Ruwa cikin cokali complete hausa novel - Chapter 7
Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 7: Ruwa cikin cokali complete hausa novel Chapter 7. Mai mashin ya ja mashin ɗinsa ya yi gaba, a inda…
3,375 words
Mai mashin ya ja mashin ɗinsa ya yi gaba, a inda Ibrahim ya bi bayan Abba da kallo har ya shige cikin gidan da ya ga Jidda ta shiga.
Sosai ya yaba da yanayin dattijon kuma daga gani ya san tabbas yana da dattako da tsayuwa a kan iyali.
A zuciyarsa ya ce
'Wannan ne mahaifin Jidda kenan?'Ya faɗa a zuciyarsa a fili kuma yana ta tunanin wace ce Ummar da ya ji Jidda ta ambata tana maganar za ta mata gorin aure, in dai kuwa haka ne to tabbas ba mahaifiyar Jidda ce a gidan ba, ko dai mahaifiyarta ta mutu ko kuma bata gidan sun rabu da mahaifin ta, a take ya ji wani tausayinta haɗe da zazzafan son ta ya ƙara dirar masa, sosai yake jin son ta a jiki da ɓargonsa ya yadda yake jin tozalin da idanunsa suka yi da ita yau sai ta ƙara fasa masa wani sabon son don tamkar ta motsa masa mikin da yake cikin zuciyarsa ne.
Haka ya baro unguwar ransa duk babu daɗi, gashi babu biyan buƙata sannan kuma ya yi wani mugun jin da zai hana zuciya da ruhinsa sakat. A daidai wani masallaci ya yi parking daga can gefe fitowa ya yi alwala ya yi ya bi jam'i sai da ya idar sannan ya shiga mota ya ƙarasa gida ransa duk wani iri, tabbas ya faɗa tarkon so son ma na wacce bata san yana yj ba, son da zai ringa saka shi fargaba tun da bashi da tabbacin mallakar wacce yake yi wa so ɗin.
Yana shawo kwanar gidansu ya figi motar da mugun ƙarfi, don yanzu hatta motar ma haushin ta yake ji, a yau ne ya ji ya tsani kuɗi da kuma kyawun da yake da shi, yana ta tunanin cewa da shi mummuna ne kuma talaka babu abin da zai hana shi tunkarar Jidda a yau. Sai dai ta wani ɓangaren ya ji daɗin jin furucin ta ko ba komai zai yi amfani da damarsa wajen kaɓa zuciyarta sai dai ya san abin da zai yi.
Horn yake da ƙarfi mai gadi da yake sallah bai zo ya buɗe ba, shi kuma bai fasa doka horn ɗin ba. Ya jima yana yi duk da ya san mai gadi ba zai ƙi buɗe ƙofa da gamgan ba, mai gadi ko da ya yi sallama daga sallah sai da ya karanta gabaɗaya azkar ɗin da ake yi bayan idar da sallah, sanna ya taso a nutse ya wangale ƙofar, ya ja baya Ibrahim ya shigo da motar da gudu yana yin wani parking a tsakiyar wajen. Fitowa ya yi daga motar mai gadi duk sai ya sha jinin jikinsa ya ɗauka ko shi ne ya ɓatawa Ibrahim ɗin rai da bai buɗe ƙofa da wuri ba, da sauri ya ƙarasa yana mai cewa.
"Afwan yallaɓai ina sallah ne" Hannu kawai ya ɗagawa mai gadin ya shige cikin gidan, bai bi ta kan part ɗin Mummy ba direct part ɗinsa ya nufa yana ta sauri shi kanshi bai san dalilin saurin nashi ba.
Yana shiga bai tsaya a falo ba ya shige bedroom wayoyinsa ya ɗora a kan madubi ya cire hula da rigar jikinsa ya cilla kan gado agogon hannunsa ya cire ya ajiyee yana hango shi a madubi sanye yake da farar singlet fara tass tamkar takarda sai wandon yadin da ya cire rigar, hasken fatarsa da kwantaccen gashin sa tamkar ba'indiye shi ya sa ya ji zuciyarsa ta tsinke saboda tunowa cewa masoyiyarsa bata son kyakkyawan namiji.
Kan gadon ya koma yana ture hula da rigar da ya cire gefe don ba al'adarsa ce jefar da kayansa a kan gado ba shi mutumin ne mai tsafta. Amma yau yanayin da ya shiga ya sa yana abu wanda ba halayyarsa ba. Tashi ya yi ya kunna AC haɗe da ƙure mata gudu a take sanyi ya haɗe ɗakin duk a nufinsa ya samu sassaucin zafin zuciyarsa da yake azalzalarsa na rashin wacce yake so. Ya koma ya zauna wayarsa ta fara ƙara amma bai tashi daga zaunen ba, har kiran ya tsinke, wani ya shigo sai a karo na uku sannan ya tashi ya ɗakko wayar ganin suna Mummy ɓaro-ɓaro ya yi saurin ɗagawa tana tambayarsa rashin shigowarsa ɓangarenta ya sanar da ita wanka yake son yi sai lokacin ta ji ɗan dama a ranta don ta san da wuya Ibrahim ya shigo gida bai fara shiga part ɗinta ya ganta ba. Suna gama wayar kiran Abeed ya shigo ɗagawa ya yi suka yi magana ya ajiye ya koma ya kwanta reran a kan gadon idanunsa a rufe yana ta nemawa kansa mafita.
Zuwa can ya tashi zaune kamar an tsikare shi da sauri ya ɗakko wayarsa, sunan direbansa ya kamo hannunsa har rawa yake don yana ganin wannn hanyar ce zai bi ya samu mallakar Jidda don zai yi duk yadda zai yi ya samu soyayyarta ya kuɓuto ta daga gorin da ya ji tana furtawa da bakinta cewa za a yi mata idan bata samu miji mai auren ta ba. Bugu ɗaya biyu direba ya ɗaya ya ce
"Barka da dare yallaɓai" Ya faɗa cike da girmamawa. Amma maimakon Ibrahim ɗon ya amsa sai ya ce
"Ina za a samu kayan gwanjo?" Tambayar ta zo masa a ba za ta amma sanin kyauta irin ta yallaɓai ɗin sai ya yi tunanin ko kyauta zai yi da su, duk da ya san kaya sabbi dal yake bayarwa.
"Za a samu wane iri?" Ya faɗa yana jiran jin amsar sa
"Daidai ni?" Maganar ta zo masa a bazata amma sai ya ce
"Ana samu yallaɓai akwai wani abokina maƙocinmu ne ma yana buɗe dila ta kaya kuma masu kyau kamar sabbi... Kafin ya gama magana Ibrahim ya ce
"Bana son wanda suke kamar sabbi na fi son tsoffi wanda suka ji joki idan son samu ne ma wanda suka fara gashi" Shiru direban ya yi sai kuma ya ce
"To yallaɓai sai dai a karɓo ƙarshen dila irin wanda aka gama zaɓewa aka bari su ne wanda ake karyar da farashin su saboda tsufansu"
Ibrahim ya ce
"Yawwa su zan saka maka kuɗi a account yanzu ka je ka samo min su" Amsa masa ya yi da
"To" Ƙit ya kashe wayar yana sauke ajiyar zuciya.
Haka direbansa ya kawo masa kayan cikin wata bakko don kuɗin da ya tura masa ko rabi ba a ɗauka ba, part ɗinsa ya kai masa ya bashi umarnin tafiya tare da crwa ya riƙe sauran kuɗin. Direban yana fita ya buɗe kayan da sauri yana fito da su, sosai sun ji jiki ba ma wannan ba warin da kayan suke irin na gwanjo su ne suka sa ya kusa yin amai, waya ya ɗaga ya kira mai wanki ya bashi kayan ya ce a wanke amma kar a goge, don a ransa ya san ba zai iya saka su babu wanki ba, don ba don Jidda ba babu mai saka shi saka gwanjo.
Yana ɗaukan kayan shi kuma ya fito ya nufi part ɗin Mummy don lokacin har ya yi wanka ya saka wani kayan sun je masallacin isha'i da Daddy, a falon ya same su yana shigowa cike da kulawa suka tashi suka nufo shi, kowa ya rungumi gefen ɗaya daga jikin Ibrahim ɗin suna matuƙar son ɗan nasu. A haka suka ƙarasa saman dining ɗin in da Mummy da Daddy suka kama shi cike da kulawa suka zaunar da shi a kujera, Mummy tana dariya cike da wasa ta ce
"Haba Daddyn Mu'azzam ya kake neman kayar min da ɗa bai gama zama ba fa ka janye hannunka" ,Ta faɗa tana kallon Ibrahim da yake ta murmushi kyawawan haƙoransa a waje. Daddy ma cike da wasa ya ce
"Wai kina nufin kin fini son shi ne?"
Mummy ta ce
"Eh mana"
Daddy ya ce
"To bari mu ji daga bakin Ibrahim ɗin, Mu'azzam tsakanin ni da Mummynka wa ya fi son ka kuma wa ka fi so?" Ya faɗa yana daga tsaye har da kama tsantsa shi ala dole yana jiran ya ji mai za a ce kar a je ba a zaɓe shi ba.
Mummy kuma ta kasa tsayar da dariyar da take marar sauti, shi kuma Ibrahim yana ta kallonsu ɗaya bayan ɗaya yana tunanin ta inda zai ɓullowa wannan diramar tasu.
Mummy ta ce
"Kai muke jira"
Ibrahim ya ce
"Duk kuna sona na sani, ni kuma na fi son...
Kowa ya yi saranda yana jiran kar a zaɓi ɗan uwansa ba zaɓe shi ba, kowa ya san idan ba a zaɓe shi ba za a masa dariya. Kamar daga sama suka ji Ibrahim ya ce
"Ni kuma ina ƙaunarku ku duka" Gabaɗaya sai aka kaure da dariya Mummy da Daddy suka nemi kujerarsu suka zauna, Mummy ta zubawa kowa abincin suka shiga ci cike da annashuwa.
Bayan sun kammala suka koma tsakoyar falon suna tattaunawa, a nan mai aiki ta shigo ta kwashe kwanukan ta tsafta ce dining ɗin.
Ibrahim ne ya musu sallama ya ce zai je ya kwanta, kasancewar dai yaƙe yake musu don kar su fahimci yana cikin damuwa, yana zuwa part ɗinsa ya shiga ya kulle, bai watsa ruwa ba kasancewar bai daɗe da yin wanka ba, jallabiyar jikinsa ya cire ya saka sleeping dress masu laushi ya kwanta tare da yin addu'a. Bayan ya shafa addu'ar ya shiga tunanin mafitar da yake a kan lamarin Jidda don a gobe ba sai jibi ba ya yi wa kansa alƙwarin sai ya je mata da kalmar so kuma son na aure!.
Tunanin wani abu ne ya faɗo masa hakan ya sa ya ɗauki wayarsa ya shiga kiran Abeed abokinsa bayan ya ɗauka yana ta masa surutu Ibrahim ya ce
"Dalla malam ka tsaya na faɗa maka abin da ya kawo ni, ka tsaya kana ta zuba kamar lalataccen famfo"
Abeed ya ce
"To dama ai kamar jiran kiranka nake ka san maganata ni da kai bata ƙarewa" Banza ya masa akan abin da ya faɗa don ya san kawai surutu ne zai cika shi da shi kp ya ringa bashi labarin ball ɗin da aka ci shi kuma yanzu ba wannan ne a gabansa ba, don ba ya so ma ya faɗawa Abeed ƙudurinsa gudun ya masa dariya ko ma ya ce sai ya bishi wajen Jiddar.
Cike da ƙosawa da kalaman Abeed Ibrahim ya ce
"Ni tambayarka zan yi ko ka san wani mai wanda mutum zai shafa ya yi baƙi kuma ya yi muni?" Ya faɗa hankalinsa kwance don shi ya shiryawa faɗawa komai a kan Jidda.
Abeed jin babu alamar wasa a furucin da abokin nasa ya yi sai ya ce
"Man da za a shafa a yi baƙi da muni ko dai mai da za a shafa a yi fari da kyau?" Shi ma ya tambaya babu alamar wasa a maganarsa kamar yadda Ibrahim ɗin ya yi.
Shiru Ibrahim ya yi yana ɗan nazarin kamar ba zai ce komai ba har sai da maganar Abeed ta katse masa tunani jin ya ce
"Magana nake maka ka ƙyaleni?" Wani yawu ya haɗiye yana fatan dai ba cewa zai yi ba a samun man ba ya ce
"A,a kamar yadda na faɗa maka mai wanda zai saka baƙi da muni, ka san dai ai ni dai in ba zabiya zan komai ba mai zan yi da fari, kyau kuma ni da indiyawa da larabawa ko za a samu bambanci bainwuce a ce ni bahaushe ba ne su kuma larabawa da indiyawa, to mai zan yi da kyau?"
Abeed ya ce
"Wai kana nufin kai ne kake neman wannan man da ka ambata mai za ka yi da shi?"
Maimakon ya amsawa Abeed tambayarsa sai ya ce
"Tambaya za ka min ko amsa min tawa tambayar za ka yi" Ya faɗa yana jin tamkar ya janyo shi daga wayar ya yi ta bugu har sai ya huce.
Abeed baki ya taɓe kamar Ibrahim ɗin yana ganinsa ya ce
"Kai malam ni ban san inda ake siyar da wannan man ba, to wai kai mai ya sa ma za ka shafa wannan man? Wane mai bada gurguwar shawarar ne ya baka shawarar nan, bayan kana da kyau wanda ƴanmata suke maka caaaa... Wani takaici ne ya cika Ibrahim jin abin da Abeed ya faɗa shi kuma a halinnda yake ciki yanzu gani yake ko wata mace aka alaƙanta shi da ita tamkar an ci amanar Jidda ne, wayar ya sauke daga kunne ya datse kiran haɗe da yin cilli da ita can gefe ya kwanta tare da juyawa wayar baya. Abeed kuwa dama ya san a rina wai an saci zanin mahaukaciya, dama ya san hakan zai ta faru don ya san Ibrahim ya tsani maimaita tamabaya.
Washe gari ko da ya tashi bayan ya yi shirin fita office, don yau shi kaɗai zai tafi kamfanin don Abba ya ce zai zauna ne ya yi wasu rubuce -rubuce a kan kayan da za a shigo da su daga waje na kasuwancinsa wanda duk manyan kasuwanni da shaguna yawanci wajensa suke sarar kayan. Yau ba kamfanin wajen gidan su Jidda zai je ba, ɗaya kamfanin yin shinkafa zai je, duk ransa ba daɗi don a ganinsa idan ya doshi hanyar wajen gidan su Jidda ma ai daɗi zai jia ransa. Bayan sun kammala break fast ya fito riƙe da jakar wajen aikinsa da wayoyinsa, suna tsaye da Mummy tana jero masa addu'a mai wankin da ya ba wankin gwanjo jiya ya zo yana mai cewa
"Barka da safiya Hajiya" Ya gaishe da Mummy cike da girmamawa, bayan ta amsa ya juya ya ce
"Barka da safiya yallaɓai" Ibrahim ya ce
"Alhamdulillah, mu je in buɗe maka part ɗin nawa ka saka min kayan, ya faɗa gudun kar ya bashi mukullin idan ya tafi kafin ya dawo Mummy ta tambaye shi kayan mene ne bakko guda a cike.
Bayan ya saka masa ya dawo ya mata sallama, kamar ya sani kuwa sai da ta tambaye shi kayan mene ne don Mummy tana da sanya ido a kan lamurinsa, duk da ya mallaki hankalin kansa amma tana lura da al'amuran da suka shafe sa.
Sanar da ita yanyi cewa wasu kaya ne da ya saya, yana mata sallama direbansa ya buɗe masa mota bayan ya shiga ma'aikatan gidan wanda suke wajen suna ta kawo gaisuwa cike da bashi girma yana amsawa, rufe masa ƙofat aka yi direban ya shiga ya tada motar mai gadi ya buɗe suka fita ya mayar ya rufe yana musu fatan alkairi, ɗago masa hannu Ibrahim ya yi da yake yau motar da ya fita da ita mai farin glass ce ana gani.
Kamar jiya ma yau ya shirya wajen ƙarfe biyar na yamma, bayan ya fito wanka bai shafa mai ko turare ba kawai wannan kayan ya ɗakko ya saka kala ɗaya riga da wando baƙaƙe, ya kalle shi a madubi, duk da tsuffin kaya ne kasancewarsu baƙaƙe sai suka ƙara haska fatarsa hakan ya sa ya ji gabansa ya faɗi don tamkar ma kyau aka ƙara masa, da sauri ya cire ya ɗauki wata jar riga wacce daga gwiwar hannun ma ta ɗan fashe, ya saka baƙin wando, duk da a cukwuikuye suke amma dai ya ga sun masa kyau. Kai ya dafe ya koma bakim gado ya zauna yana tunanin ko dai baƙin mai ko na gawayi zai samu ya dishi farin fatarsa amma sai ya yi tunanin zai koma kamar dodo kuma ba ya so ma Jiddar ta ɗauka ko mahaukaci ne ta ƙu kula shi. Wayar da ya sa direba ya siyo masa tsohuwa key pad ita ya saka sim ɗinsa guda biyu ya ajiye nasa wayoyin masu tsada a kan madubin, dakyar ya samu takalmi yana fatan kar ta gane takalmin me tsada ne, wata hular sanyi ya ɗauka duk da zafin da ake ya saka amma sai ya ga ta yi kyau, ya ajiye ya ɗauko hularsa da yake sakawa da yadi, ya ɓata karin jikin hular ya saka ya danna a kan ta rufe wannan lallausan gashin kan nasa, sannan ya fito da kunnuwan waje sai ya zama gashi nan dai kamar wani wanda ba wayayye ba amma dai in mutum yana da hankali to yana kallon fatarsa kaɗai zai gane ɗan hutu ne bai saba da wahala ba.
Fitowa ya yi kasancewar Mummy yau ta fita gidana biki, bai san bikin waye ba amma ta ce masa ta tafi gidana biki, Daddy ma ya fita shi da wasu abokansa da suka zo wajensa.
Part ɗinsa ya rufo ya fito ya saka mukullin a aljihu yana gama sakawa ya ga mukullin ya faɗo sai a lokacin ya lura, ashe ajjihun a yage yake, a ɗayan ya saka sai ya ga babu yaga.
Tun da ya fito yake addu'ar Allah ya sa kar ya haɗu da wani daga ma'aikatan gidan, cikin ikon Allah har ya je bakin get bai haɗu da kowa ba, dama ko wajen ajiye motoci bai kalla ba kasancewar yau ba a ma managar mota. A hankali ya kama ƙaramar ƙofar ya buɗe amma sai da ƙofar ta yi ƙara ƙiiƙiii mai gadi da yake banɗakinsa ya ji ƙaran taɓa ƙofa dama yana shirin fitowa ne, hakan ya sa ya ƙara ƙaimi wajen sauri ya fito yana cewa
"Waye?" Lokacin har Ibrahim ya fita ya rufo ƙofar, yana fitowa ya fara sauri don ya san dole sai mai gadi ya leƙo, kuma baya son kowa ya ganshi, mai gadi kuwa da sauri ya ajiye butar hannunsa, ɗan taku ɗaya biyu ya yi yana leƙo hanyar cikin gidan ko zai ga wanda ya shiga amma bai hango kowa ba.
Da ɗan sassarfa ya nufi get ɗin ya buɗe ƙaramar ƙofa domin leƙawa ya ga ko fita aka yi tun da ba shigowa aka yi ba, Ibrahim da yake ta sauri don ganin ya bar layin nasu jin an buɗe ƙofar don ƙaran ta ziyarci kunnuwansa, da sauri ya raɓe daba jikin wata katangar wani gida yana leƙo mai gadin har ya gama kalle-kallensa ya koma ya rufo ƙofar, Ibrahim ya fito daga maɓoyarsa ya cigaba da tafiya yana fatan Allah bashi nasara a kan abin da zai je nema, yana fatan ya samu Jidda ta amince masa don ko a gobe in ta amince ya yarda a ɗaura musu aure!.
Tafiyar tashi bata je ko ina ba ya ji ya gaji kasancewar bai saba da wahala ba, napep ya tare ya shiga tare da faɗa masa inda zai kai shi, sai da suka kusa zuwa inda za a gangara ya ce mai napep ya samu wuri ya sauke shi, haka ya fito tare karɓar account no mai napep ya masa transper na kuɗinsa har da ƙari, mai napep sai godiya yake kamar ya ari baki, amma zuciyarsa cike da tambayoyi da wasi-wasi don ya tabbtar wannan ba ƙaramin mutum ba ne duba da yanayin maganarsa irim ta wayayye kuma mai ilimi, sanna kana kallonsa ka ga wanda yake zaune a hutu ba a wahala ba, sai dai yanayin kayan jikinsa ya sa kana iya jiyo warin abin gwanjo daga jikinsa.
Shi dai bai ƙara bi takansa ba ya fara tafiya yana ta addu'ar dacewa, dacewar kuma ba ta komai ba sai ta sa'ar ganin Jidda tare da fallasa mata asirin zuciyarsa da fatan ta amince da shi....
*Akwai abaya gwanjo masu kyau da imganci akwai dila, akwai rabin dila, akwai kwatar dila akwai sayen ɗaya*
*Sannan akwai zannuwan gado, labulaye, abaya mayafai* *kayan yara takalma lesuna atamfofi shaddodi hijabai amma su sabbi ne da sauransu*
*Sannan akwai magungunan mata, kama daga daka mai kyau da matsi ba wanda ake sanyawa ba wanda ake tafasawa a shiga, akwai maganin gyaran breast ga matan da nononsu ya zube ko ya yaƙune da wanda suke yi yaye da masu shirin yaye, akwai tsumi domin dawo da darajar ki wajen miji, akwai kuma sanyi wanda shi maganinsa dole ne don idan kina da sanyi ko kinnsha magani ba za ki ga kyansa ba.*
*Akwai mayuka na gyaran fata, kama daga wanda zai saka fari da wanda baya saka fari wanda shi iya fata zai gyara ya saki yi glowing, akwai shower gel, da sabulai da dai sauransu*
*Mai buƙata ta min magana ga no ta nan a ƙasa*
MAMAN AFRAH
09025576222
[10/11, 9:47 PM] MOM MASHKR & AFRAH: https://chat.whatsapp.com/C12RFYqXnWf36AhjVZWDw4?mode=ems_copy_t
*RUWA CIKIN COKALI*
(Ya ishi mai hankali wanka)