Kenza eBookz

Rayuwa da gibi na batul mamman - Chapter 49

Rayuwa da gibi na batul mamman - Chapter 49

Rayuwa da gibi na batul mamman Chapter 49: Rayuwa da gibi na batul mamman Chapter 49. "Kada ki ɗora komai yanzu sai iya wanda za ku ci. Shi ma ɗin kaɗan.…

3,368 words

"Kada ki ɗora komai yanzu sai iya wanda za ku ci. Shi ma ɗin kaɗan. Zan ɗan fita unguwa na dawo."

Yanayinsa ya bawa Zee tsoro. Ta kalle shi a tsanake. "Abba baka da lafiya ne?"

"Me ki ka gani?" Ya ƙirƙiro murmushi.

"Wallahi duk kayi wani iri." Ta faɗi da sanyin jiki. A zuciyarta kuwa tunani take ba zai wuce kewar Yaya yake yi ba.

"Bacci ne bai isheni ba. Matata ta tafi ta barni."

Zee ƙumshe baki tayi tana dariyar shaƙiyanci. Da haka Abba Habibu ya samu ya fita ba tare da ta tsananta bincike ba.

*

Anti Zinatu da sauran yan uwan Abba Habibu sun shiga mummunan tashin hankali bayan ya gama faɗa musu halin da ake ciki. A gidan Anti Zinatun suka haɗu domin ya kikkira su kafin ya iso gidan. Cikin sa'a kuma duka babu mai uzurin da ya hana shi fitowa akan lokaci.

"Wai ba da dangin mijin Labiba ta tafi ba? Ya aka yi cikinsu babu wanda ya bi bayanta?"

Wadda tayi tambayar tana rufe baki Abdulƙadir ya yi musu alama da hannayensa akan yana so su saurare shi. Sai da yaga sun dawo da hankali gareshi ya dubi Abba Habibu cikin yanayi na jin nauyi.

"Gaskiya ina tsammanin abin da nake ji yana faruwa a Iyafot ɗin ƙasa mai Tsarki fa gaske ne."

"Me kaji?" Suka haɗa baki wajen tambayarsa.

Sai da ya ɗan jajantawa kansa girman maganar kafin ya fitar da ita. "Yaya Habibu kayi haƙuri da furucina amma magana ta gaskiya ita ce yanzu an tsananta kame da binciken masu nakasa."

Da sauri Abba Habibu ya canja zama "me? Me ka ke nufi?"

"Naga ya faru a unguwarmu. A'ilo Gurguwa ko ƙasar bata shiga ba aka aunota gida. Kuma kusan kowa ya sani cewa bara ta tafi yi."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Ya Salam. Subhanallahi..." Abba Habibu yake ta faɗi shi kaɗai. Sauran ƴan uwansu kuwa sai sallallami.

Abdulƙadir ya dubi Abba Habibu "bani da tabbas amma ina zargin haka ɗin ne. Idan ba haka ba me zai sa a kama ta?"

"Ni fa ban ce an kama ta ba" Abba Habibu yaci gyaransa da wuri "iyalin Yaya Hayatu sun san halin da take ciki. Faɗa ne ba za su yi ba a waya."

"Ba da nufin tozarci nake yi maka zancen nan ba. Na faɗi abin da na sani ne saboda ka tafi da shirinka wajen kareta."

"Maganganunka tsorata ni suke yi Abdulƙadir. A bar zancen nan kawai."

Anti Zinatu tana zubar hawaye ta ce "Habibu ko mun ƙi ko mun so fa da ƙamshin gaskiya cikin zancen nan. Kamar yadda yace ne ka tafi da shiri a zuciyarka kada gaskiya ta baka mamaki. Zuciyata sam bata son wannan tunanin to amma shi kaɗai ne muke iya hasashe."

Abba Habibu gani yayi bashi da wata hanyar kashe maganar. Sun riga sun ƙarfafa zarginsu. Shi kuwa tunanin kaɗai ma ya ishe shi fargaba. A Saudiyya, Sijin (prison) suke kai kusan duk mai laifi irin wannan su ajiye. Idan na korowa gida ne daga can ake kai su airport. Masu hukuncin kisa....inaaa. Zumbur ya miƙe ya zura takalmansa.

"Bari na ƙarasa gidan na sanar dasu su shirya su taho. Wannan magana kuma don Allah ayi shiru sai naje na ganewa idanuna."

Zaman bai ƙara masa komai ba sai tashin hankali. Ya yi imanin basu faɗi komai domin cusguna masa ba. Iya gaskiyar da suke iya hangowa ce aka faɗa masa.

A hanya yayi ta tufka da warwara akan abin da zai faɗawa su Zee. Da fari tunanin ya ce musu Inna Luba ce babu lafiya. Da sauri ya girgiza kai da ya hango saurin gano shi da za ayi. Idan basu bishi ba tabbas zasu kirata a waya domin jin yanayin jikin nata. Daga nan ita kuma nata hankalin ya tashi. Ƙarshe dai gaskiyar da yake gudu dole ya faɗeta domin duk inda yace musu zai tafi dole za su kira waya.

*

Abba Habibu ya kasa hakuri ganin ya gama bayani amma Halifa da Zee ko motsi basu yi ba. Zuciyarsa tana cike da fargabar kada su matsanta masa da tambaya akan kwaskwarimar da ya yiwa zancen. Nuna musu yayi cewa Alh. Hayatu da kansa ya kira shi yace bai dace Yaya ta tafi ita kadai ba. Shine yasa aka yi masa komai cikin gaggawa don ya tafi da wuri.

Kamar ba za su yi magana ba sai kuma Zee ta fashe da kuka. Tana jan hanci tana magana.

"Wallahi Abba tun zancen tafiyar tunanin da nake ta yi kenan nima. Kasan ko taimako take nema ba lallai ta sanar da abokan tafiyarta ba. Gashi Allah Ya kawo mata sauƙi da wurwuri."

Murmushi Abba Habibu yayi da jin zancenta.

"Hamdala ya kamata kiyi ba kuka ba."

Halifa kuwa cewa yayi "To yanzu dai gidan wa zamu je mu zauna don wallahi tsoron gidan nan zan ji idan mu biyu ne kacal"

Zee ta ce "Abba mu tafi gidan Anti Zinatu ko?"

Da tsokana Halifa ya ce "Malaminmu dai ya ce mata masu aure su dinga yin komai da izinin miji."

A fusace Zee ta tashi. Halifa ya fita da gudu ta bishi. Abba Habibu kuwa ya jinjina taimakon Allah mara yankewa. Ya gama tayar da hankalinsa sai gashi cikin sauki ya sami mafita.

*

Da ɗokin tafiyar nan Hamdi ta wuni jiya. Amma zuwa dare gabaɗaya jikinta ya mutu. Zee da Sajida da su ka yi waya ma babu ƴar zolayar nan da suke yi mata na ba saban ba za ta shiga jirgi. Hirar tafiyar Abban nasu ma sama-sama ta saka musu baki. Halifa kuwa dama list ya ce zai tura mata kamar yadda ya bawa Yaya. Harda cewa kada ta damu tunda Abba zai tafi zai rage wasu kayan.

Yanayinta ya dami Taj sosai amma kuma bashi da kuzarin yawaita magana. Ya rasa mene ne yake ci masa rai ya hana shi walwala. Haka su ka kwana a gidan kowa da abin da yake kai komo a ƙirjinsa. Da safe su ka haɗu ƙarfe tara a harabar gidan Alh. Hayatu. Wata luxury bus ɗin gidan mai ɗaukan mutum talatin suka shiga direba ya kai su airport. Jirgin Abba Habibu sai uku. Su zasu shiga Qatar Airways, shi kuma zai shiga Ethiopia.

* Saɓanin abin da ƴan uwan Taj suka yi zato na cewa zai dage sai Hamdi ta zauna kusa dashi kamar yadda tsarin boarding pass ɗinsu ya nuna, sai suka ga akasi. Daga zolaya a ka ce ta zauna seat ɗaya da ƙannensa sai suka ga ta tafi ko a jikinta. Zama tayi ta rufe idanunta tun kafin jirgin ya fara motsi. Taj kuma bai yi cigiyarta ba. Da Yaya Hajiyayye ta kula ne ta zo da kanta ta kamo hannunta.

