Kenza eBookz

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 5

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 5

Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 5: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 5. "Ku zama masu jajircewa, ku zama masu riƙe ibada tare…

3,370 words

"Ku zama masu jajircewa, ku zama masu riƙe ibada tare da jajircewa a dukkan lamuran rayuwarku, kar ku bari wani abu yale rage muku jin daɗin rayuwa, duk wanda ya riƙe Allah to tabbas ba zai yi nadama ko da na sani ba" Ta faɗa tana juyawa ɓangare Zalika ta kalle ta, ta sake juyawa ɓangare Mubin ta kalle shi, su duka har lokacin da ruwan hawaye a saman fuskar kowa.

Zalika ce ta ce

"Mamy wallahi wani lokacin sai inmke ganin kamar ba Baffa ba ne ya haife mu, to ko yana da wata matar a wani waje da wasu ƴaƴan shi ya sa su yake musu walwala mu yake ƙume mana fuska?"

Kafin Mamy ta yi magana Mubin ya yi karaf ya ce

"Ko dariya ba ya yi, sai fushi da hantararmu kamar dai ba ya son mu, ai na san idan mu kaɗai ne ƴaƴan nasa to zai so shi ma yake zaunawa da mu ko ya bamu kulawa"

Mamy ta ce

"Sau nawa zan faɗa muku ku yi haƙuri ne wai? Na ce muku akwai lokaci yana tafe wataranan mahaifinku zai zama kamar kowane mahaifi"

Zalika ta ce

"Allah ya sa amma dai ina ga sai bayan mun bar wannan duniyar don Baffa ba na jin akwai ranar da zai sauya, ko ya canja ra'ayi.

Mamy ce cike da harzuƙa ta ce

"Wai ya kuke so in yi ne?"

Mubin ya ce

" Mamy mun san kin yi ƙoƙari kuma kina kan yi amma dai ni na san tarbiyya ba ta uwa kaɗai ba ce. Uba yana da rawar gani mai girma a kan iyalansa idan ya nuna ƙauna da kulawa, ya saurari yaransa, zai fi sa su girma da kwanciyar hankali da ƙima, dan aka bar uwa ita kaɗai, yara za su rasa ginshikin ɓangaren uba amma ki yi haƙuri" Mubin ya faɗa yana saka hannu ya ɗauke hannun Mamy daga kafaɗarsa ya miƙewa ba tare da ya ce uffan ba ya bar falon.

*JIDDA*

Gabaɗaya jikinta karkarwa ya fara ganin Umma ta ɗaga hannu za ta sharara mata mari, saboda ta san zafin hannun Umma idan har ta mare ka sai ka gwammace kiɗa da karatu. Domin tana da zafin hannu don hannun ta tamkar hannun wani namiji babu laushi ko kaɗan . Karkarwar da jikinta ya fara kwandon yana neman suɓucewa, Umma wacce sai da hannunta ya kusa isa fuskar Jidda sannan ta hangi Abba ya taho daga hanyar ƙofar gida don alamar farin yadin jikinshi ta hango, sosai faɗuwar gaba ta ziyarce ta amma saboda kissa da kisisina da iya bariki irin na Umma a take ta shiga kokawa da ƙwaƙwalwarta, don ganin ta ƙirƙiri abin da zai gusar da wannan mugun ganin da Abban ya kusa yi.

Cike da tsantsar baki ta saki wata ƴar bazawarar dariya, hannun nan da ta yi niyyar marin Jidda da shi sai ta ƙarasa gefen fuskar Jiddar a hankali ta shafi kuncin Jidda ɗata hannun kuma sai ta riƙe haɓar Jiddar tana cewa

"Allah ya miki albarka Jidda ya baki miji na gari inda za ki huta, ubangiji ya baki ƴaƴa masu miki ɗawainiya kamar yadda kike mini, Allah jiƙan itayenki da rahma" Wannan kalaman na Umma ne ya sa Jidda wacce ta rikice take jiran saukar zazzafan marin na Umma da sauri ta buɗe idanunta tun daga lokacin da ta ji Umma ta shafa fuskarta haɗe da haɓarta amma jin kalaman na Ummar ya ankarar da ita akwai abin da yake faruwa.

Wani yawu Jidda ta haɗiye muƙut, ganin fuskarta ta tsira daga mari, Abba kuwa wanda ya yi mutuwar tsaye da ganin ɗaga hannun Umma mamaki da al'ajabi suka saukar masa ya fara tunanin mene ne halan yake shirin faruwa, sai dai lokacin guda Umma ta sauya masa akalar tunaninsa daga mummunan zaton da ya fara mata zuwa kyakkyawan zato da yake mata a kullum domin kyawawan halayenta da take nunawa a gabansa da kuma rashin nuna bambanci tsakanin Jidda yarinyar da yake riƙo da kuma ƴarta ta cikin ta wato Aliya.

Wata nannuyar ajiyar zuciya ya sauka tare da fata ɗaga sagaggun ƙafafunsa don tun lokacin, da ya ga Umma ta ɗaga hannu ta nufi fuskar Jidda ya ji komai ya tsaya masa cak!.

Baki ya buɗe cike da raha ya yi sallama, a lokacin Umma ta riƙe da gefen kaɗar Jidda, Jidda kuwa sai a lokacin ta gane dalilin da ya sa Umma ta fada aiwatar da ƙudurinta a kanta, yanzu ta fahimci ashe zuwan Abba ne ya dakar da Ummar daga marinta.

Umma kuma cike da nuna bata san da zaman Mai gidan nata a inda yake ba, ta juya da sauri tana ƙara faɗaɗa fara'arta ta shiga amsa masa sallama, tare da ɗauke hannu daga saman kafaɗar Jidda da ta riƙe tana mai cewa

"Maza an Jiddona a je a kai kanukan kicin" Cike da ƙarfin hali Jidda ta amsa mata da faɗin

"To" Tana nufar kicin don har lokacin bata dawo daga duniyar tsoro da fargabar marin da Umma ta yi niyyar mata ba. Umma tana sakin Jiddar ta juya da fara'arta ta irin mutanen kirki masu dattako ta nufi Abba tana ta karɓi ledojin hannunsa tana faɗin

"Sannu da zuwa sannu da zuwa, sannu da zuwa jan gwarzo, uba na gari ga ƴaƴansa miji na gari ga matarsa, Allah bada tsawon rai da kwana mai amfani, an dawo daga hidima da ƙoƙarin nemawa iyali abinci da za su ci, Allah yi jagora ya sauƙaƙa maka hanyar nema" Ta ringa jero addu'ar tana gaba yana biye da ita yana ta amsawa da

"Amin ya rabbil alamin" Ɗakinsa ya shiga, sai da ya zauna a bakin gado ta ƙara masa sannu da zuwa sannan ta fito da ledojin ta damƙawa Jidda a kan cewa komai a ajiye shi a mazauninsa, fruit ɗin kuma ta yanka. Ruwa ta kaiwa Abba banɗakinsa na ɗaki sai da ya shiga wankan ta fito, suna haɗa ido da jidda wacce take zaune da kayan fruit a gaba tana saka su a wata roba mai ruwa tana wankewa, wata gagarumar harara ta jefawa Jidda kamar idanunta za su faɗo, da sauri Jidda ta kawar da idanunta ta maida hankali ga abin da take yi. Umma wani tsaki ta doka har guda biyu tare da juyawa ta shiga kicin ɗin kayan abincin Abba ta ɗakko ta ajiye a waje guda.

Abba sai da ya yi alwala ya fito daga banɗakin jallabiya ya saka ya fesa turare ya ɗakko carbinsa ya fito, lokacin ana ta kira magriba, Jidda lokacin ta gama zubawa Abba kayan fruit ɗinsa a plate ta rufe ta ajiye a kusa da abincinsa da Umma ta ajiye, sai kuma na Ummar a wani plate ɗin sai nasu ita da Aliya a plate ɗaya, ta san wannan ƙa'ida ce in dai Abba yana nan tare suke cin abu.

Umma da ta gama alwala ta buɗe baki ta ce

"Jidda maza ki ajiye wannan kayan ki yi alwala ki yi salla, ƴar uwat taki ma ki musu magana su fito an kira sallah" Da to ta amsa ta shiga ɗaki za ta ɗakko abin sallah.

Abba ya ce

"Jidda sarkin aiki" Ya faɗa cike da kulawa yana ƴar dariya. Murmushi ta yi ta ce

"Ina jin daɗin in ga ina aiki" Murmushi ya yi ya ce

"To ai sai a je a gaishe da ubangiji kin dai ji abin da Ummarku ta ce" Da to ta amsa masa tana jin wani farin ciki don Abba shi kaɗai ne mai ƙaunarta tana jin daɗin yadda yake ƙaunarta. Yana fita sai ga Aliya da Amatullahi sun fito kallo ɗaya suka yi wa Jidda da take shimfiɗa tabarmi a tsakar gidan, tun da ita tana fashin sallah, waje suka fita Aliya za ta takawa Amatullahi, a ƙofar gidan suka yj sallama don ta san Abba ya dawo dama magana ce a kan saurayin da ta gani kyakkyawa tana cewa burinta ya zo gare ta ya bayyana kalmar so a gare ta ita kuwa dole ta yi watsi da Kasim saurayinta da yake mata wahala duk da bashi da wani ƙarfi sai don ƙaunar da yake mata kuma yana son ya faranta mata ganin tana son a bata.

Aliya sallah ta yi haka ma Umma suka zauna, Jidda tana ɗaki gudun kar a mata wani abun. Abba sai da aka yi sallar isha'i ya shigo gidan, yana shigowa da sallama vayan an amsa ya nufi tabarmarsa ya zauna, Aliya ta masa sannu da zuwa Umma ta shiga ƙwalawa Jidda kira tana faɗin mai take a ɗakin. Jidda tana fitowa ta je ta durƙusa ta gaishe da Abba tare da masa sannu da dawowa. Ya amsa cikin fara'a yana musu addu'a

Abincin da Aliya ta zubo musu a plate ɗaya suka shiga ci, Aliya tana wani jan Jidda da hirar tana ta ƴar dariya, haka ma Jiddar ta ɗan saki jiki duk da ta san kawai na ganin Abba ne. Sai da suka gama suka shiga shan fruit ɗin. Bayan kowa ya gama aka shiga hira tamkar dai babu ƴar tsama tsakanin Jidda da Umma da Aliya. Abba yana ta musu murnar kammala jarabawa da gama makarantar buɗar bakin Umma sai ta ce

"An kammala karatu kam sai shafa lalle" Ta faɗa tana ƴar dariya tare da fakar idanun Abba ta yi wa Jidda wani kallo irin na za mu ga da wanda za a ɗaura miki aure.

Abba gyaran murya ya yi ya ce

"Tabbas dama wannan ne burina duk wacce take son ɗora karatu sai dai ta ɗora a ɗakin mijin ta" Jidda gabaɗaya ta ji hankalin ta ya tashi saboda ta san Abba bashi da burin da ya wuce ya aurar da su rana ɗaya da ita da Aliya, gashi ita ko tsayayyan saurayi bata da shi bare kuma a yi zancen aure.

Aliya ma duk da haɗuwarta da Ibrahim yau hakan ya sauya mata tunani daga auren Kasim amma dai ta san ita ko da a ce mai za a yi ba za ya kasa samun miji na kerewa sa'a ba ko da a ce ana gobe ɗaurin aure ne ta tabbata ba za ta yi kwantai ba.

Haka dai aka tattauna kafin daga bisani kowa ya je ya kwanta.

Bayan kwana biyu.

Misalin ƙarfe biyu da minti ashirin na dare ne, alarm ɗin da Jidda ta saita a wayarta ya shiga ruri, cikin bacci ta ji ƙaran da sauri ta tashi ta danne wajen sifikar wayar da ƙarfi kafin ta saka hannu da dakatar da alarm ɗin. Duk da wannan namijin ƙoƙarin da ta yi amma hakan bai hana Aliya tashi daga bacci ba cike da ɓacin rai ta buɗe idanu lokacin har Jiddar ta kunna fitilar wayarta.

Zaune ta tashi tana mutsirtsika idanu, gaban Jidda ne ya faɗi amma bata ce komai ba, wata doguwar hamma Aliya ta saki ko bakin ta bata rufe ba, bata taoron shaiɗanu su shige bakin su samarwa kansu mazauni a bakinta. Cike da bala'i murya ƙasa-ƙasa gudun kar iska ta kai maganar ɗakin Abba, don ta san Abba kamar mai kunenn miciji haka yake wajen jin magana, bare shi ma da ba wani baccin dare ba yake don ta tabbatar yanzu da za a je ɗakinsa ko rantsuwa ta yi ba za ta yi kaffara a kan sallaya za a same shi ko dai yana sallah ko kuma yana karatun qur'ani.

Tana mata wani kallo ta ce

"Jidda wai mene ne hakan? Sau nawa zan ce miki ki dajna saka wannan ƙaran alarm ɗin yana katse mini bacci da mafarkai masu daɗi, ni wallahi ban taɓa jin wannan al'amari ba a zo gidan mutane a hana su sakat da sakewa ake damunsu da shiga haƙƙinsu" Ta faɗa cike da wulaƙanci tana wani kauda kai gefe, ruwa ne ya taru a kwarmin idanun Jidda ta tsaya tana ƙarewa ƙeyar Aloya kallo da yake ta juyar da kai gefe irin na wukaƙanci. Murya a dishashe ta shiga faɗin.

"Aliya ni kike yi wa gorin gida?" Kamar an wanda Aliyar take jiran tambayar ta ce

"To in fitsari banza ne kaza ma ta yi mana" Furta furucin wannan ya yi daidai da gangarowa maƙalallun hawayen da suke cikin idanun Jidda, cike da jin babu daɗi a ranta ta ce

"Aliya wai kam ko kin manta Jiddanki? Ni ce fa Jidda wannan ƙawar taki tun ta yarinta, ni ce fa wacce kike so da tsananin ƙauna, ni ce wacce muke wasa bacci kawai yake rabamu, ni ce fa za mu wuni tare amma idan za mu rabu da kuka ake rabamu saboda shaƙuwa da ƙauna. Amma Aliya yanzu saboda iyayensa sun kwanta dama ƙasa ta rufe idanunsu shi ne kike min wasu abubuwa wanda ban taɓa zato da tunanina ba, shin ko kin daina so na ne? Muna rayuwa tamkar ƴan biyu babu mai shiga tsakaninmu muna son junanmu amma lamuran duk sun taɓarɓare sun jagule shin ina matsalar take?"

Duk wannan jawabi da kalami da Jidda ta yi ta vayan kunnen Aliya ya wuce don ko gizau bata yi ba, bare Jidda ta saka ran cewa kalamanta za su yi tasiri a zuciyar Aliya, don ta lura Aliya ta sauya gabaɗaya, zuciyarta ma tamkar wanda ta ƙeƙashe daga tausayi da jin ƙai!.

Yatsina fuska ta yi ta ce

"Yankan uwa ai ya ishi ɗan tayi ishara, ke yanzu kina zaman jiran sai na furta miki kowace kalma da bakina, hankali da tunaninki basu isa su baki amssoshin tambayarki ba?"

Hawayen idanunta sun fara gudu tamkar an kunna famfo, tana jin yadda ruwan hawaye yake gangatowa har ta saman hancin ta, a gefw ɗaya yana gangara har wuyanta.

Cike da alhini da damuwa haɗe da sanyin murya ta ce

" Au haka ne?"

Aliya ta ce

"Tabbas ya kamata ki fahimci RUWA CIKIN COKALI ya ishi mai hankali wanka" Tana faɗar hakan ta juya baya ta kwanta abin ta.

Jikin Jidda sanyi ƙlaw ta juya za ta fita dama alwala za ta yi domin gabatar da sallar nafila, har ta je bakin ƙofar za ta fita ta tsinkayi muryar Aliya tana faɗin.

"Ba za ki gane ba Jidda tabbas babu ƙarya na ƙauna ce ki kuma tamkar ƴar uwa na ɗauke ki, sai dai ba zan ɓoye miki tun daga lokacin da muke zuwa makaranta tare sai kowa yake son ki ni ko oho, idan kika yi fashin rashin zuwa makaranta ko na kwana ɗaya baki da lafiya daga malamai har ɗalibai tambayar ki suke, idan na yi fashi ko shekara zan yi babu mai nemana daga islamiya har boko. Tsananin ƙoƙarin ki da farin jini ya sa Abba ma kika ciri tuta a wajensa, tun daga wannan lokacin matsayin ki a zuciyata ya ragu sannan uwa uba da muka isa munzalin ƴanmatacin samari suka miki caaa duk da kyau da diri da nake da shi na tsarin halittar ƴa mace wacce za ta ja hankalin duk wani cikakken namiji mai lafiya a jika amma sai ya zamana kowa ke yake kallo, duk inda muka taka sai dai samari su biyo mu gida idan kuwa suka zo kowa ya aiko yaro sai dai a ce ana yi wa Jidda magana!Tun daga wannan lokacin na fara kallon kyauna a matsayin muni tun da ga shi dai ana faɗin farar mace alkyabba ta mata amma ni nawa fari da kyan ya zama tamkat shuɗaɗaɗn lokacin"

Tun da ta fara magana bakin Jidda yake a buɗe ta rasa abin da za ta ce kanta gabaɗaya ya kulle tana tunanin shin dama wannn ne ummul aba,isin rabuwar kawunansu da Aliya, to ita ta ce samarin su zo nemanta ita da vata ma kula su hatta maganar malamai da ɗalibai ba ni na ce so ƙaunace ni ba ashe shi ya sa ko da muka fara karatun N.C E bata son kowa ya raɓe ni kenan hassada Aliya take min? Ta shiga jerawa kanta tambaya w zuciyarta, bata da amsar da Aliya domin tana ma tunanin lokacin sallar ta yana wucewa a banza ita kuma a rayuwa tana son ribatar lokacin ta kafin mutuwarta ta riske ta.

Ko da ta fita ta yi alwala ta dawo Aliya ta juya tana bacci bata sake cewa komai ba, sallah ta yi raka ',a huɗu ta zauna ta ringa jerowa iyayen ta addu'a domin ta san tsakanin ɗa da iyayen da suka riga gidan gaskiya babu abin da suke buƙata sai addu'a. Bayan ta gama musu ta yi wa kanta da Abba, ta yi wa Umma da Aliya tare da yi wa dukkan sauran musulmi.

Sai da ta yi sallar asuba ta yi karatun qur'ani sannan da gari ya yi haske ta koma ta kwanta bacci ya yi awon gaba da ita.

Bayan faruwar haka da kwana biyu, Aliya ta shiga wasi-wasi a kan tunanin Ibrahim da yake yawan addabar zuciyarta, sai dai ta yi sawun zuwan kamfanin da ta ga sun je an buɗe sun shige da motarsu amma ko barin ta ta shiga mai gadin ba ya yi, sai dai ta saka a ranta idan kere yana yawo zabo yana yawo watarana za a haɗu.

Ta ci gaba da riƙe Kasim ɗinta tana lallaɓawa tare da jiran gawon shanu na zuwan Ibrahim domin idan ta samu Ibrahim dole Kasim ya kama gabansa a cewar ta, shi kuma Kasim saboda ƙaunar da yake mata koyaushe sai hidima da kashe mata ɗan kuɗin da yake samu yake.

Rayuwa tana ta tafiya, yau fari gobe baƙi dama haka rayuwa take a wajen kowa ta kowane ɓangare, bijirowa da fitar da abokin rayuwa da Abba ya yi wa Aliya da Jidda shi ne abin da ya saka Jidda a wani hali, domin ta san bata da kowa, ita yanzu ko wuni za ta yi tana yawo ta dawo gida babu mai tsayar da ita bare a biyo ta gida, gashi dai ta san Abba bai san cewa bata da manemi ba, tun da shi yana wuni a kasuwa sannan ya san dai da Jidda akwai manema bai san cewa yanzu kiɗa da rawa sun sauya gabaɗaya ba. Ta shiga damuwa musamman yanzu da Umma ta sako ta a gaba da rashin manemi kuma mashini tana faɗa mata cewa sai dai a bada ita sadaka tun da baƙin jinin ta ya saka bata da manemi, duk da ita Jidda ta san Allah ne yake bayarwa kuma aure lokaci ne kamar haɓo yake idan ya zo sai an yi. Gorance gorancen da Umma take mata ya sa ko zaman gidan fita yake a ranta bare yanzu da sun kammala karatu sai islamiya Jiddan take zuwa Aliya dama ta yi bankwana da zuwa islamiya saboda ta ga Abba ba zaman gida yake ba ita kuma Umma bata takura msta wai ai ta iya karatun sallah, bata san cewa uwa ita ce makarantar farko ta ɗanta ba, ilimi ya zama dole ga kowa kuma wajibi ga mace domin ita ce makarantar farko ta ƴaƴanta da ma al'umma baki ɗaya.

Kamar kullum yau ma sa da ta gama aikin gidan tsaf ta yi wanka ta saka kaya tare da ɗora hijabin makarantar ta, fitowa ta yi tana riƙe da jakar islamiya, Umma da Aliya suna zaune suna tattunawa, sallama ta musu babu wanda ya kula ta, juyawa ta yi ta fita daga gidan, a zuciyarta tana tuno lokacin tata mahaifiyar tana raye yadda take ta mata addu'a da fatan alkairi idan za ta tafi makaranta amma yanzu saboda bata raye in har ba Abba ba ne to babu wani mahluƙi da yake mata addu'a ita damuwarta ma guda ɗaya ce da aba a san inda wani daga cikin danginta yake ba, tun daga kan dangin uwa kama zuwa dangin uba.

Tana ta zancen zuci ta nufi makarantar ta shiga aji lokacin har an fara ɗorin karatun hadisi, kusa da aawarta Salama ta zauna ta fito da nata littafin suka ci gaba da sauraron malam.

A can gida kuwa Jidda tana fita Umma ta taɓe baki ta ce

"Wahalalliya ce wannan yarinyar in banda rashin aikin yi islamiya dai tun ana yara ake abu ɗaya, yanzu an zama ƴanmata har ana shirin shiga ɗakin miji amma ba za a haƙura ba" Aliya ta yi wata dariyar rainin wayo ta ce

"Umma sai faɗi kike wai za a shiga ɗakin miji to in dai ba ita kaɗai za a saka a ɗakin ba waye zai kashi wanann?"

Umma ta ce

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull