Kenza eBookz

Taimiyah book complete document by ayshat dansabo lemu txt by hausanovels com - Chapter 25

Taimiyah book complete document by ayshat dansabo lemu txt by hausanovels com - Chapter 25

Taimiyah book complete document by ayshat dansabo lemu txt by hausanovels com Chapter 25: Taimiyah book complete document by ayshat dansabo lemu txt by…

4,485 words

TAIMIYYAH da tayi tsaye jingine da jikin kujera, ta ɗaga manyan idanunta tana jifansa da wani mugun kallo,ta buɗe baki tana faɗin, "Yah Emran please ka daina furta kalmar kana sona,hakan na sake ƙona zuciyata ne da kimsamin tsananka me tsanani.Ka ɗauka ban ji duk yadda kuka yi da Mamie akaina bane? Tana roƙonka ka so ni amma kana nuna cewa faɗuwar aji ne lafiyayye kamarka ka auri gurguwa,har kana faɗin me zaka sanar abokanka idan ka auri gurguwa? Naji komi Yah Em babu abinda zaka yaudareni da shi, gurgu irina shi yafi cancanta in mallaka masa soyayyata da zuciyata baki ɗaya.Kada ka ƙara cewa kana sona ko furta wasu kalamanka na yaudara a kaina,wallahi summa billahi Yah Emran bazan taɓa ƙaunarka ba, sai dai ƙauna irin ta jini shima bazan ɓoye maka ba a yanzu tsananka nake ji matuƙa,don haka ka daina yaudaran kanka in dai ni Zaynab ce to banzan taɓa son ka ba,kuma ba zan taɓa aurenka ba Insha Allah."

Daga haka ta juya tana tafiya cikin tsarin yadda Ubangiji ya nufeta da takawa,hannunta dafe da guiwar ƙafarta na hagu ta nufi hanyar shigewa ɗakinta,hawaye na sintiri a fuskarta har ta isa cikin ɗakin tayi banging ƙofar da ƙarfi.

A kan gado ta zube tana cigaba da kuka sosai, hawayen baƙin cikin jin kalmar soyayyah daga bakin Yah Emran ɗin na sake ɓalle mata. Ko duka jikinta kunnuwa ne ba za ta taɓa aminta da cewa sonta yake yi ba,don ta san ba son gaskiya da amana zai mata ba, sai dai so irin na sha'awa,tunda bai fara son nata ba sai a lokacin da ya tozartata ya gama ganin kyawun surarta a zahiri....."

Kukan da ya taho mata ne yasa ta kai hannu tana dafe bakinta,tana ƙoƙarin maida kukan da ke son kwace mata. Ta cigaba da sharan hawaye tana jin kewan Nass da Soayyyarsa, na sake kassara duk wata gaɓa da ke motsi a cikin zuciya da gangar jikinta....

Muryan Iyah data jiyo daga can falon alamun har ta dawo daga unguwar da ta fita,yasa TAIMIYYAH saurin share hawayenta,ta koma da baya ta kwanta akan gadonta, tana me lumshe idanunta baki ɗaya tamkar me bacci.

Iyah ta shigo cikin ɗakin kai tsaye tana nufan wajen gadon da TAIMIYYAH ke kwance,ta kai hannu ta shiga bubbuga ƙafar TAIMIYYAH tana cewa, "Maza ki tashi tun raina bai ɓaci ba Zainab,ya mutum zai taso takanas saboda ke, ki dinga wulaƙantasa haka kamar ba jininki ba,wato har yanzu kinƙi cire son wanda uwarsa ta gama tozartaki ta nuna bata ƙaunarki,tace ɗanta ba zai aureki ba sabida ke gurguwace ko? Shiyasa zaki dinga wulaƙanta ɗan uwanki na jini da zai ƙaunace ki fiye da duk wani bare,to maza-maza ki je ki zubo masa abinci don ransa ya gama ɓaci,yace kin gaggaya masa maganganu marasa daɗi,shiyasa kika dawo nan kika kwanta.Yaushe kika koyi rashin kunya Zainab da har zaki kalli Emran kina gaya masa magana? Sabida kawai yace yana sonki shine raini zai shiga tsakani, to wallahi ki kiyayi fushina a wannan karon,kuma baki da miji sai shi don ni naji daɗi da wannan maganar da yazo da it......"

Kukan da TAIMIYYAH ta sanya ne ya hana Iyah ƙarisa kalamanta,tayi sakato da baki tana duban TAIMIYYAH babu ko ƙiftawa. TAIMIYYAH ta cigaba da rusa kukanta tana cewa, "Iyah wallahi Yah Emran bani yake so ba,tsaraki kawai yazo ya yi amma ko Qur'ani akace in dafa akan cewa ƙarya yake bani yake so ba zan dafa,don Allah Iyah kar ki yadda da zancensa, kuma ni bazan sake fita wajensa ba zuciyata zafi take yi,in dai ba so kike hawan jini ya kamani ba,don girman Allah ki daina cewa banda miji sai shi,ki je kawai ki gama da shi ni kuma idan ya tafi zan waraware miki komi."

Iyah da ta kafe TAIMIYYAH da ido sai ta kasa cewa komi,ta juya ta fice daga ɗakin ranta a ɓace matuƙa.Amma tana isa falo sai ta yi ƙoƙarin saita kanta, ta fuskanci Emran tana bashi haƙury akan karya da gaskiyar da ya kitsa mata na cewa TAIMIYYAH tai masa rashin kunya.

Babah Ladi ce ta fito ta aje tray me ɗauke da drinks da abinci a gabansa,suka gaisa sannan ta juyo ta koma zuwa kitchen don ƙarisa aikinta.

Sai around 1:05pm Emran yai sallama da Iyah akan cewa zai koma,yaso ƙwarai Iyah tayi forcing TAIMIYYAH ta sake fitowa ya ganta, amma hakan bai samu ba. Hakanan ya ajewa Iyah dubu goma saman kujera, yai mata sallama ya fice zuciyarsa cike da jin zafin, yadda TAIMIYYAH ta nuna da gaske ƙinsa take yi har cikin zuciyarta.

Lokacin da Iyah ta samu TAIMIYYAH a cikin ɗaki bayan tafiyar Emran.A kwance ta ganta har lokacin sai faman sharan hawaye take yi,hakan ya sanyayar da jikin Iyah tasan cewa lallai akwai wani abu, ba banza TAIMIYYAH zata dinga kuka haka don kawai Emran ya zo ya fallasa cewa yana sonta ba.

Ta nemi bakin gadon ta zauna, tana kai hannu ta ɗago TAIMIYYAH daga kwaciyar da tayi tana cewa, "Ta shi Zainabu kukan ya isa haka,sanar dani abinda ya faru,ko yake faruwa tsakaninki da ɗan uwan naki Emran."

TAIMIYYAH ta kai hannu ta share hawayenta, cikin sanyin murya da nutsuwa ta zayyane ma Iyah duk abinda ya faru a Kano tsakaninta da Yah Emran ɗin. Bata ragewa Iyah komi ba har hiransu da Guggo Bilki da ta ji duk bata ɓoye komi ba ta sanar da Iyah,ta ƙare maganan da cewa,

"Iyah wallahi jikina yake so nina gama gane hakan,tunda tun farko ga abinda yace sannan ga yadda yaso ya tozartani ya keta mutuncina,to taya za a yi a yanzu yazo yace wai in amince son gaskiya yake min zai aureni,wallahi ƙarya ne ba son gaskiya yake min ba, don Allah Iyah ki kashe wannan maganan kada ma ya je ya yaudari Guggo Bilki ta ga kaman yayi na'am da ra'ayinta ne, alhali yaudarace yana da manufarsa akaina ne kawai,ba soyayyar gaskiya yake min ba ta sha'awace Iyah,don haka don Allah ki rufa min asiri ki dakatar da shi daga duk wani yinƙurinsa wallahi na tsanesa ya gama zube min,ni soyayyar da kowama ya fita kaina a barni inyi facing karatuna kawai,duk randa Allah ya kawo min gurgu irina sai afara min maganan auren please Iyah!"

Yadda TAIMIYYAH ta kai ƙarshen maganan cike da magiya tana kuka,yasa Iyah rungumeta a jikinta tana jin matsanancin tausayin TAIMIYYAH na keta zuciyarta.Wani irin ɓacin ran abinda Emran yayi wa TAIMIYYAH na keta zuciyar Iyah. Cikin murya me cike da rarrashi Iyah ke kwantar da hankalin TAIMIYYAH,har tayi nasaran tsaida kukan da TAIMIYYAH take yi.

"Kiyi haƙuri Zainab bansan abinda ya faru kenan ba,da ko ganinki ma bazai kuma yi ba bare har na matsa sai kin je wajensa,zan kuma kira ita Bilkin in sanar da ita komi ta fara cimin mutuncinsa kafin mu gauraya ni da shi,ashe ina masa kallon kamamme shi ɗin watsatstsene daya ɓata wayonsa,idan yana iskancinsa a waje sai ya iya keta alfarmanki inda ya samu galaba akanki? Lallai zamani ya lalace da rashin tsoron Allah,Ubangiji ka shirya mana zuriya dana ɗaukancin musulmi baki ɗaya,amma gaskiya Emran ya bani mamaki ni ma kuma ya zube min tare da fita a zuciyata fit..!"

Iyah ta cigaba da bambami cike da ɓacin rai,ita dai TAIMIYYAH sai ta ji ta sama nutsuwar zuciya a yanzu da Iyah ta san komi,ta kuma fahimce abinda take so ta fahimta ɗin,na cewa jikinta Emran yake so ba ita ba,soyayyar sha'awace yake mata da zaran ya cika burinsa zai wofintar da ita ne,tunda tun farko ya nuna zubewar aji ne kamarsa a ce ya auri gurguwa irin ta.

Har Iyah ta gama bambaminta ta fice TAIMIYYAH bata sake cewa komi ba,tayi kwance ne kawai tana jinjina ƙarfi halin Yah Emran ɗin, da ya iya shiryawa Iyah duk wani ƙarya wai yana son ta.Ta lumshe ido abinda ya faru tsakaninsu a Kano na dawo mata daki-daki,ta kai hannunta kan bakinta tana ji kaman bakinsa na tsotsar lips ɗinta ne,hakan yasa tayi saurin buɗe idanunta tar...! Tana ji wani abu na danne zuciyarta da jin tsanansa me zafi a ranta. Bata fito daga ɗakinta ba sai bayan da tayi sallah sannan yinwa yasa ta fitowa neman abinci. Tana cikin cin abincin ne kuma Yah Sadeeq ya shigo,kusan tare da shi ma suka ci abincin da ta zuba ɗin,suna ci yana mata hiran budurwansa Safiyyah. TAIMIYYAH ita ce ta sanarwa Iyah cewa Yah Deekun ya samo mata,har da amsar wayar Sadeeq ɗin tana nunawa Iyah pic ɗin budurwan tasa. Iyah tayi murna da fatan alkhairy tana jin tausayinsa cikin zuciyarta, don daga kallon da yake bin TAIMIYYAN da shi zaka gane har yanzu da soyayyarta cikin zuciyarsa. Ya jima sosai a Sasan suna hira da TAIMIYYAH wacce ke zuba masa shagwaɓar da yayi missing tsawon lokaci,don ya jima basu sama zama irin haka,TAIMIYYAH ta saki jiki suna hiransu kamar yau ba,sai kusan la'asar ya bar Sasan Iyah,itama TAIMIYYAH yana fita ta koma zuwa ɗaki don yin waya da Zee akan assignment ɗin da aka basu a skull.......✍🏻

#Ɗansabo ce# [12/14, 10:11 PM] +234 703 769 7050: *Littafin TAIMIYYAH paid book ne,ga duk wanda ta tsincesa a kowani irin group ne,kiji tsoran Allah karki karanta sai kin biya 500 naira only.*

*Za ku iya min magana ta wannan number ɗin 08167768704, ko kuma ku turo kuɗin ku kai tsaye ta wannan account ɗin*👇🏻 0504192664 aisha ibrahim dansabo GTbank.

*Sai ku tura shaidan biyanku ta wannan line ɗin 08167768704.*

Masu turo credit za ku turo katin MTN na 500 ta wannan line ɗin 08167768704.

_*Ina ƴan kasuwa masu buƙatar a tallata muku hajar ku? Maza ku garzayo da kuɗi ƙalilan a tallata muku kayan siyarwanku sai dai kawai ku ji ana kiran waya don buƙatan sayan kayan ku,ku tuntuɓeni ta layina kamar haka 08167768704.*_

*45*

*Asokoro,Abuja.*

Suhailah ce zaune daga gefen Maleek Ado,wanda ke kwance baya ɗin Zazzaɓi da ciwan kai ke damunsa. Suhailah sai faman Lallaɓasa take yi akan ya tashi ya ci abincin data ɓata lokaci wajen girka masa,don ya samu idan ya ci ya sha magana,amma shi sai wani narkewa yake yi,dama kuma shi idan ba shi da lafiya komawa yake yi tamkar wani ƙaramin yaro.

"Please! Luv ka tashi ka ci abincin in baka drugs ka sha,ko sai na kiro maka Hajjah ne wai?"

Suhailah tayi maganan cikin narke masa murya idanunta na kansa.Ya buɗe manyan idanunsa ya sauke a kan fuskarta, yana jefa mata harara,cikin low voice yake faɗin, "Yes go and call her."

Suhailah ta saki murmushi tana gyara zamanta daga gefen gadon,ta kai hannu tana ɗago face ɗinsa ta manna masa kiss a goshi tana cewa, "Sorry luv wasa nake yi amma idan baka ci abincinnan ba zan kira ta gaskiya."

A.Maleek ya lumshe idanunsa yana jin tasirin kiss ɗin da Suhailah ta bashi har ƙasan ransa.Ya yinƙura ya tashi zaune yana ɗan ɓata fuska yake cewa, "Oya bani inci kaɗan sai ki bani maganin in sha,kar ki cinyeni da wannan nacin." Suhailah dai murmushi tayi kawai tana ɗakko plate ɗin abincin ta fara bashi yana ci a hankali,sai da yaci da ɗan yawa sannan ya kauda face alamun ya ishesa haka,sai ta bashi ruwa ya sha kafin ta fara bashi maganin yana amsa yana sha.Sai faman wani ɓata fuska yake har ya gama shanye adadin wanda zai sha a lokacin. Subailah ta maida ledan da drugs ɗin ke ciki ta aje saman side drawer,sannan ta ɗauki plate ɗin don fita da shi.

"Baby please idan kin kai ki dawo ki min wanka,mu kwanta in ɗan sammaki ɗumin jikin kema kin ji wife?"

A.Maleek yayi maganar yana daga kwance ya lumshe idanunsa,ba za ka taɓa cewa daga bakinsa kalaman suka fito ba. Suhailah sai ta saki murmushi tana cewa, "Ok Luv bari in je zan dawo yanzu in Hajjah bata tsare ni ba."

Tayi maganar tana fara takawa don barin ɗakin, tana jiyo muryansa a dake lokacin da yake faɗin,

"Alright."

Wani murmushi ta sake yi lokacin da take ficewa daga ɗakin baki ɗaya,tana jinjina rigima irin ta Maleek in dai akace an taɓo file ɗinsa ba shi da lafiya shikenan magana ta ƙare.Don rigima ce zai tayi salo-salo har sai ya samu kansa,har ta kai plate ɗin kitchen ɗinta da ke nan upstairs bata bar murmushi ba.

Bayan ta aje plate ɗin ta fito ɗakinta ta nufa kai tsaye,ta sauya kayan jikinta zuwa wata ƙaramar riga mara nauyi,don ta san daga yi masa wankannan sunanta sorry,don ita ma sai ya jiƙeta tsaf sun yi wankan tare sannan zai ji daɗi.

Lokacin da ta koma ɗakin nasa a kwancen dai ta samesa idanunsa a kulle har lokacin,ba kuma bacci yake yi ba.

Sai ta isa bakin gadon ta zauna tana yaye duvet ɗin da ya rufe jikinsa da shi, ta kai hannu saman wuyarsa don ta ji ko zazzaɓin na nan,aiko sai taji jikin da sauran zafi sosai.

Maleek ya buɗe manyan idanunsa ya sauke akanta,yana kafe ƙirjinta da ido wanda ko Bra bata sanya ba,ya kai hannu wajen yana tsareta da idanunsa da suka ɗan shige kaɗan suka rage girma.

Suhailah ta narke fuska tana cire hannunsa daga wajen take cewa, "My Maleek wankan please! Bari na je na haɗa maka ruwan."

Maleek ya bita da ido lokacin da ta tashi ta nufi hanyar bathroom ɗin,ya maida idanun nasa ya lumshe har lokacin kansa ciwo yake masa sosai. Hannunsa cikin na Suhailah suka isa bathroom ɗin, lokacin da ta fito ta sanar masa ta haɗa masa ruwan wankan.

Da kanta ta cire masa kayan jikinsa,sai faman narke mata yake yi.Kamar yadda ta ruwaita a ranta cewa ,wankan su biyu zasu yi sa hakan ne ya faru,don Maleek ɗaukarta cak yayi ya sakata cikin ruwan, bayan ya zare rigar jikinta yayi wurgi da shi.

Wankan da ba a samu yinsa akan time ba kenan,sai da Maleek ya gama bidirinsa son ransa kafin ayi wankan me dalili,suka fito Suhailah nata faman zunɓure baki,shi kuma yana bin ta da wani makirin smile.

Suhailar ce ta taya shi ya shirya kansa cikin ƙananun kaya marasa nauyi,kafin itama ta nufi ɗakinta don shiryawa,ta bar Maleek na amsa kiran da ya shigo wayarsa.

Koda ta gama shiryawa cikin riga da skat na atamfa,wanda ɗinkin ya yi mata cif a jiki tare da fidda shape ɗinta,sai ta ɗauki turarenta na MISS DIOR ta fesa kaɗan tana ɗaukar wayarta ta fito zuwa downstairs. Ɗakin da Hajjah tai masauki tun xuwan su garin, yau kwanakin su bakwai kenan da tarewa,Suhailah ta shiga ɗakin bakinta ɗauke da sallama.

Hajjah da ke daga kwance tana ɗan hutawa na rashin abin yi, ta ɗago idanunta ta sauke akan Suhailah,tana amsa sallaman da ta yi. Ta tashi zaune lokacin da Suhailan ta ƙariso zuwa cikin ɗakin tana cewa, "Kin kintsa kin sakko ɗin,toh ya jikin Maleek ɗin ina fata da sauƙi sosai?"

Suhailah ta zauna akan sofa dake ɗakin, tana murmushi ta dubi Hajjah tana cewa,

"Ya ji sauƙi Hajjah wanka yayi ma yanzu bayan ya ci abinci,sai ya sha magunguna,yanzu zaki ga ya sakko zuwa gaida ki ma."

Kafin ko Hajjah tace komi daddaɗan ƙamshin turarensa na AMOUAGE ya gama cika hancinsu,ya doka sallama cikin muryansa me cike da ƙasaita.

Hajjah ta kai dubanta wajensa tana amsa sallamar tasa, shi kuma ya cigaba takowa zuwa cikin ɗakin,bai yi masauki a ko'ina ba sai kusa da Hajjah, yana zama daga gefenta kamar zai shige jikinta. Murya cike da zallar shagwaɓar da ya saba yi mata yake gaida ita,Hajjah ta saki murmushi tana ɗaura hannunta saman kansa take amsa gaisuwarsa tare da cewa, "Maleek ya jikin naka ina fata kana samun sauƙi sosai?"

Maleek ya jinjina kai yana cewa, "Da sauƙi sosai Hajjah kin san zazzaɓin yanzu matsalarsa naci ne da shi,ɗumin jikin ya hau ya sauka ne haka yake min,amma nan da gobe idan na shanye dose ɗin bai tafi gaba ɗaya ba, ina ga allura kawai zan amsa zai fi."

Hajjah ta jinjina kai tana faɗin, "Allah ya ƙara lafiya,zai tafi ma insha Allah,ya maganan komawa ta Zarian a gobe?"

Suhailah dake saurarensu tayi tsagal tana duban Hajjah tace, "Kai Hajjah don Allah ki share maganan komawarnan sai zuwa wata satin don Allah." Hajjah ta harareta tana cewa, "Aiko sam baku isa ba gobe zan koma gida, na ga alamun so kuke ku maida ni wata abokiyar wasanku,na bar bayin Allah a can daga cewa kwana biyu zan yi in juya, sai gashi har na share sati guda sannan yanzu kice kin sake wasu kwanakin, cikin wannan shegen garin da babu daɗin zama,kana ƙunshe cikin gida to badani za a yi wannan rayuwar ba,sai ku yara kune kuka dace da irin wannan zaman amma ba Hajjah ba,ku barni na koma cin ƴan aikina da jama'ar arziƙi dana saba dasu a can,gobe-gobe babu fashi zan tafi don haka kai Maleek kama sanar da duk wanda zai kaini tun yau,ga direbobi nan sai wanda aka dar je ya kaini,ai gobe sai kwanan gida ƴar nan da yardar Allah, sai kuma wani lokacin idan rabo ya kawo mu haka nake fata Insha Allah."

Hajjah ta ƙare maganan tana ɗaga kan Maleek daga kafaɗarta,wanda ya wani narke tamkar jinjirin goye. Ganin Hajjah ta ture kansa daga jikinta, yasa shi dubanta fuska a cuskune yake faɗin, "To ni Hajjah me kuma nayi ake ture kaina ina cikin jin ɗumin jikin uwata,ita zaki ki dungure kanta tunda ita ce ta takaloki bani ba fa."

Maleek yayi maganar yana faman aikawa Suhailah da ke musu dariya harara.Ita kuma ganin yana hararanta yasa ta saki dariya me sosai tana cewa, "Hajjah yanzu daga roƙonki ki zauna shine abin wannan sababin,to ni dai gaskiya sai dai mu koma tare na fasa zaman nan ɗin nima."

Hajjah ta danna mata harara tana miƙewa tsaye take cewa, "To madallah! Ni bari ku ga na baku waje don na ga so kuke yi ku manna min hauka da girmana,ni dai na gama magana gobe sai gida, in baki iya zama sai ki bini mu koma,shi kuma sai ya yo sabuwar Amarya ya saka ta cikin gidan,kin ga an huta da ƙorafi."

Daga haka Hajjah ta fice tana sakin murmushi,tana jiyo Suhailah na cewa, "Wallahi ban yarda ba Hajjah in haka ne kiyi tafiyar ki kawai bakomi."

Maleek da ya taso daga kan gadon Hajjah, ya dubi Suhailah yana cewa,

"Ashe dai mutum ƙaryan gulma yake yi,ki bita ɗin mana ki gani in ban auro ƙawarki me ƙaton mazaunai na kawota Abuja ba,tunda ke baki son zama sai da Hajjah,sabida tun farko da ita kika saba zama gidan miji ko?"

Suhailah da ta cika tai fam da takaicinsa sai kawai ta miƙe zata bar masa ɗakin,yayi saurin riƙota ya matse a jikinsa, hakan ya sanya ta saka masa kukan shagwaɓa tana cewa, "Ni ka sakeni Yah Maleek tunda har yanxu ba za ka manta da ƴar iskannan ba."

Maleek ya danne dariyan dake taho masa, yana juyo da face ɗin Suhailah ya haɗe fuskokinsu waje guda yana cewa,

"Sorry wife tsokanace kawai,haushi ki ke bani ne idan kina cewa za ki bi Hajjah."

Suhailah da har lokacin fuskarta a haɗe yake, da jin zafin ambaton sunan Zuby da yayi,sai ta buɗe baki xata yi magana Maleek ya xura harshensa cikin bakin, yana fara bata wani irin deep kiss da ya sanya ta sake shigewa jikinsa sosai.

Ya jima yana bata hot kisses tana taya shi itama,sai da ya gaji don kansa ya raba bakinsa da nata,yana jifanta da wani sassanyar kallo yake cewa, "Baby let go please! Ina so mu ɗan kwanta tare zuwa la'asar,cox i need u so much dear."

Suhailah ta sake narke masa cikin son tsokanarsa take cewa, "No Luv zan taya Hajjah hira, ka fara tafiya zan biyo ka daga baya."

Maleek ya jefa mata wani kallo yana haɗe fuska yake faɗin, "Okey idan ma kun gama hiran zaki iya xama abinki kar ki nemeni."

Daga haka ya raɓa Suhailan zai wuce tayi saurin shan gabansa, tana jifansa da murmushi,murya can ƙasa take faɗin, "Sorry my Maleek mu je ka sammin ɗumin jikin nima Baby."

Yadda take maganan tana ɗage masa gira, yasa shi kai hannu ya dungure goshinta yana faɗin, "Let's go Babe!"

Daga haka suka fito daga ɗakin suna ratsowa cikin falon Hajjah da ke zaune,wacce ta maida hankali wajen kallon tashar Aljazeera.

Ta ɗaga ido ta dube su Maleek sau ɗaya tana ɗauke kanta daga garesu.Maleek ya iso inda take zaune yana cewa, "Hajjah bari in je na ɗan kwanta xuwa la'asar, idan anyi sallah za ku fita da Suhailah da driver,sabida ki yi siyayyar tsarabar da zaki tafi da shi."

Hajjah ta taɓe baki tana cewa, "Madallah! Da dai yafi kam,Allah ƙara afuwa je kai kwanciyarka."

Suhailah ta dubi Hajjah cike da shagwaɓa tana faɗin, "Hajjah yanzu don Allah fushi kike dani, ko kallona baki son yi."

Hajjah ta harareta tana cewa, "Kai ni ku tafi ku bani waje inyi kallona, bansan damu tunda duk kun haɗu kun maida ni kakar ku."

Suhailah da Maleek duka suka saki murmushi,suna haɗa baki wajen faɗin, "Afuwan Hajjah Allah baki haƙury mun yi nan."

Daga haka suka nufi hanyar da zai kai su Upstairs, Hajjah na bin bayansu da kallo tana me musu addu'ar Allah ya dauwamar da zaman lafiya a tsakaninsu, ya baiwa Suhailah mafita da rabo me anfani kusa ko nesa.

Bayan la'asar kamar yadda Maleek ya faɗi,ya baiwa Subailah da Hajjah kuɗi me yawa suka fita yin siyayya,tare da ɗaya daga cikin direbobin da aka je musu a gidan.

Washegary Hajjah ta wuce ta bar Suhailah da kewanta me yawa,shi kuma Maleek Monday zai bi flight ɗin safe zuwa Lagos.

__________

*Zaria,* *4:15pm.*

Zuhurah da Basmah ne tsaye daga cikin kitchen, suna ƙarisa kammala haɗa abubuwan da za a tarbi Nass da shi,wanda yace wa Basmah ya kusa ƙarisowa gidan nan ba da jimawa ba.

Basmah ta gama juye lemun Zoɓo da suka cikawa sugar cikin jug, tana duban Zuhurah take faɗin, "Yah Zuhurah amma fa baki ji yadda gabana ke faɗi ba,sai tunanin yadda zan dubesa ido cikin ido nake yi a zahiri,bare har in iya sanar da shi irin soyayyar da nake masa."

Zuhurah ta aje plate ɗin da tayi raping Doughnut ɗin da suka siyo,tana duban Basmah da murmushi saman fuskarta take cewa, "Aiko bai kamata ace kina jin hakan ba, idan akai la'akari da irin son sa da ya rufe idanunki,sannan Umma ta sanar da ke cewa da zaran kun yi ido biyu da shi shikenan fa magana ta ƙare,don ji zaiyi ko me kika sanar dashi ba zai iya musawa ba,don an riga anmantar da shi wata TAIMIYYAH.Bokan fa yace ko sunanta kika kira sai yaji wani ɓacin rai ya lulluɓe zuciyarsa,ba dai kinyi wankan maganinnan na kwana uku ba,kuma yau ma kinyin turaren da yace ki yi haɗe kayan da zaki saka idan zaki wajen Nass ɗin,to sai mu zuba ido mu ga me zai biyo baya...

Zuhurah ta cigaba da cewa, "Ni dai na ga cika aiki wallahi,don yanzu Ameeru sai abinda nace ina so yake yi, wani irin zazzafan so yake min wanda ya ninka na baya, tunda nai anfani da turarennan ran da yazo."

Basmah da tai kasaƙe tana sauraran Zuhurah, sai ta saki ƙayataccen murmushi,tana jin wani ƙwarin guiwa na mamaye zuciyarta.

Shigowan Umma cikin kitchen ɗin yasa duk suka zuba mata ido, Basmah na cewa, "Umma mun kammala bari na je na shirya yana hanya yace ya kusa ƙarisowa,a falon Baba zamu sauke sa."

Umma ta jinjina kai tana cewa, "Eh hakan yayi,sai kiyi maza ki shirya ɗin ita Zuhurah sai ta je ta kammala komi a can ɗin,ki tabbatar kin wanke fuskarki da ragowar wannan ruwan rubutun,da aka ce sai randa za ku yi ido biyu da yaron za ki yi amfani da shi,yana nan na aje miki a ɗakin naku."

Basmah ta gyaɗa kai tana cewa, "To Umma bari in je Allah dai yasa kwalliya ta biya kuɗin sabulu."

Umma tayi murmushi tana bin bayan Basmah da kallo,kafin ta maida dubanta kan Zuhurah tana cewa, "Hmm! Yaro man kaza,an gaya miki a banza nake zaune da ubanku shekaru kusan talatin amma bai taɓa zancen ƙarin aure ba,ki dai yi yadda aka ce ɗin ki ga ikon Allah,amma indai aikin na bakin rafi ne bai taɓa yi ba a samu nasara ba,in dai zaka saki bakin jaka to za ka ga biyan buƙata kuwa,ki rabu da fulani kawai inda kika gansu."

Zuhurah tai wani dariya tana saluting Umma take cewa, "Wallahi na yadda Umma don na ga aiki da cikawa,sabida yanzu Ameeru ko a waya bai son ɓacin raina bare idan yana gabana,wani irin soyayya yake gwadamin ta ban mamaki, burinsa kawai ayi-ayi a ɗaura auren mu Allah dai ya ja kwana Umma, ai mu tuntuni baki karanta mana cewa kina zagayawa ta ƙarƙashin ƙasa ba."

Daƙuwa Umma ta aikawa Zuhurah tana cewa, "Zan ci ƙaniyarki Zuhurah kin raina ni ko?"

Zuhurah na dariya take cewa, "Sorry Umma ba haka bane wallahi." Daga haka ta fara kwasan abubuwan da suka kammala shiryawa tana kaiwa falon Baba Sani,ta shirya komi bisa table tana sake faffesa roomfreshner cikin falon,nan da nan ko'ina ya ɗauki sassanyar ƙamshi.

Daga ɓangaren Basmah kuwa tuni ta kammala shiryawa,cikin wasu riga da skat na wani atamfar Chiganvy gold. Kalar atamfar me duhu ce daya haska ta sosai, don tana da hasken fata tafi Zuhurah haske,ɗinkin ya zauna a jikinta sosai tare da fiddo shape ɗinta a zahiri. Push-up Bra ta sanya wanda ya sake turo da cikar ƙirjinta sosai ta saman rigar,sai ta feshe jikinta da turaruka masu tsananin ƙamshi,ɗakin gaba ɗaya ya buɗe da ƙamshi,tana cikin sanya Ɗankunni wayarta ya fara ringing.

Sai ta nufi wajen da wayar take aje tana ɗauka, ta kai kunni bayan tayi receiving tana cewa, "Yah Nass har ka iso ne,ok gani nan fitowa yanzu." Daga haka ta aje wayan ƙirjinta na faman dokawa,cikin hanzarin ta ɗauki veil ɗinta me shara-shara ta yafa, ta fito daga ɗakin nasu ta nufi ƙofan fita.

Naseer wanda tun isowarsa ƙofar gate ɗin gidan memories ɗinsu da TAIMIYYAH ya shiga dawowa kwanyarsa.Sai ya dinga jin wani zumuɗi da shauƙin son ganin kyakykyawan face ɗin TAIMIYYAH da yayi missing tsayin lokaci.

Sabida Basmah ta yaudare shi da cewa idan ya zo,ita ce zata san yadda za a yi ta jawo masa TAIMIYYAH zuwa sasan su, ba tare da Iyah tama san ya zo gidan ba.

Ya cigaba da jingina da jikin motarsa hannunwansa duka biyu harɗe saman ƙirjinsa,ya kafe ƙofar gate ɗin da kallo yana jiran ganin me fitowa daga ciki.

Basmah ta buɗe ƙofar ta fito cikin wani irin taku na ɗaukar hankali,take nufowa inda Nass yake tsaye.

Nass ya dinga bin ta da kallo yana ji kansa ya fara wani irin sarawa,tun lokacin da ya ɗaura idanunsa akan Basmah.Ta ƙariso tana kashesa da wani irin murmushi,da har haƙoranta suka bayyana,kafin tayi magana cikin narke murya tana cewa, "Sannu da zuwa Yah Nass mu je daga ciki ko."

Nass da gaba ɗaya kansa ke wani irin juyawa, sai yayi saurin dafe goshinsa da hannu yana cewa,

"Okey toh."

Readers Also Read