"Ina yi miki kallon wayayyiya za ki wani bari ƴan uwan miji su shigar miki hanci? Zaman me zaki yi a cikinsu bayan ga mijinki?"

"Nan ɗin ma duk ɗaya ne." Hamdi ta amsa da sanyin murya.

"Duk biyu dai." Cewar Yaya Hajiyayye. Ta kaita inda Taj yake. Ƙanwarsu dake zaune a wajen ta harara ba shiri ta tashi tana dariya.

"Mu fa rigima muka so haɗawa. Muce sai ya biya zata dawo nan. Amma sun manna mana hauka ko magana babu wanda yayi." Ta faɗi tana dariya.

"Sun san me suka taka ne. Gashi nan babbar yaya ta shigar musu. To mu dai duk da haka sai an biya mu. Abaya za ka saya mana dukkanin mu."

Sai a lokacin Taj ya magantu bayan Hamdi ta zauna. "Dama ku biyun nan akan ku Alhaji ya fitar da zakka. Ƴan 419 kawai. Yahoo girls."

Ai kuwa me zasu yi banda dariya. Har Hamdi sai da tayi. Da aka yi sanarwar kowa ya zauna Taj ya saka mata seat belt sannan ya kama hannunta ya sarƙe da nasa. A lokacin taji komai ya kwance mata. Raunin zuciyarta ya ninku sosai. Ƙwalla ta taru ta cika idanun fal.

"Happy" ta kira Taj da murya a shaƙe.

Ya gyara zama "Uhmm."

"Me yasa na daina ɗokin tafiyar nan?" Bata jira yayi magana ba ta fashe da kuka mai tsuma zuciya.

"Shhhh. Please...." ya ɗago haɓarta.

Abin da ya gani bai yi masa daɗi ba. She looked so confused. Ya buɗe hannuwansa ya yi mata kyakkyawar runguma. Tayi kukan mai isarta amma bata ji sauƙi ba. Suna wannan yanayin har jirgin ya gama taxi ya tashi. Riƙon da tayi masa ne kawai ya ƙara ƙarfi amma bata yarda da ɗago kanta ba. Jim kaɗan bayan jirgin ya daidaita a iska Taj yaji riƙon yayi sako-sako. Ya ɗan girgizata bata motsa ba, sai ma kwanciya da ta gyara a jikinsa tana bacci.

Ayatul Kursiyyu da Amanar Rasul ya karanta ya tofa mata sannan ya ranƙwafa ya kwantar mata da kujerarta. Baccin mai nauyi ne ya kama ta. Yaji daɗi domin jiya shi da ita marathon ɗin juye juye kawai suka dinga yi. Ba ita ta farka ba sai da ya rage bai fi minti talatin su sauka a Doha ba. Za su yi transit na awa biyu sannan su kama hanyar Saudiyya.

Kowa watsewa yayi an tafi window shopping. Masu ra'ayi kuma idan sun ga abin da suke sha'awa za su saya. Hamdi da Taj kaɗai aka bari. Suna zaune gadin kaya sannan ba hira suke yi ba.

Yaya Hajiyayye tana ankare dasu. Bata jima ba ta dawo ta sanya su a gaba.

"Wai har kun fara faɗa ne daga aure?"

"Tuf, tuf, tufff" Taj ya kama tofi da baki.

Kama ƙugu tayi ta harare shi "Ni kake tofewa Tajo?"

"Kece ana zaman lafiya zaki kawo abin da babu."

"Ai naga sai wani basarwa kuke yi. Ko laulayi kika fara ne Hamdiyya?"

Yadda ta sako maganar kai tsaye sai da Hamdi ta zabura ta hau rantse-rantsen ita bata da komai.

Shi kuma Taj sai cewa yayi "ki ka sani ko akwai?"

Wata uwar harara Hamdi ta watsa masa ba shiri. "Ni wallahi ƙalau nake."

Yaya Hajiyayye ta kallesu tayi dariya. Kunya duk ta kama Hamdi. Taj ya tashi yace ta taso su zaga su ma.

"Indai da matsala Hamdi ki faɗa min. Ko baki yi karatu da Firdaus ba kinsan dai na haifeki. Taj ɗin ma..."

Da sauri Taj ya katse Yaya Hajiyayye kafin ta gama bayar dashi a gaban matarsa. "Haba, haba Yaya Hajiyayye. A lissafin waɗanda kika haifa ai kinsan dai babu ni. Sai da na zama mutum fa aka yi miki aure."

"Wai ka zama mutum. Taj kaji tsoron Allah. Lokacin da kuke zuwa gidana fa ko tsar..."

Da wani irin sauri Taj ya tashi yana dan dukan laɓɓansa a gabanta don tayi shiru. Tuni ta gano ashe ta ɗauko hanyar bada maza. Ita da Hamdi suka ƙyalƙyale da dariya.

Ya harari Hamdi "Ke kuma meye abin dariya?"

"Ba dariya nake ba ciwon kumatu ne ya kamani." Ta bashi amsa tana gimtse wata dariyar.

A haka Yaya Hajiyayye tayi amfani da hikimar manya ta mantar dasu damuwarsu. Su ka rankaya da ita wajen ƴan uwansu ana ta raha har lokacin boarding ɗinsu yayi.

A gefe guda ta tsaya tana kallon ƙannenta lokacin da suke ta hayaniya ta saki murmushin da ya tsaya a fatar bakinta kaɗai. Jikinta a mace yake da nauyin tunani kala-kala. Zuwa yanzu ta riga ta tabbatar ko me zasu tarar idan sun haɗu da ƴan uwansu ba mai daɗi bane. Fatanta kawai Allah Yasa yazo da sauƙi.

***

JEDDAH

A cikin ƴaƴan Alh. Hayatu ashirin da takwas, mutum biyar ne basu sami damar zuwa Umrar da aka fake musu da ita ba. Daga mai haihuwa ko yau ko gobe sai uku a ƙasashen ƙetare, ɗayar kuma an saka mata ranar defence na Masters a Sokoto.

Da suka sauka daga jirgi sun yi zaton Umra zasu fara yi. Dama Abba ya yiwa Taj kwatancen inda zasu same shi idan sun fito. Basu wahala ba kuwa suka hango shi a jikin wata farar bus mai girma. Direbanta yana ciki a zaune. Da murnarsu suka nufi motar sai dai Abba sam babu wani kuzarin kirki a tare dashi sai yaƙe.

Tambayar da Taj ya fara yi masa da ya miƙa masa hannu ita ce

"Ina Happiness?"

"Suna hotel. Motar zata yi kaɗan idan dukkanmu muka taho."

"Ka san kuwa ni bana ƙaunar takura."

Kowa ya yiwa kanwarsu da tayi maganar dariya saboda ƙibarta sannan suka fara tafiya.

Taj da Hamdi wuri ɗaya suka zauna. Tana jikin taga shi kuma yana gefenta. Duk motsinsa tana karanta yadda walwalarsa ta sake ɗaukewa.

"Kamar kana cikin damuwa."

Ɗan guntun tsaki ya fara yi na frustration. "Kin san irin abin nan da mutum yake gane akwai matsala amma ya kasa pin pointing ɗinta?"

Hamdi ta gyaɗa kai.

"To haka nake ji."

"In sha Allahu ma babu komai."

Suka sarƙe hannuwansu waje guda har zuwa lokacin da motar ta fara slow. Nan fa hankalin kowa yayi mugun tashi. Sunan asibiti suke gani ɓaro-ɓaro. Daga jerin kujerun baya mafi kusa da direba Yaya Hajiyayye ta zura hannu ta kaiwa Abba duka a kafaɗa. Jikinta yana wata irin rawa.

"Abba waye a asibiti? WAYE?" Da muryar kuka ta ƙara da cewa "Dama jikina ya bani wallahi"

"Yaya ki bari mu shiga don Allah." Abba ya bata amsa da sanyin jiki.

Motar kuwa ta ruɗe da hayaniyar fargabar ƴan uwan. Direban na tsayawa suka dinga fita da sauri. Taj ne kaɗai bai fita ba kuma ya hana Hamdi tashi sai da kowa ya fita.

"Ka tashi mu fita don Allah." Ita kanta a gigice take.

"Happiness ne fa bashi da lafiya. Ina jin ma babu shi gabaɗaya."

