Mar’adam’s book 2 by aysha a bagudo - Chapter 11
Mar’adam’s book 2 by aysha a bagudo Chapter 11: Mar’adam’s book 2 by aysha a bagudo Chapter 11. ganin ya sauke numfashi tare da d’aura hannuwansa duka sama…
3,354 words
ganin ya sauke numfashi tare da d’aura hannuwansa duka sama jijiyarsa ya dafe ,ta sake durkushewa a gabansa ta tsura masa ido “ina sonka adamcyn mami wallahi bazan iya rayuwa babu kai ba . sonka yayi min mugun kamu I love you my adam, sonka da qaunarka sun yi min kamun da bazan iya fushi da duk wani wulakanci da zaka min ba .”ta sake kai hannunta qirjinsa tana adduar allah yasa kar ya farka ya kamata cike da matsanancin tsoro ta fara shafa qirjinsa tana sauke numfashi .”wani wahallen numfashi ya sauke yana mai jin wani mugun felings a gabad’aya ilahirin jikinsa, ita kanta wani iri ta dinga ji ajikinta tmkr ana jona mata wutar lantarki .”
ta sauke numfashi tana mai matso da bakinta dai dai nashi nan warin sigari ya bugi hancinta amman cikin ikon allah sai lumshe idanunta tayi tana jin dadin shakar kamshin sigari da numfashi shad’e ” Cike da tsoro ta soma tsotsan lip’s dinsa na kasa tana hura masa numfashinta tana tsotsa lip’s dinsa tana shafa kwantaccen gashin qirjinsa cikin wani irin yanayi ya kai hannunsa d’aya yana shafa sumar kanta yana ma bakinta wani irin sha yana juya harshensa tmkr yana neman wani abu acikin bakinta har ya samu yayi nasarar cafko harshenta ya fara tsotsa cikin kwarewa yana sha yana had’awa da hakoranta da lip’s dinta sosai ata ya dinga sarrafa bakinta cikin rashin sani .”
Allah sarki maryam wani irin farinciki ne da mugun tsoro ne ya shigeta alokacin d’aya dadinta yadda yake sarrafa bakinta tsoronta kuma ya farka ya gansu haka nan da nan dadin take jin yana bin jikinta ta daina jin komai sai tsananin tsoro da fargaba dan tayi imani muddin ya bud’e idanunshi ya ganta ta mutu sai dai wata maryam din ba ita ba bayan tozarci ma sai ya kusan kasheta da duka dan haka cikin tsananin tsoro ta zare bakinta tare da d’auke hannunta a saman qirjinsa tana rawar jiki .”
Shi kuma jin ta zare bakinsa ya fara motsi yana fitar da numfashi da sauri sauri yana neman abinda ya kufce masa ya dawo masa domin shi zatonsa mafarkinsa ne . maryam ta tsura masa ido sosai cikin tsananin tsoro ganin yadda yake fidda numfashi yana damke jijiyarsa da hannuwansa duka qoqarin bud’e idanunshi yake taí saurin juya masa bayanta qirjinta na wani irin luguden bugu “.
Idanunshi ya bud’e da kyar yana jin sauyin yanayi a gbdy ilahirin jikinsa bai ce uhm ba bare uhm illa kallon saman parlour’n da yake batare da yace uffan ba ,cikin yanayi najin fad’uwar gaba ya sauke idanunshi dake cike da bacci akanta duk da baya kawai ya gani amman yasan wacece ko dan mugun gajartata, mamakin ganinta yayi adaidai lokacin da suke tsakar dare” me take yi tsaye ya kai idanunshi ga bangon parlour’n daidai inda agogo yake manne “hudu saura ya tabbatar karshen dare suke ya ‘bata a qalla minti biyar sannan yayi wuf ya mike tsaye yana tafiya da kyar ya isa gabanta ya tsaya idanunshi cike da bacci .”
“Ke me kikeyi anan ?ta tsura masa ido tana kam kame jikinta waje d’aya “ko dai mayya ce ke ?still shiru tayi tana jin mummunar fad’uwar gaba Kmr ta kwasa da gudu ta haye sama “ina miki mgn kinyi min shiru “mayya ce Ke?okay okay !!na fahimta kin tashi rawar dare ne ko ?maganarsa taso bata dariya amman tasan muddin tayi mugun duka ne zai biyo baya “idan ma mayya ce ke sai dai kin cinye kanki da uwarki da ubanki amman ni namana da daci nonsense girl kawai kizo kin wani tsaya wa mutun akai zaki shanye min jini “ya qarasa mgnr yana jan tsaki ya nufi hanyar sama .”
Tabi bayansa da kallo qararrawar zuciyarta na kad’awa fiyye da kaida yana shiga d’akinsa bai koma ya kwanta ba ,ya shiga bathroom yayi wanka dan yana jin jikinsa wani iri ya d’auro alwala ya fito ya saka rigarsa ya tada sallah .”koda ta hau sama ta tsaya bakin kofar d’akinsa ta tura kofar d’akin ahankali a saman abun sallah ta ganshi zaune yana jan casbaha ,ganin zai juyo ta juya da sauri ta shige d’akinta ta kulle ta kwanta tare da qudundune jikinta tana jin feelings dinsa na ratsa lugun da sako na jikinta .”shi kuwa bai koma ya kwanta ba sai da yayi sallolinsa sannan ya koma saman gadonsa ya kwanta bakinsa d’auke da tasbihi ga I bangijinta ahaka bacci mai dadi ya daukesa .”
bai tashi ba sai wajajen karfe tara da minti talatin ya sauko da kyar ya shige bathroom, minti shabiyar tsakani ya turo kofar bathroom ya fito d’aure da towel a kugunsa yayinda jikinsa ke jike da ruwa ya tsaya a gaban mirrow yana goge jikinsa da gefen towel kamar ance ya kalli cikin mirrow ganinta yayi tsaye tana watsa da yatsun hannunta wani dogon tsaki yaja yana d’auke kanshi cike da dakewa da daure fuska tmkr bai ganta ba ya cigaba da goge jikinsa yana mamakin abinda ta shigo yi kamar ba ita yayi wa kyakkyawan warning ba akan zuwa inda yake ba .”
Bayan ya gama goge jikinsa ya shafa lotion ajikinsa ya bude ma ajiyar kayansa ganin haka yasa ta juya masa baya tana mai jin nauyi da fad’uwar gaba madadin ya d’auki kayansa sai ya gyara daurin towel din kugunsa da kyau yayi taku uku ya qarasa inda take da sauri ta d’auke numfashi sakamakon wata irin damka da taji ta bayan wuyanta “wani razananniyar qara ta saki wanda yasa gbdy gidan ya amsa ,bai tsaya wata wata ba ya jata kiiiiii yayi waje daita bai tsaya akoina ba sai d’akinta yayi wuli daita a tsakar d’aki sauran kad’an gefen idanunta ya bugu da abun gado allah ya kiyaye “dan ubanki me ya shigo dake d’akina “?
ta mike a matukar gigice tana dubansa “ban fad’a miki bana son ganin wannan bazan fuskar taki ba ?ka..ka !! fad’a min daman ..”tass tasss taji ya d’auke da wasu maruka masu kyau sai da wani haske ya gilma acikin kwayar idanunta ta fashe da kuka tana dafe kuncinta“idan kikayi qoqarin shiga rayuwata zaki sha wahala a hannuna domin kuwa zan bata miki fuska ta hanyar canza miki kamani , tsay a way from me I don’t want to see your face “yana gama fad’ar haka ya juya a matukar fusace ya bar d’akin .” Durkushewa tayi a wajen tana fashewa da kuka mai tsanani “ta rasa wani irin tsana ya adam yayi mata wani irin kuka take saboda ciwon abinda yake mata ,ta share hawayenta alokacin da taji motsin rufe kofar d’akinsa “.
Ahankali taji taku takalminsa yana taka step wanda duk takun da yayi daidai yake da bugun zuciyarta jikinta a sanyaye ta mike ta soma d’aga kafafunta tana zubar da hawaye har ta kai bakin kofa taji motsin takunsa alamun yana haurowa da hanzari ta koma da sauri tana jin fad’uwar gaba tsayuwarsa ta gani a bakin kofar yana cewa “Ke ina kwalin sigarina? muryarta cike da in ..ina tace “amm uhm na ..na ..”sai kuma tayi shiru ta kasa qarasa mgnr dan tasan tana fad’a masa ta zubar a shara sai ta gane bata da wayo ya qara taku biyu ya shigo cikin d’akin sosai yana mata wani irin mugun kallo wanda yasa hantar cikinta kad’awa “ina kwalin sigarina ?akaro biyu don’t let me repeat my self .”
“Na ..na zubar a shara “ta fad’a hawaye na ganga rowa bisa kuncinta “what !? ya fad’a a matukar tsawace tayi baya da sauri ta manne da bangon d’akin tana bashi hakuri “kayi hakuri dan allah .”“sigarin nawa kika zubar ashara saboda Ke dakikiya ce ?bansan cewar baka gama dashi ba amman kayi hakuri “ numfashi ya fesar tare da rike kugunsa ya taka ya isa bakin window ya yaye labulan window yana kallon haraban gidan masu tsaronsa ne suke shawagi da alamun sun gama shi kawai suke jira ya saki labule da karfi wanda yasa maryam ta firgita cikinta ya duri ruwa. fuskarsa a murtuke yace “ki tabbatar kin nemo min sigarina kafin na dawo gidan nan idan ba haka ba wallahi wallahi ki kuka da kanki “yana fita kamfani ya nufa .”
cikin hanzari suna isa ya fito.”kai tsaye ya d’auki hanyar comfrence room domin wata gagarumar matsala dake son kunno kai cikin kasuwancinsa kuma tunda ya sanarwa P.A dinsa yasan by this time shi kad’ai ake jira yana shiga ya iske kowa kamar yadda yayi expecting har ma da ammar da hisham cike da girmamawa manya ma’aikatan da dake zaune suka dinga gaishesa tare da qoqarin kashe wayoyinsu dan sun san dokarsa idan yana magana baya son jin motsin kowa bare qarar waya ya mikawa ammar hannu batare da ya kalli inda hisham yake ba shima kuma bai kallesa ba .”ya samu waje ya zauna.”
sun dade suna tautaunawa da manyan ma’aikatansa domin kawowa kamfanisa cigaba ahankali P.A dinsa mustapha umar hassan dinsa ya mike ya kawo masa coffe karfe biyu daidai ya sallame kowa shima ya fito tare da ammar suka nufi massalacin dake cikin kamfani yana bawa direbansa umarni cikin harshen tsadadden turancinsa su juya kan motoci fita zai yi da zarar ya fito .”Ina kuma zaka ?zanje naga sweetheart dina “ya fad’a cike da jin fad’uwar gaban da bai san dalili ba”.
a natse suka qarasa wajen yin alwala suna magana kasa kasa ATA yace “share maganar hisham kai bakasan abinda yayi min ba muddin kaga mun dawo kamar da to naga auta kuma naga kwanciyar atare daita bayan sun idar da sallah ammar ya rigasa fitowa ya tsaya acikin wata runfa rungume da hannuwan sa a qirji yana jiran fitowar ata yana tsaye ya hango bayan maryama idanunshi kyam akanta har sanda ATA ya qaraso ya tsaya kusa dashi yana cewa “me ya d’auki hankalinka da kayi concentre haka ?zubin halitta mai kyau nake kallo ”ya bashi amsa da haka kana ya cigaba da magana “ kalli can abokina ka gani tsayuwarta ma kawai abun burgewa ne .”
ATA yaja tsaki yana cewa “nonsense ! ba tsaki zaka já ba ka kalla ka gani kai kanka zaka fahimci abinda nake nufi, yarinyar da nake fada maka ce, ata da yayi niyyar kallonta ya fasa ya cigaba da kallon ammar fuskar tashi nan babu wani annurin kirki sai dai bugun zuciyarsa ya qaru sosai fiyye da duk wani tunanin mai karatu ” maryama mai kyau !Ammar ya kira sunanta “saurin juyawa ATA yayi yanayin bugun zuciyarsa bai saisaita ba, maryama kuwa juyowa tayi ahankali sanye cikin kanki bautar kasa ta nade kanta da qaramin hijab kayan sun matukar yiwa jikinta kyau “ mr ammar ta hango tare da bayan wani tsaye .”
“Mai kyau qaraso mana mu gaisa “ tayi murmushi wanda yake qara tafiyar da imaninmu mutun “ahankali ta soma takowa zuwa inda suke tsaye tana wata irin tafiya da mutane suke ganin tsabar yanga ce tayi mata yawa nan kuwa rashin kibar da bata dashi né ya janyo haka “kalleta abokina gashi tana nufomu zaka fi qare mata kallo sosai wallahi yriyar ta had’u” bazan kalleta ba tunda ta had’u ka aureta mana ,duk kabi ka damu mutane Kmr wanda bai ta’ba ganin mace ba “bai fi sauran taku biyu ta karaso zuwa inda suke tsaye ba ATA ya soma d’aga kafafunsa bai tsaya akoina ba sai a inda motarsa take tun kafin ya qaraso masu tsaronsa sun zagayesa .”
Murmushi kawai ammar yayi yana d’auke idanunsa daga kallon bayan ATA “mr ammar barka da rana ya fama da jamaa ?tayi mgn a natse cikin sanyayyar muryarta “na kusan sumewa da wannan murya fa “ maryama ta d’an zaro ido tana cewa “wace ni dan allah ka rufa min asiri kar madam tasamu wannan labarin na shiga uku na “mu shi uku dai “ya fad’a had’e da murmushi, cikin marairaicewa tace “kaji ba ashe kaima tsoronta kake ji “yasa dariya adaidai lokacin da motocin ata suka fice yayinda ammar ya cigaba janta Kmr yadda ya saba .”
kai tsaye abdullahi estate ata yace a wuce dashi ana gama daidaita parking ya fito ya nufi gidan mami tana daga zaune taji ana yunkurin bude kofar ta tsaida idanunta akan kofar dan ko baa fad’a mata ba jikinta ya gama bata d’an lelenta ne ke tunkarota “a natse ya turo kofar ya shigo kana ya maida kofar ya rufe akan mami idanunshi suka fara sauka bayan ta kallesa ta dauke idanunta akanshi zuwa wani gefe tana jijiga kafarta tayi tmkr bata ji dadin ganinsa ba alhalin kuwa wani farinciki ne ya mamayeta domin tun da ta gansa tasan tayi winning yazo ban hakuri ne .”
Ahankali ya tako zuwa inda take zaune akan kujera wanda zuwa lokacin tunin ta runtse idanunta durkusawa yayi a gabanta yana sauke numfashi tare da d’auran hannuwansa akan gwiwowinta “Kiyi hakuri sweetheart ki yafe min nasan ban kyauta miki ba ,ban san abinda yasa na aikata haka ga mahaifiyata ba wacce bani da kamarta ,duk duniya itace take dani nake daita.”nan da nan hawaye ya jike gashin idanun mami “yanzu zagin wad’an da suka manyanta a zamaninku ya zama wani abun ado shiyasa kayi min son ranka kuma agaban matarka , me kake tunani idan ba maryam ka aura ba ? “kaga kenan ka siya min raini ne a wajenta ko kuma nuna mata kofar yi min abinda ta ga dama .”
“ sweet heart na aikata hakan ne abisa kuskure amman kiyi hakuri dan allah “ ta d’aura hannunta a saman nashi kawai batare da ta sake cewa komai ba tana jin tsananin qaunarsa .“Kiyi hakuri kiyi min addua sweetheart ko allah zai sa min son diyarki a zuciyata ko kad’an ne , sweetheart har yanzu na kasa manta mafarkina ina tsananin sonta gashi bansan inda zan sameta ba sannan duk yadda naso na cireta araina na manta daita na kasa manta komai nata .”bugun zuciyarta, numfashinta fuskarta da kamshinta idanuwanta murmushinta hawayenta sautin numfashinta sweetheart bazan boye miki ba na sha saduwa daita acikin mafarkina .”
Mami ta tsura masa idanunta tana kallonsa “na fara shan sigari duk dan saboda ita haka zalika a qoqarin na manta daita ne na fara shan giya ina danne zuciyata akanta ,nayi iya yina domin na manta daita amman wallahi sweetheart abun yaki aiki har yanzu koina na juya ciwo nake ji acikin zuciyata “mami tayi shiru zuciyata cike da tsananin tunani abu daya ne yayi mata dadi acikin magangunsa shine rokon adduarta na allah ya saka masa son mrym ko kad’an ne wannan abu ya sanyaya zuciyarta kuma daman tana wannna adduar .”
“Sweetheart nifa abun tausayi ne abun a tausayawa ne akwai ciwo mai zafi acikin qirjina bana buqatar tausayawar kowa sai taki kece kawai zaki tausaya min domin kece kawai kika san ciwona kuma kece kawai kike sona tsakanin da allah.“mami ta numfasa tana cewa “adamcy nah ina tsananin sonka da tausayinka kai ma ka sani ..”“na sani sweetheart amman akan yarinyar nan kin canza min koma nace kinfi sonta akaina,mami ta kallesa kawai “sweetheart ki janye maganarki akaina zan cigaba da rayuwa daita Kmr yadda kika bukata amman batu na samammarta farinciki babu shi domin ni kaina zuciyata baa cikin farinciki take ba dan haka dan Allah ki janye magarki akaina .”
Ta girgiza kai alamun a’a “sweetheart kin janye dan idan nayi kuskure kin bin umarninki wani abu zai faru dani idan kuma wani abu ya sameni kece kike da asara sam ita ba asararta bace kina ji kuma kina gani zata komawa wani ta bar miki d’anki da rayuwar daya tsinci kanshi .” muryarta a sanyaye tace “babu abinda zai sameka adamcy kuma Ina rokon Allah ya kawo maka saukin abinda Ke damunka "ta qarasa fada tana rufe fuskarta da tafin hanunta hadi da rushewa da kuka .”
“why sweetheart me yasa zaki min asarar hawayenki bayan kin min addua?”addua nafi bukata daga gareki kuma kinyi min na kuma gode Kiyi haquri don Allah ki daina kuka ni dai kin janye furucin ki akaina “na janye kai ma kuma kayi min alqawarin bazaka takura rayuwar maryam ba .”dan allah ka barta tayi farinciki a gidanka wallahi bancin mutane zasu zageni da na raba aurenku kowa ya huta“ “sweetheart babu mai zaginki kuma da zaki min haka wallahi da naji dadi da samun kwanciyar hankali “uhmm adamcy taa girgiza masa kai “kayi hakuri kawai adamcy zan maka addua kamar yadda ka bukata ya sauke wani numfashi yana mikewa ya zauna gefenta ya zauna yana kiran sunanta .”
“sweetheart!” “ina jinka adamcy “ina son zan qara aure“bazan hanaka qara aure ba adamcy amman dan allah ka bari zuwa nan gaba kad’an dan bazan ta’ba yarda ka shigo da wata gidanka ba alhalin diyata bata da matsayin komai a wajenka “why sweetheart “?mu bar wannan maganar adamcy muyi wata dan bana son jinta for now shiru kawai yayi yana mai runtse idanunshi shi kad’ai yasan zafin da ciwon da zuciyarsa keyi .”
“Sweetheart cikin satin nan in sha allahu zan bar kasar nan zuwa holland “da sauri mami ta kallesa sam maganar bata mata dadi ba ,kuma tasan dan ya nisanta kanshi da maryam ne “zaka bar kasar nan saboda maryam ko ?tayi maganar kamar zatayi kuka “ko d’aya sweetheart “saboda me zan yi tafiya saboda ita ?”kema kinsan tafiye tafiye yana cikin tsarin aikina” mami tayi shiru ya riko tafin hannunta cikin nashi “sweetheart!”ta sake kallonsa “ki kwantar da hankalinki nifa banki na daina tafiya zuwa koina ba saboda ke “wa na ajiye a inda zani ?”
“Me zakaje yi a hallond?yayi shiru yana kallonta “naga duka yaushe maryam ta tare da zaka tsiro tafiya gsky nidai idan son raina ne ka bar tafiyar nan ka wakilta wani ka d’an zauna da maryam “shikenan sweetheart “ya bata amsa da hakan cikin halin damuwa ya mike tsaye yana mata sallama murmushi ta sakar masa amman gida zaka wuce ko ? ya gyada mata kai kawai “to allah yayi maka albarka ka gaishe min da maryam anjima manu direba zai kawo maku abinci “to !kawai ya fad’a a takaice sannan yasa kai ya fice daga parlour’n massalacin ya nufa domin gabatar da sallar laasar .”
Hisham zaune akan kujera yana waya da nuzla “eh har yanzu ina office , allah kuwa da gaske nike amman bari nayi sallar laasar na tura miki babu mamaki ma idan na tashi aiki zanzo na gaki kafin na wuce gida , sosai kuwa ya fad’a yana murmushi kmr yana gabanta ,ahankali yaji ana Knocking din kofar office dinsa amman ya share yaki bada umarni shigowa ya cigaba da waya da nuzlah har kusan mintuna shabiyar sannan yace wa nuzla “bari zan kiraki nan da minti biyar acan bangaren nuzla cike da shagwaba tace “a’a ban yarda ba “okay to shikenan zakiji komai da zanyi “yana gama fadar haka ya bada umarni shigowa ga diyar aminin abbansa dake aiki akarkashinsa .”
Zakiya ta tura kofar office din ta shigo ahankali ta tsaya agabansa amman bai d’ago ya kalleta ba ya cigaba da wayar da yake .”a tsanake ta bude bakinta ta kira sunansa “hisha…yayi saurin d’aga mata hannu yana cewa alamun tayi shiru dan da yasan itace bazai bada umarnin shigowa ba “a’a abdull ne ya shigo akwai maganar da zamuyi dashi shiyasa nace ki bani minti biyar “okay naji da zarar na gama dashi zan kiraki ya katse kiran sannan ya kalli zakiya yace “yaya akayi ?sai data numfasa kana tace “akwai matsala fa “me ya faru “ya budurwa zata zauna ta dinga tayar maka da hankali haka?” nifa abokiyar aikinka ce kuma kusan yaruwarka wacce ko matarka tasan da zamana bata ta’ba nuna damuwarta ba sai wata can .”
“aa dakata zakiya banason haka matsayin nuzla dabam a wajena tana sama da kowacce mace a wajena ba wai wata bace kin fahimta ko ?“ kana nufin har matarka ?“eh bakiji nayi generalizing ba nace kowa , tafi kowace mace dan haka bana had’a maganarta data kowa ki kyaleni ke bani ma abinda ya kawoki ki bar min office menene ma ya kawoki “ ? ”mr Ibrahim yace ka tura masa idan ka gama “tô naji zaki iya wucewa please ya fad’a yana nuna mata kofar fita da yatsun hannunsa .”