Kenza eBookz

Labarina 1 to end complete 1 - Chapter 2

Labarina 1 to end complete 1 - Chapter 2

Labarina 1 to end complete 1 Chapter 2: Labarina 1 to end complete 1 Chapter 2. Zo muje ku gaida mame tana dakin ta ae na dauka bata nan, ina huni mame ina…

4,486 words

Zo muje ku gaida mame tana dakin ta ae na dauka bata nan, ina huni mame ina gajiya ya me jiki hm gata ta warke taki koma wa, ae angama ma lectures sauran mu exam to Allah ya taimaka adage da karatu tom mame,

Na kira ki jiya wayar ki switch off kema kin san indai ba amfani zan da ita ba kashewa nake sbd yanxu nan sai wani ya bata ma rai shiyasa, to me ya faru komai ma. Yanxu me za'a kawo muku kinji kamar wasu baki,komai ma kawo, Kinga wannan ni'iman ta fara sa'anar ta dan Allah ki katse wayar kwacigaba anjima kullum kuna manne da juna iyawa chewingom Ke dan baki san dadi soyayya ba shiyasa kika ce hk shukra bata lbr kun fi kusa, ba ruwa na jiya dadyn mu yace ya fada ma Jameel in ya shirya ya fito Allah wallhi ah kace zamu sha biki uhmmm ae kuma bayan nan to ki fara fada masa kan ya dawo, kin ga sai ya fara shirin kin kawo shawara,

Yawwa mufeeda wllh tunda ya Isma'il yaga pics dinki yake damu na, wai na bashi number din ki sbd nasan halin ki nake zame masa, hmmm Kinga irin ta ko,ko answer ta ki bayarwa,

to me zance miki kin san dai yanxu ba soyayya ce a gaba na ba, Ke mufeeda taso mu tafi kar yamma tayi anjima zamu fita da mama unguwa kar naje na tarar ta tafi,

To ae ko gyara fuska kwayi Ke ni kyale ni wace kwalliya zanyi bayan likaf zan sa, Ke dai ni'ima yi ina jiranki,

Kokarin sa likaf nake sai ga wani matashi d gani Kasan yayan shukrah ne dan suna kama haske kawai ta fi shi, yawwa mufeeda kinga yaya Isma'il din,

ya sai ayita ta kare yaji bani nake hana shi number din ki b,

Ya naga kun fito ko har zaku tafi eh ae mun dade,

mufeeda ba magana cikin daure fuska nace ina wuni ban tsaya jin amsawar sa ba na wuce ina kokarin daura nikaf dina.....

*Love you all my fans* 😍😍😍😘😘😘 [2/15, 7:20 PM] ‪+234 703 962 5239‬: 💕💕💕 *LABARI NA* 💕💕💕

*written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~

Page 70-75

Wai Ke mufeeda me yasa kin fiye wulakanci ae ko ba komai yaya nane kya saurare shi ko dan ni, to inna na ki fa zaki dake ni ko zakimin dole, ni kadai ce macen da zai gani yace ya yana so ga yammata nan a gari, na'ima zo mu tafi in kuma bazaki tafi ba ni ma tafi, to ki tsaya ya fito mu kai ku gida bana so ina da ishashshen kudi kuma ban nagode Allah ya kara sauki,

nai ficewa ta batare da jiran na'ima ba, ya salam wata ran mufeeda Nada matsala wllh, ina mufeeda ta Ke? yaya ta tafi sbd me😳 Maman su ce tace tai sauri taje kai ba sai ta jira na fito ba ku xo mu tafi ko zamu ganta a titi tom ko da suka fito mufeeda har ta tafi rai bace. Kash ta tafi Kila tana fitowa ta sami abun hawa. To ba sai mu biya ta gidan nasu ba cikin jin haushi shukrah tace a'a kawai mukai ni'iman Kaga ita unguwa zasu tafi d Maman su ko munje baza mu same ta ba,

Ko da tashi ga gida rai bace tai dakin umma tace umma na dawo sannun ki yana ga kindawo rai a bace wllh umma nagaji kuma bacci nake Ji bari na je daki na kwanta...

Koda tashiga daki kwanta wa tai tana tunani can wayar ta tasoma ringin mtsw..tayi tai ta ajiye har ta katse, ni'ima ce ta kuma kira akaro na biyu tai kamar baza ta dauka ba ta dauka, wai laifin ya shafe ni nima oho ya akai na fada rai bace gaskiya mufeeda baki kyauta ba abinda kika ma yayan a hurrah me son ka yafi me kin ka, Ke kinga dakata wai meyasa zaku yanke hukunci ba tare da dalili ba ni bance bana son sa kawai, banda lokacin yin soyayya a halin yanxu to Allah ya sawwake amma ki sassautawa ranki bazan sassauta ba to aunty masifa Ke dai kin fiye matsala wllh, eh naji din wani ne yace a shiga sabgata, gobe zaki shiga skul ban sani ba, Ke kinga bani na kar zomon ba sai anjima na'ima ta kashe waya..

Ko da na shiga skul ban neme su ba har nai submitting project din da nake, na fito zan tafi nagan su nai kamar bn gansu ba nai sauri barin wajen tare da nufar hanyar fita mufeeda mufeeda kwalan kira na'ima take amma nai kamar ban Ji ta ba nashige adaidaita,

Allah ya kara gashi nan kema ta yimi ki wulakanci Hmmm.. Shima yayan wllh beda zuciya dani ce da tuni na bar sabgarta Ke tunda kikaga hk mufeeda tana da kwakkwaran hujja da take haka amma yakamata muji ta bakin ta kar muyi sauri yanke mata hukunci.

Ke kanki kin san ba haka halin ta yake ba oho ma dai

Haka nai ta buye musu duk hanyar da nasan zamu hadu na daina bi tun abun beta damun shukrah har ya fara,na'ima gaskiya shariyar nan da mufeeda take mana bana jin dadi, Wllh nima hk kuma gashi ta kashe wayar ta bata hawa WhatsApp bare fbuk, Kuma nasan tana shigowa skul hmmm na tura mata da messages amma shiru To Allah ya sawwake in mun hadu online mayi magana, Ni bana jin dadi tafi batare da ita ba, Bayan sallhar magrib nadaukko wayata na kunna zankira yaya zainab,ni'ima kamar jira take na kunna kiranta ya shigo nadauka tare da sallama haba aminiya me yai zafi hk zaki mana yaji haka,to ae kune kun ki ku gane nufina ne, Naga kun dau zafi da yawa shiya sa nace bari ku huce a cigaba da harka, To miko ma WhatsApp muyi magana nace to,Allah sarki kawayena Ashe yanda ma damu da ku haka kuka damu dani,hmm nima kawai daurewa nake, Sakon shukrah naga ni ta group din mu wanda muka bude mu uku,haba aminiya ayi haquri wai menene dalilin ki nakin yi soyayya, Hm kuyi haquri akn abnd nai muku ina da dalili shiyasa, ni'ima to menene dalilin oh forget about matter, A'a mudai ki fada mana in muna da shawara sai mu baki ko ba haka ba, Pls it's my personal issue karku damu ya huce kawai...........😘 [2/15, 7:20 PM] ‪+234 703 962 5239‬: 💕💕💕 *LABARI NA* 💕💕💕

*written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~

Page 80-85

Uhmm ki fada mana abinda Ke damun ki mana haba aminiyar mu, nace muku ya huce kawai,to tunda baza ki fada mana ba shikke nan, Ke zurfin cikin ki har yayi yawa hmmm To yanxu ya maganar kayan da zamu sa, wane kaya fa ah nagama skul mana, kai na'ima saurin me kike to ne a'a ba sauri nake ba kin san yanxu zaki Ji ana zance fara exam amma fa kusa kafe time table, to me ya kamata musa, ku bari mana sai mun hadu a skul sai a tattauna maganar sannan, tom shikke nan mufeeda tace daga nan musan kalan nikaf din da zamu sa, hhhhhhhhhhhhhhhh gaba dayan su suka sa dariya, shukrah tace tab ae ko Ke baki isa ki sa ba,kullum nikaf sai kace matar liman, ni ban taba ganin mayyar nikaf irin ki ba ko Mayafi kika sa sai kin daura haba Ke ko damun ki baya yi, na'ima ni fa idan nasa nikaf sai naji numfashina yana sama, dan nima dai haka,dan dai baku saba sawar bane,Allah yasa mijin da za ki aura baya son nikaf tab ae ko yana so ko baya so sai na sa,haka suka cigaba da hira cikin farin ciki da jin dadi,

Mufeeda aunty sauda tamin waya tace in angama hada turaren wutar da humra abaki ki kaimata,au daman ba'a kai ba eh barin sa nai ya kuma tsumuwa sai a kai amma nace mata yau ko gobe za'a kai mata, in anjima sai ki shirya ki kaimata to umma bari rana tai sanyi in anyi sallahn la'asar sai in tafi tom,

In fa kika tsaya nauyi sai magariba tayi baki fita ba gani nan umma nagama,to gashi nan ki gaishe ta zata Ji,gidan aunty sauda na nufa kanwar ummana ce, Ah yau Ke ce da kan ki wllh aunty ina huni, lpy ya Umman ta ku tana lpy wai ga turaren,kai amma yai kamshi,aunty ina su hafsa da ameera sun tafi gidan bikin kawar su,ya makarantar taku aunty lafiya lau gashi ma muna shirye shirye fara exam to Allah ya taimaka Ameen, Amma dai Kwana zaki aa yanxu xan tafi ah haba,aunty sbd karatu shiyasa amma in mun gama exam ae zan zo,nasan fada kawai kike bazuwa zaki ba kullum kina makale da umma har yanxu baki daina kiwa ba,kai aunty kiwa da girma na,uhmm in akai auran ki naga yanda zaki yi, Kai yau kece a gidan tab, Ke baku iya sallama zaku shigo da ihu mame tunga gate Ameer yace mana wannan mara zumuncin ce tazo,kai nice banda zumunci hafsa lallai Ke zuwa kike,zumu shiga daga jiki, hafsa da mufeeda sakwanni ne,zo mu shiga daga ciki,akwai labari Ke nan kai labari daya ma Ke nan labarai zaki ce,shikke nan aunty mufeeda ko ki min magana ah yi haquri sister kin san hafsa in tafara magana kamar aku,bari na fito, Tunda suka shiga daki suke hira har sai da akai sallar magariba,sannan mufeeda ta fito aunty zan tafi to ga wannan takalma ne da turare nasan ki da san turare to aunty nagode Kice mata zan kira ta a waya tom, Ku koma dg nan na karasa ga malamin tahfiz nan naga yazo kar ya jira ku tom gaida duk yan gidan tom, A nutse nake tafiya sbd duhu ya fara na cire nikaf din dana sa ta wani layi nabi wanda ba jama'a ina sauri sbd na bar layin, gashi ba wani ishashshen haskene da hanyar ba, Nakai tsakiyar layin naji wasu samari suna cewa ah baabaa ka gawata yarinya cikin muryar su irin ta en shaye-shaye dayan yace bari ta kara so kawai mu afaka mata,innalillahi wa'inna ilaihir raju'un nake ambata gaba daya jikina rawa yake gashi bakowa,inna sa gudu zasu iya biyo ni, wai ga wa ne na hango wani mutun a tsaye saurin juyawa nai nakarasa inda yake yana danne-dannen waya nace banwan muryata na rawa nace Bawan Allah,dagowa yai sannan ya kara mayar da kansa kan waya, dan Allah ka taimakan ka wuce dani can wajen sbd wadan can en shaye-shayen,cikin ko in kula yace kawai Kije ba abinda zasuyi miki, Ban san sanda nace na shiga uku ba,kuma kallon sa nai naga hankalin aa na kan wayar, Tafiya nai ina karanto duk addu'ar da tazo bakina sbd ba wata hanya yawwa Kaga ta dawo daman nafada ma rabon muce, Kafafufa ne suka fara hardewa amma ban dae na tafiya ba har na karaso inda suke,dan Allah kunyi haquri zan baku duk abinda kuke so wata irin dariyar mugunta suka sheke da ita,kaina sukayo daya yana kokarin cire min mayafi idona na runtse tare da addu'a dan nasan ba me temako na sai Allah.............. [2/15, 7:20 PM] ‪+234 703 962 5239‬: 💕💕💕 *LABARI NA* 💕💕💕

*written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~

Page 90-95

Can shiru naji ba'a taba ni ba kuma da maganganu, a hankali na bude idanuna wanda na fara neman temakon sa na gani rike da hannun daya daga cikin su, wato irin ku ne masu bin yammata kuna ko kakarin lalata wa sannan ku kwace musu abun dake hannun su ko, matsar dani yai bayan sa san nan yace, to yau zan ma abunda in akace ka kuma tare wata baza ka iya ba,dan Allah kayi haquri kan ya kuma wata magana ya bashi wani kyakkyawan mari dayan da yaga haka yai kokarin guduwa wani wawan naushi ya kai masa a baki sai da yaga wasu taurari sun gifts, da yake basu da wani kwari duk shaye shaye ya lalata musu jiki, duk su biyun ya hada yai musu jina jina tn suna kokarin guduwa har suka kasa, sai da ya gaji dan kan sa sannan ya kyale su,ya daukko handkerchief na goge hannun sa, Juyo wa yai wajena wanda tuni tsoro ya gama cika min ciki kamar kace min ket nasa gudu, Shige mu tafi ba musu na bi shi sbd gabada dayana a tsorace nake, har muka karaso wajen wani mota budewa yai ya shiga, sannan ya bude daya bangare yace shigo ba musu na shiga, Be min magana ba nima bn masa ba, naga dai yana ta dube duben sa can yace muga wayar ki, bude jaka nai na daukko tare da mika masa sa number din sa yai sannan yai dialling call a gidan baya ya jiyo ringin din wayar ya kashe sannan ya miko min, Bayan ya daukko wayar ya tada motar sai a sannan na kalle shi,shima kallo na yake, yace ina muka nufa gida na bashi amsa ba tare da na kuma kallan sa ba, Sai da muka hau titi sannan yace min wane unguwa,hanyar gidan sarki na bashi amsa a takaice sannan muka cigaba da tafiya ina fada masa inda zamuyi, kiran sa akai a wayar sa,sai da yai dan karamin tsaki sannan ya dauka,haba ya za ae ka shanya mutane tsawon 5-10 minutes muna jiran ka,komai akace masa dg can bangaren oho nadai Ji yace ni dai natafi ma hadu wani karan ya kashe wayar,

ina lura da kallon da yake min, ta gefen ido ba wanda ya kuma yin magana har muka karaso yace nan yayi nace eh, sai a sannan nace nagode Allah ya saka da alkhaeri yace amen, Na bude na fito shima naga yai sauri fitowa tare da sama motar key, Muje ko da sauri na kalla shi,da gan gira yai alar eh ko baki so na raka ki har kofar gida,murmushi kawai nai batare da nace masa komai ba,a haka har muka kara so gida nace masa nan ne gidan mu, OK bye ya juya zai tafi nace masa nagode fa Allah ya saka da alkhaeri tsayawa yai cak yace to naji godiyar ya isa haka, Har ya tafi ina tsaye ina shakar kamshin turaren sa, ban shiga gida ba sai da na daina ganin sa, Haka kawai naji mutumin yana burge ni,na saki wani murmushin dani kai na ban san ma'anar sa ba, Umma na dawo ya kika barta lpy lau tace tana gaishe ki kuma zata kira ki,bari na shiga huta daga nan nae sallah tom,

Ko da na idar da sallah na dau waya ta naji kamshin turaren sa ajiki,tsintar kaina nai ta rufe ido ina shakar kamshin turaren,hmmm me hakan yake nufi🤔

Koda na kwanta kasa bacci nai ina ta juyi ina tunanin sa, gashi ko sunan sa ban sani ba,amma wannan unknown guy din ya hadu daga gani yana da aji, a dan satar kallon da nai masa na gano kyawunsa,

Wai ni mufeeda da nake zance maza sun dai na burge ni sai gashi ina tunanin wani, wata zuciyar tace min ae sabida taimakon da yai miki ne a hk na barshi amma fa ban fasa tunanin sa ba.

Daga bangaren sa wato muhseen tunda ya koma gida yake tunanin wannan yarinyar,gata da kyau ga nutsuwa shi abnd yafi fizgarsa game da ita kamun kanta da nutsuwar ta ga hankali, tunanin ta ya hana shi tabuka komai, da sauri ya tashi ya daukko wayar sa dake bedside ya fara dubo number dinta Alhamdulillah ya fada cikin farin ciki,cikin zumudi ya danna kira...

Cikin zurfin da nai a cikin tunani najiyo wayata da Ke gefe tana kara........... [2/15, 7:20 PM] ‪+234 703 962 5239‬: 💕💕💕 *LABARI NA* 💕💕💕

*written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~

Page 100-105

Cikin zurfin da nai a cikin tunani najiyo wayata da Ke gefe tana kara, har ya katsa ban dauka ba sai da akai wani sannan na dauka, wata murya ce me dadi sauraro ta amsa sallamar da ne daga daya bangaren, nai shiru bance komai ba ina tunanin inda nasan muryar, Ya kika je gida lapiya lau, baki gane me magana ba nace masa eh, Ina jiyo sautin ajiyar muryar sa, yace to ya tsoro sai a lokacin nagane cikin jin kunya kamar ina gaban sa nace hmmmm,,,,

Sai a sannan na kuma cewa nagode da taimkonka ki godewa Allah, to na godewa Allah da ya baka ikon zuwa ka taimkan, amma fa godiyar tai yawa sai kace wadda aji ma wani abu to ae dole nayi godiya Kasan hausawa sunce yaba kyauta tukuci,

To naji wannan ya huce Allah ya kiyaye gaba na amsa da ameen, Wai mene sunan matsoraciyar? Nifa ba matsoraciya bace kawai da, kawai dai me kinsan kuwa duk addu'ar da kike yi a fili kike yi haba dai ina jiyowa dg inda nake sai a sannan na biyo bayan ki,dan da ban yi niyar zuwa ba, sbd wasu emmatan sai a hankali ana iya hada baki dasu a cuci mutun, Murmusawa kawai nayi nace sunana mufeeda, nice name ni kuma sunana muhseen, ban san lokacin da na maimaita sunan ba, Sunan yai tsufa ne a'a amma kuma koda yake ma shikke nan sai da safe bari na barki ki kwanta, sai da safe na kashe wayar, sannan na turo masa sakon kamar haka..

_Am really appreciate for ur concern tnkx alot gud night_

na kashe wayar bacci me dadi yai awon gaba dani,ko da asuba da natashi naga ya turo min message na bude na karanta

_fatan kin tashi lapiya ya ma'abociyar kyau da nutsuwa_

haka na yini ina karantawa dan message din yayi min dadi, [2/15, 7:20 PM] ‪+234 703 962 5239‬: 💕💕💕 *LABARI NA*💕💕💕

*Written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~

Page 110-115

_na sadaukar da wannan page din ga duk en Hausa novels group_

Ba wai irin massage din ne ba a taba yimin ba a'a an min wanda ya fishi ma sai dai komai na muhseen burge ni yake,

Muna zaune ni da umma tana aiki a system dinta ni kuma inai mata hirar dunyi nace umma kinga su bakara (wadda muke uba daya dasu) Gani suke asirin da sukai min ne yai ta siri uhmm basu san Allah ya fisu ba,umma tace kaf din su ba suyi halin uwar su ba,har gwanda mazan,ni wllh umma har Maman ma haushin ta nake ji, Dan ita ce bata tsawatar musu, shiya sa sai na fi sati ban shiga bangaren su ba, to Allah ya sawwake ta kuma cigaba da kare mu Ameen,

Mu tara ne 'ya'yan umma aunty Jidda,aunty mas'uda,sai aunty Farida,aunty zainab sannan kuma ni mufeeda,sai kanina Abdul yayi candy Sadiq yana last year a secondary Muhd yana ss1 sai kuma fadila a jss1, ita kuma mama tana da mata hudu maza uku, Mayan 'ya'yan Abban mu su uku ne Maman su ta Haifa ta rasu maza biyu mace daya,da yake ummana ce amarya😜

Su fadila har yanxu basu taso dg ismaliyya ba,sarakan fada yanxu zaki Ji su dan lokacin ta shi yayi su har yanxu basu gama hankali ba, Kin ji ihun su kai Allah ya shirya, Ni dai umma bari na shiga daki na yanxu sai su sama mutane ciwon kai kyaji da shi Ke dai Kice zaki ki je ki sana'ar taki ta bacci kai umma na dade ban baccin rana ba,

A bangare muhseen kuwa yana zaune yana karanta jarida mukhtar abokin sa ya turo kofar tare da sallama, Ah abokina Kaine tafe haka ba dole na zo ba,kai da na nace ka jira ni gani nan sai zuwa nai na tarar ka katafi to ba dole na tafi ba, Ka shanya ni kamar kayan wani to afuwan aboki ya huce,yanxu ya akai uhmm abokina ban baka labari ba name kuma, Uhm ae tsayawar da nai jiran ka,ya zamar min alkhaeri ko me ya faru cikin sauri mukhtar ya tambaya, Na hadu da wata yarinya,me hankali,nutsuwa ga kuma kyau, kai Kace wannan tai sa'a,tai sa'a ko nai sa'a ae ba irin wannan emmatan bane wanda ka sani wannan ta hadu,to yaushe zamu na ganta ne,saurin me kake haka ne ae ko fada mata banyi ba,sai da nai dabara sannan na sami number dinta da address na ta,nan ya kwashe labarin abin da ya faru ya fada masa,to ya kuma za kai da Angelina tsaki yai sannan yace kaima Kasan wannan ba son ta nake ba ita kanta ta sani koda ina kasar su bana biye mata bare yanxu dana dawo,ta cigaba da shirmenta har ta hakura ta daina,to amma ya kamata ka fada ma madam din taka kar kaje wani ya riga ka bayan kai kuma ka afka,zan je har gidan na su muyi maganar,bari naje duk yanda kukai da ita ka fadan Allah ya bada sa'a Ameen in ma da iskanci ka fada,

Ko da yamma tai ina kitchen ina girki ina tunanin muhseen ni ba abin na kira ba nace masa me, Tuwon alkama miyar kubewa tare da busasshen kifi nake shirya mana,ina cikin dogon tunani na waya ta dake gefe ta soma kara ina dubawa na ga muhseen ne,cikin farin ciki na dauka amma sai da ta kusa katsawa sannan nai picking iri dan Jan ajin nan namu na mata😜,

Cikin muryar sa me dadi yai sallama na amsa masa, Kwana biyu kin buya murmushi nai sannan nace ina nan amma baki nema na, uhmm ya kake lapiya ya umma tana nan kalau, kina ina haka ne,me kaji kawai tambayar ki nai ina gida ina girki, Har da zance miki zan zo, uhmm tom in na gama ba sai ka zo ba, tom shikken me kike girka mana haka tuwon alkama miyar kubewa woow delicious asa dani tom sai kazo,

Ciki sauri na kammala girkin na zuba a flask sannan naje na cema umma zanyi bako,cikin mintinan da ba su fi 20 ba nai wanka na shirya cikin doguwar riga ta atamfa blue me adon pink,ina kan sallaya na idar da sallar magariba ya kira yace ya kara so, Na tashi na kuma gyara fuska ta sannan na feshe jiki na da turare,na kira fadila nace takai shi dakin baki sannan ta jera abinci a dakin, Sannan nace ma umma zan fita haka kawai na Ji gaba na yana faduwa,na daura na karasa bakin dakin nai sallama na shiga sai da ya katse wayar sannan ya amsa sallamar...... [2/15, 7:20 PM] ‪+234 703 962 5239‬: 💕💕💕 *LABARI NA* 💕💕💕

*Written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~

Page 120-125

Tsayawa yai yana kallona a haka na nemi waje na zauna,cikin sanyi murya nace ina huni lpy lau gimbiya ya kike,alhamdullilah sakkowa na katsa na fara zuba masa abinci nan da nan kamshin miyar ya cika dakin, ina dagowa muka hada ido da sauri na dauke nace ka sakko kaci abinci,too gashi kuma a koshe kake ah haba bayan kai Kace na sa da kai in baka ci ba bazan Ji dadi ba,to zuba mana muci tare dawa 😳 na dago da sauri hakan da nai shi ya bashi dariya yace da star shine cike da mamaki na maimaita sunan star shine uhmmm,a koshe nake ban yarda ba naci kamin na fito, Anyya ma kuwa kina cin abinci yadda ya kamata, me ka gani kalle ki kamar iska ta bushe,a hakan kalle ni fa na fi ka kiba dariya yai sosai sannan ya fara cin abinci ya ci yana xuba santi, sai yau na kare masa kallo lallai muhseen kyakkyawa ne a jin farko gashi har ya fin fari, Kallon me kike min haka ne,ni ba kallon ka nake ina kokarin zuva masa kunun aya,amma ba Ke kikai girkin nan ba, me kaji yai dadi sosai na dade ban ci abinci me dadin sa ba,kadai kawai kana santi na mika masa kunun ayar bayan ya sha, yai hamdala sannan yace bazo muyi magana amma kin cikan ciki da abinci anyya zan iya magana ma kuwa, to me zai hana ammm mufeeda amsawa ne batare dana dago ba dan jiki na ya bani ni yake kalla,gaskiya na ya ba da halin ki da nutsuwar ki kuma tunda muka hadu naji zuciya ta ta kawo min wani bakon lamari, fatan Allah yasa ba wahala zan sha ba,tunda ya fara magana ban daugo ba sai yanxu nace wahala kuma yace eh ina nufin, Allah yasa wani be rigani ba, Dan idan haka ne ban san dame zan bawa zuciyata haquri ba,mufeeda zuciyata ta kamu da son ki ta farat daya, da sauri na dago muka hada ido sai naji naka sa cema sa komai, saukkowa yai kasa ya zauna ya cigaba da Fatan zuciyata zata sami abokiyar rayuwa,pls mufeeda wllh ina sonki ki taimakan ni wllh da aure nake son ki bana son a ja dogon lokaci,ban san haka so yake ba,dan bana kule kule Kinyi shiru kiyi magana mana cikin sarkarkiyar murya nace masa to kabani lokaci zanyi shawara,haba mufeeda Wacce shawara, Kawai Kice kin yarda aa kabari sai nayi tunani zuwa nan da 1week da sauri yace me? Sati fa kika ce gaskiya is too long sai dai in baki sona shine zaki ce haka,amma na baki zuwa nan da gobe aa Kwana uku dai uhmm tom shikke nan,bari na tafi sai munyi waya, Ga wannan kya siyawa fadila sweet aa ka barshi karbi aa nagode ba sai na karba ba, ajiyewa yai ya fita sai na kira,

Cikin sanyi jiki na kwashe kayan na kai kitchen daki. Umma na nufa sallah na tarar tana yi, nima toilet na nufa nai alwala na dawo dakin umma nai salla sannan nake fada ma umma yanda mukai da shi,sannan na nuna mata rafar en dari dari da yaba yar a bawa fadila to ki bashshi a wajen ki in zakuyi wata bukatar sai kuyi amfani dashi nace to,

To mufeeda ya kika ga halin sa gaskiya umma ni banga wani hali mara kyau a tare dashi ba, yana da nutsu gaskiya a yanda na fuskan ce shi, To Allah ya tabbatar da alkhaeri nace Ameen mun dan taba hira sannan na tashi na shiga daki nai wanka nai shiri bacci amma juyi nake naka sa bacci sbd tunani, A gaskiya ina tsoron kar sai shima na fara son sa ya yaudaren,kuma gashi muhseen ya yimin dan komai nasa burge ni yake yi,

Da sauri na tashi na shiga toilet nai alwala sannan nadawo nai salla raka biyu ta neman zabi a wajen Allah, akwai addu'ar da ake karantawa idan an idar da sallah kamin ae sallama tana nan a cikin husnun musleem na dade ina addo'o'i sannan na shafa, Na kwanta ina tunani har bacci ta kwashe ni, Da asuba har makara nai sabida ban samu ishashshen bacci ba da daddare [2/15, 7:20 PM] ‪+234 703 962 5239‬: 💕💕💕 *LABARI NA*💕💕💕

*Written by*✍✍✍ *Salmah Ali Wada* ~*(Aunty)*~

Page 110-115

_na sadaukar da wannan page din ga duk en Hausa novels group_

Ba wai irin massage din ne ba a taba yimin ba a'a an min wanda ya fishi ma sai dai komai na muhseen burge ni yake,

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull