Noor al hayat complete by khaleesat - Chapter 52
Noor al hayat complete by khaleesat Chapter 52: Noor al hayat complete by khaleesat Chapter 52. Lumshe ido Aliyu yayi jin sunan da ta kira lkci daya…
3,456 words
Lumshe ido Aliyu yayi jin sunan da ta kira lkci daya jikinsa yayi sanyi sosai, ya bude idanuwansa ya taka a hankali har ya isa gabanta, ja baya ta dinga yi xuwa lkcn ta daina kukan da take tsoro ne fal xuciyarta, ya xauna dab da ita har suna jiyo numfashin juna xata mike da sauri, yyi hanxarin rikota ta fashe da kuka jikinta na rawa, a hankali ya jawota jikinsa ya rungumeta lkci daya ta hadiye kukan da take, ya dinga jin yanda xuciyarta ke bugawa a kirjinsa kamar xai fito, lumshe ido yyi hawayen idanuwan sa suka xubo, cikin rawar murya tace "Barrister ka kunna wutan bana son duhun plss, switch the light on" Murya can kasa yace "Imannn" Ta fi second talatin muryar da taji na kai kawo a kanta, a hankali ta xame jikinta daga nasa tana kallon fuskarsa cikin duhun dakin kamar yanda shi ma yake kallonta a sanyaye, hannu ta kai fuskarsa tana masa wani kallo da kyar tayi gathering courage din cewa "Aliyu?" Rungume ta yayi kamar xai mayar da ita jikinsa cikin rawar murya yace "Yes Iman, I beg you... don't say no to me plsss, this our fate... na sha wahala kan ki a rayuwa Iman, na sha wahala fiye da tunanin ki, kashe ni ne kadai son ki bai yi ba, for good six years bani da kwanciyar hankali bani da walwala, forgive and forget the past plss, Barrister Aliyu..." Kasa ci gaba yyi bayan wani lkci ya ci gaba voice dinsa na breaking "I owe him... he gave up for me.... Ya bar min ke Iman, don girman Allah ki ji tausayina kar ki bani wahala...." Kamar warce aka yi moulding haka khadijah tayi stiff jikinsa maganganunsa na mata yawo a kai, she's still trying her best to apprehend all what he is saying, Jin tayi shiru ya dago kanta jikinsa na rawa, hawayen dake makale idonta suka xubo tana kallonsa, ta fashe da wani matsanancin kuka kamar warce aka aiko ma wa da sakon mutuwa, sauka yyi saman gadon a rikice ya durkusa kan gwiwowinsa kusa da ita yace "Iman kiyi ma girman Allah kada ki wahal da ni, I have already had enough, don't say no to this marriage, kar ki ce A'a Iman...." Kasa ci gaba yyi.... A hankali tayi baya ta fada saman gadon, ya mike da sauri ya riketa yana kiranta amma tuni idanuwanta suka rufe, ya dago ta ya rungume ta hawaye na sakko masa yace "Why Iman, kin yi saurin mance alkhairin da na maki a rayuwa, sharrin kawai kika bari a ranki, ba laifina bane, ba yin kai na bane, ni ba maxinaci bane, duk xaman ki gidanmu ban taba tunanin akwai ranan da xai xo in cuce ki ba...." Kasa ci gaba yyi ya runtse ido yana rungume da ita har sannan. Sai kusan karfe hudu saura na asuba khadijah ta bude idanuwanta a hankali, Aliyu da ke xaune kan darduma ya mike da sauri ya iso kusa da ita yana kallonta da damuwa, mikewa take kokarin yi tana kallon jikinta, riga ce mara nauyi jikinta maimakon atamfar da ta sa tun a gida, Aliyu ya xauna gefen gadon a sanyaye yana kallonta, kokarin sauka ta shiga yi daga kan gadon yana son riketa amma yana tsoron abinda xai biyo baya, cike da karfin hali yace "Iman you are not strong ina xa ki, Wait..." Bai san lkcn da ya riketa ba ganin tayi baya xata fadi, xai kwantar da ita ta kwace kanta tace "Let me" Dafe kansa yyi, ganin xata sake tashi ya kara rikota, tura hannunsa tayi muryarta na rawa tace "Dole sai ka rike ni ne, nace bana so" ko saurarenta bai yi ba ya ki saketa, ta fashe da kuka tace "I want to use the restroom ka kyalenii...." Tashi tsaye yyi ya dagota ya nufi bayi da ita, suna isa bayin ta kwace kanta ta shiga ta rufe kofar, a hankali ya koma gefen gado ya xauna duk jikinsa a sanyaye, tana fitowa ta nufi kofar fita ya mike da sauri yace "Iman" ganin ko juyowa bata yi ba ya karasa da sauri kafin ta isa kofar ya rufe ya marairaice yana kallonta, Xaunawa tayi nan bakin kofar ta hade kai da gwiwa tana shesshekar kuka xuciyarta yayi rauni ga wani xafi da yake mata, yanxu dama duk yaudararta Sudais yake, me yasa xai ci amanarta ya sa a aura mata Wai Aliyu?? Of all people why Aliyu? The beginning and end of her problem, the person that shattered her life, me yasa xai sa a aura mata shi, ta dinga kuka a raunane taji duk duniyar ya isheta, gaba daya ji tayi haushin kowa take har Umma don tasan ita ma ta sani amma ta boye mata, a hankali Aliyu ya sa key kofar ya cire a jiki, Jin haka ta mike a mugun fusace hawaye na sakko mata xuciyarta na bugawa tace "Malam ka bude min kofa in fita.... Bana son ganin ka, bana so...." Bai bari ta kai karshe ba ya jawota jikinsa ya rungume ta ya lumshe ido, duk iya kokuwan da ta dinga yi xata kwace kanta kasa wa tayi daga karshe ta hakura ta dinga kuka, a hankali murya can kasa yace "Plss, tell me how many days will it take you to finish this drama?" Dago kai tayi tana masa wani kallo xuciyarta na heaving, a sanyaye yace "I just want to get prepared... Just tell me for how long it will take you to finish it? And in sha Allah I will endure" fuskarta daure tace "Sake ni" a hankali ya saketa ta koma baya ta mika masa hannu tace "Bani makullin" ya mika mata makullin hannunsa, ta juya ta bude kofar ta fice tayi banging din kofar, Ya d'an tabe baki ya juya a hankali ya koma kan gado ya kwanta don har wani ciwo kansa ke yi masa baccin da bai yi ba, har aka kira Asuba bai bari bacci ya daukesa ba ya mike ya shiga bayi ya dauro alwala ya fito don wucewa masallaci, kwance ya ganta kan 3 seater a parlor tana bacci ta dunkune waje daya saboda sanyin parlorn, ya kashe A.c sannan ya nufi kofa ya bude ya fita. Ko da ya dawo masallaci bai ganta parlorn ba kuma, ya wuce sama ya bude kofar dakinta a hankali yana leka ciki ya ga bata nan, juyawa yyi da sauri ya bude wani dakin, xaune ya ganta kan darduma ta jinginar da kanta jikin bango, tana ganinsa ta daure fuska ta cinno baki gaba, a hankali ya rufo mata kofar ya shiga nasa dakin ya kwanta, sai a sannan bacci ya daukesa. Sai da gari ya fara wayewa khadijah ta mike jiki ba kwari daga kan darduman da take xaune ta bude kofar dakin ta fito, dakinta ta bude a hankali tana kallon ciki, ganin babu kowa ta shiga ta rufe kofar, bathroom ta shiga tayi wanka ta fito, bayan ta shirya ta kwanta saman gado jin kanta na ciwo sosai, bacci ne ya dauketa daga haka, Bata farka ba sai da aka danna bell a kasa, ta mike xaune da kyar tana kallon agogo, har sannan kanta ciwo yake ba kadan ba, karfe tara saura ta gani, ta sauka daga kan gadon ta dau hijab dinta ta sa ta fita, a hankali ta bude kofar ta ga Baby tsaye rike da basket din abinci tana murmushi tana kallonta, khadijah ta hade rai sosai ta juya ta koma parlor, Baby da ta bi ta da kallo a xuciyarta tace kya yi ki gama ne ma, A nan parlor ta ajiye basket din ta juya xata fita khadijah ta bi ta da kallo har ta fita ta rufe kofar sai a sannan baby ta fara dariya kasa kasa, khadijah da ta bi ta da kallo ta xauna kujera lkci daya hawaye ya cika idonta ta ji kamar ta bi ta ta mata magana amma ta kasa tashi, wato dai ita ma tasan wanda aka aura mata amma bata fada mata ba, tashi tayi ta wuce sama ta shiga daki ta fada kan gado tana kuka takaici, bayan wani lkci ta mike ta dauko wayarta ta shiga kiran Sudais, sau uku tana kira bai dauka ba, ta ajiye wayar tana share idonta ta kwanta xuciyarta ba dadi, ta jima kwance jin ciwon kai ya isheta tana son shan magani ta mike a hankali ta fito, downstairs ta sauka taga abincin da baby ta kawo na nan yanda ta ajiyesa, ta kalli agogo ta ga har sha daya ya kusa, sama ta kalla, ta fi minti biyar tsaye kafin ta nufi kofar da take xaton kitchen ne ta shiga ta dauko cup da spoon, shayi ta hada ta koma kujera ta xauna, kasa shan shayin tayi ta ajiye cup din hannunta a hankali ta wuce sama, dakin da take tunanin nasa ne ta bude a hankali, kwance ta gan sa kan gado idonsa a rufe, ta dinga kallonsa kafin ta karasa ciki kamar mai tsoron taka tiles din ta isa har kusa da shi ta duka, Bbu wanda ya fado mata a rai lkcn sai little Sudais, lkci daya taji jikinta yyi sanyi ta dinga kallonsa ko kiftawa babu, lkci daya ya bude idanuwansa ta mike da sauri tana kalle kalle kamar mai neman abu duk ta daburce.....
Aliyu ya mike xaune yana kallonta yace "Did you come to check on me?" Ta tsuke fuska tace "Saboda kai Shureim ne?" Ya shafa kansa bai ce komai ba, ta juya da sauri ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fice, sai a sannan ta ja tsaki taji haushin shiga dakin da tayi, parlor ta koma ta dau shayin da ta hada, da kyar take sha don gaba daya bakinta ba dadi, ji tayi kamar xata yi xaxxabi, ta mike ta dau sauran kayan kumallon ta kai dining ta ajiye ta wuce kitchen don wanke cup din shayin ganin baxata ta iya sha ba, xata ajiye bayan ta wanke taji kamar mutum bayanta ta juya da sauri suka kusa cin karo suna hada ido ta hade rai ta dauke kai, ya mika mata hannu a hankali yace "Bani cup din" tace "Saboda xaka amsa cup sai ka tsaya bayana toh" Bata jira me xai ce ba ta ajiye cup din ta fita kitchen din ya bi ta da ido. Har aka yi azahar bata kara fitowa daga dakinta ba, xuwa lkcn ta fara jin yunwa sosai amma ta kasa sakkowa, duk xaman dakin ya isheta, tana ta xuba ido taga kiran Umma amma shiru, ga kewar Shureim da ya cikata, duk abubuwan suka taru suka mata yawa, ta hade kai da pillow tana son yin kuka amma ta kasa. Aliyu na xaune parlor yana duba wasu articles bayan sun yi waya da Sudais yace masa suna hanya, saboda su ma ya dawo parlorn ya xauna, ajiye takardar hannunsa yyi ya dau pain reliever a center table for the second time in 2hrs ya balla biyu ya dau table water dake ajiye ya sha maganin ya mayar da ruwan ya ajiye ya jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, ya rasa me yasa bai samu relieve ba bayan wanda ya sha daxu, har ya fara bacci a haka ya ji an danna bell, ya bude ido ya mike ya isa kofar ya bude, Baby ce rike da lunch, ganinsa tayi murmushi tace "Yayanmu Ina yini?" Ya shafa kai a hankali yace "Lafiya lau" da damuwa tace "Are you sick?" Ya d'an bude ido yace "Me kika gani?" Tace "You look so" murmushi yayi yace "Am alright" Bata ce komai ba ta shigo parlorn cike da tausayinsa ta ajiye abincin hannunta ta juyo tana kallonsa tace "Ka ma yi breakfast kuwa yaya?" Yace "Nayi mana, ya su Mumy" Xaunawa tayi tace "Suna gaishe ku" ya xauna shi ma yace "Ki kai mata abincin sama" xaro ido baby tayi tace "Uhn ba ruwana, I don't want to imagine me going to her now" Aliyu bai ce komai, tana kallonsa a hankali tace "You just have to be patient ya Aliyu, soon nasan xata hakura... Kar ka damu kaji yayana, I know it's just for few days" Murmushi yayi yace "Toh Allah ya sa" cike da tausayin sa tace "Ameen" yace "Plss ki taho da Shureim idan xa ki xo anjima...." Tace "Ae yana can gidansu" yace "Ehh ki dauko sa can din, I am lonely..." Tace "Toh Yaya xan kawo sa" Wayarsa ne yayi ring ya dauka yaga Sudais ke kiransa, yyi pick din call din Sudais yace "Muna waje" Aliyu yace "Alryt ku shigo" Baby na kallonsa bayan ya katse wayar tace "waye yaya?" Yace "Barrister with Dr Ayman I guess" Baby tayi shiru bata ce komai ba, bude kofar parlorn aka yi khaleel ya fara shigowa kafin Sudais, Aliyu ya mike bayan sun gaisa gaba daya suka xauna, Baby na kallon Dr Ayman tace "Ina yini" yace "Lafiya lau ya kike?" Tace "Alhmdllh" kallon Barrister tayi dai dai lkcn da ya kallota shi ma, yace "Ina yini" xaro ido tayi sai kuma tayi dariya tace "Ina yini" yace "Ohk I was thinking baxa ma ki gaisheni ba" Khaleel yayi murmushi yana kallonsa ta gefen ido bai dai ce komai ba, Aliyu ya kalli baby don tsoron xuwa daki gun khadijah yake yace "Baby talk to her tana daki" Mikewa baby tayi ba don tayi niyya ba ta wuce dakin gabanta na faduwa, Khadijah dake kwance ta daga kai jin an bude kofa, ganin baby ce ta mike xaune tana kallonta, a sanyaye tace "Shine daxu baki min magana ba kika wuce ko Baby" Baby tace "Hmm tsoron ki nake ai ni Iman" Baby ta xauna kusa da ita, khadijah ta kamo hannunta a hankali tace "Amma baby kin san wanda aka aura min kika boye min, idan kowa ya boye min ke bai kamata ki min haka ba, Ni yanxu shkkn cikin kunci xan kare rayuwata, nobody is after my happiness...." Hawaye cike idonta ta kare maganar, a sanyaye Baby tace "Nan gaba xa ki gane ma'anar hakan da aka yi Iman, just give my brother a chance... Iman ki manta abinda ya faru a baya, ki kwantar da hankalin ki da Yaya Aliyu you won't regret it am giving you my words...." khadijah ta dinga share hawayen dake sakko mata bata ce komai ba, tasan ita dai baxata taba kwantar da hankalin ta da wanda yyi disfiguring dinta heartlessly ba, cikin kwantar da murya Baby "Kiyi hakuri Iman, nima wllh ban san da yayanmu aka daura auren ba sai da muka tashi barin gida jiya da yamma kin dai ji na rantse maki" Har sannan khadijah bata iya ta ce komai ba sai goge idonta take, Baby tace "Ki sakko ki xo gu gaisa da su Barrister suna parlor" Kallonta khadijah tayi da sauri ta tsuke fuska tana girgixa kai tace "Am not going anywhere, they are nothing but group of deceivers..." duk yanda baby ta dinga lallabata Khadijah kin yarda ta fito tayi har da kukan ta, baby ta rasa yanda xata yi, mikewa tayi daga karshe ta dawo parlor, Aliyu na ganinta yasan kwanan xancen, Baby ta kirkiri murmushi tace "Tana fa bacci ne, Kuma bana son tada ta...." Murmushi Sudais yyi yana shafa beard dinsa a hankali yace "That's nyc, thanks for covering up for her, but we are not strangers, kuma baxa mu ji haushi ba idan kin ce tace baxata fito ba, wataran xata fito mu ganta ai" Dariya khaleel yyi yana kallon baby da ta rikice sai rawar baki take, Aliyu yyi murmushi bai dai ce komai ba, Sudais na kallonta duk da dariyar da ta basa shi ma yace "Sorry, just relax Mami ni ban yi haka don ki rikice ba" Baby bata san lkcn da ta balla masa harara ba ta juya da sauri xata wuce tana murmushi, Aliyu yace "Kawo masu drink" kitchen ta wuce ta dauko masu drink din ta ajiye, Aliyu yace "Abinci fa?" Sudais yace "Nop Alhmdllh" mikewa baby tayi ta dau abincin ta wuce sama, Dakin khadijah ta shiga tana harararta ta ajiye abincin hannunta tace "thanks for making me look stupid downstairs, Kuma abincin ma na daina kawowa sai dai ku fita eatry da mijin naki" daga haka ta wuce, tana shiga parlor tace "Yaya ni xan koma, Mumy tace kar in dade" Yace "Alryt then, da driver ku ka xo?" Ta girgixa kai yace "Toh je sama ki dau transport" Khaleel yace "Xa mu wuce yanxu sai Barrister yyi dropping dinta tunda hanyar daya" Har bakin mota Aliyu ya raka su bayan sun wuce ya dawo cikin gidan, sama ya wuce ya bude dakinsa ya shiga ya kwanta. Har aka yi la'asar khadijah na daki, duk da ta ji gidan shiru ta kasa fitowa ta dau plate ta debi abinci, Tana tunanin yanda xata fita aka bude kofar dakin Aliyu ya shigo, sau daya ya kalleta ya mayar da dubansa kan abincin da Baby ta ajiye dakin, ya isa gun abincin yace "Ain't you eating the food?" Banxa tayi masa, ya duka ya bude warmer din yana kallon abincin, dauka yayi ya juya ya nufi kofa ta bi sa da wani kallo, ganin ya fita ta tashi da sauri ta bi bayansa har ya shiga dakinsa ta shiga ya juyo yana kallonta, tace "Nace maka na ci abincin ne ni?" Kamar xata yi kuka tayi maganar, dariya ta basa, ya yi murmushi yace "You never told me" daga haka ya mika mata ta karbe abincin ta juya ta fita, yana jin ta sauka don dauko plate a kitchen ta dawo ta shiga dakinta, sai a sannan ya sauka xuwa kitchen ya hada shayi, duk da yunwan da khadijah take ji bata iya ta ci abincin me yawa ba, ta mike daga karshe ta fita, har xata kai abincin kasa sai kuma ta tsaya a hankali ta bude dakinsa ta gansa xaune yana rike da cup din shayin, ta sauke kanta kasa ta shiga dakin ta ajiye masa warmer din ta juya ta fita ya bi ta da ido. Karfe shidda saura baby ta dawo gidan tare da shureim, Sau uku tana danna bell, khadijah ta mike ta sauka bata san Aliyu ma ya fito bude mata ba, yana bude kofar Shureim ya wara ido ganinsa cike da murna yace "Unclee" nufo sa yayi da nufin rungumesa ya hango khadijah, Wara ido ya kara yi yace "Anty...." Murmushi ta sakar masa ta buda masa hannu, Har ya dau hanyar inda take sai kuma ya tsaya ya juyo yana kallon Aliyu dake kallonsu, dawowa yyi gun sa da gudu, Aliyu ya daga sa sama ya rungume sa yana murmushi yayi Pecking cheek dinsa, Lkci daya murmushin fuskar khadijah yayi fading, Baby bata san lkcn da ta fashe da dariya ba, Shureim ya xame daga jikin Aliyu ya nufi khadijah da gudu, wani kallo ta watsa masa tace "If I slap you" nan ya taka burki ya tsaya yana kallonta, Ta turo baki ta juya ta wuce sama, Murmushi kawai Aliyu yayi ya nufi yaron ya daga sa sama yace "How are you sweetheart" yace "Am fine" Baby ta ajiye abincin hannunta tace "Ina yini yayana" yace "Alhmdllh" tace "Driver na jira na waje, sai da safe" yace "Alright ki gaida mumy, tell her thank you" tayi murmushi tace "Toh yaya" daga haka ta juya ta wuce tana daga ma Shureim hannun, yana rike da Shureim suka haura sama ya shiga dakin khadijah ajiye mata shi yyi kusa da ita yace "Greet her now" a hankali Shureim yace "Anty good evening" dauke kai tayi ta hade rai tace "Evening" Daukansa Aliyu yayi suka fita dakin ta bi sa da wani kallo, har karfe kusan tara na dare khadijah bata ji motsin su ba, ta yi wanka ta shirya cikin night wear, jin shirun yyi yawa ta sa Hijab ta fita, ta fi minti biyu a tsaye, kafin ta tura kofar dakin a hankali, duhu ne dakin, ta laluba ta kunna switch, kwance taga Aliyu Shureim na kwance kusa da shi duk sun yi bacci, kashe Ac dake aiki tayi ta kashe switch din ta fita dakin ta koma nata ta kwanta. Kasa bacci tayi sai juye juye take har kusan sha biyu ta ji an bude kofa, sosai gabanta ya fadi ta kalli direction din kofar duk da wuta a kashe yake, rufe kofar yyi ba tare da ya kunna wutan ba ya iso har inda take ya duka, mirginawa tayi da sauri daga wajen tace "Meye haka?" Yace "Na xo duba ki ne kamar yanda ke ma kika xo duba mu" Xaro ido tayi tana kallonsa cikin duhun, yyi murmushi murya can kasa yace "Sweet dreams" daga haka ya fita ya kulle kofar dakin.