Kenza eBookz

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 18

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 18

Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 18: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 18. "Me ya sa mu shiga mana ki raka ƴar uwarki kin san…

3,327 words

"Me ya sa mu shiga mana ki raka ƴar uwarki kin san dai ba zama za a yi ba yanzu za a fito a tafi raka ki naki ɗakin, kuma kin san dai Abbanku yance hatta ƙawaye kar a bar kowa a gidan amarya su zauna wani siyan baki gabaɗaya za a tafi a bar amarya" Aliya wacce take jin idan ta shiga ciki ta ga ɗakunan tamkar za ta haɗu da taɓin hankali hakan ya sa ta ƙara togewa duk wanda ya zo sai ya raɓe su ya wuce. Ƴar uwar Umma ta rasa ya za ta mata gashi dai ita bata shiga ba, suna nan sai ga wasu daga cikin matan sun fara fitowa suna shiga mota hakan ya sa Auntyn ta kama Aliya ta mayar da ita motar duk da motar ma tana ɗaya daga cikin motocin da suka zo ɗaukan Jidda daga ɓangaren Ibrahim.

A can ciki kuwa tun da aka shiga da Jidda bata bari addu'a ta kufce mata ba, don sai da ta yi lokacin fitowa daga gida, da za su shiga gidan nata ma ta yi a zuciyarta duk da lokacin ne Aliya ta tada musu hankali. Har aka zaunar da ita a bakin gado tana ta maimaita addu'o,in neman tsari inda mutane suke ta mata sam barka da addu'ar zaman lafiya, wasu kuma ƴan baƙin ciki suna taɓe baki musamman Amatullahi ƙawar Aliya wacce take jin haushin ni'imar da Jiddar ta samu, wasu kuma suna mata fatan alkairi, wasu suna jin dama su ne suka samu wannan daukar da wannan kyakkyawan mijin, don kana shigowa babban falon da tangamemen hoton Ibrahim za ka ci karo yana wannan kyakkyawan murmushin nasa mai tafiya da zukatan ƴan mata da yawa!.

Jidda tana bakin gadon a zaune tana lulluɓe kanta a sunkuye sai wasa take da yatsunta da suka sha kyakkyawan ƙunshin baƙi da ja duk da kasancewarta baƙa amma lallan ya haska hannun tamkar ka gudu da hannun. Sai dai idanunta yana ta hawaye rana ta tuna mahaifanta sannan zuciyarta a cunkushe da damuwar da ta lura ƴar uwarta Aliya. Salama ce ta je ta dafa ta ta ce

"To amarya za mu tafi sai mun sake dawowa, a toh wallahi ba don Abba ya hana a zauna ba da sai na jira zuwan abokan ango!" Ta faɗa tana dariyar wasa Jidda ta buɗe dashashshiyar muryarta ta ce

"To yanzu ma sai ki zauna" Murya Salama ta rage tana magana ƙasa-ƙasa ta ce

"Ko na zauna na miki zaman ɗaki?" Daga cikin lafayan take kallon ta Jidda da take kallonta don ta san zolayarta ne take yi.

Jin Jiddar bata ce komai ba sai ta ɗora da faɗin

"Taɓ ba zan zauna ba wannan angon naki ya yi ƙuli-ƙulin kubra da ni don daga gani ya shiryawa wannan ranar a toh za a kashe arna" Wata ƙawarsu da ta zo kusa da su ta ce

"Ai yau angon nan va arna kawai zai kashe ba musulmin ba ba zai barsu ba" Suka fashe da dariyar zolaya ita da Salama duk Jidda tana jinsu. Jin ana ta horn suka fara mata sallama suna fitowa.

Ƴar uwar Abba ko da ta fito ganin Aunty da Aliya a tsaye a gefe da Amatullahi ta ce

"Haba Aliya ai dai kin raka ƴar uwarki ɗaki kun yi sallama amma ji zo har cikin gidan baki shiga ɗakin ba wannan ai sai wani ya ɗauka wani abu ne, kin san dai mutane ba a iya musu" Jin hakan sai Aliya ta yi tunanin kar Jidda ta yi tunanin wani abu da ban hakan ya sa ta ce za ta shiga don yanzu ba ta son wani abu da zai nuna rashin ƙaunar Jidda a tattarw da ita, duk da ta ciki na ciki, ta fi so suke basaja kamar yadda suka shirya hakan da Umma.

Ƴar uwar Abban ce ma ta kama hannunta suka nufi ciki, Aliya daga cikin laffayar ta kafe hoton Ibrahim da yake kafe a falon a take ta ji wani abu ya tsarga mata, tana tunanin da a ce ita ce yau a wannan gidan da kuma wannan mijin lallai da ƙawaye da dangi sai sun raina kansu amma dai gashi Allah ya san halin jaki da bai bashi ƙaho ba!.

Dakyar take taka ƙafafunta daurewa kawai take, a haka suka wuce ɗakin da Jidda take wanda a ƙasa yake ba a sama ba, wani sanyi da ni,imtaccen ƙamshin turarukan wuta wanda aka siya a wajen Zainab Muhammad tahir wacce take da zafafan turarukan wuta ƴan sudan kowa ya san yadda turarukan wutan sudan suke da ƙamshi nata sun sha bamban domin turarukan wutan suna kama ɗaki ƙamshin su mai daɗi da sanyaya rai 0814 209 8878 ta number wannan suka mata magana suka mallaki nasu ga duk mai buƙata zai mata magana tana siyar da ɗaya tana bada sari a farashin sauƙi siyan na gari mayar da kuɗi gida!.

Yanayin yadda kayan ɗakin suka karɓi ɗakin tamkar dama don su aka ƙera ɗakin tangameman wadataccen ɗaki, Allah ne kawai ya sa Aliya bata yanke jiki ta faɗi ba, ko da suka shiga ɗakin cikin ƙarfin hali ta furta

"Jidda!" Jidda ta ɗago kai tana kallon Aliya ta amsa kawai sai Aliya ta je gaban gadon ta rungume Jidda tana sakin kuka, a zahiri kukan rabuwa ne amma a baɗini kukan baƙin ciki ne. Jidda ma ta fashe da kukan sai da suka yi mai isar su ƴar uwar Abban tana basu haƙuri kafin Aliya ta ce

"Jidda ƴar uwata ƙawata da bani da tamkar ki, mun zauna shekara da shekaru amma yau aure zai raba tsakaninmu sai dai zumunci amma babu kwanan gida ɗaya a ɗaki ɗaya, ina roƙon ki yafe min iya zamanmu sannan ina miki fatab alkairi" Jidda jin kalaman bogin da Aliya ta yi sai zuciyarta ta yi rauni hakan ya sa ta fashe da kuka mai tsuma zuciya tana cewa ta yafe mata ita ma ta yafe mata, haka aka fita da Aliya rai cike damƙuna da hassada!.

Sun saka ta a mota tana ta kuka wanda kukan ya zame mata biyu, hassada babban ciwo da kuma kukan zuwa gidanta da take ganin bashi da maraba da kurkuku a wajenta ita yanzu sam Kasim ba ya birgeta. Jidda lokacin da ta ji rufowar get sai gabaɗaya ta fashe da kuka har da sheshsheka.

Bayan kamar minti hamsin ta ji horn da kuma ƙaran buɗe get, shigowar motoci ta ji amma dai ba za ta bambance biyu ne ko uku ba, jim kaɗan ta fara jin ƙaran rufe ƙofofin alamun fitowar wanda suke cikin motar. Hayaniya ta fara jiyowa a falon inda take jiyo muryar Ibrahim yana faɗin

"Daga na kirawo ta kun gaisa za ku fita ku tafi gwauraye su je ɗakin gauranci masu aure su tafi wajen matansu" Ya faɗa cike da zolaya. Tana jin yadda falon ya kaure da maganganinsu amma bata iya gane mai suke cewa sai dai ta san tsiya ce suke masa don ta ji sai dariya suke yi.

Shigowarsa ɗakin ya sanya gabanta faɗuwa, sai ta ji duk wani nauyinsa take ji tamkar dai ba wannan Ibrahim ɗin nata da suke kasancewa kullum a waya suna magana ba ko idan sun haɗu kamar ba za su rabu ba.

Duk wata kunya ta rufe ta sai take jin dama su Salama basu tafi ba duk da ta san umarnin Abba ne hakan, amma a ganinta da suna nan za ta ji sauƙin kunyar da ta mata ƙawanya a zuciya duk da ta san dai ko suna nan dole za su tafi ba za su kwana a gidan ba. Abin mamaki lallai sai lokacin ta tabbatar maza basu da kunya ita tana jin nauyinsa da kunyarsa da ya shigo ɗakin amma shi kuma yana kusanto kansa gareta, domin bai yi wa kansa masauki a ko ina ba sai a kan gadon inda take zaune ya zauna dab da ita kafaɗarsa tana gugar tata kafaɗar, wani ƙamshin turarensa wanda take jin na yau ya sha bamban da na kowacce rana ko don kasancewar yau ranar ta musamman ce a tarihin rayuwarsu Allah masani. Yana zama sai ta ji tamkar ta nutse jin jikinsa yana gugar nata, abu ne sabo tsakaninsu da bai taɓa faruwa ba ko ta ce abu ne sabo wanda a iya rayuwarta bata taɓa kasancewa da wani ɗa namiji da kusanci kamar hakan ba, sai ta ji duk jikinta ya fara wata irin tsuma.

Tana cikin wannan tunanin sai kawai ta ji ya ɗora hannunsa a kan hannuwanta da take wasa da su, wani irin yammm ta ji tamkar an haɗa shokin bata san lokacin da ta yi saurin janye hannun ba, sai dai saurin ƙara riƙo hannun nata wannan karon hannu biyu ya saka ya riƙe nata, cikin wata murya mai sanyi da daɗin amon a kunnen mai sauraro kuma ga ma,abota soyayya ya ce

"Habibty an zo lafiya?" Bakinta bai bata haɗin kai ba wajen bashi amsa sai ta ji ya sake ɗorawa da faɗin

"Ina fatan kin zo da shirin tarɓar mai gidan naki domin kuwa zai zame miki raƙumi da akala, sannan zai zama tamkar ƙaramin yaro a wajenki karki manta sarauniya kike a fadata, amma ni zan zama tamkar bawa a fadar sarki a gare ki wallahi ina sonki Jidda ba zan iya daina sonki ba har ƙarshen numfashina!" Kalmomin nan da ya ambata sun sanya kunnuwana yin dummm har lokacin ban ce komai ba sai ya saki hannun ya ɗage laffayar da ta masa shamaki da ganin fuskata, yana buɗewa ya yi saurin saka hannu yana share lemar hawayen da suke kwance a fuskata sannan ya ce

"Karki ƙara zubar mini da hawayenki, hawayenki suna da matuƙar muhimmanci Jidda kin zo inda ba za ki sake zubar da su ba sai dai kukan daɗi amma ba na baƙin ciki ba, aure ana yinsa ne don faranta ran juna ni kuma zan zamo mai faranta miki, zan zama daban a cikin maza je, don sai na saka kin zama da ban a cikin mataye" Mainakon in daina kukan kamar yadda ya ambata sai wasu sabbin hawayen

suka zubo don in har abin da yake faɗa haka ne haƙiƙa na yi dace da miji na gari kuma mijin ƙwarai.

Ban yi zato ko ankara ba sai na ji ya rungumeni wani irin fargaba na ji kasancewar karo na farko a rayuwata da faruwar hakan, ɗiff na yi ina jin yadda ƙirjina yake dakan lugude, shi kuma Ibrahim bai ma san mai take yi ba abu ɗaya ya sani hakan ya haifar masa da wata irin nutsuwa mai wuyar misaltawa.

Kiran da Abeed ya shiga masa shi ya ankarar da shi, da sauri ya sake ni yana faɗin

"Taso mu je kar wannan ya fasa min dodon kunne" Yana faɗar hakan ya miƙe tsaye, tare da kama hannuna na miƙe ya saka hannu ya lulluɓe min fuskar kamar yadda ya same ta a lalluɓe yana faɗin

"Kar a gane min fuskar amaryata, ni dama in ban da sun kafa min tsiya da babu wanda zai rako ni" Ni dai ban ce komai ba kawai dai na ji hannunsa cikin nawa ya kama, babu yadda na iya haka na biyo shi muka fito kunya duk kamar na nutse. Tun da muka zo falon suka mana caaa wai mun Ibrahim ya ƙule da amarya a ɗaki ya manta da su, shi dai cewa yake

"Ko ma mai na yi ai ba haramun ba ne" Suna ta wasa da dariya, ya zaunar da ni tare da zama a kusa da ni, nan aka shiga yin addu'o i da kuma mana ƴan nasihohi daga ƙarshe suka mana fatan alkairi suka mana sallama suna cewa ya zo ya raka su yana faɗin ai ko nan da ƙofa ba zai fita ba, haka suka tafi suna mana tsiya, ina jin lokacin da suka fice mai gadi ya rufo get ɗin.

Suna fita ya buɗe min fuskar ya kama ni, wani ɗaki muka shiga kusa da ɗakin da aka kaini, komai na ɗakin sabo dal amma ba kayan ɗakin da Abba ya saya min ba ne na ɗakin da aka kaini nan ne kayan da Abba ya saya mana, haka ma kujerun falon, banɗaki muka shiga tare bayan mun saka takalman da suke ƙofar bayan sabbin silifas ne yellow da kuma ja. Ni dai na tokare a bakin ƙofa na sunkuyar da kai ganin haka ya shiga yin uzurinsa ni dai ina jin ƙaran ruwa amma ban san ruwa yake kamawa ba ko kuwa alwala, jim kaɗan ya ce

"Wuce ki yi alwala ko kuma ni in zo in miki... Tun kafin ya ƙarasa na rama gefensa na wuce kasancewar banɗakin ma yana da girma tamkar ba banɗaki ba.

Shi kuma dariya na ga ya min sai ya ɗaga hannu ya fatsa min guntun ruwan hannun nasa a fuska, har hakan ya sa na murmusa, juyawa ya yi ya fita yana dariya ni kuma na yi tsarki tare da yin alwala na fito, a ɗakin na ga ya shimfiɗa sallaya gida biyu, ɗaya tashi a gaba tawa a baya haka ya yi kabbara muka gabatar da nafila raka'a biyu bayan mun salance ya ɗaga hannu ya yi addu'a muka shafa. Bayan ya juyo ya dafa kaina ya yi addu'a sannan ya tashi ya fita jim kaɗan ya dawo ɗauke da leda babba sai kuma plates.

Bayan ya ajiye ya fita sai gashi ya dawo da lemuka da madara masu sanyi ya jera ya koma ya ɗakko kofuna na glass duk tana kallonsa sannan ya dawo ya zuba komai sai ya ce

"Ki sa hannu mu ci" Ta ce

"Na ƙoshi" Hannu ya kai ta lakato hancinta ya cr

"Yau akwai ɗura kenan" Idanu ta ɗaga tana kalle shi tare da sauke idanun a kan gasashshsiyar kazar da take ta turiri kai ta shiga girgizawa kafin ta samu furta wani abu sai gani ta yi ya yago naman kazar tsoka ya nufi bakinta tare da faɗin

"Jiddanah yi bismillah" ,Yadda ya yi furucin kawai ya isa ya nuna maka tabbas yana cikin mazan da zai ba mace kyakkyawar kulawa da nuna soyayya a zaman aure!.

*ALIYA*

Tun da suka fito daga gidan Jidda ranta yake suya ji take dama a ce mafarki ne take ba wai zahiri ba. Motoci suna ta wulwula gudu saman titi tana zancen zuci cewa yanzu duk rabi da kwatan motocin na domin ɗaukan Jidda suka zo ita kawai albarkaci take ci.

Sun yi tafiyar mai nisa kafin suka kusa wata unguwa da hasken fitilun motocin ne kawai suka haske unguwar, motar gaba wacce ita ce abokin Kasim yake ciki su ne jagora zuwa gidan amarya Aliya, Aliya sai saukar guɗar mata take ji kamar za su cire hanci ita kuma tana jin guɗar har tsakiyar kanta.

Wani gida madaidaici wanda yake ɗan sheƙin fenti don yanzu tana satar kallon windown don ta ga gidan da za a kaita hasken fitilun ne suka nuna mata sabon fentin da aka yi wa gidan, don motocin da suke gaba sun fara tsayawa a saitin gidan, idanu ta runtse da ƙarfi tana jin tsanar Kasim a ranta, ganin gidan Jidda duk yawan motocin sai da suka samu matsugunni a cikin gidan amma sai gashi ita babu get ɗin da ko mota ɗaya za ta samu mafaka, hasali ma ƙaramar ƙofa ce a gidan, ba ma wannan ne abin mamaki ba yadda bata hango hasken ƙwan fitila a gidan ba sai ta fara zancen zuci tana faɗin

'Kar dai Kasim don baƙin talauci inji ma bai saya ba, saboda babu nepa a ce gidan amarya, amaryar ma kamar ni amma babu haske?' Ta faɗa a zuciyarta tana saka haƙorin sama na bakinta ta dantse leɓenta na ƙasa bata ankara ba ta ji Aunty ƴar uwar Umma tana faɗin

"Fito da Bismillah Aliya, kin zo gidanki, ki shiga da addu'a Allah sa gidan zamanki ne Allah sa abokin rayuwa ne sai mutuwa ce za ta raba" A fili Aliya ta sako ƙafarta ta fito a zuciyarta kuma ta ce

'Ba amin ba' Ƴar uwar Abba ita ce ta amsa da amin, mata kuwa sai guɗa suke rafkawa an samu abin da ake so, mata kenan akwai son shagalin biki su dai su je biki (Lol)

An fara cusuwa zauren gidan inda ake ta faɗin

"A jira wasu su gama shiga mana, ai zauren ne ƙarami" Aliya da ake riƙe da ita kamar ta kurma inu haka take ji, sun shigowa gidan hakan ua yi daidai da jan ƙaramin inji da aka yi wato aka tada, amma wajen ja uku injin bai tashi ba, a ja na huɗun ne sai ga haske tarrr ya haske gidan, mata aka fara faɗin

"Haba haske ai rahma ne" Wata mata da Aliya bata gane wace ce ba sai ji Aliya ta yi ta

ce

"Gidan Jidda kuwa haske tarr har muka tafi bamu san ma ta inda hasken yake zuwa ba babu ƙara injin" Wata ta kusa da ita ta ce

"To ko sola ce"

Sai matar ta ce

"Abinki da babban gida wataƙila wajen injin ma da aka tanafa na musamman ne yadda ba zai damu masu gidan ba" Aliya kamar ta zazzage su haka ta ji.

Falon aka shiga da amarya, hakan ya yi daidai da mutuwar injin sai fitulun waya aka kunna wata mata tana faɗin

"Gyara fa ake yi shi ya sa"

Ɗakin aka wuce da amarya tana ganin ɗakin na Jidda ya yj biyar ɗin nata, Jidda ta samu komai idan ta ce komai tana nufin komai ciki kuwa har da kyakkyawan miji.

Har aka watse in ji bai tashi ba tana jin ƙaran ƙwale-ƙwalen ƙarafe a tsakar gidan da tashin maganar mutanen guda biyu, da alama ma in jin ba sabo ba ne ko kuma dai matsala ya bayar.

Tana jin motocin suka tashi suka tafi, tana zaune dilim a duhu sai hasken fashashshen screen ɗin wayarta. Lulluɓin ta fisge tana ƙarewa ɗakin kallo ɗakin ya yi kyau babu laifi har jeren da aka yi amma saboda hassada da hangen na sama da ita gabaɗaya baƙin gidan da ɗakin take gani Sai da aka yi wajen minti talatin kafin suka samu injin ya tashi, sallamar Kasim da wasu da bata san su waye ba ta ɗauki dai muryar abokinsa Salis, tana ji masu gyaran injin suka tafi su kuma suka shigo falon suka zazzauna, suna ta yi masa tsiya ango na amarya tana jin suna faɗin

"Wai ina amaryar ne?" Kasim ya ce

"To ku haka za ku ga amarya ba a muku iso ba, ai sai na nema muku izini sannan zan kawo maka ita" Gabaɗaya suka hau masa tsiya shi dai ya nufi ɗakin domin kawo amarya.

Maimakon ya ganta a lulluɓe sai ya ga fuskarta warai babu lulluɓi abin ya ɗaure masa kai ma tamkarnwata zararriya haka ya ganta, mamakinsa ya danne ya ƙarasa yana sakin yaƙe duk da gabansa yana faɗuwa don ya san ko kaɗan Aliya bata ɗokin aurensa tun daga ranar da ya kai lefe a baro.

Zaunawa zai yj sai ya ji a faɗace ta ce

"Karka zauna a kusa da ni don ban gayyatoka ba" Fasa zaman ya yi ya shiga mata nuni da hannu yana mata alama cewa da mutane a falo a gefe ɗaya yana mata alama da cewa ta yi ƙasa da muryarta. Cikin hargagi ta ce

"Ina ruwana da mutane, ko akwai wanda na kaiwa katin gayyata, da suka kwaso koɗaɗɗun ƙafafu suka zo, to yadda suka zo haka za su ɗauki ƙafa su koma inda suka fito" Kalamanta sun kusa saka ya zauce saboda ɗimuwa, ya san dai duk abokansa sun ji abin da ta ce, bai taɓa zato ko tsammanin hakan ba, wannan ranar babbar rana ce a gare shi mai ɗimbin tarihi amma yanayin Aliya ya nuna so take ta rusa komai, so take ta tada fitina, so take ta shayar da shi ruwan guba mai ɗaci ba ruwan zuma ba, a ce a ranar farkonta a gidansa tana magana kamar za ta kai masa duka anya zaman zai iyu?.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull