Kenza eBookz

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 3

Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 3

Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 3: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 3. Burin iyayensa yanzu su ga ya yi aure domin su ga sun…

3,359 words

Burin iyayensa yanzu su ga ya yi aure domin su ga sun samu jika, kasancewar shi kaɗai Allah ya basu. Sai da ya gama shiryawa tsaf ya saka fararen wando da riga sai dai rigar tana da dogon hannu, kayan sun yi matuƙar amsar jikinsa ya ƙara komawa gaban madubi ya taje gashin ya kwantar da shi da brush kumb. Turaruka ya sake fesawa kafin ya ɗakko wayoyinsa da jakarsa da zai tafi kamfani kasancewar Daddy ya ce za su fita da wuri akwai baƙi da za su yi yau, za a tattauna a kan wasu kayan.

Wayarsa ya duba sai ya ga ƙarfe tara hakan ya bashi tabbacin ya sha baccin bayan komawarsa da gari ya waye, ganin miss call ɗin Daddy a ransa ya ce

"To fa! Daddy ina ga ya fita ma ya barni" Ya faɗa yana ɗakko takalminsa a wajen takalma ya saka ya shiga sakkowa daga matakalar benen, a hankali cikin hutsuwa, Ibrahim mutum ne nutsatstse kuma yana da ibada.

Yana baro part ɗinsa direct part ɗin Daddy ya nufa, sai dai ya samu babu kowa sai ƙaran AC da tv a falon, fitowa ya yi ya nufi part ɗin Mummy da sallama ya tura ƙofar falon, sai dai babu kowa sai mai aiki tana goge -goge, cike da girmamawa ta shiga gaishe da shi ya amsa ko kallon inda take bai yi ba amma dai a muryarsa da ta saurara babu wulaƙanci kuma kowa ya san shi ko a bayan idanunsa suna yabonsa domin ya san daraja da muhimmancin ɗan adam.

Sai da ya je tsakiyar tangamemen falon ya zauna a kujera mai zaman mutum biyu ya ce

"Ina Mummynah" Dakatawa ta yi da goge -goge ta ce

"Yanzu ta haura sama"

Iska ya hurar daga bakinsa ya ce

"Ki mata magana bana son haurawa saman" A ladabce ta amsa masa tana tahowa za ta yi w Hajiya Faty magana, ganin yana danna waya ta saci kallonsa a ranta tana kissima cewa tabbas duk macen da ta samu Ibrahim a matsayin miji haƙiƙa ta dace.

Kusan tare suka sakko da Hajiyar lokacin yana waya da Daddy Mummy ta ƙaraso ta zauna a kusa da shi, har ya gama wayar ya kashe yana kallonta da murmushi a saman fuskarsa ya ce

"Ina kwana Mummy nah" Dariya ta yi tana masa kallo mai cike da ƙauna irin ta uwa da ɗa ta ce

"Ka manta da asuba ma da kuka dawo daga masallaci ka gaishe da ni?" Ta faɗa tana dariya mai bayyana haƙora.

Shi ma murmushin ya yi ya ce

"To Mummy ko sau nawa ɗa ya gaishe da mahaifiyarsa ai ba wani abu ba ne" Kai ta gyaɗa masa ta ce

"Mai za ka ci?"

Fuska ya shagwaɓe ya ce

"Ni ba na jin yunwa, tun da kuka rigani karyawa"

Mummy ta ce

"To Mu'azzam rigimamme, ai kai tun da sarkin bacci ne waye zai jira ka yunwa ta masa lahani, Daddyn ka ma da ya ce za ku fita gajiya ya yi da maka waya ya ce in ka tashi ka bi shi"

Yana ɗan yatsina fuska ya ce

"Yanzu na kira shi ya ce yana kamfanin siminti kin san baƙin nan da za a yi magana da su ba ƙaramin kaya za su saya ba"

Haka suka ci gaba da tattaunawa ta zubo masa abincin ya zauna a kafet ya ci ba wani da yawa ba, dama dankali ne da wainar ƙwai sai shayi da ya sha shi ma kaɗan. Bayan ya gama ya mata sallama ta masa addu'a ya fito riƙe da jakar da wayoyinsa, ya samu an wanke gabaɗaya motocjn da suke wajen an goge sai sheƙi suke, direba da sauri ya matso ya karɓi jakar ya saka a baya yana gaishe da shi da girmamawa ya amsa, da kansa ya buɗe bayan ya shiga ya zauna direban ya rufe masa marfin ya shiga ya tada motar mai gadi ya wangale musu tangamemen get ɗin suka fita yana ɗaga musu hannu ya mayar da ƙofar ya rufe.

Sun haura titi suna tafiya sai karatun qur'ani da yake tashi a ciki, wanda duk direbobin sun sani idan Ibrahim ne a mota ba a kunna masa waƙa. Sun kusa ƙarasawa kamfanin inda direban ya gangara gefen titi kasancewar ba a farko bakin titi kamfanin yake ba sai an gangara.

Gangarawar da direban ya yi ya fara tafiya kaɗan akwai akwai wani wuri da ruwa ya ɗan taru da yake wajen daga gefen car wash ne da alama ruwan wajen ne ya ɗan gangaro, wasu ƴanmata guda biyu sun taho ɗaya tana ɗagawa wani napep hannu, direban cikin rashin sani tayar ta shiga cikin ruwan, sai ruwan nan ya fantsala bai yi masauki a ko ina ba sai a jikin ƴanmatan nan guda biyu, farar ita kawai ruwan ya fatsu da jikin takalmin ta ne, inda baƙar kuma gabaɗaya ruwan ya ɓata mata rigar jikin ta.

Direban ne cikin nuna rashin jin daɗin abin da ya yi ya ce

"Subhanallah" Ibrahim da yake danna waya ya ɗago shi sai lokacin ma ya ga abin da yake faruwa, amma sai ya rasa ma mai zai ce. A waje kuwa Aliya ce cike da masifa ta danƙaro wani ashar mai gunna ta yi tana kallon motar ranta yana matuƙar ɓaci ta ce

"Wannan daga gani ƴan Allah baku mu samu ne, wato karere masu cin arziƙi don babu yadda za a yi wanda ya taka arziƙi ya san darajar wannan kyakkyawar motar ya saka ta a cikin ruwan caɓali" Ta faɗa tana kama tsantsa, yayin da direban ya yi parking a gefe yana neman izinin Ibrahim a kan zai fita ya basu haƙuri. Ibrahim ne ya ce

"Sai ka kula ka ga Daddy yana kirana tun ina gida, gashi ka zi ka janyo wannan duk ta cikawa mutane kunne da hayaniya" Da to ya amsa, ita kuma Aliya kasancewar bata ganinsu da yake glass ɗin baƙi ne baka ganin wanda yake cilin motar.

Jidda wacce take kallon rigar jikinta yadda ruwan nan ya ɓata, fuska ta ɓata ba tare da ta ce komai ba tana tunanin yadda za ta koma gida ba ta sauya kaya saboda duk sun jiƙe, kuma gashi makarantar fa za su je exam za su shiga.

Direban yana fitowa tun kafin ya buɗe baki Aliya ta fara zaginsa tana cewa

"Ai dama na san sai dai direba wanda ba a gaji arziƙi ba kuma ba a san darajar kuɗi ba, shi ya sa kake zunduma wannan kyakkyawar motar a ruwa marar kyau, da a ce ma kuɗi ne za ka biyani ladan mata min takalmin da ka yi da ba haka ba, to yanzu dai na san haƙuri ka fito ka bani kuma wallahi ina so ka sani ko za ka tafi tsirara sai ka biyani diyyar ɓata min takalmi" Ta faɗa tana ɗaga jijiyoyin wuya, shi kuma direba ya dage sai bata haƙuri yake kamar zai ari baki ya ce

"Haba baiwar Allah, yanzu ki kalli ƴar uwarki ita ce aka yi wa abin da ya cancanci a bata haƙuri, kalli yadda aka ɓata mata jiki amma ke da ruwan ma kaɗan ne ya taɓa ki kike wannan abin" Jidda ganin suna hayaniya ta ce

"Kai Aliya dan Allah ki yi haƙuri mana, kin zauna kina ta ɗaga jijiyoyin wuya a kan wannan abin ƙanƙ... Hannu ta ɗagawa Jidda ta ce

"Dalla malama rufewa mutane baki, ana maganar waɗanda suka san ciwon kansu a kan haƙƙi ai ke bakya saka baki ba, ni idan ni ya ɓatawa kaya kamar yadda ya ɓata miki da tuni na sharara masa mari" Da sauri direban ya kai hannu ya dafe kumatunsa tamkar dai an mare shin.

Jidda kuma ranta ne ta ji babu daɗi jin an ce mata bata san ciwon kanta ba, kuma dama ta san za a rina wai an saci zanen mahaukaciya.

Aliya ce ta ɗaga hannu ta miƙawa mutumin a kan ya bata kuɗi, ɗari biyun da ta rage ya fito da ita ya miƙawa Jidda, yana cewa

"Baiwar Allah ki karɓa ki saya omo ki wanke kayan da na ɓara miki" Kafin ya kai kuɗin saitin Jidda Aliya ta saka hannu ta warce tana cewa

"Matsiyaci wai ɗari biyu, to na karɓe dama an ce sata a gidan ɓarawo rance ce, kuma raba arne da makami ibada ne" Ta ce tana saka kuɗin a jakar hannun ta.

Jidda ce ta buɗe baki ta ce

"Bawan Allah da baka wahalar da kanka wajen bayar da kuɗinka ba, da ka bari za su maka amfani amma ka ɗauka ka bayar, kuma ai kowane ɗan adam ajizi ne sannan yana iya yin laifi" Kai direban ya shiga gyaɗawa jin maganar hankali da hikima duk abin da ake yi Ibrahim yana kallonsu ta glass daga cikin motar.

Ya yaba da hankali da nutsuwar Jidda, sannan ya lura ta san daraja da muhimmancin ɗan adam kamar yadda shi ma ya sani.

Aliya kuwa ta wuce Jidda tana aika mata harara a inda da za ta wuce ta saka hannu ta daki bayan motar, napep take tsayarwa amma bai tsaya ba hakan ya sa ta tsallaka titin ta koma ɗaya ɓangaren, a nata tunanin ta tafi ta bar Jidda don ba za ta juri har sai ta jira ta ta koma gida ta sauya kaya ba, ba ma wannan ba ita a rayuwa ta tsani take tafiya da Jidda kasancewar Jidda baƙa kuma mummuna a zahiri Jidda bata da wani kyau, baƙa ce tana da faɗin fuska sannan tana da matsakaicin tsawo, tana da manyan idanu sai daj hancinta gajere ne kuma mai faɗi. Saɓanin Aliya da take fara tas kyakkawa ajin farko, tana da tsayi sannan tana da doguwar fuska dogon hanci wanda ake yi wa laƙabi da kamar biro duk wani abu da ya danganci kyau Aliya tana da shi wannan dalilin ne ma ya sa take ganin ta ciri tutar da sai ta zaɓi miji ta darje, miji ma na nunawa sa'a mai hannu da shuni wanda take ganin ko da ɓarawo ne in dai yana da kuɗi kuma yana da kyau to fa ta ga mijin aure don shi ne zaɓi kuma burinta.

Tana daga can inda ta tsallaka tana hango direban nan da yake ta faman ba Jidda haƙuri kafin ya juya zai je ya shiga mota, ita ma Jiddan tana ta ƙoƙarin tafiya Aliya a zuciyar ta ta ce

'Hmmm! Ka ji da shi cuwon ajali a ɗan yatsa, tun da dai ka gama jiƙa mutane ai sai ka san inda dare ya maka, baka san cewa wannan baƙar mummunar da ita da bola mu duk ɗaya muke ganinsu ba, ni ma nan da ka ganni ƙaddara ta haɗani tafiya da ita, saboda kan nan nawa dusa ce ko in ce fanko ne babu komai a ciki, ko bihim ban sani ba wamda zan rubuta a exam ɗin da za mu yi, shi ya sa ma nake so mu tafi tare da ita tana rubutawa ina copy, dama ita take goyani a kowacce exam' Ta faɗa tana ɗan taɓe baki, tare da duba agogon da yake hannun ta.

Ibrahim kuwa da sauri ya saka hannu ya buɗe ƙofar ya fito lokacin Jidda ta fara tafiya, yana zuro ƙafafunsa farare tas da suke cikin baƙin takalmi mai yatsa, Aliya tun daga tsallaken titin da take ta hangi an buɗe bayan haɗaɗɗiyar motar wannan wacce ta gama yi wa direban motar ɗiban albarka, mamaki haɗe da al'ajabi suka haɗe suka cunkushe kwanyarta, wani irin bugawa ƙirjinta ya yi da ƙarfi lokaci guda zuciyarta ta aiko mata da wani saƙon tambaya kamar haka

'Dama akwai wani a cikin motar ba direban ba ne kaɗai, kenan mamallakin motar ne wannan ya fito?' Ta tambaya kwata-kwata ta gagara ƙifta idanunta don gani take idan ta ƙifta tamkar wanda take hangowar ɓacewa zai yi.

Ibrahim kuwa lokacin da ya fito Jidda ta masa ɗan nisa, domin ta saka gabata can tana ta zabga sauri, sannan shi bai ma san sunanta ba abu ɗaya kawai ya sani shi ne saboda ita ya fito daga motar. Direban ne ya buɗe ya fito, cikin hanzari ya gewayo inda Ibrahim ɗin yake cike da girmamawa ya ce

"Yallaɓai kana buƙatar wani abu ne?" Ɗan shiru ya yi kafin daga bisani ya ce

"Kawai na ga baka kyautawa yarinyar can ba ne, kuma na ga ita ko uffan bata ce maka ba" Cike da alhini direban ya ce

"Wallahi yallaɓai ta san darajar mutane, duk da na yi abin ne cikin rashin sani kuma dama ɗan adama ajizi ne amma sai na ji ko kaɗan ban kyauta mata ba" Iska ya huro daga bakinsa yana sanya haƙorin gaba na cilin bakinsa ya dantse leɓansa na ƙasa, idanu ya mayar hanyar da Jiddar ta yi yana iya hango gidan da ta shiga daga can gefe wasu gidaje da suke a jere, sai ya ɗan jujjuya kamar mai neman wani abu, sai kuma ya kama ƙofar zai shige motar.

Aliya kuwa da take jin duk kan motsinsa tamkar da bugun zuciyarta yake, hakan ya sa ta fara tunanin ita yake nema, bata yi ƙasa a gwiwa ba ta fara ƙoƙarin tsallakowa, garin sauri har wata mota ta kusa kashe mata ƙafafu, amma hankalin ta ya yi gaba, tana fatan wannan mai kuɗin ya zamana cikar burinta da kuma mafarkinta da na mahaifiyarta, don yanzu ne take ganin za ta cika burin kyawun da Allah ya bata.

Garin sauri har harɗewa take, sai gata ta ƙaraso wajen a 360, Ibrahim ya ja ƙofar yana shirin rufewa don direban tuni ya shige mazaunin direba, kawai sai ya ga mace kamar an jefo ta, tana zuwa ta kama hannun ƙofar motar ta ce

"Gani" Cike da mamaki yake bin ta da kallon rashin fahimta, kunnuwansa suna dawo masa da sautin furucin da ta yi ɗazu tun daga kan ashar da kuma cin mutuncin da ta yi wa direbansa, cike da takaici ya ce

"Wa yake neman ki?" Inda-inda ta fara jin tambayar da ya mata, rai ya haɗe ya ce

"Dalla matsa zan rufe mota" Da baya ta ja tana jin ƙamshin turarensa na masu aji, ya kaure ko ina na mashaƙar numfashin ta, ba ma wannan ba tsananin kyau da farin da yake da shi gashi kuma a gefe ɗaya ɗan gayu ne wannan ne abin da ya damfaru a zuciyarta, tana jin inama wannan ya zama mallakin ta tabbas da ta huta, babu ita babu kukan muni ko talaucin miji, don ta raɗawa zuciyarta wannan shi ne mijon da ake kan yayi, kuma shi ne wanda za a yi ta yayi har abada!.

MAMAN AFRAH

09025576222

[10/11, 9:47 PM] MOM MASHKR & AFRAH: https://chat.whatsapp.com/B6ZgynXRCc3LWNggTkzg7X

*RUWA CIKIN COKALI*

(Ya ishi mai hankali wanka)

NA

MAMAN AFRAH

. *Daga marubuciyar*

*Ci* *ma zaune, malamin* *bogi, ƙazamin* *miji* *Bonono, ruɓaɓɓiyar igiya, ƴan adaidaita sahu, ƙara'in inna delu, jalli* *joga, Beelal, ƴar zaman wanka, ungozoma* *da* *sauransu*

*09025576222*

BOOK 1

PAGE4️⃣

IBRAHIM

Yana gama rufe ƙofar ya ba direban umarnin su tafi, jan motar direban ya yi suka ƙarasa ƙofar tafkeken get ɗin kamfanin yana zuwa ya danna horn aka buɗe musu, ya cilla hancin motar cikin get ɗin.

Aliya da take tsaye a wajen kamar an dasa ta, idanunta ƙurrr a kan motar da take sheƙi tana ɗaukan idon sabunta, har suka shiga bata ɗauke idanunta ba, sai da ta ga an rufo get ɗin sannan ne ta dawo hayyacin ta, wata nannauyar ajiyar zuciya ta sauke, tana rayawa a zuciyarta cewa tabbas idan da rai da rabo ta ci alwashin mallakar wannan kyakkyawar halittar inda kuma take ganin za ta huta domin muddin ta auri wannan ta yi ban kwana da wata kalma wai wahala ko rashin kuɗi. Idanu ta lunshe tana hango kyakkyawan farin hannunsa mai ɗaure da tsadadden agogo a idon zuciyarta, tana iya hango yadda kwantaccen gashin hannun yake a jikin hannun yanayin fatarsa kaɗai tamkar wanda ba a Nigeri'a yake rayuwa ba, bata san lokacin da wani murmushi ya suɓuce mata ba don har ta fara hango irin soyayya da kulawar da za ta samu idan suka mallaki juna a matsayin ma'aurata.

Jidda kuwa lokacin da ta ƙarasa gida da sallama ta shiga, amma maimakon Umma ta amsa mata sai ta mata banza, sai da ta yi sau uku amma Umma ko ɗagowa bata yi ta kalle ta ba, bare ta saka ran za ta amsa mata, hakan ya sa cikin sanyin jiki ta shiga gidan tare da nufar ɗakin nasu don ta sauya kayan ta san matuƙar ta tsaya jiran sai Umma ta amsa mata sallama to har rana ta faɗa bata samu hakan ba. Gashi kuma tana son ta je kar a shiga jarabawa.

Tana shiga ɗakin ta nufi wajen jakar kayanta, dakyar ta ɗakko wata doguwar rigar atamfa roba ta saka duk atamfar ta koɗe, amma a haka ta saka saboda duk kayan nata idan Abba ya ɗinka musu Umma take ƙwace nata ta bayar sai ta sayi mai araha ta bata wani lokacin ma sai ta hanata mai arahar, shi kuma Abba da yake ba a gidan yake wuni ba kullum yana kasuwa ba sanin mai yake faruwa yake yi ba. Hijabi ta ɗauka ta saka shi ma duk ya ɗan yi fari, kayan ta mayar ta rataya a saman ƙofa a cewarta idan ta dawo daga makaranta sai ta wanke tun da yau jarabawa biyu za su yi.

Fitowa ta yi da jakarta a hannu, ganin Umma tana zuba ruwa a buta, ta ce

"Sai mun dawo Umma" Wata uwar harara Umma ta jefa mata, da ba za ta yi magana ba ma sai dai ta ce

"Ko ki dawo ko ki dawwama a can duk uwar ubansu ɗaya" Jikin Jidda sanyi ya yi hakan ya sa ta kalli Ummar kamar za ta yi kuka duk da wannan kalamai ne wanda ta saba jin su amma a koyaushe aka mata su sai ta ji su tamkar sabbi ne dal a leda aka buɗe, suna zame mata sababbi a koyaushe domin kalamai ne mararsa daɗi ƙiri-ƙiri ake nuna maka an tsane ka.

Ganin yanayin da Jidda ta shiga Umma ta ce

"To baƙa mai baƙar zuciya, kun ƙura min ido ni kar ki cinye ni kurwata kurrr, ni wallahi ban san dalilin da mutum zai ɗakko bare ya kawo cilin iyalinsa ba, ina dalili kawai a ɗakko mana annoba a kawo mana gida shekara da shekaru, ni yanzu ban ma san ranar da zamanki a gidan nan zai yanke ba, to wannan abu baƙiƙƙirin hanci kamar ƙofar gari abu babu fasali ta ko ina wane namijin ne ,ai kwasa? Tun da dai aure shi ne mafita ɗaya da za ki bar mana gida tun da babu dangin iya bare na Baba, babu inda za a kai ki ko ki raɓa mu ɗin dai mu ne ƙaryar taki, amma wallahi ba za ta saɓu ba bindiga a ruwa, dole idan kuka ƙarasa makarantar nan tun da yanzu jarabawa ta rage idan baki samu mashinshini ba ko sadaka ce ba bayar da ke ko ga ladanin masallaci ne" Umma ta faɗa tana tashi tsaye daga sunkuyon da ta yi tana zuba ruwan a buta.

Jiki sanyi ƙalau Jidda ta juya tana ɗaga ƙafa kamar an mata dabaibayi a ƙafafu, fitowa ta yi daga gidan tana ɗaga ƙafa ta kamo hanya fito da wayarta keypad ta yi daga jaka ta duba ta ga lokaci ya kusa tana fatan kar a samu goslow a hanya.

Hango Aliya tsaye idanu a rufe ya bata mamaki, tana ƙarasowa ta ce

"Aliya lafiyarki kuwa?" Da sauri Aliya da idanunta suke rufe babu abin da take hangowa sai gasu nan sun yi aure da wannan kyakkyawan matashin tana cikin daula tana wulaƙanta ƴan aiki da kuma dangi ƴan uwa, hatta Jidda sai da ta ganta ta zo gidanta tana saka masu tsaron ƙofa su yi waje da ita wai bata santa ba.

Yatsina fuska Aliya ta yj lokacin da ta buɗe idanun, a maimakon ma ta ba Jidda amsa sai ta juya ta fara tafiya, ita Jiddar sai ta take mata baya suka ƙarasa bakin titin, napep suka tsayar suka shiga. Sa'adatu Rimi suka nufa domin a can ne suke karatun N.C.E suna shekararsu ta ƙarshe saura jarabawa biyu ma su kammala karatunsu.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull