Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 13
Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 13: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 13. Suna ta dariyar ƙeta inda Umma ta ce wallahi sai ta…
3,344 words
Suna ta dariyar ƙeta inda Umma ta ce wallahi sai ta ga ƙwal uwar daka don sai ta ga baron ma, haka aka riƙe mata ta ɗane katakon har ɗaya ƙawarta tana faɗin da kin yi haƙuri har gida za a shigo da su. Tana hawa ta yi ido huɗu da baro lokacin mai baron yana sakko da akwatunan, dariya har da hawaye garin dariya kaɗan ta faɗo daga saman bencin haka ta diro har tana cewa su Aliya suke sassauta murya kar Abbansu ya san suna gidan tun da kamar rashin kunya ne a kawo maka kaya kana gida.
Su Umma a ɗakin suka bar su Aliya suka fito waje suka zauna suna ƙusƙus ransu fari ƙal suna fatan ba abin arziƙi ba ne a akwati biyun don a ganinsu lefen ma kamar na bazawara. Su Umma suna fita su Aliya suka koma saman bencin suka kasa suka tsare a windwon kamar a mafarki kyawawan motocin suka yi wa layin tsincke kowacce tana fitar da ƙyalli na sabunta, a jere suke iya ganinka dole su birgeka daga Amatullahi har Aliya mutuwar tsaye suka yi baki sake domin motocin su tafi da su, sai dai abin da ya sa suka shiga ruɗu shi ne motocin basu tsaya a ko ina ba sai a ƙofar gidan su Aliya, kallon kallo aka shiga yi tsakanin Aliya da ƙawarta, bakin Aliya kamar ƙofar gari ya ƙi rufuwa sam saboda mamaki tana tunani a ranta cewa dama Kasim har yana da abokan da suke da motoci na alfarma haka, amma bata taɓa ganin sun zo da su wajenta ba ko dai abokan nasa ne suka masa hanya ya samo wannan motocin irin wanda take mafarkin samu, ko da sau ɗaya ne tak ta shiga ciki ta yawata, amma kash! Bata da wannan damar, basu tsinke da lamarin ba sai da suka fara ganin mutanen ciki suna fitowa suka ga gabaɗaya babu kalar talauci a cikinsu sai kuma direbobin da suka fito suna buɗe ƙofofin motocin inda guda ɗaya direba ya saka hannu ya fito da wata ɗirkekiyar akwati wacce kai kana gani ka san an kashe maƙudan kuɗi wajen sayan akwatin kaɗai, jikin Aliya karkarwa ya fara saboda farinciki jin ta take tana yawo a cikin gajimare.
Yadda ake ta fito da akwatin nan kala-kala ne ya sa ta tabbatar cewa ba iya goshi ta yi ba har da ƙeya!. Da sauri ta diro daga saman bencin ta tsaya a tsakar ɗakin hannunta yana karkarwa ta dokawa Kasim waya, Kasim wansa yake kwance lifet a katifa yana jiran kiran ko ta kwana daga Aliya jin ƙaran wayarsa gabansa ya ninku da faɗuwa amma haka ya daure ganin sunanta ya ɗauki wayar ya danna ya kara a kunne kamar daga sama ya ji muryarta rana faɗin
"Na gode Kasim, na gode!. Na gode, wallahi na matuƙae gode ina sonka Kasim zan rayu da kai har ƙarshen rayuwata!" Bata jira ya ce komai ba ta kashe wayar don bata cikin nutsuwar da za ta tsaya ta ji mai zai ce. Lokacin da take wayar nan Amatullahi ta diro daga saman bencin ta yi tsakar gida tana faɗin
"Umma wallahi a motoci haɗaɗɗu aka kawo kayan Aliya, kuma akwatunan ni kaina ban iya irga yawansu ba, kamar ma va set ɗaya ba kuma ba biyu ba ni ban ma san nawa ba ne kuma ma su tsada!" Wata wawiyar guɗa Umma ta saki sai da ta yi uku a jere ƙawayenta suna taya ta, inda Aliya da Amatallahi suka haɗu da su Umma aka rungume juna!. Bayan an gama murna su Aliya suka koma ɗaki.
Jim kaɗan wasu samari guda biyu suka shigo ɗaya yana riƙe da akwati ɗaya, ɗayan kuma akwati da kit ɗin nan su ne kayan da aka kawo a baro. Bakin Umma a washe ta nuna musu kan ƙaramar tabarma da take shimfiɗe a gefe ta ce su ajiye, suna ajiyewa har rige-rigen tsegumin mene ne a ciki suke.
Suna fita aka fara shigo da akwatuna masu kyau wannan karon samarin guda huɗu ne suke shigowa da akwatunan, Umma garin saurin ɗakko manyan tabarmi har zaninta neman faɗuwa yakr duk sun ruɗe don Aliya da take windown da yake tsakar gidan suna leƙowa daga falon Umma har ta fara tunanin ko dai dama Kasim mai kuɗi ne ya rufe ta amma daga ganin kayan abin ya fi gaban wasa an kashe naira.
Dozin biyu haka aka jere a gefe Aliya ko zama ta kasa yi da mazaunanta hango irin iyayin da za ta ɗiga take a wajen ƙawayenta. Wayar Jidda ta kira da Jiida ta ɗauka ta ce
"Jidda an kawo akwatunan ki guda biyu da ƙaramin kit" Buɗar bakin Jidda sai ta ce
"Ubangiji ya sa albarka a auren" Wani uban tsaki Aliya ta ja kafin ta kashe wayar tana kiran Jidda da ƴar wahala!.
Atamafa kala takwas leshi kala biyar shadda uku material uku, takalmi da jaka kala biyu sai takalmi marar jaka kala biyar mayafai buyar hijabi huɗu, sai sauran tarkacen kayan shafawa da sarƙoƙi ƙaramar kit kuwa qur'ani ne da sallaya. Su ne kayan da suke cikin akwatunan biyu kayan bacci ma huɗu ne da kuma under wears.
Akwatunan kuwa na leshi da ban akwatin atamfofi da ban kaya ne iya ganinka kamar hauka, hatta sarƙar gwal ma kala uku ce a ciki tun su Umma suna ganin kayan da marmari har suka gaji da ɗagawa kawai faɗi suke shikenan Aliya da Umma sunw arke. Aliya kamar wanda taɓi ya same ta gami take za a taɓa ta a ce ta tashi daga nannauyan baccin da take, a nata ganin kawai mafarki ne take yi.
Baba kuwa daga zauren gaba suka yi saboda bayan masu kawo kayannsun tafi sai mata suka fara tururuwar zuwa daga maƙota, Umma ta maƙale gwal a cinyarta sai dai a gani a bata don mutane da suka cika gidan wasu ko akwatunan nan masu biyu da kit wato na Aliya wanda suke a mazaunin na Jidda babu wanda yakr ɗagawa kowa kayan akwatunan nan yake gani wanda suka san iyayen Kasim suna mamakin inda Kasim ya tara wannan dukiyar da ya yi wanna kayan kamar an buɗe shago!.
Ibrahim ya kasa tsaye ya kasa zaune jira yake ya ji ta bakin Jidda kar ta janye ƙudurin aurensa idan ta san waye shi, hakan ya sa bini-bini sai ya buga mata waya amma sai ya ji bata ce masa komai ba, sai dai ta ce masa har yanzu tana gidan su Salama.
Sai da aka yi isha'i Abba ya shigo gidan, lokacin Aliya har ta gaji da gwada tsadaddun abayoyin Jidda na lefe wanda take tunanin nata ne, takalmi da jaka ma har rasa wanne za ta gwada ta yi ga sarƙoƙi fassion abin kawai ba a magana komai ya yi. Jin motsin zuwan Abba hakan ya sa ta gudu ɗaki don dama Amatallahi tuni ta tafi gida tana faɗin sai ta dawo ganin kaya na biyu don ta fi so sai ta zo ta musu ɗai-ɗai za ta gani.
Lokacin da Baba ya zo gabaɗaya an ajiye akwatunan a waje ɗaya sai sheƙi suke, ga guda biyu da kit su ma a gefe don ba a ma haɗa su waje guda ba. Bayan ya zauna ya ci abinci Umma tana ta masa surutu kamar za ta ari baki, sai faman faɗin Aliya ta sha kaya take ta yi sai kuma ta ce Jidda ma ba laifi tana yin hakan ne don kar Abba ya ce ta nuna bambanci tsakaninsu.
Tana ta faɗa masa abubuwan da suke ciki a daidai nan ne Jidda da Salama suka yi sallama suka shigo bayan an amsa. Abba suka gaisa da shi sai suka shige ɗaki, yau ko fuska Aliya bata tanke musu ba sai ma labarin uban kayan da aka zuba mata a lefe take basu akwatuna 24 Jidda sosai ta ji farincikin jin Aliya ta samu kaya masu yawa, suna cikin haka Umma ta dage ta ƙwalawa Salama kira Salamar da Umma ta tsani ma ta ga ta zo gidan amma yau saboda tana so ta mata kaju kuma ta tura mata haushi. Amsawa Salamar ta yi ta fito ta zo cike da ladabi ta ce
"Umma gani"
Umma ta ce
"Cewa na yi to kya shiga ɗaki ai sai ki zo ki ga kayan ƙawar taki da na ƴar uwarta idan kina ɗagawa ma har Abban naku ya gani shi ma yanzu ya shigo" Abba ya murmusa yana jin daɗin yadda Ummar bata nuna bambanci ba ya ga tana farinciki da abubuwan da kowa ya samu ashe dai ta yarda kowa rabonsa yakw samu, tunaninsa ko za ta ji ƙyashi ashe ma gurguwar fahimta ya mata da ya ƙi bayyana kuɗin da aka kawo.
Salama ta durƙusa a gaban akwatunan da Ibrahim ya yi Umma ta yi karaf ta ce
"Ke kuwa ai da kin fara da na ƙawar taki" Ta faɗa tana nunawa Salama akwatunan nan guda biyu wanda Kasim ya kawo har da cewa
"Ku ne iyayen zuwa islamiya gashi nan har qur'ani da sallaya ya saka a kit ɗin maimakon sarƙoƙi da ake sakawa" Cike da Mamaki Abba yake kallon akwatunan da Umma ta nuna sai lokacin ya tuna ashe fa bai cewa samarin nan su ce ga na Aliya ga na Jidda ba. Zaune ya tashi daga ringishen da yake ya yi gyaran murya ya ce
"Wancan akwatunan mai guda biyu su ne lefen Aliya fa" Aliya da take ɗaki a tsaye tana danna waya suna chart da Kasim bata san lokacin da ta saki wayarta ba, Jidda kuma jin furucin Abba gabanta ya buga da mugun ƙarfi tana tunanin to ta yaya hakan zai kasance bayan ta san Ibrahim talaka ne, sannan abin mamakin dai guda ɗaya maganar daga bakin Abba ta fito bare ta ce akwai gyara a ciki.
Umma wacce ta saki baki tana kallon Abba ta ce
"A'a fa Abban yara, wannan akwati guda biyu da kit su ne na Jidda waɗan nan guda 24 su ne na Aliya" Abba ya murmusa ya ce
"Tsakanin ni da ke waye ya fara karɓar kayan?" ,Hankalin ta ne ya fara tashi ta ce
"Kai kuwa mene ne na wasa?"
Hannu ya sa a aljihu ya ciro wani mukulli ya ajiye a gabansa ya ce
"Magabatan Kasim su suka fara zuwa da wancan akwatunan biyi da kit a baro, wannan akwatunan 24 su ne magabatan Ibrahim suka kawo a mota, dama miliyan goma suka kawo kuɗin gaisuwa da saka rana ni ne na ƙi karɓa dakyar na karɓi miliyan uku, to yau kuma kin ga lefen da suka kawo wannan mukullin motar ta ne haɗe suke a lefen motar ita ce a waje tana nan!" Jidda ƙarfen windown ta dafe idanunta suka fara hawaye a inda Aliya ta yanke jiki ta faɗi ji kake yaraf, Umma tsaye ta tashi a kiɗime tana zare idanu...
MAMAN AFRAH
09025576222
[10/20, 3:08 AM] Maman boy: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/E3Pn5QPLfOVGFdNgMR6ltU?mode=wwc
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)
NA
MAMAN AFRAH
. *Daga marubuciyar*
*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*
*09025576222*
BOOK 1
PAGE 🔟
*JIDDA*
Cikin sauri ta saki ƙarfen windown da ta riƙe ta yi kan Aliya da gudu tana kiran sunanta, Umma wacce ta tashi tsaye a kiɗimen jin lefen Jidda da miliyoyin da ta ji ya lissafa amma sai ta wayence tana sakin murmushin yaƙe, sai kuma ta yi ɗaki da sauri tana tambayar abin da ya faru duk da ta san musabbabin abun domin zancen gizo ba ya wuce na ƙoƙi ma'ana ta san cewa furucin Abba ne ya saka Aliya faɗuwa.
Salama ma wacce take son fahimtar inda abin ya dosa musamman ma da yake ta san abubuwan da suke faruwa a cikin gidan ita ma bin bayan Umma ta yi, a kusan tare suka ƙarasa da Abba da ya biyo bayanta yana tambaya. Jidda ce cikin kuka ta ce
"Ni ban san mene ne ba na ga ta saki wayarta da take dannawa, kuma sai ta yanke jiki ta faɗi" Abba ya ce
"Subhanallahi dama bata da lafiya ne?" Jidda ta ce
"Lafiya take Abba" Abun ya ɗaure masa kai, Umma kuma kuka ta fashe da shi tana mai ɗaga Aliyar, wanda kukan ya zame mata biyu ga na canjin lefwn bazatan da ya ziyarce ta ga kuma faɗuwar Aliya tana fatan dai abin ya tsaya iya faɗuwa kar wani ciwon ya samu Aliya, ta san a yadda zuciyar Aliya take da riƙe abu da kuma ƙyashin Jidda ta samu wani abu ta san da wuya idan wannan abin bai mata mummunar illah ba.
Jidda bil haƙƙi kuka take saboda ganin ƴar uwarta kuma ƙawarta a cikin wani hali domin ko numfashi bata yi ta sandare kamar wata gawa. Gabaɗaya Jidda ta ma manta da cewa an faɗi abin da ya gigita mata tunani na kaya da kuɗin da aka ce Ibrahim ya kawo mata, yanzu damuwar Aliya ce a zuciyarta tana son Aliya da soyayyar Aliya ta tashi sai dai daga baya da Aliyar ta sauya mata shi ne babu yadda za ta yi yanzu ma ji take tamkar ta cire duk wata damuwar Aliyar ta mayar kanta.
Abba ganin Umma tana kuka wiwi ya ce
"Haba Ummar yara yanzu mene ne abin kukan" Tana riƙe da kan Aliya a cinyarta ta ce
"Bata numfashi fa, ya hankalina ba zai tashi ba, ƴar ɗaya tallin tal kamar rai" Ta faɗa tana rushewa da wani kukan. Salama kuwa sai taɓe baki take don ta san zuciyar Umma da ta Aliya ko kaɗan bata da kyau.
Abba ganin sun rikita gidan da koke -koke sai yanzu ma tunanin yayfa mata ruwa ya zo masa, da sauri ya ce
"Salama maza ɗakki ruwa a kofi" Juyawa ta yi bayan ta amsa da to ta ɗakko ruwan da sauri ta kawo, Abba yana karɓa ya fara yayyafa mata amma Umma cikin kuka cewa take
"Ni dai a samo abin hawa mu tafi asibiti" Kafin ya samu zarafin bata amsar sai Aliya ta sauke wata zuciya inda Umma ta shiga rarraba ido tana kiran sunanta amma idanun Aliya a rufe, Jidda ma sunanta take kira inda Umma ta faki idanun Abba ta aikawa Jidda wata muguwae harara don ta san ita ce ummul aba,isin faruwar komai ji take kamar ta samu filo ta dannawa Jidda har sai ta daina numfashi!.
Abba ganin tanyi ajiyar zuciya kuma tana motsi ya ce
"Alhamdulillahi ta farfaɗo, ni ban san mene ne ya sanya ta yanke jiki ba" Ya faɗa yana riƙe da kofin Salama a zuciyarta ta ce
'Mene ne kuwa zai sa ta yanke jiki in ba baƙinciki kyashi da kuma hassada ba' A fili kuma ta ce
"Wataƙila ko dama bata da lafiya ne" Jidda kuwa har lokacin kallon Aliya take da tausayawa, Aliya wacce idanunta yake a rufe ta fara magana don har lokacin bata ma san insa take ba ta ce
"Wallahi akwatunan masu ashirin da huɗu haɗe da mota su ne lefena" Baki Abba ya buɗe da mamaki inda Salama a zuciyarta ta ce
"Humm! Ai dama zancen gizo ba ya wuce na ƙoƙi, sai dai ki yi gawa kuwa wallahi don akwati biyu da kit ne naki sai dai in baron da aka kawo kayan za a koma a karɓo ta zama motarki, am a mota ai sai Jidda'
Umma kuma gudun kar Abba ya fara zarginsu sai ta yi saurin kai hannu tana rufewa Aliya baki tana cewa
."Yi shiru Aliya, na san bakya cikin hayyacinki dama an ce idan mutum ya mutu yana tashi ne a ƙiyama da abin da ya mutu yana aikatawa, to ina ga suma ma idan mutum ya yi to yana farfaɗowa ne da ambaton abin da ya suma ana ambato wato lokacin da ta suma ana maganar akwatuna ne shi ya sa ta farfaɗo da maganar akwatin. Abba sai ya ji ya gamsu da maganar da Umma ta yi tana share hawaye, dama shi bai zargi komai ba tun da iya sanin sa bai san da wata maƙarƙashiya a ƙasa ba.
Umma kamo hannayen ta ta yi tana kiran sunanta idanu ta buɗe warai tana kallon kowa, a take ta fara zubar da ruwan hawaye daga idanunta wanda ba hawayen komai ba ne sai hassada da baƙin cikin abin da aka yi wa Jidda, a take ta ji ta tsani Kasim domin ya yi mata abin da ya tozarta ta ya zubar mata da kima, bayan tana ganin mutanen unguwa da ƴan uwa duk sun gama ganin kyawawan akwatuna da manyan lesuna a matsayin kayanta yanzu kuma a ce akwati biyu da kit mai sallaya shi ne nata kayan da gabaɗaya idan za a haɗa ba za su kai yawan kayan da suke cikin akwati ɗaya na kayan Jidda ba!.
Muryar Abba ce ta katse ta da ya ce
"Sannu Aliya mene ne yale damunki?" Aliya cike da kukan baƙinciki wanda take rerashi a zuci wanda ya fi na fili ciwo ta ce
"Abba ni ma ban sani ba, kawai dai na ji cikina ya murɗa mini sai kuma ban ƙara sanin inda nake ba, amma yanzu ba na jin komai" Abba ya ce
"Ah Alhamdulillahi to, bari na shiga na watsa ruwa" Ya faɗa yana juyawa ya fice. Yana fita Salama ta ce
"Sannu Aliya Allah baki lafiya" Banza Aliya ta mata don yanzu a halin da ake ciki duk wani abu da ya shafi Jidda ta tsane shi tsana ta har abada kuwa!.
Jidda tana share hawaye ta ce
"Sannu Aliya" Tamkar ta watsa mata ruwan dalma haka ta ji a kunnuwanta, bata taɓa jin tsanar Jidda da ƙyashin alkairin da ya same ta ba sai yau, wani baƙi ta ga ta ƙara yi gashi kanta ya kulle tana son yin nazarin cewa kenan dai Ibrahim ɗin nan matsayinsa na farko wanda ta fara ganinsa a matakin a ranar farkon da suka haɗu shi ne dai matsayinsa, kenan basaja da ɓadda kama ya yi ko mai yanzu take jin da na sanin wulaƙanta shi a ranar da ya zo unguwarsu ta watsa masa ƙasa a ido, da yanzu ita ce da duka waɗannan abubuwan da Jidda ta mallaka tana jin dama bata riƙe wulaƙanta mutane a matsayin wata turba ba, kenan dai wasu mutanen suna cikin rigar tsiya ne yayin da kuma su masu arziƙi ne, a zuciya ta furta
'Na tsane ki Jidda kin hau matsayin da nake so na taka!" A fili kuma sai ta mayar da idanunta ta rufe saboda ganin Jidda baƙanta mata rai yake ƙara yi. Salama kuwa juyawa ta yi ta koma kan tabarmar tsakar gida.
Umma tana hararar Jidda kamar idanunta za su faɗo ta ce
"Baƙar munafuka, wato mu za ku haɗu ku rufa ke da wannan soloɓiyon, ashe dai shi kura ne lulluɓe da fatar akuya, har mu za ku yi wa bazata ni za ki kunyatw a idon duniya Jidda? Ni za ki sincewa zani a kasuwa, in rufa miki asiri in riƙe ki tun kina ƙanƙanuwarki amma yau za ki kunyata ni a idanun jama'a kenan yanzu dole in ke cewa akwatuna ashirin da huɗu naki ne?" Gabaɗaya idanun Jidda ya cike da hawaye da sauri ta sunkuyar da kanta don bata son irin kallon ƙiyayyar da Umma take jifanta da shi. Bata samu bakin magana ba ita yanzu tunanin da take ma ta matsu ta yi waya da Ibrahim ta ji ya aka yi aka haihu a rageya.
Kiran da Salama ta ƙwala mata shi ya sa ta tashi ta fita daga ɗakin, da take jin ta tamkar a kan ƙaya. Fitowar Abba daga ɗakinsa bayan ya yi saka jallabiya shi ya dakatar da Umma da Aliya da suke kukan takaici marar sauti, ta hanyar kiran da ya ƙwalawa Umma. Sumi-sumi Umma ta fito daga ɗakin tana ta fatan Allah ya taimake ta kar kuka ya ƙwace mata ta fi so ta ci gaba da yaudarae Abba yadda ba zai taɓa gane ko ya fahimci mugun hali da mugun nufin da take da shi a kan Jidda ba.