Tafin hannu Hamdi tasa ta rufe masa baki. Sai ga hawaye ya sauko daga idanunsa. Hamdi ta rungume shi ita ma ta soma nata kukan. Tayar da ita yayi suka fita gaba na faɗuwa. Suna sauka daga motar suka ga Ahmad da Mubina.

"Hamdi ban so maganata ta tabbata ba. Kinga Dr. Mubina" ya nuno mata su "dalilin Kamal ta zo na tabbata."

Jikinta ya sake yin sanyi ƙalau har suka isa inda suke. Ahmad ya ɗan bugawa Taj kafaɗa. Mubina kuma ta rungumo Hamdi jikinta suka shiga lift kamar tana so ta rarrasheta. Mamakin hakan ya kama Hamdi. Ba wai bata damu da Kamal ba, amma a ganinta akwai waɗanda suka fita buƙatar rarrashi akan sa ko me ya same shi.

Tamkar wanda bashi da laka Taj ya dinga tafiya da ƙofar lift ɗin ta buɗe. Suna yin kwanar farko ya hango zugar gidansu harda iyayen a corridor ana ta koke-koke. Taj ya kalli sama inda aka rubuta 'Room 7' sai yaji hankalinsa ya sake tashi. Wani zafi ya mamaye jikinsa. Bai san yadda aka yi ya isa gaban Alh. Hayatu ya tsaya ba.

"Alhaji me ya same shi?"

"Kidney transplant aka yi masa." Ya bashi amsa amma hankalinsa yana kan Hamdi. Wani irin nauyinta yake ji.

Taj yayi gaba da sauri zai shiga ɗakin idanunsa sun yi wani irin ja mara misali. Bishir ya riƙe shi da ƙarfi ya janye shi daga wajen. Umarnin likitocin Kamal ne suka ce kada a shiga ɗakin duk da ya farfaɗo. Yana buƙatar hutu sosai. Ita Hamdi bata kula da abin da ya faru ba. Hankalinta yana kan su Inna. Ta rasa me zata yi saboda kowa hankalinsa a tashe yake. Kawai sai ta duƙa da nufin gaishesu. Umma tayi saurin tareta a jikinta.

"Tashi Hamdi. Zo mu ƙarasa can ki zauna."

Ta girgiza kai. "A'a zan zauna a nan nima."

Ga mamakinta da na sauran Alhaji da kansa yace ta bi Umma.

"Ku je Hamdi."

Bata da zaɓi sama da bin Umman. Kallo duka sai ya dawo kanta. Haka ta bisu cike da tsarguwa. Me yasa za a ce ita kaɗai ta tafi? Ko sirri zasu yi? Ko dai Kamal ɗin ya...

"Hamdiyya"

Muryar Hajiya ce ta fito da yanayi mai ban tausayi. Hamdi ta juya ta ganta a tsaye. Hajiyan ta da ta sani da wannan dake gabanta da bambanci. Ramar da alamun rashin kwanciyar hankali sun yi yawa sosai.

"Hajiya yaya mai jikin?"

Hannuwanta Hajiya ta kama ta rufe da nata yatsun. Hamdi ta ɗaga kai taga Inna, Mama da Umma duka suna kallonta da wani irin yanayi na tausayi. Idanuwansu sun nuna alamun an sha kuka. A take jikinta ya soma rawa. A take taji gwiwoyinta sun saki ba za su iya ɗaukar nauyinta ba. Bata san jikinta ƙasa yake yi yana neman wajen zubewa ba sai da Hajiya ta rungumeta a jikinta.

Da kuka Hajiya tayi mata magana suna wannan yanayin. "Hamdiyya na rasa me zan fara ce miki. Godiya zanyi ko haƙuri zan baki?"

"Hajiya ku faɗa min abin da yake faruwa. Wallahi ji nake kamar zuciyata za ta buga don fargaba."

Jin haka sai Hajiya ta ja hannunta har gaban Inna ta haɗa hannuwansu.

"Kai ta."

Gaba na matsananciyar faɗuwa Inna ta riƙe Hamdi har ICU ɗin mata. Ta jikin gilas ɗin ƙofa Inna ta nuna mata gadon da Yaya take kwance.

"Wwwwaaaa..yyyyeee?"

Ta matse hannuwan Inna ba tare da ta sani ba tana kuka. Jikinta kuwa tamkar mazari yana ta rawa.

"Rage sautin muryarki kada ace mu bar wajen."

"Na rage. Nayi shiru...."

Hamdi ta soma faɗi sai ta kasa ƙarasawa. Wani abu ta lura dashi daga yanayin kwanciyar mara lafiyan duk da bata ganin fuskar. Ta saki hannun Inna ta sanya duka hannuwanta ta dafa gilas ɗin ta sake kara fuskarta da kyau. Realization hit her kamar an jefeta da dutse.

"Yaya?" Ta juya da sauri "Inna, Yaya ce a kwance?" Sai hawaye kamar famfo.

Inna ta gyaɗa kai, itama wani sabon hawayen yana zubo mata.

Kokawa Hamdi ta fara yi da ƙofar ɗakin sai dai ko gezau taƙi motsi. Inna tayi saurin riƙe mata hannuwa tana turjewa.

"Yaya ce Inna. Ku barni na shiga."

"Ba za su bari ba Hamdi. Zo mu je nayi miki bayani."

Hamdi taƙi tashi sai kuka kawai da take yi tana roƙonsu da su faɗa mata gaskiyar halin da Yaya take ciki. Mubina ce ta tafi da niyyar kiran Taj suka haɗu a hanya. Muryar Hamdi ya jiyo shi ne ya taho da sauri.

"Me ya same ta? Me aka yi mata take wannan kukan?"

Mubina ta haɗiyi yawu. Ganin bata da niyyar faɗa masa sai ya ƙara sauri ya zagaya ta inda suke.

Inna na ganinsa ta fara cewa "Taj kama min ita mu bar wurin nan kafin..."

Riƙe hannunta yayi zai janyeta duk da cewa hankalinsa yayi masifar tashi sai yaji ta turje. Maimakon ta bishi sai ta janyo shi jikin ƙofar ta nuna masa Yaya ta gilas ɗin da ake hangota. Da sanyin murya mai tsinka zuciya Hamdi tayi masa magana.

"Yaya ce. ICU aka rubuta kuma Yaya tana ciki. Ji nake duniyar ta tsaya min. Ka taimakeni..." ta juya tana kallon su Inna "ku taimaka min. Ku taimaka mata."

Ta sulale a ƙasa a hankali tana ajiyar zuciya. Kukan ma ya ɗauke mata. Taj kasa taɓata yayi saboda maganganunta tamkar almara yaji su. A kiɗime ya koma jikin gilas ɗin ya sake kallon wadda take kwance. Ya dawo ya riƙo hannayen Inna jikinsa yana tsuma

"Inna da gaske Yaya ce?"

Hannunsa da na Hamdi ta kama ta nufi hanyar lift. Su biyun a take suka nuna ba zasu fita ba.

"Zaman ku babu abin da zai ƙara musu. Addu'a suke buƙata. Ku zo muje mu samu wuri nayi muku bayani."

Tana rufe bakinta Mal. Salisu mai shara ya iso wajen. Idanuwansa akan Hamdi suka tsaya. Inna ta lura da haka. Sai ta ce,

"Ƴarta ce."

Mal. Salisu ya jinjina kai "wannan ne mijin nata ɗan uwan Kamal?"

Inna ta gyaɗa kai.

"To ku zo muje. Alhaji yayi magana da Dr. Hadifi ya sama muku inda zaku keɓe ku yi magana."

A baya su ka bi Mal. Salisu har zuwa bakin wata ƙofa ta wani ƙaramin ɗakin taro. A nan suka tarar da Alhaji, su Hajiya da Yaya Hajiyayye, Yaya Kubra da Dr. Mubina. Hamdi bata san da yaya ta ƙarasa shiga ciki ba. Ta dai ganta zaune a kusa da kujerar Alhaji. Kwantar da kai da murya yayi sosai babu isa da ɗagawa wajen yi mata bayani.

"Dashen ƙoda aka yiwa Kamal. Ciwo yayi masa tsanani..."

Hamdi bata tuna da wata surukuta ba ta katse masa hanzari a firgice tana kallonsa da dara-daran idanunta. "Ta Yaya aka dasa masa?"

"Ki yi haƙuri Hamdi." Mama ta ce cikin kuka.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull