Kenza eBookz

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 19

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 19

Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 19: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 19. Kafin ya gama shan ruwan mamakin da Aliya ta shayar…

3,292 words

Kafin ya gama shan ruwan mamakin da Aliya ta shayar da shi, ji yake kamar ya nutse don kunya shi bai ma san ta ina zai fita falo kuma da wane ido zai kalli abokan nasa ba don ya san sun ji komai, kawai sai ya ga ta miƙe tsaye ta shiga warware laffayar jikinta, ya zamana daga ita sai leshin jikinta, wanda ya matuƙar amsar kyakkyawar fatar jikinta baƙin lalle da ja da ya ƙara haska kyakkyawar fatarta, ji yake yana son kaɗaicewa da ita a wannan daren mai ɗimbin tarihi amma hakan zai iyu?.

Na ce muku hakan zai iyu😃😃😃 ku bani amsa wato cmmnt ma sai kun bushi iska kuke yi a toh nima ai kuna gani a ƙwaryar shanku sai na bushi iska nake typin😒😕 labarin nan yana da tsayi akwai darasi akwai cakwakiya, abubuwa masu kamar almara za ku ji yadda.... Ba zan dai faɗa ba kawai ku biyoni mu cigaba da tafiya ko ni ina jin labarin a cikin raina.

MAMAN AFRAH

09025576222

https://chat.whatsapp.com/I3Lo5jRFh1CDcU1leu8VXW

*RUWA CIKIN COKALI*

(Ya ishi mai hankali wanka)

NA

MAMAN AFRAH

. *Daga marubuciyar*

*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*

*09025576222*

BOOK 1

PAGE 1️⃣3️⃣

*SADIYA*

Maganar Hajiya ta saka Sadiyar shiga ruɗani sannan abu ne wanda bata taɓa zaton cewa ko a mafarki Hajiyar za ta ambata ba, domin cikin ai ba na shege ba ne da za a yi maganar zubar da shi. Maganar da Hajiya ta ƙara yi ne ya dawo da ita hayyacinta jin Hajiyar tana faɗin

"Don haka ki ɗakko mayafi ki zo mu tafi a cire cikin, saboda gidan nan ba matattarar yara va ce ta yaya za a ce daga yin yaye har kin sake ɗurar wani cikin " Cike da jin nauyi da kuma jin kunya Sadiya ta ce

"Hajiya ni ma Allah ne ya ƙaddara ya bani wallahi ba da sani na ba ne...

Hajiya tana ɗaga mata hannu a harzuƙe ta ce

"Sadiya an ce miki jahila ce ni ban san Allah yake bayarwa ba?" Kai Sadiya ta shiga girgizawa alamar a'a, Hajiya bata jira cewar Sadiya ba ta ɗora cike da ɓacin rai take faɗin

"Ke duk ƴan dabarun nan na mata bakya yi, shin mai ya sa vaki saka tsinke a hannu ba ko kuma kin je an saka miki na bakin mahaifa, ko ki sha magani abubuwan tsarin iyali gasu nan barkatai amma kika yi hirim da ke kika sake ɗaukar ciki, saboda baƙin hali da mugun kishi saboda za a yi amarya ku mata dama damuwarku gado shi ya sa baku da aiki sai gasa a haihuwa so kike kafin ta zo kin tara bataliyar ƴaƴa yadda ba za ta taddo ki ba, to albishirinki ba wani dogon lokaci za a ɗauka ba da har kike tunanin tara ƴaƴa a kwana kusa Nasir zai angwance" Idanu Sadiya ta ɗaga ta kalli Hajiya sai kuma ta sunkuyar da kai.

Hajiya ta ƙara kallon Sadiyar kallo irin na ƙasƙanci don ita duk ladabi da biyayyar Sadiya da kuma haƙuri ba wani birgeta yake yi ba ta ce

"Ina so ki sani ciki dole a zubar da shi idan kuma har ƙin ƙi to shawara ta ragewa mai shiga rijiya, ko ya faɗa ko kuma ya sauya shawara, zaɓi biyu ne ko dai ki yarda a zubar ko kuma ki zauna ki raini cikin amma ki sani ɗawainiya ce kika ƙarawa kanki, don Nasir bashi da ƙarfin riƙe mata biyu da yara biyu a yanzu ga kuma hada-hadar shirye-shiryen aurensa shin da wanne zai ji? Wallahi wasu matan baku da lissafi"

Sadiya a fili ta ce

"Ki yi haƙuri Hajiya amma ba zan iya kisan kai ba"

A zuciyarta kuma ta ce

'Duk irin rufin asirin da yake da shi ai a samun Nasir ko ƴaƴa goma ne ba zai gagara ya riƙe ba amma saboda son zuciya da sarewa sannan kuma bai yi dacen mahaifiya ba shi ne kuke raina ni'imar da Allah ya bashi'

Hajiya ta sake cewa

"Dama na zo in kai ki a zubar ne amma tun da kin ce kin ji kin gani to ga wajen nan"

Tana faɗar hakan ta juya ta fice, zuwa jimawa can sai ga Nasir kamar an jefo shi mamaki ma take dama bai tafi wajen kasuwancin ba, ko arziƙin sallama basu samu ba haka ya shigo kamar wanda ya zo filin yaƙi, yana shigowa ya ce

"Sadiya wato kin rainani kin raina mahaifiyata, Hajiya ta zo har gidan nan amma ki ambula mata ƙasa a ido ke ga ishashshiya da mai ko? To ki sani tun da kika ƙi zubar cikin nan ni ba zan dawwama da wahala ba kullum kuna jinya ke da yara ga shirin auren nan" Ya faɗa yana tada jijiyoyin wuya.

Sadiya a zuciyarta ta ce

'Wai namiji da Allah ya ɗora masa gabaɗaya ɗawainiyanda kulawa da iyalansa amma shi ne yake gajiyawa, bayan babu wani abu da Allah ya ɗorawa mace ta sayawa kanta ko ta sayawa ƴaƴa sai dai don kyauatatawa gabaɗaya ɗawainiya kan namiji take kama daga ciyarwa shayarwa tufatarwa lafiya da sauran abubuwan da baki ba zai iya furtawa ba' Ganin ban ce komai ba ya ce

"Aure dai babu fashi idan ma kin yi haka ne don in ji tsoron ɗaukar ɗawainiya in janye batun aurena, ko kina so ko bakya so sai wata ta shigo gidan nan, don mi ban gina gidana don mace ɗaya ta zauna ba, ni mijin mace huɗu ne!".

Cikin halin nuna tashin damuwa da kalamansa ta ce

"Allah nuna mana, ya sanya alkairi!." Wannan maganr da ta yi ta ƙara fusata shi, ya so a ce ta ji haushi ya ƙuntata mata amma sai ya ga bata damu ba, a zuciyarta ta ce

'Mace tana kishi ne a inda aka san darajarta, zuciya tana damuwa da wanda ya damu da ita ne wannan shi ne cancanta mafi daraja amma mijin da bai ɗaukeka a bakin komai ba mijin da yake wulaƙanta ka kishin mai za ka yi a kansa?'

Kamar zai kai mata duka ya ce

"Idan ma ba har zuciyarki kika faɗa ba can ta matse miki" Yana faɗar hakan fuuuu ya fice daga gidan, Sadiya tana mamakin mahaifiyar Nasir da bata kawo zaman lafiya a cikin gidansa ita da ƴaƴanta kullum ƙoƙarinsu su famfa shi, su rura wutar gutsiri tsoma a gidan bata tunanin su Husna ma mata ne kuma dole watarana gidan miji za a kai su, basa ma tsoron a musu abin da suke yi wa wani tun da duk abin da mutum ya yi shi ake yi masa.

Tun daga wannan rana sai al'amura suka ƙara taɓarɓarewa a cikin gidan, idan Nasir ya bada ɗanyen abincin da ba zai isa su ci ba sannan sai ya hana kuɗin cefane, gashi babu abin da take siyarwa bare ta samu abin da za ta yi amfani da shi, ta yi masa magiya har ta gaji amma ko a kwalar rigarsa, sannan wani abin ɓacin ran ta fahimci yanzu abincin gidan ma sai ya ga dama yake ci, sai dai ita da Kalifa su ci wataran ma sai dai ta saka musu ɗan gishiri su ci ko babu mai don yanzu abin na Nasir ya ta,azzara ko maggi ya daina siya bare mai komai yanzu ya janye jikinsa daga siya, ta rasa yadda za ta yi da rayuwarta.

Duk da kasancewarta mace mai sirri da ƙin bankaɗa damuwarta amma haka take faɗawa ƙawarta Noor wasu abubuwan tun da ita Mama ko ta kira ta a waya za ta zayyana mata damuwarta sai ta dakatar da ita idan ma ta fara faɗa sai ta ƙaryata tun da har yau Nasir yana hidima da su in aka shafi kwanaki yana basu kuɗi wannan dalilin ya sa suke ganin ma kawai shaci faɗi ne don dai ta ɓata masa suna. Tun da a ganinsu idan har gida bai ƙoshi ba ai ba a ba wa na waje ba da a ce a gidansa bai wadata su ba ai ba zai ke ba sirikansa ba, basu san duk wannan yana cikin shika-shikan rashin mutuncin Nasir ɗin ba.

Noor ita take kwantar mata da hankali sannan ita take bata ɗan wani kuɗin ta saya wani abu da bta da shi, duk da bata fitowa ta faɗi komai da komai sai dai bahaushe ma yana cewa labarin zuciya a tambayi fuska. Akwai lokuta da dama da wani yake cikin damuwa ko cikin halin son a taimaka masa saboda wata matsala amma kuma bakinsa yana da nauyi wajen sanarwa da wasu damuwar tasa, sai dai ba kowane lokaci ne sai mutum ya faɗi ainihin a taimaka masa ba, ko kuma sai ya bayyana buƙatarsa, wani a ɗan fashi baƙin da zia faɗa ko bai warware komai ba hakan ya isa a gane a taimaka masa inda hali ba sai ya yi roƙo ba wani yana jin nauyin ya roƙa, wannan halayyar ce take faruwa tsakanin Noor da Sadiya.

A wannan halin ne har ta kwashe wata biyu, sai dai daga ɓangaren Nasir bata sauya zani ba don har lokacin yana nan a kan bakansa na ƙin wadata su, sai kuma ƙuntata mata da ya ci gaba da yi don a zuciyarsa burinsa damuwa ta mata katutun da zai yi sanadin zubewar cikin don shi yanzu buri da fatansa da duk wani tunaninsa yana kan amaryarsa Meenal.

A wata ranar talata da safe ta tambaye shi zuwa gidan kakarta mahaifiyar Babanta, hakan ya amince cike da zumuɗi don shi ya fi so ma take yawo amma kullum tana gida bata yawan fita, sannan ya san gidansu ba wani iya riƙe ta za su yi ba shi ya sa ko ta je da wuni uban yake koro ta, wannan ya sa yake cin karensa babu babbaka kuma yake gara Sadiyar don ya san zaman gidansa ya zame mata dole sannan kuma farilla ne tusa a cikin bacci.

Ta shirya tsaf ta shirya Kalifa ta rufe gidan duk da akwai tazara amma haka suka yi tafiyar ƙasa don bata da kuɗin napep. Da farinciki Kaka ta tate su tana ta yi wa Kalifa wasa, zama suka yi ta ɗakko fura wacce ta ji nono ishashshe ta dama musu suka sha, sannan Kalifa ya ci gaba da wasan sa. Zuwa can Kaka ta ce

"Halima" Sadiya ta amsa Kaka ta ce

"Kowa ya ganki ya san kina cikin damuwa dubi yadda duk kika lalace kin yi baƙi kin rame duk kin fita hayyacin ki" Sadiya ta ce.

"Kaka ina cikin damuwa tabbas, kuma mafita ce ma bani da ita, kin san dai yadda aka yi auren nan to yanzu Abban Kalifa yana takura min ne kamar ma ya gaji da auren shi kuma Baba ko gidan na je babu wanda yake sauraron damuwar da nake ciki daga shi har Mama, da a ce suna jin damuwata kuma su ja masa kunne da abubuwan za su yi sauƙi, amma sun nuna masa bani da daraja, wataran ma Baban haka zai ce in koma ko da kuwa sun san zaluntata ake yi"

Kaka ta ce

"Sadiya tabbas Bala ba shi da hali kina gani dai ban isa in shata masa layi a kan komai ba, ni sai in manta ma ban ganshi da idanun nan nawa ba, idan ma ya zo a tsaitsaye zai gaisheni ya kama gabansa" Ta faɗa cike da takaici bata san mai ya sa wasu ƴaƴan ko kaɗan basu san darajar iyayensu ba.

Sadiya ta ce

"Yanzu babu ruwansa da damuwarmu so yake ma in ke ɗaukan ɗawainiyar kaina tamkar wacce take zaman kanta ko kuma zaman zawarci, wallahi kwanaki har gorin sana'a ya min ni kuma bani da jari sannan shi ba tallafa min ba zai yi" Kaka ta nisa ta ce

"Dama idan mace tana gidan aure kuma take son yin sana'a ai mijinta ne zai tallafa mata ya bata jari sannan ya bata ƙwarin gwiwa amma in baka da shi ina ake so ka je ka samo? Ko sata ake son ka yi, wasu mazan basa yi wa kansu adalci suna da halin da za su wadata iyalansu da abu amma sai su hana su sannna su fita waje suna yin bajinta da birge wasu mutanen, in ba bajinta ba ke bai baki ba ya je yana ba iyayenki" Ajiyar zuciya Sadiya ta sauke mai nauyi kafin ta ce

"Ai lamarin Nasir sai dai addu'a amma ya fiya son kansa da yawa duk da yana samun gudummuwar mahaifiyarsa" Kaka ta ce

"Kowa ya yi na gari kansa Halima, sannan komai zai wuce ya zama kamar ba a yi ba, idan har yana sane yake yi Allah zai ƙwatar miki haƙƙin ki watarana zai gane kurensa sakayya tana nan tun da Allah ba ya yafe laifin wani a kan wani" Sadiya ta ce

"Haka ne" Kaka ta ce

"Wancan ƙatuwar akuyar tawa zan siyar dama jiya maƙocina ya saya ragon nan da na turki, to zan siyar da ita sai a cika, akwai Fauziya wancan amaryar da gidanta yake kallon gidan nan, na ji tana cigiyar wanda zai saya firjinta da yake ƙarami ne ita kuma tana siyar da pure water da kemon mango, da zuɓo sana'ar ta karɓe ta shi ne take so ta siyar ta sayi babbar freezer, sai in fansa miki nata firjin in auna miki zoɓo in bak ɗan kuɗin da za ki riƙe na siyan pure water ki je ki fara sana'ar kayan sanyin idan Allah ya saka miki albarka sai kin samu warakar wasu matsalolinki" Da sauri Sadiya ta matsa kusa da Kaka ta rungume ta idanunta har da ƙwallar farinciki cike take da murna jin Kakarta ta sama mata mafita abin da mahaifiyarta da ta san ciwonta ta kasa yi mata lallai yau tana cike da murna.

Kaka tana ta dariya tare da faɗin kar ta karyata, Kalifa ma ganin abin da yake faruwa ya taho ya zo ya tsaya yana kallonsu yana dariya duk da bai san musabbabin farincikin ba. Ta yi ta godiya ta kuma yi wa Kaka addu'a daga ƙarshe Kaka ta ce mata za ta kira ta a waya idan ana kammala cinikin sai a ba mai baro ya kai mata. Sai da ta yi magriba ta baro gidan Kaka zuciyarta washe.

Ko da suka dawo gidan ƙofar babu mukulli da alama mai gidan yana ciki, da sallama ta shigo ya amsa ciki ciki ta masa barka da gida, zaune yake yana cin doya da ƙwai da kuma naman balangu sai lemonsa fanta a gefe doyar ya ɗaukamda naman yanka biyu ya miƙawa Kalifa amma abin mamaki sai Kalifan bai karɓa ba, shi kansa Nasir ya yi mamaki sai ya ɗauki kofi ya tsiyaya lemon ya bashi sai ya karɓa ya sha ya miƙa masa kofin. Tana shirin shiga ɗaki ta ji ya ce

"Yau har aka kai dare lallai ko don gidan Kaka ne shi dama Baba ai ba ya ma bari a zauna a gidansa" Bata ce masa komai ba don ta san magana ya yaɓa mata, haka ta shige bedroom ɗin.

Da dare bayan ta kwanta, bacci ya kasa ɗaukarta, saboda farincikij da take ciki, ko da ya hayo gadon sai bai mata magana ba ya shiga latsa waya, yau a falo ta yi wa Kalifa shimfiɗa don ra ga ya fara wayo kar wani lokacin ya je ya falka suna wani abin wannan dama lallata tarbiya ne wato kwanciya da yara masu wayo ɗaki ɗaya.

Sai da ya gama danne -dannensa ya ajiye wayar ya juyo yana fuskantar ta dama bai kai ga kashe fitilar ɗakin ba ya ce

"Sadiya an Baba" Furucinsa kaɗai ya tabbatar mata da cewa lokacin amfaninta ya yi wato lokacin da zai nemi biyan buƙatarsa, tun da a wannan lokacin ne take iya ganin farin haƙorinsa ko mata magana babu hantara.

"Uhmm" Ta ce ba tare da ta kalli shi ba.

Ya ce

"Haƙƙina nake so yau kwana nake so in yi ina aiki" Cike da tsoro ta yi saurin kallonsa ya ɗage gira ɗaya ya ce

"Yes" ,Ta marairaice fuska ta ce

"Ka ga dai ƙaramin ciki ne da ni amma ya za a yi ka kwana kana abu ɗaya?" ,Ya ce

",Oh wato ke har wani lissafi kike da ban, to ni wannan cikin ma na manta da shi kuma ba na saka shi cikin lissafi" Maganar ta mata ciwo amma ta ƙyale shi, tare da bashi haƙƙinsa sai danya gaji don kansa ya barta, bayan komai ya lafa ta yi wanka ta zo yana zaune yana goge ruwan kansa ta ce

"Ina so za mu yi magana" A taƙaice ya ce

"Ina jinki" Ya faɗa yana ɗaure fuska dama ta san ƙarshen maganar tun da da ta gama masa amfani.

Cike da fargabar amsar sa ta ce

"Kaka za ta siya min frige in fara sana'ar siyar da ruwa da zoɓo ina ga har ƙanƙarar yara zan ke siyarwa... Tun bata ƙare maganar ba yake aika mata mugun kallo wani tsoronsa ne ya ɗarsu a ranta don ita bata buƙatar ko kaɗan ya ci mata zarafi baƙaƙen maganganunsa rai suke ɓata mata sai dai ta san akwai lokacin da Allah zai ganar da shi shayi ruwa ne!.

Cike da gadara ya hau faɗin

"Wato saboda tona min asiri roƙo kika je kika yi don ki zubar mini da mutunci ko Sadiya, to da na ce ki yi sana'a ai ba sanar kayan ruwa za ki yi ba don babu wani ƙato da zii shigo min gida sayen wani abu" Yadda yake rada jijiyoyin wuya kamar dai ba shi ne ya gama samun buƙatarsa yanzu daga gareta ba. Kamar za ta yi kuka ganin tana farincikin samun mafita amma yana neman daƙilewa saboda cuta, tana sassaita kalamanta ta ce

"Don Allah karka hanani sana,ar nan kuma ai kakata ce ba wai na tona maka asiri ba ne, ta ce za ta siya min ne ganin Baba bai siya min ba sannan na maka alƙawarin babu wani namiji da zai shigo gidan nan sayen abu" Tun da ta faɗa masa take ta karanto sunayen Allah a zuciyarta a kan Allah ya ɗora ta a kansa, maimakon ya ce wani abu sai ya ce sai ya yi shawara, haka ya kwanta ita ma ta kwanta ranta duk babu daɗi tana taraddadin ko zai amince?.

Da safe yana zaune Kalifa ya je wajen ƴar yawo zai taɓa wayar jiki, ai da ya masa wata tsawa take yaron ya kiɗime ya yi wajenta da gudu yana ƙanƙame ta tare da sakin kuka, wani abu ta ji ya soke ta a zuciyarta, ganin Nasir bai san jan yaro a jiki ba bai san nunawa yaro soyayya ko kulawa ba kawai dai ya haifi yaron ne amma babu wani jin ƙai irin na mahaifa a tattare da shi.

Bayan ya fita wajen Hajiya ya je bayan ya karya da break fast mai rai da lafiya, su Sadiya kuwa waina ce ya siya musu ta ɗari uku ba don ta ishe su ba kasancewar gidan kakar da ta je bata yi tuwo ba shi ma sai da ya gama mita sannan ya sayi wainar. Hajiya ya korawa bayani jin haka kuwa ta yi uwa da makarɓiya cewa ai dole ma ya bar Sadiya ta yi sana'ar ba don wai tana son ƙwatawa Sadiya ƴanci ko haƙƙi ba sai don ta nuna masa alfanun hakan zai ke ƙaruwa ne tana bauta masa a gidan, sai lokacin ya ji sanyi a ransa da ya ji shi ma zai ƙaru da sana'ar don shi ya sha'afa da cewa ya ce mata ma ta kama sana,a kawai dai da ya ji cewa har frige xa a saya mata bayan ya ɗauka sana,ar ƙarama za ta yi yadda daga ya sakar mata da abubuwan gidan jarin zai karye katsak saboda mugunta.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull