Kenza eBookz

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 16

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 16

Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 16: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 16. Bayan ta gama gyaran gidan ta yi wa Kalifa wanka ita…

3,323 words

Bayan ta gama gyaran gidan ta yi wa Kalifa wanka ita ma ta yi, wanke wanke ta yi da wankin banɗaki ta gyara kicin tas. Ganin Kalifa ya yi bacci ta haɗa kayan wanki ta je ta wanke, duk abubuwan nan da take gabanta yana faɗuwa domin tana ta juya maganar Nasir a ranta a kan maganar ciki, ita kanta bata son ta samu ciki yanzu ba ma yanzu ba ita idan son samu ne Kalifa ya zama shi kaɗai ne wanda zai zama rabo tsakaninta da Nasir domin ta san gidan nan ba gidan dauwamarta ba ne, babu ma alamar zaman zai ɗore duk da ta san mutuwar aurenta tamkar rasa wani sashe na zaman lafiyarta ne a gidan mahaifinta amma dai tana zaman jiran tsammanin ta inda mafita za ta zo mata watarana!.

Tuno da tsinken pt na awon ciki wanda lokacin da take shayar da Kalifa Nasir ya zargi ciki ne da ita ya ringa mata rashin mutunci da hana rayuwarta sakat, shi ne da ya ga babu haza ya siyo pt ɗin ya ce ta gwada, tana dubawa babu ciki shi ne ya ringa jero hamdala kamar dai wani abu ne daban, sai ka ce ba shi ne mamallakin cikin ba, kamar dai ba shi ne yake lallaɓowa ya karɓi haƙƙinsa ba.

Kasancewar lokacin guda huɗu ne sai ta ajiye ukun yanzu ta ɗakko guda ɗaya domin ta gwada, sai ta ajiye masa idan ya zo ya ga layi ɗaya ne babu ciki sai ya sakar mata mara ta yi fitsari. Tana ɗakkowa ta je ta samu wani ɗan murfi ta shiga bayi ta yi fitsarin ta fito gabanta sai faɗuwa yake tana fargabar sakamakon.

Ko da ta zo ta ɓare pt ɗin ta tsoma a fitsarin ta ciro yayin da fitsarin yake tafiya a cikin pt ɗin domin fitar sakamako tare da matsananciyar faɗuwar gabanta yake tafiya. Lokacin da ya gama tafiya idanunta ra runtse da ƙarfi tana ta karanto addu'a a a zuciyarta a kan Allah ya sa ba ciki ne da ita ba, in ban da ma irin rayuwar da ta samu kanta a ciki a ce wai kana fargabar ganin kana ɗauke da ciki sai ka ce wani cikin shege!.

Hannunta karkarwa yake, kai gaba ɗaya ma sai jikin nata yake karkarwa shahada ta yi ta buɗe idanunta warai sai a kan sakamakon layi biyu ne a jiki raɗo-raɗo ƙafafunta da ta ji suna barazanar jumurin ɗaukar gangar jikinta da sauri ta zube ƙasa tana zaunawa zaman dirshan a fili tana furta

"Innalillahi wa inna ilahi raji'un"

*JIDDA*

Kunnuwanta ta sakawa auduga daga maganganun da su Umma suke yadawa a cikin gidan, duk wanda ya shigo gidan ganin kaya tana jin yadda Umma take nuna musu akwatuna 24 a matsayin lefen Aliya ta faɗa musu har da mota duk da motar Abba ya ɗauke ta ya kai gidan abokinsa aka ajiye ta, sannan sai ta nuna akwati biyu da kit a matsayin lefen Jidda mutane su yi ta faɗin Aliya ta yi goshi don wasu ma ganin kayan ya sa sun ɗauka wani hamshaƙin mai kuɗi ne Aliyar ta aura.

Umma duk ta kasa sukuni sun hana ransu sakat da ƙyashi da hassada ji take tamkar ta sauyawa Aliya da mijin Jidda a nata ganin ai Jidda ba za ta auri wanda ya fi mijin ƴarta Aliya ba.

Hassada suke nunawa a fili amma ita Jidda ko a jikinta, sai dai kuma da ya rage saura sati guda biki sai Umma da Aliya suka keɓe a lokacin da Jidda bata nan tana gidan su Salama sun tafi rabon cingam da kati, duk da har gidansu Ibrahim Salama ta rakata da Mummy ta ce sai ta je ta gaishe ta, sun ga tarɓa ta mutuncin kuwa a nan Jidda ta fahimci ta samu surukar arzii, sannan ta ƙara fahimtar ba ƙaramar ƙauna take yi mata ba, hakan ya sa ta ƙara jin hankalinta da kwanta da auren Ibrahim ko ba komai idan uwar miji tana sonka za ka samu salama a gidan mijinka.

Umma ce ta kalli Aliya da ta zuba uban tagumi, duk ta bi ta rame ta yi duhu ta ce

"Aliya na faɗa miki ki dajna saka damuwa a ranki, kar ki je ki samu wani ciwon kin san dai dama an ce hassada mugun ciwo ce bare kuma ta haɗu da damuwa a zuciya abin sai ya miki illa don abin sai ya yi yawa wai shege da hauka" Aliya ta buɗe bakinta da kuka yake son ƙwace mata ita damuwarta idan ta tuno kayan akwatin Jidda sai ta ji duniyar ta mata zafi, gani take gabaɗaya kayan da ita suka dace ba da Jidda ba saboda ita ce kyakkyawa kuma ita ce ma dai ta dace da auren miji kamar Ibrahim ba Jidda ba.

Tana jan hanci ta ce

"Wai Umma ya kike so in yi ne? Ina zan saka raina yanzu gwala gwalan da aka sakawa Jidda a lefe ni fa idan aka cire zoben ciki gabaɗaya sai ya saya kayan lefena har da canji, ga wasu miliyan uku a ajiye, sannan da kunnena na ji Salama tana cewa wai miliyan biyu ya bada kuɗin ƴanmatanci amma saboda Jidda matsiyaciya ce dakyar ta karɓi dubo ɗari biyu shi ma sai da Salama ta saka baki, yanzu da ni ce ba shikenan na samu wajen baje hajar karɓar kuɗaɗe ba, kina dai gani dakyar Kasim ya bani dubu hamsin shi ma yana min ƙorafin babu a rayuwa na tsani a furta min kalmar babu yanzu dubu hamsin mai za ta mana" Umma ta sauke ajiyar zuciya tana jin babu daɗi ta ce

"Ai ni yanzu ban san ba ya za a yi ma, wallahi na rasa mafita ko kaɗan gashi su Jidda ita da ƙawayenta Ibrahim ya biya musu kuɗin gyaran jiki ya kwaso kayan da za ta raba ya kawo mata suna nan jibge a ɗaki kamar babu gobe" Aliya kawai sai ta rushe da kuka ta ce

"Har kuɗin ƙunshi ya biya fa, jiya da dare ma kuɗin da ya bata ta miƙo min dubu ɗari wai ko za mu ƙara ni kuwa na jefa mata kayanta kar ma ta yi tunanin kuɗinta wata tsiya ne a wajena"

Umma tana zaro idanu ta ce

"Dan ubanku kika bata kuɗin? Wane shegen ya ce miki ana mayar da hannun kyauta baya, ai kai faƙiri baka biyewa mai arziƙi bayan kin san kina da buƙatar kuɗin"

Aliya ta ce

"Umma akwai damuwa fa a ce wai ni ce Jidda za ta taimakawa, ki ga wata shegiyar haɗaɗɗiyar mota wallahi da ni motar nan ta dace Umma" Ta faɗa tana kukan takaici.

Umma tana jin tamkar ta dishashe auren ma, amma abun da Allah ya nufa ya daɗe da yi, hakan ya sa ta ce

"Yanzu tun da dai Abbanku ya ce walima za a yi kin ga kayan can da Ibrahim ɗin ya kawo mata ya isa ku rarrabawa ƙawayenku to ya za ki yi tun da Allah ya ƙadarta miki talaka za ki aura, ai kawai mu bada kai bori ya hau"

Cikin rashin fahimta ta ce

"Umma ban gane ba"

Umma ta ce

"Aliya dole mu sauya taku, dole mu ɗauki haƙuri da jumurin halin da muka tsinci kanmu, ina nufin yanzu dole mu fito mu nunawa Jidda soyayyar ƙarya, mu danne duk wani ɓacin rai da za mu ji a tattare da ita, mu jata a jiki ta haka ne za mu samu shiga jikinta ta saki jiki da mu ko bayan an yi auren in ya so sai mu yi amfani da damarmakinmu wajen cika duk wani buri da muke da shi nan gaba!" Shiru Aliya ta yi tana nazarin maganar Umma duk da tana jin hakan da wuya ta iya amma kuma in har hakan ne dole ko da dariyar yaƙe ta yaƙi Jidda ta ga ko za ta yi nasara a kanta!

Tsaye Aliya ta tashi ta rungume Umma ta ce

"Umma ta kin fi ta kowa, Umma mikiya mai hangen nesa, tabbas ta haka ne za mu samu abin da muke so, don na ci alwashin sai na mallaki Ibrahim ko ta halin ƙaƙa, sai na zamewa Jidda ƙadangaren bakin tulu" Ta faɗa tana sakin Umma ta shiga juyi a tsakiyar ɗakin ta ce

"Umma kalli diri da kyauna ban dace da Kasim ba da Ibrahim na dace, ban dace da rayuwar talauci ba da gidan arziƙi na dace"

Umma ta ce

"Ai ki saka a ranki ƙwace goruba a hannun kuturu ba zai yi wahala ba, ke ko zaman kishi ne gwara ki yi da Jidda"

Aliya ta ce

"Wallahi kuwa tun da ba uwarmu ɗaya ba uban ma kowa da nashi, bare a ce auren miji ɗaya ya haramta a garemu!".

Haka suka ringa tsara yadda abubuwa za su kasance wajen yaƙi da zukatansu ganin basu nuna ƙiyayya a fili ba.

Da daddare Ibrahim ya zo wajen Jidda bayan ta fita sun gaisa suna ɗan tattaunawa tana zaune kan wani dakali da yake daga can ƙofar gidan shi kuma yana tsaye ta jingina da jikin motarsa, hira suke cikin natsuwa da kwanciyar hankali, tsaftatacciyar hira ba irin hirar da wasu ƴanmata da samarin zamani suke yi ba wacce hira ce da ta saɓawa addini da kuma al'ada, wanda yawanci wasu samari da ƴanmatan sun ɗauki hakan a matsayin wayewa, bayan ba wayewa ba ce jahilci ne da rashin tsoron Allah da kuma tuna makoma.

Hira da taɓa jikin juna, ko hirar marar kyaun sauraro, gabaɗaya ya saɓa addini sannan daga ke har shi ba za ku yi daraja a idanun junanku ba sannan ko da Allah ya yi kun yi aure za kuke zama da zargi!.

Cikin hirar tasu ne Ibrahim ya ce

"Jiddanah!" Murmushi ta yi ta ɗago tana kallonsa ta ce

"Na'am" Ya ce

"Ina so na miki wata tambaya amma ina jin nauyi" Ta ɗan yi shiru tana jin babu daɗi a ranta don ta yi tunanin ko magana zai mata a kan lamarin Aliya sai da ta ɗan ɗaure fuska don ita bata son wai don za ta auri namiji ko kuma bayan ta aure shi, ta tsaya yake sanin sirrin gidansu ko kuma yake faɗawa wasu daga danginta magana ba za ta lamunci hakan ba, ko yaya naka-nake ne sannan duk daren daɗewa ana iya sauya miji amma ɗan uwa ba a sauya shi, don haka duk yadda nake yake to naka ne idan ka ba namijin ƙofar ya san sirrin gidanku to tabbas wataran gori ko wulaƙanci zai iya biyo baya idan ma hakan bai samu ba babu wani alfanu ga mace take kwashe sirrin gidansu tana faɗawa miji.

Ta ɗan sauke ajiyar zuciya ta ce

"Ka faɗa in har da sarari zan faɗa maka" Ya hurar da iska daga bakinsa ya ce

"Kawai idan ba damuwa ne ina son sanin tarihinki ma'ana ina son sanin asalin labarinki na san mahaifanki sun rasu amma bayan haka ban san komai ba, kuma ba don wai wani abu ba kawai dai ina son sani" Sai da ta kalle shi sannan ta mayar da idanunta tana kallon ƙasa ta ce

"Sunana Hauwa ana kirana da Jidda, mahaifina ɗan asalin ƙasar Niger ne a wani gari da ake kira Doso, mahaifina saboda halin babu da kuma wasu matsalolin wanda yarinta bata bari na san su ba kasancewar lokacin shekarata goma. Wannan dalilan ne suka saka ya baro ƙasarshi ya dawo Nigeri'a , lokacin da ya zo ya dira a garin Kano bai san kowa ba cikin ikon Allah suka haɗu da Abba ya taimaka masa, ka ga wancan gidan shi ne gidan da muka zauna da mahaifana a ciki muka rayu" Ta faɗa tana nuba masa wani gida da yake kallon gidan Abba, wanda gidan yanzu a rufe ma yake babu kowa a ciki, waiwayawa ya yi ya kalli gidan kafin ya juyo yana kallonta ganin idanunta sun cika da ruwa, bata yi ƙasa a gwiwa ba ta ɗora da faɗin

"A kwana a tashi abota mai ƙarfi ta shiga tsakaninsu don Allah har kasuwa tare suke zuwa da mahaifina Malam Abdullahi, koyaushe mahaifina yana faɗawa mahaifiyata girma da darajar Abba a wajensa a ganinsa ba kowane mutum nr zai nuna karamci kamar yadda Abba ya nuna masa ba, abotarsu ta saka ƙawance mai ƙarfi ahiga tsakanina da Aliya, koyaushe muna tare muna son junansu sanann mahaifanmu mata ma basa nuna mana bambanci gidanmu tamkar gidansu Aliya haka nima. sai dai ita Umma bata ƙawance da mahaifiyata sai dai in an haɗu a gaisa ko wani dalili mai ƙarfi" Ta faɗi hakan tana jan hanci da alama dai akwai wani abu da take kusa zuwa wajen faɗa yadda ya ji muryarta tana rawa, ko kuma labarin da take bashi ne yake taɓa mata zuciya.

Ta ci gaba da faɗin

"A watarana wacce ba zan taɓa mantawa da ita ba, ita ce ranar babu makaranta domin ranar asabar ce, muna zaune muna ta hira da mahaifiyata na ce mata wajen Aliya zan tafi haka na fito zan tafi muka haɗu da mahaifina a ƙofar gida zai shigo, nan na masa sannu da dawowa ina faɗa masa wajen Aliya zan je yana faɗin ai dama ya san zancen gizo bai wuce na ƙoƙi, a nan har yake nuna min ledar hannunsa yana cewa maƙocinsa ne na gaba da mu kaɗan ya bashi ɗanyen rogo da yake ya noma kasancewar ina son rogo na hau murna ina cewa zan dawo in ci idan an gama dafawa, wannan ita ce baƙar rana, wannan ita ce rana mafi muni kuma mafi tarihi a cikin rayuwata" Ta faɗa tana kuka tare da share hawayenta shi ma Ibrahim hawaye yake yana bata haƙuri sai da ta ɗan numfasa kafin ta ce

"Ashe wannan rogon shi ne ajalin iyayena, ni kuma kwanana ne a gaba shi ya sa ban ci ba, bayan mahaifiyata ta wanke ta dafa ta zuba min nawa ni da Aliya ta ajiye mana suka ci nasu daga cin wannan rogo sai ciwon ciki babu wanda ya san ciwon cikin har ya yi ajalinsu gabaɗayansu sai da muka je ni da Aliya mu ci rogo a nan na yi tozali da gawar mahaifana kwance kowa da dafara a bakinsa" Kukan da take yi ne ya hana ta ci gaba, sai da ta tsagaita ta ce

"Ashe dai wannan rogon taki ne aka zuba mai ƙarfi a gonar wanda gubar da jikin takin da yake jikin rogon bai fita ba shi ne ya yi ajalinsu duk da cewa an dafa shi amma dai takin bai bar jiki ba" Daga shi har ita kuka suke ta ci gaba da faɗin

Tun daga wannan rana na yi bankwana da iyayena, sannan Abba ya je har Doso amma neman duniyar nan ba a samu wanda ya san mahaifana ko wani wanda yake da alaƙa da su, riƙona ya koma hannun Abba har kawo yanzu" Ta faɗa tana share hawaye, ko a fuska bata faɗa masa irin ƙalubalen da ta shiga bayan mutuwar iyayen ba da irin canjin da ta samu daga Umma da Aliya ba wanda shi ne har yau bata sauya zani ba, a ganin Umma babu yadda za a yi Abba yake riƙe da ƴar da bai san wani dangi nata ba, sai kuma ƙoƙari da farin jininta wanda shi ne ummul aba,isin faruwar komai.

Ya daɗe yana jimanta abin sai ya ji wani mugun tausayinta ya shige shi, tabbas tsautsayi ba ya wuce ranarsa sannan rashin sani ya fi dare duhu da sun san rogon zai yi ajalinsu da basu ci ba, amma dama rai ba bakin komai yake ba. Haƙuri ya ringa bata har dai ta huce da za ta shiga gida ya ɗakko waya iphone 16 ya bata a kwalinta, dakyar ta karɓa sai da ya ɓata ransa, don dama kayan fitar biki da ya ɗinka mata cewa ta yi kar ya kawo saboda ita ko kaɗan bata son ran Aliya ya sosu.

Da sallama ta shiga gidan, Umma ta amsa tana washe baki, suna zaune da Abba suna magana ita kuma Aliya tana ɗaki ko da ta shigo a kan tabarmar ta durƙusa ta miƙawa Umma kwalin wayar tana mata bayanin wanda ya bata, Umma sosai ta nuna murna tana nunawa Abba ya karɓa ya saka albarka, Umma ta miƙo mata ta karɓa ta nufi ɗaki, abin mamaki tana shiga Aliya ta ce

"Ƙawata ƴar uwata" Lafazin ya zo mata a bazata har ta kasa riƙe farincikinta ta ajiye kwalin wayar a kan katifa ta je ta rungume Aliya tana faɗin

"Aliyata ta dawo gareni haƙiƙa na yi farin ciki" Ta faɗa har lokacin tana rungume da Aliya, tabbas tana son Aliya, Aliya kuwa ji take tamkar ta shaƙe Jidda amma haka ta daure ta danne zuciyarta ta nuna mata farincikin ta.

Bayan sun saki juna ta ɗakko wayar cike da murna ta nuna mata wani abu ya caki zuciyar Aliya wai Jidda ce za ta riƙe Iphone bayan ita tana fama da waya mai screen a ragargaje, haka ta danne zuciyarta ta nuna mata farincikin ƙarya, don yanzu dai ta ga Jidda ta kere ta a komai.

An shiga hidimae biki a inda Umam ta ɗauko duka kayan kicin ɗin da ta saya domin Aliya ta raba a biyu ta ce kowa ya ɗauki ɗaya a fili tana nufin saboda soyayya amma a baɗini ta bayar ne don su ƙara saka yarda a zuciyar Jidda, ita kuma Jidda sai take ji tamkar bata yi rashin mahaifiyata ba irin yadda Umma take nuna mata soyayya da kukawa. Ana saura kwana huɗu biki aka je aka yi jere mutane anguwa da kuma ƴan uwa, gidan Aliya suka fara zuwa ciki da falo da banɗaki sai ɗaki ɗaya da kuma kicin shi ma ba mallakin Nasir ba ne mahaifinsa ne ya bashi a kan cewar kafin ya mallaki nasa. Ranar da ya kasance saura kwana uku aka je aka yi wa Jidda sam barka jama,a suna ta yabon gida da kuma yadda kaya ya amshi gida faɗa ma ɓata baki ne.

Amare sun sha gyara don sai Aliya da ƙawayenta suka bi ayarin gyaran jikin su Jidda komai dai a na Jidda aka musu suka fito gwanin sha,awa an sha lalle ja da baƙi.

Umma aka samo mata number maman afrah marubuciya a jikin littfinta ta ruɓaɓɓiyar igiya, jin ana ta yabon kayan matan maman afrar mai suna DARAJAR MATA haka ta saya musu tsumin ƙorama, maganin sanyi mai suna a fatattaki sanyi kasancewar duk wani maganin mata ba ya aiki in dai akwai sanyi a jikin mace. Daka mai suna sirrin ma,aurata wanda yake saukar da ni,ima ga mace sai ɓulɓul na gyaran breast sosai maman afrah ta musu haɗi na kece raini wanda zai kankaro musu mutunci wajen mazajensu Umma ta yi hakan ne don Jidda ta yarda ɗaya suke da Aliya. Mai buƙatar maganin sanyi ko magungunan mata ya yi wa maman afrah magana a 09925576222

Duk haɗe haɗen da aka musu amma Aliya don ta fi Jidda sai da ta samo wami group na wata mai siyar da supplement mai suna mom farhan ta saya wani haɗi na combo wanda ta ga an rubuta a jikin set ɗin kamar haka Hajia indai mgnr emergency ne toh wanan shine kankat

Indai matsalar ki rashin niima da matsi ne toh ki siya wnn combo din zaki gode min, ina masu cewa sun sha magani har sun gaji basu taba sanin ya dadin se yake ba toh dan ALLAH ki gwada wannan combo din, ai Aliya tana ganin haka ta kwafi no admin ɗin kamar haka 0814 153 5308 ta mata magana ta turawa mom farhan hoton combo ɗin ta faɗa mata kuɗin ta tura mata aika aika mata ta ɓoye don ma kar Jidda ta gani.

An yi biki an sha kyau amma Aliya saboda baƙin hali duk wanda suka zo ƴan makarantar su sai ta faɗa musu cewa ai Jidda riƙw ta ake yi a gidansu ita ba uwarsu ɗaya ba ba ubansu ɗaya ba, amma a bayan idanun Jiddar take faɗa.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull