Kenza eBookz

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 4

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 4

Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 4: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 4. Lokacin da suka tashi ƙarfe biyu na rana ne, lokacin…

3,363 words

Lokacin da suka tashi ƙarfe biyu na rana ne, lokacin rana ta take, dakyar suka samu napep ɗin, sai dai kuɗin da ya yanka musu na Jidda naira hamsin bata cika ba hakan ya sa ta nemi alfarmar ya rage mata amma ya ce ba zai rage ba saboda shi ma ba ruwa yake zubawa a napep ɗin ba mai yake zubawa, suka tsaya a kan cewa idan an kusa zuwa za ta sauka haka ta amince. A daidai wani gidan mai ya sauke Jidda saboda har rance ta ce Aliya ta bata amma ta ƙi bata kuma akwai kuɗin a wajen Aliyar. Tana ji tana gani haka ta sauka da ranar nan ga yunwa da suka kwaso.

Aliya har da wani taɓe baki ta yi da sakin murmushin mugunta, dama da a tafiya ne sai ta ranta mata ko don saboda ta bata amsar exam tun da idan basu tafi tare ba sun zauna a kujera ɗaya ba sai dai ta bayar da takardar a haka ba tare da ta rubuta komai ba, kasancewar banda dusa babu komai a kan nata hasali ma bata karatun shiririta kawai take a makarantar da biyewa ƙawaye ƴan ƙarya, ita kuma Jidda karatun take yi gata da ƙoƙari kanta yana ja sosai da sosai saboda tana da mayat da hankali.

Tafiya take har ta ƙaraso wajen kamfanin simintin nan nasu Ibrahim, tana tafiya sai gumi ne kwance a fuskarta kasancewar ranar da ta take, Ibrahim wanda tun zuwansu da direban ya ce direban ya tafi da motar gida, saboda da Daddy za su tafi gida, ƙarfe biyu da rabi suka tashi Daddy da Ibrahim ne a baya sai direba yana jan su, mai gadin ƙofar kamfanin ya buɗe musu get suka fito, Ibrahim wanda tun bayan zuwansa kamfanin yake ta tunanin Jidda duk da bai san sunanta ba amma tabbas ya yaba da hankali da tunaninsa yarinyar ta birge shi sosai.

Suna fitowa kamar an ce ya ɗago fuskarsa sai kawai ya sauke a kan Jidda wacce take tafiya cikin natsuwa kanta a ƙasa, gabaɗaya ya mayar da kallonsa kwacakom kanta, yana ganin yadda hijabin ya mata kyau, shi dama yana son ya ga mace tana suturta jikinta, tambayar zuciyarsa ya fara yi yana cewa

'Ko ina fitsararriyar ƙawar nan tata, wacce bata san darajar ɗan adam ba, wannan ko kaɗan baku dace da zama ƙawaye ba, ana cewa sai hali ya zo ɗaya ake ƙawance amma dai ku kun sha bam-bam a halayya' Ya faɗa yana bin bayanta da kallon don lokacin ta gifta, ta kama hanyar gidan da ya ga ta shiga lokacin da ta tafi da safe, kuma yana ji a jikinsa inda ya ga ta shiga da safen nan ne gidansu, ko yanzu ya so a ce babu Daddy da sai ya tambaye ta ko da sunanta ne.

Direba yana ɗan waige-waige domin zai haura hancin motar saman titi, a daidai nan Daddy ya lura da Ibrahim ya juya bayansa yana kallon waje daga cikin motar, a nutse Daddy ya ce

"Mu'azzam" Amma da yake ya yi nisa bai san Daddy ya kira shi ba, duk da suna zaune a kusa da juna, sai da Daddy ya maimaita ya ce

"Mu'azzam" Ya faɗa yana ɗan taɓa shi, sannan ne Ibrahim ya juyo da sauri yana ɗan murmushi ya ce

"Na'am Daddy" Daddy da ɗan mamaki a fuskarsa ya mayar da hankalin wajen da Ibrahim ɗin yake kallo a ƙoƙarinsa na ganin ya hangi abin da ya ɗaukewa tilon ɗan nasa hankali. Sai dai iya ganinsa bai ga kowa ba, saboda wajen akwai mutane kowa yana dabgar gabansa sannna ita wacce Ibrahim ɗin yake kallo wato Jidda ta riga ta miƙe ta yi ɗan nisan da Daddy ba zai fahimci ita Ibrahim yake kallo ba, kuma ko da a ce ya hango ta ba lallai ya kawo cewa ita ɗan nasa yake kallo ba kasancewar ba halayyar Ibrahim ɗin ba ce kallon mata don su a halin da ake ciki ma yanzu burin su bai wuce ya fitar da mata su masa aure ba, amma ya ƙi sai ya ce wai akwai lokaci!.

Daddy kallonsa ya mayar kan Ibrahim lokacin har sun haura kan titi direba ya ɗau hanya ya ce

"Mu"'azzam mene ne ya ɗauke maka hankali har ya hana ka jin kirana?" Murmushi Ibrahim ɗin ya yi ya ce

"Kawai dai ina kallon jama'a ne Daddy" Ya faɗa saboda ba ya son ya faɗawa Daddy cewa mace yake kallo ya san idan ya faɗa masa gaskiyar abin da yake kallon shikenan kuma yau haka za su wuni suna tsokanarsa shi da Mummy.

Ɗan zantawa suka shiga yi a tsakaninsu irin na ɗa da uba.

A ɓangaren Jidda kuwa lokacin da ta isa gida ta tarar Aliya da Umma suna zaune a baranda a tabarma suna hira, Aliyar tana cin abinci, babu wanda ya amsa sallamar da ta yi sai ma wani kallon tsana da ƙasƙanci da Ummar take bin ta da shi.

Ɗaki ta nufa ta ajoye jakar hannun ta, ta cire hijabin ta fito ta ɗauki ruwa a buta ta shiga banɗaki, ruwa ta kama ta fito dama fashin sallah take shi ya sa bata ma yi sallah a makaranta ba. Sai da ta zo saitin su Umma ta ce

"Umma ina abincina?" Kallon sheƙeƙe Umma ta mata ta ce

"Wanda kika kawo na ajiye miki?" Ta faɗa tana kallon Jidda da take wasa da yatsun hannun ta.

Jin bata amsa mata ba ta ce

"Na ce wanda kika kawo min in dafa miki?" Kai ta girgiza, sai Ummar ta ce

"Tun da kin san baki kawo ba kar ki tambayeni"

Aliya jin ta ƙoshi sai ta ajiye cokalin ta ture plate ɗin gabanta ta saki wata gyatsa, haɗe da komawa ta kwata tare da ɗora kanta a kan cinyar Umma tana mai cewa

"Wash Allah na ƙoshi kuma na gaji"

Umma ta ce

"To ba sai ki huta ba, dama an je ana taa gwagwarmayar jarabawa, Allah dai ya baki sa'a"

Aliya ta ce " Amin Ummana, ai daɗin mai uwa a gaban murhu sai ya ci ya ƙoshi"

Jidda jin wannan furucin ya sa ta tuna da tata mahaifiyar hakan ya sa ta ji ƙwalla ta taru a idanunta yanzu shekara goma sha ɗaya kenan da ƙada ta rufe idanunta idan ta tuna lokacin mahaifyarta tana raye duk abin da ta ci sai ta ajiye mata, ko da bata nan haka za ta ajiye mata wani lokacin ma ita ta haƙura ta ajiye mata, amma yanzu mutuwa mai rabawa ta raba su, mutuwa mai yankan ƙauna ta raba tsakani.

Ɗaki ta nufa ta je ta hau kan ƙaramar katifar ta, kwantawa ta yi rubda ciki ta ɗora kanta a kan filo, idanu ta lumshe tana jin yadda yunwa takr addabar ƴaƴan hanjin ta, wanka ma take son yi amma kuma yunwa ba za ta barta ba.

Idanu ta rufe wasu zafafan hawaye suna gangarowa, tana jin tamkar yau ne ta rasa mahaifanta, tana jin kewarsu a zuciya da ruhinta, abubuwan da suke faruwa bayan mutuwarsu masu ɗaure kai da kuma al'ajabi su ne suke saka take ta tunanin shin dama haka rayuwa take?.

Juyi ta yi sai kuma ta ji Umma tana ƙwala mata kira, da sauri ta tashi zaune tana goge idanun ta, sai da ta tabbatar cewa babu hawayen sannan ta fito ta ce

"Gani Umma"

Umma ta ce

"Gashi nan sai ki ɗauka, wato kin je ɗakin kin ƙule sai ya dawo ya zaci wani abun aka miki ya ishe mutane da tambaya" Ta faɗa tana turo mata plate ɗin da Aliya ta ci abinci ta rage, kaɗan aka ƙara abincin a kan sauran Aliyar, ba tare da ta ce uffan ba ta ɗauka ta juya tana dab da shiga ɗaki Aliya ta ce

"Eh mana kya ɗauki ki tafi ai ko godiya babu, tun da ga baiwar ki da kika ajiye ta girka miki ta dafa ta baki" Juyowa Jiddan ta yi ta ce

"Na gode Umma Allah ya saka fa alkairi" Ta faɗa jin Ummar bata amsa ba kuma dama ta san hakan ba mai yiwuwa ba ne, sai ta juya ta shige ɗakin.

Tas ta cinye abincin duk da bai wani ishe ta ba, amma dai ta ji yanzu ta dawo dai-dai shiru ta yi tana tunanin mai ya sa Umma ta sauya, mai ya sa a da can baya lokacin iyayenra suna raye bata nuna ta tsane ta ba sai yanzu? Mai ya sa a da take nuna mata ƙauna daga ita har Aliya amma yanzu tamkar basu taɓa son ta ba ma. Ta jima tana saƙa da warwarar kafin ta fito da kwanon lokacin ana kiran sallar la'asar banɗaki ta shiga ta yi wanka ta fito Umma ta kalle ta ta ce

"Haka kawai kike yi wa mutane wasan ruwa da sabulu, abin da duk wankan da za ki yi ba sauyawa ,a ki yi ba kina nan a baƙar ki" Bata ce komai ba ta shige ɗakin.

Bayan ta saka wani kayan ta ɗakko kayan ta da ta ɗora a kan ƙofa da safe ta haɗa da wanda ta je makaranta da shi ta wanke ta shanya. Ganin rana ta yi sanyi ta sharo ɗakin nasu duk da babu datti, tsakar gidan ta fito ta share tas ta kwashe. Kayan wanke-wanke ta haɗa ta wanke, bata gama gyaran gidan ba sai da la,asar lis.

Butoci ta ciccika ta ajiye, lokacin Aliya suna ɗaki ita da ƙawarta Amatullahi.

Tahowa ta yi za ta kai kwando kicin cikin rashin sani ta bige Umma da ta fito daga kicin, a ƙufule Umma ta ɗaga hannu za ta wanke fuskar Jidda da mari, a daidai nan Abba ya shigo da sallama, turus ya yi yana kallon Umma...

MAMAN AFRAH

09925576222

*🩺 GHT HERBAL SOLUTIONS 🩺*

*Maganin da ke dawo da lafiya, da izinin Allah!*

Muna sayar da ingantattun magunguna na zamani da aka gwada kuma suka shaida aiki.

*Duk wannan cutar ana warke wa sosai mutum ya dawo nml*

*Ga wasu daga cikin cututtuka da muke da magani a kai:*

✅ Ulcer

✅ Hawan jini

✅ Ciwon zuciya

✅ Ciwon Suga (Diabetes)

✅ Ciwon daji

✅ Ciwon koda & hanta

✅ Zazzabi mai tsanani

✅ Ciwon gabobi & ciwon jiki

✅ Ciwon ido & kunne

✅ Asma, tarin fuka & mura

✅ HIV

✅ Matsalar rashin haihuwa

✅Gyaran data

✅Na kurajen fuska

✅Na rage kiban

✅Na Saka kiba

✅Na infection

🟢 Da sauran su...

*Me ya bambanta GHT?*

🌿 Magungunan mu halal ne kuma an tsaftace su.

🔬 Sun wuce binciken lafiya da gwaji.

🌟 Suna da matukar tasiri – an samu sauki ga dama-dama.

🧕🏽 Muna kula da sirrin marasa lafiya.

🚚 Muna da isar da magani kai tsaye (Delivery available).

*Kira yanzu ko shiga group ɗinmu don karin bayani da order:*

📞 [08161316781]

*GHT — Magani cikin Sauki da Aminci*

*“Lafiyar ku shine babban burinmu”*

[10/11, 9:47 PM] MOM MASHKR & AFRAH: https://chat.whatsapp.com/B6ZgynXRCc3LWNggTkzg7X

*RUWA CIKIN COKALI*

(Ya ishi mai hankali wanka)

NA

MAMAN AFRAH

. *Daga marubuciyar*

*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*

*09025576222*

BOOK 1

PAGE 5️⃣

*ZALIKA*

Zaune suke a ƙaton falon da ya gaji da haɗuwa, hira suke sama-sama kowanne yana danna wayarsa. Mubin ne ya jingina da jikin kujera yana ajiye wayarsa a kusa da shi ya kalli Zalika ya ce

"Ina son magana da Baffa amma wallahi tsoro nake" Baki Zalika ta taɓe da kamar ba za ta yi magana ba sai kuma ta ce

"Maganar mai? Kaima da ka shafawa kanka lpia da wannan tunanin ka san dai ko ma wace magana ce Baffa ba saurarenka zai yi ba gwara ma ka faɗawa Mamy, don ni yanzu na cire faɗawa Baffa abu ma saboda ba saurarena zai yi ba" Ta faɗa tana maida hankalin ta kan waya.

Ajiyar zuciya ya sauke ya ce

"Ni ba wata magana nake so mu yi ba kawai dai ina so mu zauna mu tattauna, ina nufin mu yi hira irin na ɗa da uba" Ya faɗa idanunsa suna yin jawur tamkar zai yi kuka hatta a muryarsa raunin hakan ya bayyana.

Zalika ta ce

"Uhum in ji mai ciwon haƙori, ni wallahi har mantawa ma nake da Baffa idan magana ko damuwa ta same ni, kuma ko da na ji shauƙin son magana da shi a matsayinsa na mahaifina ina kawar da hakan domin na san abu ne mai wahala, shi ya nuna ba ya buƙata to mu ma mai zai hana mu danne zuciyarmu?" Iska Mubin ya fesar haɗe da sakin ajiyar zuciya ya ce

"Ni wallahi ina kasa jurewa wani lokacin, abin yana birgeni kuma yana bani sha'awa idan na je gidan abokaina na gansu suna hira ana raha da mahaifinsu amma mu mun mallaki komai na rayuwa amma mahaifinsu bashi da lokacinmu, sannan ba wai ayyukan ne suka masa yawan da ba zai sauraremu ba, shi fa tun asali ma haka yake babu ruwansa da lamarin ƴaƴansa, sai dai Mamy ta maye mana gurbin mahaifi da mahaifiya" Mubin ya faɗa cike da damuwa.

Mamy da take laɓe tana jin su duk sai jikinta ya yi sanyi, tabbas ta san kowane ɗa yana da burin mahaifinsa ya tattuna da shi ya ji damuwoyinsa, amma su basu san daɗin mahaifinsu ba gashi dai yana raye amma sun zama marayu ta ɓangarensa, ita kanta ba ya zama da ita, ƴaƴansu sai ita za ta kula da su, kama daga tarbiyarsu da zama da su ta ji abin da yake damunsu ko shawara fa sauransu.

Shi abin da ya ɗauka guda ɗaya shi ne idan ya ajiye kayan abinci da kuɗi to ya gam da fannin iyali, ya ɗaura ragamar tarbiya da komai a wuyan mahaifiyarsu a cewarsa shi uba ɗaukan nauyin gidan ne kawai ya rataya a wuyansa, ita kuma uwa ita ce za ta basu tarbiya, bai san cewa tarbiya ba ta mutum ɗaya ba ce, tarbiya ta uwa da uba ce duka, ba zai yiwu a ce uwa kaɗai ta ɗauki wannan ragamar ba, don tarbiya ta kowa ce.

A hankali ta fara takowa daga inda take dama a ɗan koridon bedroom ɗinta na ƙasa ta tsaya take jin hirarsu da take dakar mata zuciya. Tana tahowa tana ƙarewa falon kallo yadda aka kashe dukiya a gidan amma kuma an samu naƙasu a wajen gudanar da zaman gidan, ta rasa mijin ta wane irin mutum ne shi kaifi ɗaya da ba ya sauyawa daga kan aƙidarsa.

Tana zuwa cikin falon ta buɗe baki cike da kulawa, fuskarta washe kamar gonar auduga ta yi sallama cike da kulawa da nuna soyayya da ƙauna ga yaran nata, Zalika ce ta amsa ita ma tana murmushi saɓanin Mubin da ya sadda kai bai amsa sallamar ba kuma bai kalli Mamy ba. Duk da Mamy ta ji babu daɗi a ranta na ganin yanayinsa kuma ta san damuwarsa domin ta ji abin da suke tattaunawa, ko da a ce bata ji ba to dama ta san damuwar ƴaƴan nata tun da basu da wata matsala a rayuwa sai ta mahaifinsu, matsala ce wacce tun asali aka tashi da ita kuma ta yi ƙoƙarin kawo gyara da maslaha amma abin ya ci tura!.

Idanunta ne suka nemi fitar da ruwa, amma ganin Zalika ta mayar da hankalinta kwacakom kanta sai ta yi ƙoƙarin dannewa, faɗaɗa fara,arta ta yi ta ƙaraso falon ta zauna tana mai cewa

"To ko dai falon iya ƴan uwa ake buƙata a ciki ni na zo na kawo kaina" Ta faɗa cike da wasa rana son kawar da damuwar da ta gani shimfiɗe a fuskar Mubin, amma har lokacin bai ɗago ba kuma bai yi magana ba. Zalika ce ta ce

"Kai Mamy har ma da wani hirar ƴan uwa da za a ce uwa ba za ta zo ta ji ba, bayan ke kaɗai ce ginshinƙin mu ke kike kulamu ke kike ɗauke duk wani nauyin da zukatanmu suka yi" Ta faɗa tana kallon fuskar mahaifiyar tata.

Mamy ta gane mai qannan kalaman na Zalika suke nufi amma kuma bata son ta ɗora ƴaƴanta a ragamar da za su cigaba da ganin laifin mahaifinsu duk da ta san yanzu sun yi wayo sun fahimci komai game da halayyar mahaifinsu, duk da a baya ma tun suna yara suna iya ganewa domin suna tamabayarta bare kuma yanzu da suka mallaki hankalin kansu.

Cikin zolaya ta sake cewa

"To ai na ga ɗan uwanki ko ɗaguwa bai yi ya kalleni ba, ba dole na ce ko zancen da ya shafi ƴan uwa kuke yi ba" Ta ce tana kallon Mubin.

Mubin wanda rauninsa ne yake son bayyana kamar ba namiji ba abin da ya sa ya ƙu ɗago fuskarsa ba ya so Mamy ta ga yana cikin damuwa kuma ya san damuwarsu damuwarta ce ko kaɗan bata sukuni a duk lokacin da ɗayansu ba ya cikin walawal, sannan abu ɗaya ne ya hana shi yin magana shi ne va ya son muryarsa ta fallasa abin da yake cikin zuciyarsa.

Mamy da take kallonsa cikin sanyin murya ta ce

"Mubin ɗina" Zuciyarsa ce ya ji ta ƙara karaya ya fara tunanin cewa wannan kalmar tana faranta masa rai fite da tunanin mai tunani, sai dai tabbas daga ɓangare ɗaya yake jinta wato ɓangaren mahaifiyarsa, zai so a ce ya ji daga mahaifinsa ma amma ina tun da yake bai taɓa ganin wani sassauci ko kulawa da soyayya daga mahaifi ba. Idan ya ga abokansa suna yabon mahaifinsu a status ko dun ɗora hoton mahaisin suna my hero, farin cikinmu Allah ja da kwana mahaifinmu, wasu suke faɗin mahaifina abokina, wata ta ɗora bani da aboki ko abokin shawara sai mahaifina. Waɗannan kalaman suna sosa masa zuciya abu ne da bai samu ba abu ne da yake ganin mahaifinsa ya tauye musu jin daɗi da kulawa.

Mamy a karo na biyu ta ce

"Mubina ɗina taurarona" Bai san lokacin da ya ɗago kansa ba ya zubawa mahaifiyarsa jajayen idanunsa tamkar ranar ya fara arba da fuskarta, kallonsa suke daga ita har Zalika, idanunsa jajawur fuskarsa cike da damuwa ƙarara, a gefe ɗaya idanunsa suna kwararar da wasu hawaye. Yana ɗagowa sai ya buɗe bakinsa dakyar ya haɗa laɓɓansa ya ce

"Mai ya sa sai mu? Mai ya sa daga ni sai ƙanwata ne muka rasa wannan damar Mamy? Mai ya sa mahaifinmu babu ruwansa da bamu kulawa Mamy, kullum fuskarsa a ɗaure, bama ganin dariyarsa tamkar ba a taɓa halitta tausayinmu a zuciyarsa ba" Zalika ita ma da Mubin ya sosa zuciyarta domin ita ma ƙarfin hali kawai take yi, kalamansa sun tada mata mikin da ke cikin zuciyarta a take nata idanun suka shiga tara ƙwalla, domin ta san a rayuwa babu mai gane damuwarka sai wanda yake cikin irin halin da kake ciki, ma'ana yanzu da take jin kalaman Yayanta da kuma ganin ruwan hawayensa suna kwaranya sai ta ji duk duniya babu wanda zai fahimci damuwarsa sama da ita domin ita ma tana damuwa makamanciyar tasa.

Mamy kuma idanunta ta ɗauke daga kallon Mubin ba tate da ta furta ko uffan ba, ba tare da ta bashi amsa ko da ɗaya ba ce daga cikintambayoyin da ya jero mata ba, amma har ga Allah ji take tamkar ta rushe da kuka ko ta samu sauƙi da salama a zuciyarta a kan halin da take ganin ƴaƴanta a ciki, saboda ta san ita kaɗai ba za ta basu kulawar ɓangare biyu ba ko da ta yi ƙoƙarin hakan su dole zuciyarsu za take wasi-wasi a kan lamuran cikin gidan nasu wanda mahaifin nasu ne sila.

Danna zuciyarta ta yi domin a matsayinta na mahaifiya a gare su babu buƙatar ta nuna rauninta a wannan waje domin damuwar za ta musu illa, hakan ya sa ta ɗago ta yi murmushin yaƙe wanda ya fi kuka ciwo ta ce

"Kowane ɗan adam yana da jarawarsa a rayuwa, sai dai idan ya jure watarana komai zai zama labari, komai zai zama tarihi tamkar ba a taɓa yi ba" Ta faɗa yana ruƙo hannun Mubin ta dawo da shi kusa da ita ya zamana suna zaune a tare Mamy a tsakiya su kuma kowa yana gefenta hannuwanta ta sanya ta dafo kafaɗunsu ta ce

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull