Rayuwa da gibi na batul mamman - Chapter 36
Rayuwa da gibi na batul mamman Chapter 36: Rayuwa da gibi na batul mamman Chapter 36. Murmushi Abba ya yi. Yaya da Inna Luba su ka shiga ɗaki. Basu daɗe ba…
3,353 words
Murmushi Abba ya yi. Yaya da Inna Luba su ka shiga ɗaki. Basu daɗe ba kowacce ta fito cikin shiga mai kyau. Yaya lace ɗin da Mama ta aiko ta ce mata ankon manya ne ta saka. Kai kana ganinta banda lalurar ƙafa da ba ƙaramar mace za ayi ba. Fuska dai kam Masha Allah. Akwai kyau irin na Katsinawa wanda ƴaƴanta su ka haɗa da na Simagade su ka fito gwanin ban sha'awa.
***
Ƙarfe bakwai da minti arba'in da biyar daidai Amma ta kira Taj ya ce mata suna wajen parking.
"Bari a sauko da amaryar sai ku shigo."
"Amma tare muke da Yaya."
"Tun ɗazu nake lalubenta cikin baƙi. Gani nan fitowa."
Da kanta taje wajen motar ta riƙo Yaya su ka shigo. Mama na hangota daga wajen zaman iyaye ta tada Umma su ka ƙarasa. Hajiya ma ta ce da Inna lallai ta tashi. Tunda aka ce Taj ne ya kawota ta san tana tattare da jin nauyin shiga jama'a ne. Mutane sun fara kallon Yaya ana ƙusƙus da faɗin uwar amarya ce sai aka ga matan Alh. Hayatu Sule masu aji sun je inda take suna yi mata maraba. Kayansu ita da matan da Amma iri ɗaya. Sannan su duka har ƙasa su ka gaishe da Inna Luba. Wannan abu yasa duk mai abin faɗa ta haɗiye kayanta. Dukkan alamu sun nuna su ɗin suna cikin farinciki da son juna. Gutsiri tsomar ƴan gayya bata da tasiri.
A ɓangaren amarya kuma ƴaƴan Amma wato Ihsan da Amira da kuma Anisa sun haɗu da masu ƙananun shekaru cikin ƴan gidansu Taj da Anti Zahra sai kuma Sajida da Zee wajen rako amarya. Gabaɗaya matan doguwar riga su ka saka ta wani yadi sky blue da ɗigon fari da pale yellow wadda aka yiwa wani irin ɗinkin bubu mai kyau. Umarnin Hajiya Gambo kenan. Duk wata jininsu da tayi ɗinki mai fitar da shape a gida zata ci bikinta. Babu head sai rolling da su ka yi da pale yellow ɗin yadi mai santsi. Babu yadda za ayi ka gansu basu burgeka ba. Modesty and elegance at its peak!
Amarya Hamdiyya kuwa gown ɗinta fara mai dogon hannu kuma wadatacciya. Bata bi jikinta ta tona sirrin wanda ya bada sadaki a gaban kowa da kowa ba. A kanta anyi mata ɗauri da net silver wanda aka ɗorawa wani abin ado mai duwatsu sky blue na gashi ya kwanta ta ɓari ɗaya. Daga tsakiyar ɗaurin inda gashinta yake a suturce aka ɗora farin net dogo har ƙasa. Wuyanta sarƙar farin gwal ce. Sai clutch bag ɗinta da takalmi mai tsini sky blue. Tayi kyau har ta gaji.
Ƙasa suka sauko sannan aka zo bakin ƙofa aka jera yadda za a shigo. Kallo ɗaya Anisa ta yiwa Hamdi tunda sai yau su ka iso ta ganeta.
"Mai kukan uber?" Ta faɗa ba tare da wani tunani ba.
Hamdi ta ɗago su ka haɗa ido. Ta saki murmushi mai ban sha'awa. Haka kawai sai Anisa taji ƙuncin zuciyarta ya kau. Ta matsa kusa da ita tayi musu selfie sannan aka ce su tsaya kamar yadda aka tsara musu.
Matan layi layi suka yi hagu da dama har layi shida. Sai Hamdi a tsaye. A bayanta kuma Bishir da Abba. Sai kuma Kamal da Ahmad a bayansu. Sanye su ke da yadi pale yellow da aka yiwa ɗinki ma hannu da ya wuce gwiwar hannu da kaɗan. Daga hula har zuwa takalmi komai nasu iri ɗaya in banda agogo. Hamdi tayi zaton tafiya za su fara yi don hankalinta a tashe yake tun a nan ga hasken flash ana ta ɗaukar hoto. Ƙofar hall ɗin aka buɗe ta soma jin sanyi da ƙamshin wajen na buso ta sai ji tayi hannuwa sun kama nata da gentle riƙo. Tsigar jikinta tashi tayi da tsoro da kuma gane hannun waye. Tsayuwarsa kaɗai a kusa da ita ta sanya sanyin nan ya ragu don kansa. Ta ɗaga kai su ka haɗa ido.
Kayan jikinsa sky blue ne harda babbar riga irin wadda ake yi ta zamani ba burum-burum ɗinnan ba. Shi ma hannun rigarsa ta ciki ƙarami ne kamar na ƴan uwansa. Ya sanya hula da takalmi cover shoe navy blue mai duhu sosai. Gashin baki da gemunsa da basu cika yawa ba sun sha gyara.
"Ya Rabbi, har na fara tsoron ko ni kaɗai zan shiga" Hamdi ta faɗi a hankali tana kawar da kai don kallon nasa babu rissina a ciki.
"Ina tare dake kowanne taku. Ki daina jin tsoro." Ya bata amsa a kunnenta.
Hannunta zai saki yaji ta kuma damƙe nasa.
"Don Allah ka riƙeni har mu zauna. Zan iya faɗuwa da takalmin nan." Ta marairaice masa idanu har lokacin tana magana a hankali don kada na gabansu ko baya su ji.
"Awwwnnnn, zuciyata" Taj ya dafe ƙirji kuma da gaske yadda tayi ɗin ya shige shi ne sosai.
Fari tayi da ido tana harararsa "A nan ɗin ma sai kayi?"
"Kin gama dani ne Mrs Ha..."
Wani abu su ka ji kamar harbin bindiga da ya katse masa magana. Sai kuma muryar MC yana sanar da shigowar ango da amarya da umarnin kada kowa ya bar wurin zamansa da sunan ɗaukar hoto. Wani irin kiɗan taushi ne yake tashi babu waƙa a yayinda suke shigowa wajen cikin nutsuwa. Matan dake gaba basu mai rawa sai ɗan kwanon hannunsu mai fulawoyi masu kyau da su ke ta watsawa sama.
Da su ka iso gaba Yaya ta ƙyallara idanu ta hango ƴan matanta, bata san lokacin da idanunta su ka tara ƙwalla ba. Ta dinga hamdala a zuciyarta. Ashe Inna Luba ma hakan take a wajenta. Sai dai ita bata iya ɓoye nata hawayen ba. Jikokin kenan sai Halifa cikon na huɗu. Sai kuwa na yayarta abar alfaharinta har kullum. Amma dai jininta da take da cikakken iko dasu waɗannan ne. Da kanta ta dinga bin ƴan uwan Yaya wato ƴqƴan abokiyar zamanta mazansu da matansu a samu mai zuwa bikin nan amma yadda su ka ƙi zuwa na Sajida wannan ma ƙi su ka yi. Ta roƙi maigidanta ko sau ɗaya ne ya yi musu magana ko ya zo ƴarsa taji daɗi ya ce ba zai taɓa murna don ƴaƴan ɗan daudu sun yi aure ba. Su je can su ƙarata. Godiya kawai take ga Allah domin bai haɗa mata zuri'a da lalatattun mutane ba. Dukiyar bata tsole mata ido ba. Girmamawar daga surukan ƴaƴan shi ne komai a wajenta.
A teburin gefensu Iyaa ce da su Ummi, sai kuma surukar Sajida da ƙannen Safwan. Shi da Baballe suna can ɓangaren maza.
Amarya da ango sun sami waje sun zauna sannan ƴan rakiyar su ka koma nasu waje. Aka shiga cikin taro ka'in da na'in.
An fara da addu'a daga bakin babbar baƙuwa Malama Maimuna. Bayan ta gama aka ce ta faɗi kalmomi biyu zuwa uku na shawara ga ango da amarya.
"Tajuddin da Hamdiyya. Abu ɗaya zan faɗa muku. Duk abin da za ku yi ku tuna cewa kowa cikinku mai kiwo ne kuma abin tambaya akan kiwon da Allah Ya bashi. Duk wanda ya tozarta amanar Allah sai Ya tanadi amsar bayarwa."
MC ya karɓi mike ya ce "wannan fa damu duka take. In kin san satar fita kika yi ki ka zo nan babu ruwanmu. Kai kuma mai shirin samun sabuwar budurwa a nan domin ka ci zarafin ta gida ta hanyar kwaye mata baya kana tona mata asiri to kai ma dai ahir ɗinka."
Dariya aka yi sannan ya ce ina Hajiya Amina aminiyar Inna. Tasowa tayi ita ma ya buƙaci kalmar shawararta.
"Kada ku yarda soyayya ta sanyaku saɓawa Mahalicci. A komai na rayuwa ba a yiwa umarnin da ya saɓawa Allah biyayya ga kowa."
Godiya aka yi musu sannan MC ya ɗora. Agendarsu ta gaba ita ce gasar da aka shiryawa team ɗin ango da amarya. Tambayoyi ne da za su amsa game da juna. Aka sanya kujeru biyu suna kallon juna su ka zauna. A team ɗin ango akwai Sajida, Zee da Halifa.
Team ɗin amarya kuma Yaya Hajiyayye da ta ce ta fi kowa sanin duka ƙannenta, Kamal da Ihsan ɗin Amma.
"Ba zan tambayeku birthday ɗin juna ba."
Ya raba musu takardu guda goma. Kowa a takardarsa zai rubuta amsa da taimakon team members ɗinsa. Wanda ya yi na ɗaya zai sa wanda ya faɗi yin duk abin da yake so.
Ƴan biki aka kasa zaune aka kasa tsaye da ganin wannan sabon salon. Kowa ya zata rawa za a sha yadda aka saba ana liƙi a gaban DJ.
MC ya ce "a rubuta min cikakken kwanan watan ranar da ku ka fara haɗuwa a cikin sakan talatin."
(12/08/2021)
Kusan tare su ka ɗaga takardunsu kafin lokaci ya cika.
Kemara ta ɗauka aka haska a manya manyan talabijin dake manne a jikin bangon hall ɗin ta kowacce kusurwa.
Daga nan ya dinga yi musu tambayoyi akan juna. Kamal, Yaya Hajiyayye da Ihsan da ta rayu da Taj kafin tayi aure a US sun taimakawa Hamdi sosai. Kazalika su Sajida. Aka gama tambayoyi suna kunnen doki.
"Dole a sami na ɗaya da na biyu fa. Team members ku koma ku zauna a barsu su kara su kaɗai."
"Banda ke Hamdiyya, wa Taj yafi so? Kai ma banda kai wa tafi so?"
Suna gama rubutun su ka ɗago kai.
"Happy Taj wa ka fi so?"
"Alh. Hayatu Sule Maitakalmi" ya faɗi da murya mai ban tausayi. Inna sunkuyar da kai tayi ta bar su Amma dasu Mama su da share ƙwalla.
"Amarya wa ki ka rubuta?"
Takardar ta ɗaga masa (Alhaji) ta rubuta.
Ƴan uwan Taj su ka dinga tafa mata suna murna.
"Wa ki ka fi so amaryar Happy Taj?" MC ya tambayeta.
Da murmushi ta ce "Mamana, Yaya" tana mai kallon inda Yaya take a zaune. Baiwar Allah ita ma ƙwallar ta kama yi.
"Taj wa ka rubuta?"
(Duka iyayenta)
MC ya nuna Hamdi ya ce "a tafawa amarya Hamdiyya."
Wurin ya kaure da hayaniya da murnar mutane. Wurin amsa tambayoyin nan ba ƙaramin kiɗima jama'a suka yi ba tun ma suna tare da masu taimaka musu.
Taj ya fitittike ya ce bai yarda ba. "Ni fa da gangan na faɗi saboda nayi zaton ba za ta iya amsa nawa ba tunda ban taɓa faɗa mata ba."
MC ya ce "Kaga rigimammen ango" aka bushe da dariya "abin da za ta saka ka kake gudu?"
"Eh wallahi. Na san me wahala za ta saka ni." Ya sha kunu da wasa.
"Wai haka?"
"A'a" ta amsa mischieviously. Kai kana ganin farincikinta ka san amsar bata kai zuci ba.
"To ke mu ke sauraro"
Hamdi ta zaro ido "wai a nan zan faɗa?"
"Eh mana" cewar MC
"Iyayenmu fa duk suna nan" ta kalli saitin teburin iyayen nasu a kunyace.
"Ga takarda ki rubuta masa ba sai mun ji ba."
(Don Allah ka daina yi min waƙar India)
Tana bashi ya saka loudspeaker a bakinsa ya karantawa kowa. Aka fara dariya da ya ce a bashi fili.
"Waƙar ƙarshe zan yi irin wadda ake mirginawa a ƙasa ana kuka a gidan boss."
Hamdi duka hannuwa tasa ta rufe fuskarta.
"Na fasa kada tayi mana kuka." Taj ya faɗi yana murmushi.
Mutane suna ta dariya. MC ya ce Taj ya faɗi wani abu kafin su koma mazauninsu.
"Nagode Allah da Ya bani Hamdiyya Habib Umar. Allah Ya bamu zaman lafiya."
MC ya turawa Hamdi speaker saitinta "ke kuma me za ki ce?"
Ta kalli Taj ta rufe fuska da gefen mayafi "Amin....au mungode zan ce."
"Awwnnnnnnn" ɗin mutane kamar ta fasa dodon kunne. Aka dinga tafa musu har su ka zauna.
Mutane sun nishaɗantu matuƙa. Daga nan aka fara rabon abinci wanda a yau ma'aikatan Happy Taj su ka baje kolin basira wajen yin wanda yafi na kullum daɗi. Nau'in girki na gaske kala kala aka yi. Luciousbites da kanta ba saƙo ba kuma ita tayi snacks da kuma daddaɗan youghurt da furarta wanda ake sha ana santi. Juice kuwa sai wanda mutum ya zaɓa. Babu mutum ɗaya da zai ce ya tafi gida da yunwa. Kowa yaci ya ƙoshi.
Bayan an gama ne DJ ya soma nasa aikin. Anti Zahra tana bawa Hayat ruwa ta hango Ahmad yana yi mata signal. Wayarta yace ta duba. Tana ɗauka call ɗin Salwa na shigowa. Kira yafi arba'in. A zatonta abin da zai ce ta duba kenan shi yasa ta ɗauka.
Salwa ta saki wata wawiyar ajiyar zuciya "Anti ina ta kira..."
"Banji ba ne Salwa. Ya gida?"
A gadarance ta ce "ina waje tun ɗazu. Kin taho da katina?"
Anti Zahra ta kalli Ahmad da har yanzu alamar duba waya yake yi mata da hannu tace "wane katin?"
"Ba a aiko min ba?"
"Ke da kike Bauchi ai ban san za ki zo ba."
Tashi tayi ta bar yaran a wajen ƴan uwanta da suke seat guda ta ƙarasa wajen Ahmad. Waje su ka fita saboda hayaniya.
"Ya zance ki duba waya ki tsaya amsa kira kuma?"
"Sorry, na zata kiran Salwa kake nufin na duba." Ta nuna masa missed calls.
"Ƙyaleta. Nayi miki text nace na taho da Mami bata da lafiya. Gobe zan kai ta asibiti in sha Allah."
"Subhanallah. Shi ne muke nan? Bari na ɗauko su Aisha mu tafi."
"Kada ki damu. Salwa na gidan. Bana so mu koma ne kiga baƙi. A can ma ya dace na sanar dake to kuma ban sami nutsuwa ba."
Murmushi tayi masa "babu komai. Amma Salwa fa ta ce min tana waje."
"Waje kuma?"
"Eh, kati take so in..."
"Koma ciki."
Yayi maganar yana sauko matattakalar da za ta sada shi da hanyar fita. A waje ya ganta tsaye can gefe ta rakuɓe kamar wata almajira. Duk sauron wajen nan ya tabbata ya gama cinyeta. Ta ɗan bashi tausayi amma bai nuna mata ba.
"Taho mu je."
Masu gadin suna ganin shi su ka bata hanya ta wuce. Magana ta so yi masa amma babu fuska. Da sauri sauri ya ding tafiya sai da su ka shiga hall ɗin sannan ya nuna mata inda ango da amarya suke.
Taj da Hamdi ke tsaye a filin rawa taƙi motsi. Ya riƙe hannayenta yana magana tana dariya. Ce mata yake ko dai ta saki jikinta ko ya kama break dance yanzun nan.
"Kin gani Salwa? Ke ya fara sani kafin Hamdiyya. Da yana sonki da kece a tsaye a can. Don Allah ki samawa kanki lafiya ki jira naki mijin."
"Na haƙura Yaya. Tafiya ma zan yi." Ta ce kamar gaske.
"Jirani a nan in faɗawa Zahra. Nan da kamar 15 minutes sai mu tafi."
Yana barin wajen tayi gaba. Ido rufe ta nufi inda su Taj su ke. Sun bar rawar sai hotuna da ake ta ɗauka. Tun kafin ta ƙarasa inda suke Hamdi ta hangota. Gabanta ya kama faɗuwa sai ta soma karanta Ayatul kursiyyu. Salwa na zuwa ta shige tsakaninsu ko sallama babu.
"Ya Taj ayi mana hoto."
Yadda kafaɗarta take gugar tasa ko Hamdi da suke tsaye tun dazu bata yi wannan tsayuwar dashi ba. Matsawa yayi da sauri yana a'ziyya a zuci sai ji yayi ta riƙe masa hannu. Wani maiƙo maiƙo da danshin da ya yi zaton na gumi ne daga hannun nata duk ta shafa masa.
Idanun Hamdi a take su ka rikiɗe sai dai ganin idon mutane sai ta daure zuciyarta. Taj na jan hannunsa ya fara jin ciwon kai Salwa sai ta sake ƙarfin riƙon.
Basu san daga ina ba kawai sai wani hannun su ka ji ya kama hannayensu dake haɗe ya raba.
"Zan ci mutumcinki Salwa akan yarona kin ji ko."
A matuƙar tsorace Salwa ta dubi Inna. Hanjin cikinta su ka kaɗa. Layar da take shirin sakawa a baki ta tauna sannan ta umarce shi da ya biyota ta saɓule ba tare da ta sani ba. Barin wurin tayi da wani irin sauri. Tana tafiya Inna ta duƙa da sunan Allah a bakinta ta ɗauki layar. Sunan ɗanta ta gani ɓaro ɓaro a jiki. Ta haɗa ido da Hamdi da taga komai ta matsa kusa da ita.
"Kama shi ku zauna. Zan faɗawa Amma a rufe taron haka."
Kai Hamdi ta gyaɗa. Ta riƙo Taj da idanunsa su ka birkice. Bayan sun zauna tana ta tofa masa addu'a a fakaice ya dawo daidai. Ya ce ta tashi ya kaita gida.
"Su Yaya fa?"
"Bishir zai kai su. I need alone time with you."
"Na'am?"
"Nace muje na kama mana hotel."
"Wallahi ba haka ka ce ba." Ta faɗa a tsorace.
Dariya ya yi mata "Ki ka ce baki ji ba."
"Da wasa nake."
"Matsoraciya."
Addu'ar rufe taro aka yi. Kowa ya tashi cikin murna da jindaɗin wannan biki mai ban sha'awa. Baballe ya ɗauki Zee, Safwan ya ɗauki Sajida sannan Taj ya tafi da Hamdi.
Ahmad da Anti Zahra kuwa mamakin duniya ne ya kama su da su ka shiga gida su ka tarar ana bushashar cin shinkafa dafaduka da farfesun kifi wanda ɗaya daga cikin ƴaƴan Anti Zabba'u ta dafa. RAYUWA DA GIƁI 28
Batul Mamman💖
This page is sponsored by SAFFADEMPORIUM the world of amazing scents. Kun san da wuya na tallata abin da ban sani ba. To jama'a akan saffademporium ni ɗin jiyau ce kuma ganau. Ido ya gani, hanci ya shaida! Safiyya Ummu Abdoul our one and only Chairlady ta Fikra Writers Association ita ce mamallakiyarsa. Komai na Fikra kuwa daban yake. Akwai Raudha turaren carpet da kujeru, Naeema airfreshner, oils zafafa guda biyar, turaren kaya na maza da mata. Khumra masu tsayawa a rai da kuma turaren wuta.
Za ku iya samunta a manhajar instagram @saffademporium ko wannan layin 07010137848. Sayen nagari...mayar da ƙamshi gida!
~~~~~~~~
Kun kira Kun turo saƙo Kun zo dubiya har asibiti Ni kuwa me zan ce da masoyan SonSo idan ba kyakkyawar addu'a da fatan alkhairi ba?
A yayinda da nake post babu abin da yake yi min daɗi sama da kyawawan addu'o'in biyan buƙata da ku ke yi min. Wannan addu'ar ita ce babban abin dake ƙarfafa min gwiwar typing ko da jikina baya min daɗi domin bawa bai san alkhairin bakin mutane ba. A yau ina mai ƙara godiya ga Allah da ku bakiɗaya. Na sauka lafiya na kuma sami lafiyar jiki bayan aikin da aka yi min. Ahmad Amir dani da duka ahalinmu muna godiya da karamcinku.
Nayi kewarku da sharhinku mai sanya ni nishaɗi. In sha Allah zan cigaba da posting sai dai ba zai zama kullum ba. Sai kun ƙara haƙuri saboda yanayi ya ƙara canjawa. Ga ƙaramin goyo, yara, ɗawainiyar gida da aiki. Duk da haka kada ku sare da tunanin jira zai dinga tsaho. In Allah Ya yarda labarin zai cigaba cikin amincin Allah.
SonSo
***
Idan kaga yadda ake shiga gidan Alh. Hayatu sai mutum ya rantse gayyar mutane ce masu zuwa biki. Nan kuwa kaf ɗinsu ahalin gidan ne. Babu bare ko ɗaya sai masu aiki. Ƴaƴansa ne da jikoki. Kuma a haka wasu ba a nan za su kwana ba. Falon kamar ba zai ɗaukesu ba saboda yawa. Da yake an gama gajiya, rabon wajen kwana kawai aka tsaya yi.
"Duk wanda ya san ya fita ya bar kaya a falo ko cikin ɗakuna tun wuri aje a kwashe. Ba za ku dame mu da cigiya ba gobe." Cewar Ummukulsum ga jikokin. Ita ce babbar ƴar Yaya Hajiyayye kuma jika ta farko a gidan ta girmi Firdaus ƴar ajin su Hamdi.
"Ni dai ban ga kayana da na ajiye a nan ba..."
Cigiyar da take gudu tunda ta san komai wajenta ƙannen za su zo nema mazansu da matansu aka fara yi daga rufe bakinta. Kula su ka yi falon a gyare yake. Aka tambayi masu aiki kowacce ta ce ba ita tayi ba kafin su tafi. Abin da mamaki dai.
"To ko dai Alhaji ne? Naga motarsa..."
Hamɓare bakin mai maganar Yaya Samira tayi kafin ta kai ƙarshe.
"Baban namu ne zai yi muku gyaran falo don rainin wayo?"
"Gani Mugenbo shugaban marasa kirkin duniya ko?"
Muryarsa su ka ji kafin su gan shi yana fitowa daga ƙofar ɓangarensa dake cikin falon. A gurguje masu ƙuruciyar ciki su ka yi kansa saboda sabon da su ka yi dashi. Ƴan matasan kuwa su ka shiga sunne kai.