ta waiwaya a hankali tana duban qananan fuskoki uku. Qananan hannaye uku.

Ta kasa magana,kawai kallonsu takeyi,sai ta waigo ta kalli haisam,nan ma ta tarar shima kallon yaran yakeyi kamar wanda aka cire masa numfashi.

"Haisam." Bai amsa ba.

"Haisam." Ta sake kiransa.

A hankali ya kalleta,Idanunsa sun sauya launi da yanayin dake nuna yanayin ya taba jikinsa sosai.

"Yan uku." Ya maimaita a hankali

"Three." Ta sake maimaita masa,sai ya yi murmushin da ba kasafai ake gani ba. Murmushin farin cikin da ya fito daga zuciya.

"Allah has a sense of humor." Sai ya kama hannunta. Ya sumbaci bayan hannun.

"You gave me a kingdom." Ya fada da wata murya me kama da rad'a.

Lallausan murmushi tayi cikin hawaye,tana jin wata falala da ni'ima daga Allah tana lullubeta.

A ranar ba kamfanoni ba ne. Ba dukiya ba ce. Ba sarauta ba ce. Abin da ya fi komai muhimmanci ga haisam shi ne matarsa da kuma qananan yaransa uku da Allah ya ba shi lokaci guda. Kyautar da baiyi zato ba.

Daya bayan daya ya daukesu,yayi musu huduba kaman yadda addinin musulunci ya tanada. Tana daga kwance bacci yanason kwasarta,amma shine a idanunta. Shi da yaranta. Shi dasu kewaye a gabansa yana daukarsu daya bayan daya.

Ko sanda zai gama musu hudubar bacci yayi awon gaba da ita. Ya taka zuwa gabanta a nutse ya tsaya murmushi yana fita daga fuskarsa. Ya dora hannunsa saman sassalkan gashinta me tsaho da santsi da hular dake kanta ta zame saboda santsin gashin. Ya tsugunna a hankali yayi kissing goshinta.

"Allah yayi miki albarka" Ya maimaita har sau biyu yana jin yadda soyayyarta take ratsa zuciyarsa da wani sabon babi da muhalli na daban.

Yinin ranar gaba daya asibitin ya zama wani guri na zirga zirgar jama'a. Familyn motii aba jifar gaba daya a hautsine yake da murnar samun yara uku lokaci guda. Yaranma wadanda suka fito ta tsatson yarima muhammad haisam.

Batasan gata suna ya tara ba sai yanzu.....batasan gara a rayuwa hawan hawa bane sai bayan data haifi yaran.

Zamanta a asibitin ya sanya ta gane a baya qaryar gata take. Zamanta a asibitin ya sanya ta gane tsananin zurfin son da haisam yake mata wanda a baya bata gama fahimtarsa ba ashe kwata kwata.

A zaman asibitin ta sake yarda dashi da dukka komai nata. A zaman asibitin taga other side dinsa cikin kwanaki uku kacal. Baya kunyar kowa a kanta,baya shakka ko kowanton nuna mata kulawa. Baya barin kowa da hidimarta. Komai shike mata,abinda ya sanya ta sake tsinkewa da lamarin. Idan ka ganshi zakayi tunanin ba shine wannan yariman ba.....ba shine mamallakin manyan kamfanunuwan turare......fitaccen malamin nan.....jinin sarauta daya tara dimbin ilimin addini dana boko ba.

Hatta da saka drip allura bada magani dake wuyan nurses ya azawa kansa shi. Kome yake idan lokaci yayi zaka ganshi ya iso asibitin ya shigo dakin. Ko a gaban waye zai dauki yaransa ya rungumesu,ya gaya musu yayi missing dinsu. Zai matsa gaban gadon,zai riqe hannuwanta,zai gaya mata yayi kewarta,zai kuma tambayeta dame dame tayi sanda baya nan?. Dame dame take buqata a yanzun?.

Cikin yaran waye yayi kuka?,wayi yayi bacci sosai?. Bame zazzabi?,bame wata damuwa?,idan kaga yadda yake tambayar komai daki daki sai ka dauka ya jima basa tare,kaman tazarar kwanaki ne suka raba tsakaninsu ba 'yan qananun awanni ba. Yawancin lokuta yana shigowa dakin kowa ke fita ya basu guri. Cikin kwanakin wani abu daban take gani a qwayar idanunsa da ya ninka wanda take gani a baya.

Kwana uku kawai.....amma ya zame mata wata duniya ta daban. Ya bar mata tarin memories da har abada ba zasu taba shafewa daga rayuwarta ba.

Batasan adadin mutanen data gani ba masu zuwa marabtar yaran.....a hakanma asibitin da haisam sun iyakance adadin masu ziyara a kullum.

Har a ranar da suka cika kwana ukun bataji komai game da sunan yaran ba. A ranar ne kuma group na 'yan shidansa suka iso asibitin dukkaninsu a tare don ganin yaran.

Yana dakin a sannan,yana zaune a gabanta,ya tsirata da idanun nan nasa yana bata magani tana karba tana sha da qyar. Ya rasa wanne irin rashin jituwa ne tsakaninta da magani,ita kuma ya mata kwarjinin nan nasa da bazata iya musa masa ba. Allah ya taimaketa daya daga cikin yaran ya farka,ya tashi kuwa kuka sosai dake alamta yunwa yakeji.

Tsam ya miqe zuwa gadajensu,wani irin gado me kyau hade da rumfar da bazai bawa ko qura daman shiga ba bare wani abu na daban.

Da murmushi a fuskarsa ya ciroshi yana rarashinsa kamar me magana da babba. Daya daga cikin abubuwan da idan yanayi yake sanyata tattara hankalinta gaba daya tayita kallonsa riqe da yaran.

Ya qaraso gabanta,ya tsaya dab da ita har tana jin saukar wannan lallausan qamshin nasa. Sai daya tabbatar da nutsuwar yaron sannan ya daga idanunsa ya sauke a nata.

"Gyara ki feeding nasa" Idanu ta fiddo tayi narai narai. Ta yaya zata fara haka a gabansa?..

Yaci gaba da kallonta yana karantar reaction dinta.

"Eheennn" Ya sake fada yana dubanta. Ya jima yanaso yaga yadda take shayar da yaran,amma saidai ko sau daya a kwanakin bata bari ta basu a gabansa ba,tunda ana hada musu da madarar yara kafin jikinta ya qara daidaita.

"Haisamm" Ta fadi ganin yana matsowa dab da ita ya miqa hannu yana qoqarin zuge zip din gaban rigarta.

Idanu ya zuba mata yana kallonta,saidai kafin yace komai ta zame hannunta daga saman nashi a hankali,ta rufe idanunta tana jin yadda iska ke ratsa fatarta alamun ya zuge zip din gaba daya.

Sai da yaji wani abu ya tsarga masa tun daga tsakiyar kansa zuwa tafin qafarsa sanda idanunsa ke sauka a kansu. Farare tas sun cika sosai,suna tsaye kuma kamar yadda ha sansu. Ya lumshe idanunsa a hankali sannan ya budesu,ya matsa yana dora mata shi saman cinyarta ta hannun damanta ya sanyata ta daidaita zamanta.

Tana jin sanda ya saka hannu ya ciro masa ya saka a baki,tana jin yadda yaron ke cin abincinsa.....tana kuma jin sanda ya koma kawai ya zauna ya zuba mata idanu yana kallonta ita da yaron gwanin sha'awa.

"Me zai hana.....kowanne shayarwa kimin alfarma" Sai ta bude idanunta a hankali a kansa.

".....kiyi alwala kafin kowacce shayarwa" Ya qarasa maganan da alamun akwai abinda yakeson ya sake cewa. Amma bai samu wannan damar ba,noorah da tunda akayi haihuwar ta tare a asibitin ita da camera dinta tayi knocking. Ya bata izinin shigowa,ta shigo da lallausan murmushin nan nata tana cewa..

"Obboo.....yaa maleek......ya khadeem......"

"......da omar" Ya qarasa mata. Kanta ta gyada da murmushi,sai ya miqe a nutse yana duban akhnan.

"Birra zata shigo,ki shirya please,banason kowa yaga komai.....inkin kammala shayar dashi ki fadamin sai mu shigo" Sai ya matsa yayi kissing goshinta yana janyewa da baya a hankali idanunsa a kanta ita da yaran gaba daya,sai kuma ya juya yana ficewa da wannan takun nasa me cike da qasaita yana daga wayarsa data fara ruri,wanda da alama kira ne daga su omar din dake waje suna jiran a musu iso.πŸ’Ž *L U'U L U'U* *_(The diamond)_*πŸ’Ž

*H U G U M A*

*BOOK 03///PAGE 153* _________________________ *_INGANTACCEN MAGANIN SANYI NE SADIDAN,WANDA BA'A CAKUDASHI DA KOMAI BA SAI ZALLAR SASSAQE DA ITATUWA MASU AMINCI_*

*_KAYAN GYARA MASU INGANCI DA WARWARE MATSALAR MATA TA FUSKAR CIWON SANYI WANDA YA KASA JIN MAGANI_*

*_GARZAYA A SIRRANCE KI WARWARE MATSALARKI,KI TUNTUBETA TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE_*

+234 810 914 9876 __________________________

Ajiyar zuciya ta sauke a hankali,ta maida idanunta saman fuskar yaron dake shan madararsa a hankali. Ga mamakinta kamar yasan fuskarshi take kallo sai ya riqe yatsanta gam cikin nasa da nata yatsan. Ba shiri murmushi ya subuce masa,ta zuba masa idanu tana kallon yadda hankalinsa ke kwance a jikinta.

"Ko yaya sunanshi?" Ta tambayi kanta,daidai sanda birra ta turo qofar dakin tana shigowa. Fuskarta dauke da murmushi,idanunta akan gadon yaran kamar kullum kafin ta dauke idanunta ta maida kan akhnan.

"Yarima yace nazo na gyaraki....akwai baqi zasu shigo" Ta fada da girmamawa da kulawa.

"Bari na kammala bashi tukunna" Matsowa tayi daura da akhnan din,tana kallon babyn dake kan cinyarta. Duk bayan sakanninsai ta gyarawa akhnan daukan yaron,idanunta da hankalinta dukka suna kansu. Ta daga kai ta kalleta sanda take karbarsa daga hannunta ta dorashi a kafada don yayi gatsa.

"Birra" Ta kirata wanda ba Kasafai take hakan ba.

"Na'am" Ta amsa tana dubanta.

"Inaso ku fitar da miji ke dasu buhaina......aure zan muku" Ta fada kai tsaye.

"Aure?" Ta tambaya tana fidda idanu waje.

"Eh aure,yara mata ne ku da kuke da chance na aure da haihuwa kamar kowacce diya mace,bai kamata ku zauna kawai rayuwarku ta qare a haka ba". Wata kunya ta gani cikin idanun birran,sai ta sunkunyar dakai tana takawa zuwa gadon da sauran 'yan uwanshi suke ta kwantar dashi a cikinsu,sannan ta dawo ta taimakawa akhnan din ta rufe jikinta da wata kyakkyawar after dress mara nauyi. Ta juya ta fita don sanarwa da haisam sun kammala.

Tun daga nesa ta fara jiyo muryoyinsu,daura da dakin da 'yar tazara kadan.Tun daga corridor din,dariya.....tsokana.....hayaniyar tsaffin abokai da wani irin aminci da yarda da juna da kuma shaquwa me zurfi suka shiga tsakaninsu.

Muryar omar tafi ganewa,don muryar tasa ma tafi ta kowa fitowa.

"Move" Taji Omar din yace.

"Kai.....kabi guy dinnan a hankali,yanzu ya fika matsayi.....he can throw you out ya hanaka ganin babies dinka".

Tuni akhnan ta fara murmushi,Saboda ta san wadannan mutanen,wadannan 'yan shidan....kullum idan suka hadu zaman lafiya kuma ya qare. Sun yita dauki ba dadi a tsakaninsu. Ba can baya da suke zamartaka ba,har yanzun da kowannensu ya zama mahidanci ma,gashi har sun fara tara 'ya'ya.

Qofar ta bude a nutse,kaman ba sune take jiyo hayaniyarsu daga corridor ba. Haisam ne a gaba,kamar wanda ke jagorantar wani taro na musamman. Idanunsu suka hadu da nata,murmushinta ya qara fadada. Yau kam zata ga yadda zaiyi.....mutumin da baison cikakken hayaniya ko doguwar magana. Yau ga 'yan shida ciwon kansa kenan,batasan ya zasu qarke ba.

Maida mata yayi,ya mata magana da ido dake nufin

"Bari kiga wannan rigimar"

"Behave yourself" Yayi maganan yana shan mur.

"We're not children fa captain sheikh....."

".....gaya masa,speak for your self captain" Dariya yayi,irin boyayyar dariyar nan da saidai tasa fuska kawai ta washe.

Daya bayan daya suka fara shiga,dukansu cikin tsari....classy...legant. Da wannan nutsuwar da kamar dukkaninsu sun samu tagomashinta. Kana kallonsu kaga matasan dake tafiya kafada da kafada da nasara. Irin matasan da sukasan kansu suka kafa duniyarsu arziqinsu da komai nasu da ilimi nutsuwa da halal cikakkiya.

Kowanne sai da yayi sallama sanda suke shigowa. Haka ta amsa musu daya bayan daya suna neman sofas din da aka ajiye daga can gefan dakin saboda zuwan baqi irin haka.

Daya bayan daya suka gaidata,abin daya sanyata jin nauyi da kunya kenan. Su kam wai suna mantawa ne da matsayin da suke dashi a idanun duniya?. Me yasa suke da sauqin kai har haka dukkaninsu,wanda idan daga nesa ka kallesu sam basuyi zubi ko kama da mutane masu sauqin kai haka ba.

Ta dauka zata ga su khadeem dasu shehnaz,tunda tunda ta haihu wayarta na ajiye,amma sai ta kasa tambaya.

Omar ne kawai basu gaisa ba,don haka ya matso gaba kadan.

"Sannu da jiki, Princess." Akhnan ta amsa da murmushi.

"Nagode." Ta furta da murmushi tana tuna wasu abubuwa. Tana tuna sanda ta fara sanin da zaman sheikh haisam cikin masarautar agadez. Tare ta sanshi da omar. Omar din kuma shi kadai ne take ganin wargi wani lokaci a idanunsa,amma badai haisam ba.

"Wallahi ka bamu tsoro." Mutallab ya fada yana,nan take Haisam ya daga ido ya kalle shi. Daga hannuwansa mutallab din yayi.

"I'm serious!" Ya fadu kansa tsaye sannan ya kalli Akhnan.

"Mutumin nan ya hana mu sakat." Akhnan ta dan yi dariya tana aza idanunta kadan kan mutallab. Ya tsare mutallab din da ido,saidai a yadda ta fahimta sai mutallab ya gama fadin albarkacin bakinsa bazaiwa haisam shuru ba kaman yadda yakeso.

Omar ya gyada kai. "Three days." Ya nuna haisam.

"Three days yana kiran likitoci fiye da yadda yake kiran mu?." Dariya duka suka sanya masa,akhnan ma tayi qasa da kai tana boye tata.

"Harda ke?" Ya fada da sigar tambaya yana dage dukka girarsa sama hannuwansa harde qirji.

"No....ba laifina bane..." Ta fada tana qoqarin hadiye dariyar.

"Wait....." Amjad ya fadi wanda tuni yakai bassinet din da yaran ke ciki. Juyowa yayi garesu,sannan ya maida dubansa still cikin bassinet din. Ya sake juyawa ga haisam dai.

"Three?"

"Yes." Haisam din ya amsa masa yana hade gira,don yasan halin Amjad da b'allo magana.

"Three actual babies?" Haisam ya kalle shi.

(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)

"Do they look imaginary to you?" Dariya ta kaure a dakin. Har da haisam din,har Amjad dinma da saboda dariya sai daya dafa kujerar kusa dashi.

"Bance haka ba.....amma sun shammaceni ne. Kasan naje Amsterdam.....daga can na biyo flight muka hadu da naseeb,basu gayan triple bane wallahi.....amma dai" Sai ya tsaya yana duban fuskokin sauran.

"Nikam daga yau na sallama.....you're a true hero.....a shekara daya three babies?.....congratulations to us" Ya fada yana miqawa haisam hannu

Haisam ya kalli hannun da amjad ya miqa masa,sai ya sauke idanunsa kan jariran,sannan ya dawo da kallonsa kan Omar.

"Congratulations to us?" Ya maimaita cikin nutsuwa. Duka dakin ya fashe da dariya. Amjad kuwa bai janye hannunsa ba.

"Of course, us." Ya amsa da cikakken qarfin hali.

"Ka manta shekaru nawa muke tare? Wannan nasara ce ta qungiya." Ya fada yana shan mur saidai yanayin tsokana a fuskarsa yana nunawa sosai.

Khadeem ya ballawa amjad harara sannan ya yi qwafa.

"Ka ji dan rainin wayo ko." Amjad din ya nuna shi da yatsa.

"Kai ka yi shiru kawai. Kai ko cat ba zaka iya raino ba." Akhnan ta kasa hana kanta dariya,don bata taba ganin wannan game din nasu har haka ba irin yau.

Dole ba yadda haisam zaiyi da halin Amjad,a qarshe ya miqa masa hannu suka yi musabahar.

"Thank you." Haisam din yace. Amjad ya dan tsaya,saboda ba kasafai Haisam yake fadin irin wannan kalmar ba. Ya sani,tunda ya fadi masa hakan zasu hadu ne a gaba. Amma ya maze yana boye dariyarsa.

"You're welcome." Ya amsa masa.

"Wallahi da gaske har yanzu ban gama yarda ba." Omar ya fada yana duban haisam. Ya nuna na ukun.

Readers Also Read

More by Huguma