Kenza eBookz

Nayi nadama book 1 complete - Chapter 31

Nayi nadama book 1 complete - Chapter 31

Nayi nadama book 1 complete Chapter 31: Nayi nadama book 1 complete Chapter 31. Hannun Yusuf ya damk'o ya jashi suka fito harabar gidan sauran ma suka…

3,356 words

Hannun Yusuf ya damk'o ya jashi suka fito harabar gidan sauran ma suka biyosu a baya cikin tsokona a hankali yace

"Hamma Yucut kaji ko Auta tamin alk'awarin mai suna, Kuma ni har ga Allah Na yarda naku gamsu da Nadamarta, Plss Hamma Yusuf a rink'a nunawa yaran pictures d'ina Dan su sanni"

Kai ya gyada mai cikin sanyi yace

"Insha Allah Babiker ai dama dole zasu sanka Abbinsu guda fa"

Juyawa yayi cikin Happy ya ruggume d'an uwansan.

Ciki sauk'e ajiyar hrt yace "Ina sonka Hamma Yusuf ina sonka ina sonka" har baki 3

Shi ko Yusuf ido ya tsura mai ya bude baki zai mgn kema.

Yai sauri ya shige mota Fuska na zubda qollah yace Na sani kaima kana sona d'an uwana ya juya gun sauran Cikin share K'ollah yace "Kuma na San kuna sona nima ina sonku Amman Sai wota rana".

Yana kaiwa nan yaja mota ya fice yana d'aga musu hannu.

Gaba d'ayansu binshi da ido sukayi jiki a mace, har zuwa d'an wani lkci sannan suka koma cikin gida.

Shiko Yusuf d'akin shi ya koma haka kawai yaji jikinshi Na rawa Sai dai ya zauna kusan awa 2 sannan ya mik'e cikin kasala yaje Gaban mirror ya cire agogon hannushi zai ajiye kenan idanshi ya k'ellah kan agogon Babiker d'inshi.

Ki ranshi yayi a woya yana d'agawa yace

"Ya akayi ne Hamma Yusuf"? cikin sanyi yace

"ka manta agogon kafa"

Cikin dry yace "Na baka" Da mmk yace "Na Daimon d'innanne fa da kake so sosai"

"Ehh Na sani toh inada Wanda zan bawa ne da ya wuceka"

Dry yayi yace "toh ngd k'anina"

Cikin dry suka sallami juna,

Shiko ya fada toilet yayi wonka zuwa lkcin An kira azabar ya wuce massalaci Bayan an idar ya ya bi bayan su Ahmad suka shiga cikin gida.

Su Ahmad d'in sun isa tsakiyar parlon Shiko yana bakin k'ofan parlon yaji kira ya shiga woyarsa Sai da ya shiga cikin parlon sannan ya amsa kiran ganin Abubakar ne da mmk "yace har ka isa ko"? Yana mgnan yana hararan Aysha dake Tsaye a k'ofar kitchen.

Gaba d'aya ido suka zuba mai jin ya saki woyarshi da k'arfi,ta tarwatse a kan tais d'in

Ahmad ne yace lfy cikin mik'ewa ya nufi gunshi Ina kafin ya k'arisa gunshi Sai haggoshi sukayi yayi Luuu cikin sakin wani irin numfashi ya zube k'asa a.............

By garkuwan Fulani [4/18, 10:14 PM] Aisha Aliyu Garkuwa: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣6⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_ P.M.L.W

Cinkin firgici da rud'ani da bugawar zuciya Ahmad, ya tallabo shi ya d'aura shi kan cinyarsa, jikinshi na rawa ya tallabo fuskarsa cikin kasa mgn ya rink'a girgiza kai kawai, zufa Na keto mai tako ina bugun zuciyar sa💓💔 Na harbawa da k'arfi.

Aysha ko cikin tsoro da zare ido da bugawar hrt da jin wani irin suka a k'akon zuciyarta 💘💔 ta iso garesu Murya Na rawa ta tallabo fuskarsa tana juyawa cikin d'imuwa ta rink'a ki ranshi da d'an k'arfi tana.

"Hamma Yusuf, ka bud'e idonka menene ya sameka? me aka gaya ma"?

K'ara shigewa jikinshi tayi cikin tsonanin tsorita, tace,

"Wayyo Allah Na wayyo Hamma Yusuf na ka tashi ka gaya min meke faruwa? me ya sameka"?

Juyawa tayi cikin kid'ina ta kamo hannun Ummu wace ta ke kamar an dasata ne Sai sanyi da ya rufe mata jikinta sanyin har cikin hanjinta a fili kuma Sai zufa ke keto mata.

Jijjiga Ummin tayi cikin kuka tace.

"Wayyo Ummi Hamma Yusuf dina Ummi in ya mutu nima nasan bazan rayuba, wayyo Allah na Ummi kiga baya numfashi baya motsi".

Adam ne ya Dan juyo gareta cikin k'arfin hali yace,

" Aysha ki nitsu kibar kukannan".

Suna cikin haka phone d'in Ahmad ya d'au suwa kamar bazai duba ba sai kuma ya d'aga ganin Sunan Babiker ne a fuskar woyar Jiki Na rawa ya d'aga ya d'an kara a kunne.

Lkci d'aya kuma ya saki woyar a k'asa cikin kid'ima ya rink'a juya kanshi Sai yanzu ya samu bajinshi ya bud'e kai ya rink'a juyawa yana.

"Kai kai kai Sai kuma ya ruk'k'ume Yusuf a jikinshi da k'arfi ya saki wani irin kuka mai cin zuciyar mai sauraro. Kuka yake yana rawan sanyi yana k'ara k'amk'ame Yusuf d'in. Adam ne cikin tsoro da firgici Yace "Innalillahiwainnailaihi raji un yace haba Ahmad ka sanar damu meke faruwa"?

Nenne da ta shigo yanxu jin kukan Ahmad yasa ta k'aroso da sauri Jiki na rawa tace.

" meya faru me ya samemu a zuciyar nan? me ubangiji ya hukunta a kammu? Ahmad Ka gaya mana"?

Ummi kam hannu tasa duka biyu ta tallabe cikinta da k'irjinta tare da cewa Wayyo Allah Na cikina sanyi kamar hanjina zasu tsinke"

Da sauri Nenne ta k'arisa gunta cikin cewa "meke faruwa damu ne"?

Aysha ce ta kamo hannun Ahmad cikin sakin wani irin kuka mai siririn sauri tace

"ya Ahmad meya faru"?

Cikin kukan da kifa kai jikin Yusuf a hankali Yace,

"Aysha Babiker" Sai kuma kife kanshi.

Ita ko Aysha cikin tsoro ta juya ta zubawa Ummi ido Sai ta kuma sakin kuka.

Cikin rawan murya Ummi tace "Aysha me woyar ta kamo min? yau kuma gaya min ya zanyi da mu k'addari"

cikin kuka da carkewar mgn tace "Ummi ya .. Ummi ya.. Ummi ya Abubakar"

Allahu Akbar uwa da d'a Sai Allah Sai mutuwa, Ummi da fari murmushi tayi tana Kullum nafsin za,ikatil maut. Allah sarki Abubakar Na ase ban kwana kamin da gsk Ya Allah Na ka jik'an wanna bawa naka Abubakar".

Ina Sai kuma zuciyar ta ta d'an yace Cikin sanyin sauti ta saki wani irin kuka tare da rik'e cikinta tana Wayyo cikina Allah Na Na godema da wannan jarrabawa rabbi ka fini son Abubakar Allah kasa can yafi mai nan Abubakar Na yafema duniya da lahira".

Nenne kam itama kukan take sosai. tana Abubakar d'in ?"

Adam ko Komawa yayi ya zauna dirsham ayyah Usman Dasu Abba da baba bello yanzu suka shigo gidan.

Suna shiga cikin tsoro baba bello Yace "meya faru"?

Ba Wanda ya samu da mar mgn Sai kuka Cikin firgici da hatsala yace,

"Ku gaya min meya faru? kunyi shiru"

Adam ne cikin kuka da wani irin voice Yace "Baba Abubakar Abubakar ne ya".

Sai kuma ya kasa k'arisawa.

Allahu Akbar cikin mutuwar jiki da tsoro Abba da Baba ballo suka zame kan kujera Usman ko da Rabi,u da Abdul, Hade kai sukayi wurin d'aya suna wani irin kuka mai sanyin sauti.

Cikin k'arfin hali baba bello ya rink'a musu fad'a shi dinma kamar a gigice yake yana.

" Haba Ahmad yanzu wannan shine matan da zakuyi wa d'an uwanku Adam har kai dinma kuka shine abinda zaku aikawa Abubakar Usman ase ba Addu,a zakiyi mai ba"?

Ina shi ma Abba kanshi ya jingina jikin kujera yana ta nanata Addu,a Amman INA hawaye Sai zuba suke Ganin kukan Abba yasa Aysha sakin wani irin kuka sosai ta rink'a jin tausayi Abban.

Cikin yin Hamdala Ummi tace

"Ahmad accident ne Abubakar yayi"?

Kai ya jinjina alamun a,a" Cikin mmk tace

" toh me ya sameshi"?

Murya Na rawa yace

"Ummi kashe Abubakar akayi"!

Gaba d'aya parlon suka juyo gareshi cikin rud'u da alamun tabbaya Abba ne yace waya kashe min Abubakar "?.

Cikin sanyi yace

"wani yaronsa ne Adamu "

Baki Na rawa har suna had'a baki sukace Adamu, Adamu Dan y'iware nan"? Cikin gyada kai Yace shi ne.

Adamu wani Yaron Abubakar ne shike wakiltan sojojin kan hanya Na yankin Taraba zuwa binuye state kuma yaron ya dad'e da farautan rayuwar Abubakar Dan yana hank'k'o kanshi a matsa yin Abubakar kuma yana jin takaicin yedda Abubakar ke ta kai mai birki kan halinshi Na zalumci.

Toh da suka taso suna tfy har suka isa cek point na kan hanyar Y'iwaren ya samesu a lkcin azabar tayi sai ya tsaya sunyi sallah da driver shi cikin sanyi yace.

"Sani muyi salla anan gunsu Adamu Sai mu wuce ko"?

cikin tab'e fuska Sani Yace 'ni wlh oga ban son Adamunnan mugune"

Dry ya danyi cikin sanyi yace

"kake kyautatawa dan Adam zato kaji ko Sani? ba abin da zai faru face da sanin Allah"

Shi dai Sani ba Don ya soba suka tsaya sauran sojojin suna ta murna da ganin ogansu Gashi da halin kyauta Sunyi sallansu Sani ya fito musu da Abinci da Ummi ta had'a musu sukaci tare da sud'in.

Sun gama komai zasu tafi Wani daga cikin su yabi bayan Abubakar cikin sanyi yace

"oga Dan Allah kake kula da kanka a Gaban oga Adamu"

Dry yayi Yace ba komai Allah Na tare dani.

Har ya shiga mota Adumun ya bishi rik'e da sanda irin ta kiwon shanu.

Cikin dry Yace 'kai Oga tsaya ba kai kace Fullo bane Sanda bata cinka bari mu gani"

Cikin dry ya d'an juyo yana "ai fulanin da nacema bana yenxub.. Kafin ya k'arisa Sai sand'ar yaji kauuu a k'eyarsa zai juyo ya kuma sake mai d'aya a gadon bayanshi ya yunk'ura zai taso ya k'ara mai d'aya a tsakiyar kanshi,

Ganin abin ba Na wasa bane yasa sauran suka rarumoshi suka danne.

Shiko Abubakar cikin azaba ya fad'a jikin Sani.

yana numfashi da k'er yace "Adamu yanxu nizakayiwa haka Amman ka sani Sai Na rama" A take Sai ko ya fara aman jini.

Ihu bayan hari ganin haka Sai Jikin Adamu ya d'au b'ari cikin tsoro da kuka Yace.

"Na shiga uku Abbakar aman jinin kakeyi Dan Allah ka gafarceni"

Cikin aman Yace

"Sai Na rama fa"

Cikin kukan Yace ka rama indai zaka yafe min Dan Allah Abubakar ka gafarceni".

Sai ya kuma sakin kuka

Shi kuma aman yak'i tsayawa cikin galabaita Yace Na yafema Dan Allah tunda Allah ma da kanshi yana son masu hak'uri da yafiya"

Cikin nishi Yace

"Sani kira min d'an uwana kira min Hamma Yusuf d'ina".

Shine fa a lkcin ya kira Yusuf.

Shiko yana jin muryar d'an uwanshi

Cikin fizgar numfashi yace

" SLM Hamma Yusuf Adamu yamin dukan kisa ni nasan zan mutu Amman Na yafe mai Hamma Yusuf ko Na mutu Ku barshi Na yafe maiii, Sai ya d'aura da Kalmar shahada...

ganin haka yasa Sani zare woyar cikin firgita Yace..

"Hamma Yusuf Oga Abubakar ya rasu ya tafi ya barmu".

Furucin kenan da ya buga zuciyar Yusuf ya sashi sumewa.

Cikin Sauri Abba ya mik'e tare da cewa baba bello Yaya mu tafi mu d'auko gawarsa muyi mai su tura".

har sun mik'e Cikin kuka Aysha tace Abba " kalli Hamma Yusuf shima a sune yake tun dazu bai numfashi "

Su gaba d'aya Sai yanzu suka Ankara kan Yusuf dake ruk'ume jikin Ahmad.

Kai Abba ya jinjina ya zo suka d'aga shi shi da Ahmad Sama suka haura dashi har kan gadon Abban suka direshi Abban ya duk'ufa kanshi cikin zubda qollah. A Ranshi yake cewa Rashin d'an uwa bai da misali".

A hankali ya samu ya farfad'o sannan Abban ya mai Alluran bacci.

Su kuma suka wuce.y'iwaren Kafin su iska sarkin garin yasa akayi mai sutura akayi mai sallah Aka kaishi gidan shi Na gsky da yake abokin bappa yaya ne su Abbanma Sai k'abarinshi aka kaisu suka gani washe gari da safen sukayi sammako suka dawo Adamu kuma da kanshi ya kai kanshi hukama dasu Abba sukazo aka kawoshi garesu Abba kam Na ganinshi Sai hawaye Shiko baba bello cikin kuka Yace

"Adamu kaci amanar abota a duniya"

Haka suka dawo gida aka zauna karb'ar gaisuwa

Shi ko Yusuf tunda ya farfad'o akayi mai Allurar bacci bai tashiba Sai washe garin da safe bayan su Abba sun dawo.

A hankali ya bud'e idanshi cikin wani irin tsinkewar zuciya da tuni abinda Sani Yace mai ya mik'e jiki Na rawa Toilet ya shiga Alwala yayi cikin firgici kar acemai gsky ne abin da yaji Sallolinshi ya rama sannan ya fara jera nafilfili.

Yana cikin sallanne Ahmad ya shigo ganin yana sallah yasa ya juya.

Parlon Ummi yaje cikin dashewar murya yacewa Aysha

"Auta kije d'akin Abba B'iyaye ya tashi ki tafin mai da abinci"

Aysha dake kwance jikin kakarsu innayi Fuska a kub'b'ure fuskar tayi jazir ga wani zazzabi mai zafin gske cikin jin jirin ta mik'e tana goge k'ollah.

Kakace ta d'an rik'o hannuta cikin sanyi tace "Kar kije mai da kuka"

Kai ta gyada cikin share k'ollah A hankali ta haura saman cikin sanyi ta bud'e k'ofar d'akin Abba ta shiga kanta a sunku ye Shiko jin motsin bud'e k'ofar ya juyo a firgice.

ganin Aysha ya sashi tsura mata ido cikin son ganin fuskarta Itako jin jirin yasa ta zame gabanshi ta rik'o hannushi.

Ido ya zaro cikin rawan lips d'inshi ganin hawaye a idon ta cikin tsoro Hamma Yusuf ya fad'a jikinta kanshi ya manna a tsakiyar k'irjinta ya Sa hannushi ya ruk'k'ume ta cikin tsoro ya rink'a juya kanshi yana murzawa a k'irjinta kamar yaro cikin alamar kar ta gaya mai baya sonji K'ara tura kanshi yake a k'irjinta Itama Sa hannu tayi cikin kuka ta manna shi da jikinta ta k'ara matsoshi shi kuma k'ara narkewa yayi a jikinta.....

```WANNAN NOVEL D'IN NA SADAUKAR DASHI GA Y'AN UWANA YAYUNA YA ABUBAKAR DA AHMAD ALLAH YA GAFAR TA MUKU Y'AN UWANA RABBI YA SANYAYA MUKU MAKON CINKU Yasa Aljannace makomarku".```

By garkuwan Fulani [4/18, 10:14 PM] Aisha Aliyu Garkuwa: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👆🏻👆🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Pure moment of life writer's P.m.l.w

www.aishaaligarkuwa.blogspot.com

Lkci d'aya jikinshi ya rink'a bari yana tsuma hatta jijiyoyin kanshi saida suka taso sama fuskarsa tai jazir sai k'am-k'ameta yake, ita kuwa kuka ta saki cikin dashewar murya ta sa hannuta ta tallabo fuskarsa ta rink'a juya mai kanta alamar yayi shiru, Shiko bai ma san halin da yake cikiba gaba d'aya ya resa me ke mai dad'i a duniya.

A parlon kuwa Abba ne da Baba bello suka shigo Dan gaisawa da su innayi da suka iso bada jimawa ba har sun juya zasu fita, Baba bello ya kalli Ahmad dake zaune gefen kaka cikin sanyi yace.

"Ahmad har yanzu Yusuf bai tashi bane "? Kai ya d'an jingina a hankali yace.

" a a ya tashi".

yana fad'a mai haka Sai suka fasa fitan suka juya suka haura gun Yusuf d'in.

Cikin d'akin kuwa Yusuf duk ya rikice Aysha sai kuka take shima cikin azabar zuciya ya samu kukan ya kufce mai da samun kukan sai ya daina rawan jiki sai zamewa yayi kan cinyarta ya kife kanshi ya rink'a wani irin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro kukan da ka jishi kasan akwai k'una mai tsananin yawa a zuciyar mai yinshi.

Itama Aysha kukan take tana k'ok'arin tallabo shi.

Dai dai lkcin su Abba da Ummi da Baba bello da Ahmad suka shigo, Su Na shiga Kukan Yusuf da Aysha da yedda suka ruk'ume juna suna kukan. ya tona musu zuciya lkci d'aya Ummi ta zame gefen su Cikin kauda kai Baba bello ne yayi k'arfin halin mgn Bayan duk sun zauna sun sasu a gaba Cikin dauri yace.

"Haba Yusuf wannan kuka ya isa haka meyasa bazamu d'au dangana ba shin ase ina yebonka ase kai d'in kafi kowa sakewar zuciya ji yedda kasa matarka a gaba kana kuka yanzu kasan tsawon wani lkci da Aysha ta d'auka tana kuka kalli fuskarta fa ka tausaya mata mana itafa abu 2 ne ya had'e mata kukan rashin d'an uwanta da kukan tausaya wa halin da kai mijinta zaka shiga na tabbata da ta ga ka daure da matsalarta zata regu kuyi haquri Yusuf am".

Kai ya d'an d'ago Cikin kallon iyayen nashi lkci d'aya kuma ya fad'a jikin Abban su ya saki wani irin sautin kuka yana.

" Abba shi ke nan Babiker Na ya tafi bazai dawoba ya tafi har abada"

Allah sarki Abba shima kukan d'an nashi sai ya sashi kuka cikin kukan yace.

"Yusuf Abubakar baiyi gaggawa ba kuma muma bamu makara ba hanyace wace dole ko wanne mai rai sai ya bita Yusuf ba Abubakar zamu yiwa kuka ba kanmu mukewa kuka, sabo mukewa kuka duk yedda muke sonshi Allahn da ya bamu shi ya fimu sonshi ka dena yiwa d'an uwana kuka, insha Allah muna zata masa Rahama ka tunafa kashesa akayi".

Kuka ya k'ara saki Cikin k'uncin zuciya yace.

" Wlh ba dan Babiker da bakinshi yace min ko ya mutu shi ya yafewa Adamu kuma yace min koya mutu kar muyiwa Adamu komai, badan hakaba wlh da Adamu Sai yaga k'ask'anci da sai ya d'an d'ani hukunci Amman Babiker yace kar amai komai".

Jin haka yasa Ummi ma sakin kuka.

Aysha ce cikin kuka tace.

"Hamma Yusuf ka gani fa kasa Abba da Ummi kuka Hamma Yusuf kayi haquri ka bar kukannan".

Ahmad ne ya matsoshi Cikin sanyi yace.

"Biyaye Abubakar yafi buk'atar Addu,armu da kukannan dan Allah ka daure ko iyayenmu Sa samu sauk'in abin".

kai ya rink'a jinji nawa Cikin sanyi Ahmad d'in ya rink'a goge mai k'ollan.

A hakan suka samu ya d'an dawo hayya cinsa sannan suka jashi suka fita wurin amsar gaisuwa. Suna fita gefen kakansu suka zauna shi da k'anneshi dasu Adam Allah sarki bappa Yaya Sai hawaye ke wonke mai fuska ganin yau Allah ya zare mai d'aya daga cikin jikokin nashi. Cikin zubda k'ollah ya rink'a yi musu nasiha.

Da deddere Abba da kanshi ya kira Yusuf Yace yazo d'akin shi su kwana tare su Adam kuwa baba bello Yace su d'auki matansu su koma gida jensu da safe Sa kuma zuwa kafin ai safakar uku.

Shi ko Yusuf tun da suka shiga shi da Abba ba abinda yake Sai bawa Abba lbrin irin hirarrakin da Babiker d'in shi ya rink'a yima mai da yazo. da k'er Abba ya lallabashi jin kukan da yake har numfashin Sa Na fita, shiko Kasa baccin yayi Sai tashi yayi ya d'auro Alwala ya rink'a karatun k'ur,ani mai girma karatun yake da Farin Yana kuka daga baya kuma Sai kushi,i ya halarto mai Amman haka ya kwana ba bacci kam Sai rawan sanyi da yake.

Itama Aysha a d'akin Ummi kukan da tasha ya k'ara ingiza zazzabi jikinta ga rashin cin abincin da takeyi lkci d'aya jiri ya sark'a feta ga amai da take Na wahala tayi kakari har ta banu amman ba abinda za harar kafin zuwa safiya duk ta galabaita.

Kashe gari da sake ta kama ranarce za,ayi sadakan uku Dan da wuni akayi lissafin. Tun asuba su Abba da baba bello da su Ahmad da Yusuf dasu Hydar gaba d'aya dai zuciyar tasu suka hallara a masallaci gidan nasu da maqota da abokan arzik'i . Akayi Sada kan uku ana watsewa su Ahmad kuma da k'annesu suka suka d'auki k'ura,anai suka rink'a karatu da Addu,a da nemawa mamacin gafara.har zuwa Tara da rabi sannan suka koma Cikin gida, a safiyar Dr Umar ardo da Goggo Aysha ma suka koma Yola Cikin jimamin rashin da sukayi, Hydar kam Yace bazai komaba tukun, su Bappa Yaya ma sun koma Anuty Sadiya ma Abba ya sata tfya dole tana kuka.

11 da kadan Na safe su gaba d'aya suna zaune a parlon Ummi harda Nenne duk Dan su d'ebewa juna kewa.

Ummi dake ta zirga zirga ta fito jiki a mace ta kalli kaka a hankali tace.

"Kaka jikin Ayshan Na fa yak'i duk ta gala baita gashi ko ruwa tasha Sai ta harar ni Na tsorita da abin" .

Hydar ne Cikin sauri yace.

"Toh Ummi mu tafi asibiti mana"

Kakan ma Asibitin tace suje, Shiko Yusuf ido ya zuba musu cikin rashin abin cewa, Sai Nenne ce tace

"toh Ummi ta fito mu tsfin yafi ai ko"?.

Kai ta jinjina cikin sanyi tace.

" ko tsayuwa fa bata iyawa jiri da rawan sanyi, Amman dai bari Na tallabota".

Ummi Na shiga ta sameta ta fito wonkan da ta tayata ta shiga da Dan matsa ruwan kuma Sai ta d'an ji k'arfi kadan duk da tana jin jirin, mai ta d'an shafa mata sannan ta taimaka mata ta zura doguwar riga sai d'an gyelenshi ta yafa, sannan ta Dan kamata suka fitoh parlon sunan isa, parlon sai jirin da wani irin duhu ya rufe nata ido, Cikin sanyi da rashin k'arfin tace "Wayyo Ummi zan fad'i duhu nake gani".

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull