Tarko complete novel - Chapter 30
Tarko complete novel Chapter 30: Tarko complete novel Chapter 30. ****** ********* ****** Zaune muke a gida yau weekend ne ban shiga school, Dom haka muke…
3,411 words
****** ********* ****** Zaune muke a gida yau weekend ne ban shiga school, Dom haka muke ta zuba, hiran mu ni da Anty da,su Amira yaran anty, Anty Amarya ke ce min ashe haka akayi da Abubakar lokacin tarewan amaryan sa kan dakin ki, Kirjina naji ya bada dam duk da ban kai gajin may akayi, ba, Anty Amarya tace sai shekaran jiya muna hira da yaya Saratu take fada,min ai, Anty halan mi an,kayi ? Cikin kaguwa don son jin abinda ya faru da dakin nawa, Dariya Anty Amarya tayi tana cewa, abin ma ni walle dariya yaka bani, Wai samun wuri don kawai jan magana wai su alla dole sai dakin ki zata zama, Dariyan yake nayi nace to ai sai a bata tai tazama, ko Washi nan ai basu isa ba wallahi don ko yasa ta dasai takwashe kayan ta da hannun ta , Ai ance sai da mahaifin shi Abubakar ya buga mai wayan cin mutunci a kai, Ido na lumshe yayi da ni irin bakin ciki da bacun rai ya tokare min makoshi na, Sai kuma naga Anty na kwasan dariya ita kadai tace ance auta su Baban ku ya na cen shi da sarakuwar ku, A hankali na ce baba Wadda ko ? Anty Amarya tace to shiya, Shi da wani aboki nai makwabcin ku suka dinga zabga masu bulala sai da suka watse gidan, Nima abin ya dan bani dariya don nadan yake saboda nasan halin Baba Wadda zai iya yin hakana, Tsaki naji Anty taja tana cewa kyale banza wai so tayi ta ciza tagani inda jini, Ke ga da tasamu shiga dakin da shike nan ke baki da mutunci sam ga idon ta da kowa nata, kuma, Kuma ance tsohuwa ta don duk ta girmay maku wai ? A sanyaye nace gaskiya ne Anty don dai gaskiya ba yarinta ba, Ke ma san ta ke nan ko? Na ce ai tazo wai ganina da kuma yi mashi murnan samun girma, Anty tace yar iskan tsohuwa kawai, duk tagama zubewan ta a titi ta dawo ta nade dan yaro,, Gaskiya sai kunyi da gaske don irin su ba karamin sheri da kisisina sunka iya kullawa ga namiji ba, Yazaman to sauran basu gane komai gare shi sai dai ita uwar iyayi, Amma ta makaro wallahi don dai babu yadda zatayi dake, ke kan, A sanyaye na ce Anty ni wallahi har tunane nakeyi yadda zan zauna tsakiyan wa yan nan matan don dai gaskiya babu warin yi na cikin su, Da sauri na Anty ta girgiza min kai tace ki kwantar da hankalinki babu abinda zai, faru, dake sai alheri insha Allah kuma ki ce na fada maki, Ke dai ki fake duk abinda kowa ka fada maki, in ma har wani abu ya shige maki duhu ga wayanan ki kirani dashi, A sanyaye na ce ro Anty na gode, Fita anty tayi tabarni falon zaune, sai tunane nake yi yadda zan bullowa al,amarin nawa, Wata zuciya tace min haba meenatu duk wanan nasihan da akai maki kirasa na dauka dazai fishe ki, Bansan lokacin da nayi wani irin murmushi ba ni kadai,
****** ********* ****** Shirin sallaman su mamay ya keyi fon ta samu sauki sai dai check up din da zata dinga zuwa kawai yanzu, Bawani shirin azo a gani yai masu ba saboda babu mai bashi shawaran kwarai a kai, Amma ya basu kudi masu dan yawa su rika tare da yi masu alkawarin zuwa idan an kwana biyu, Motar ma,aikatar su yasa a kai su mama har binin kebbi, Sun isa gida, lafiya inda mutane ke zuwa, yiwa mama ladi barka da arziki da fatan Allah ya tsare gaba, Labarin zaman gidan yaya Abubakar mama ta hana duk su Anty mariya da Baba Wadda fadin yadda zaman su ya kasan,ce a gidan, Abinda bata sani ba shine labari ya riga su isowa ko kamar a gaban su akayi, Har a zuciyar mama ladi bata kaunar taji zancen gidan dan ta yanzu,,
Yanzu yaya sai faman zuwa garuruwa yin aiyu ka yake yi dan haka bai samun zama garin sosai,yanzu saboda yawan tafiye tafiyen da yake yi, Wanan daman da suka samu yasa Salawatu yin yadda taga dama ita da abokan ta, a gidan batare da wani tsangwama ba, Daga Lagos, yau yake tafe bai fadawa kowa cewa zai dawo a ranan ba, Sai ganin shi kawai su kayi girshi a ranan, a lokacin Salawatu da mutanen suna zaune a falo sai shewa su keyi hankalin su a kwance, Batare da yace masu komai ba ya kutsa kanshi shigowa gida, wa yanda yasamu a falo sun fi wan da ya baro a wajen gidan,, Indon shi ya sauka a kan abincin da sukaci a falon sunyi baja, baja da shi, ko ina tsakiyan falon,, Direct ya wuce zuwa dakin shi batare da ya tanka masu ba,, A dakin shi yana shiga ya dafe bangon dakin tare da, dafe goshin shi saboda tsananin bacin rai, Jin an shigo dakin ne a lokacin, yadan sashi bude idon shi da sukayi ja, Salawatu ce, tashigo tana sake mai wani shu,umin dariya, Tana kokarin, zuwa rugunmar shi, ne yadakatar da ita cikin wani irin yanayi,. Dakatawa tayi don ganin yadda yanayin shi ya nuna Bai ya ce mata komai ba ya fada bathroom din shi tare da cire kayan jikin shi ya watso ruwa don yaji sanyi, Ita ko Salawa komawa tayi ta Sallami bakin ta cikin gagawa tana sheda masu cewa su tafi don Allah kafin oga ya fito, Da sauri tasa a ka gyara ko ina na gidan tankar babu abinda ya faru a gurin, Sallah yaya Abubakar yafara gabatarwa bayan fitowan shi yadan jima wurin sallah zaune, Sai ga Salawata dawo wanan karon fuskan ta da damuwa sosai acikin sa, Sau guda ya daga kai ya kalle ta bai iya cewa komai ba, Wayan shi ce tai kuka a lokacin don haka ya mika hannu ya dauka, ALIYU ne abokin shi ke magana dashi a lokacin, Zance sukeyi kan cewa mijin sister shi ya samu accident din mota suna asibin sokoto dashi, Sosai ya jajan tawa, Aliyun irin halin tashin hankalin da suke ciki, Salawatu dake tsaye, ta samu gefen bakin gadon shi ta zauba tana jiran shi, Yana gama waya da Aliyu, ya shiga neman noba na, a lokacin, Ina tsaye, a bakin laundry din gidan uncle ina kokarin a je kayana da zan wanke, Ganin wanda ke kirana yasani saurin barin gurin zuwa dakin mu, don in karba mai , Saman gadon dakin na kwanta nai rub da ciki ina mai kokarin kar ba sallama, Da sallama na dauki wayan na,shi tare da mashi barka da wuni,, Cikin dan yanayin murya ba walwala, ya an,sa, min Cike da zargin yadda naji yanayin shi nai, mai ya aiki ya iyali ? Sai lokacin naji ya dan sauke yar murmushi da ga yanayin shi, Ba wani magana sai tambaya ya jefo min da cewa, Yaushe ne zaki gama exam din kine wai Meenatu,? Cikin sauri Salawatu da ke zaune idon ta na kallon center carpet din dakin ta dago kanta tana kallon shi cikin mamakin jin ya kira wata agaban ta, Cikin dan ida,inda na ba shi ansa da ce wa yaya dama ai, ko da mun gama zamuyi continues semester ne, Murmushi na ji yayi alamar rashin yadda da zance na, Amma Uncle Nafi,u ya sheda min cewa idan kun gama zaku dan yi hutu ai ko ? Manya idanuna nazare tankar yana kallo na tare da gyada kai,, Ban bari ya cimma zancen ba na ce, mai ya jikin Mama tasamu sauki dai ko? Hmm najiya yace look Meenat ki zauna da shiri don zan zo anytime from now, in dauke ki,don zaki zo hutu nan ne, Saboda ba,zan yarda ace ko hutu bazaki dawo dakin ki kiyi ba,, Cikin son in dauki excuse naji yace, kinji na fada maki, don nasan cewa kun rufe school tun last week, Don ban gida ne yasa ban damu da ki dawo ba a lokacin, Nace amma yaya kasan yanzu karatu ya ke min sosai don ban da enough time da zan zauna, Baijira na gama magana naba naji ya kashe wayan ta hanyar cewa ki gaida kowa agidan sai nazo kenan, Ya kashe wayan tare da komawa ya jingina kan shi ga kujeran dake, kusa dashi yana mai lumshe idon shi, Da kyat Salawatu ta iya saita muryan ta tana cewa, Sir ka dawo lafiya ? Cikin daurewa yace mata lafiya, Wani tambaya ta jefo mashi da cewa, Meenatu zata dawo nan ne kuma ? A hassale ya dago kai yace mata Salawatu will you live me alone please ? Ganin cewa rayuwan shi duk a bace ya ke saboda, yadda ya samay su taf a gidan nashi daya dawo dazun, Sai kawai ta zube kasa gwiwa bibiyu tana mai daga hannayen ta sama tankar mai neman gafara tana cewa, Sir please iam so sorry yan uwa nane su kazo tayani murnan aure daga garin mu, But daga yau bazan kara shigo da baki batare da ka sani ba, Sai a lokacin yadan ji sanyi azuciyar shi ganin irin yadda tai mai ladabi saboda ta yi laifi taba da hakkuri, Abinda Sadiya bata taba yi mai ba duk da tsoron, shi da take dan ji, A hankali ya furta give me a cup of tea please ?
****** ******** ****** Bayan mungama wayan dashi, wayan nawa na bi da kallo tankar shine a tsaye maimakon wayan, wayan , ya koma min abin mamamaki Numfasawa nayi gami,da gyara zama, wata sabuwa nace a raina, Muryan Anty, Amarya ne naji tana shigowa dakin daga kitchen, da take girki, Ganin irin yanayin da ta ganin a ciki, yasa ta min wani irin kallon tuhuma tana cewa lafiya dai ko ? A sanyaye, nace Anty, yaya Abubakar ne ya kirani, Ta ce tau, pa Ya kukayi shiru nayi tare da dukar da kai, na kasa a hankali nace wai cewa yayi in shirya anytime zai zo ya dauke ni, Yar dariya Anty ta sake tace ashe zaki bamu kewa, don tun da yace zai zo zaizo din ne, Wayan ta na,ga ta hau dan nawa tana cewa hello hajiya Don Allah a hadawa meenatu gunba da tsumin ta don ta kusa wucewa, hutu,, Tsam na mike don komawa gurin laundry don in wanke kayana, Har zuwa lokacin da, nagama wakin na shanya, Bayan mugama komai da dare, muna zaune ne anty ta,dubeni cikin, Son yin magana mai muhinmanci, don zuba min idanuwan ta tayi cikin nawa, tace, Meenatu Nace na,am anty, Sai kuma naji tai shiru kamar may tunanen wani abu can daban, Sai tace ina fatan duk abinda aka fada maki yana a cikin zuciyar ki, Wani irin abu naji azuciya na kamar shakku, anya kuwa zan iya, ? Muryan Anty na ji ta kara kiran sunana a karona biyu, tana ce min Kar ki boye min komai ki daukeni tankar yayan ki na ciki daya, Fada min yadda kika fahinci zaman ki da Abubakar a kwanan baya da kika tai, hutu, can gurin su, Kaina kasa na fara labarta mata dan zaman da mukayi da su, sai da ba dukka ba, Saurare na takeyi inda ta zuba min idon ta har na kai karshe, Ajiyan zuciya naji tayi tana cewa Alhamdullahi don fa zancen ki idan kinci gaba akwai kyakyawan fahinta da zai biyo baya nan gaba, A sake na tambaye ta da cewa yanzu may zanyi Anty ? Don kinga cewa ita wanan matar da take gidan yanzu ba irin Anty Sadiya bace, Tsaki Anty amarya taja tana cewa kyale tsohuwar banza ai kurciyar ki zaki nuna mata kin fita iya bariki, Muma matan hausawa mun iya duk wani barkado da suke yi wajen kwace miji Fuska a daure tace ai kawai shi Abubakar, aki sakewa jiki ki kauda duk wani kunya a idon ki, Don fa rashin samun irin hadin kan da har ya kai shi da hangen gurin Salawatu zai samay shi, Don fa tunda kikaga har ya kiraki akwai matsala duk yadda akayi, Don haka rashin samun hadin kai daga gurin ki, zai iya haifar da matsalan da zai sa ya koma gurn ta, Na nisa nace to Anty zanko iya ashe,? Murmushi tayi tace min cikin girgiza kai, ke dallah wuce can sai kace ba yar Birnin Kebbi , Murmushi nayi tare da cewa na gode Anty, Takarashe da cewa gobe zan shiga kasuwa in sayo maki sabbin nightgown masu kyau, Da kuma kayan sawa sabbai don ki canza kin san kudin ki suna hannun uncle dinki yasa a banki,
****** ********** ****** Tun wanan ranan na,fara shan abubuwan hadin da mama hajiya ta hada min Sai anty ta tabbatar da na shanye abinda takawo min a cup san, nan zatabar dakin, Kafin wani lokaci jikina sai sheki da daukan ido ya ke ni kaina nasan na canza sososai irin yadda nake jin bakon al,amari a tare dani, Aikin komai, anty amarya bata yarda na yi, shi a cikin kwanakin nan, Dinkuna masu kyau da daukan ido anty ta dinko min tare da night gown masu kyau da tsada,
ZEEE MAKAWA YELWA 🕸🕸🕸TARKO🕸🕸🕸 🕸🕸🕸🕸🕸🕸 4⃣9⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA
ALLAH -AL-KABEER
Shafikune yau uwa masu kauna Hajiya RABI, Assibitin Murtala sokoto, da Hawa,u Abdullahi school of health and Technology Gwadabawa, sokoto,state, Nutrition department,,
Kaman yadda Anty ta umurce ni da kada in fassa shirin da nake don anytime din da yace zan iyaganin shi,kamar yadda ya fada, Don haka ban fasa ba kullun sai ta tsure ni da yan dabarun ta na mata, tana a tsaye zan shaye komai tas inbata kofi, Barci nake yi yayin da ake ta kwada ruwan Sama a gari wuri ya koma wani irin cool weather, Anty naji tana tashina daga barci ina bude ido sai ta miko men wani plate, da ke dauke da naman yan tsuntsaye guda biyu a plate, din, Naman na tsurawa ido zuwa wani dan lokaci ina nazarin ko maye haka ? Ki wanke bakin ki kizo ki ci naman tantabarane don naga kina masu wani irin kallon, Fuska na ya mutse alaman ban so haka ba, don dole na mike zuwa bathroom wanke bakina, Anty na saman kujera ina daga kasa zaune ina ci ina ya mutse, fuska, don ba dadi, Na dago kai inda anty take tana gyara wani abu a cikin roba, Nace fuska bace naci anty, tsuki tayi gami da daka min tsawa tace, Dalla malama cewa akayi ki cinye dukka ki kuma shanye romon gaba daya, Ido nafitar wajw sai kuma na kwabe fuska kamar zanyi kuka nace, Wallahi anty ba dadi ko kadan, a cikin shi, ta galla min harara tace baki dadi ko ? To ko babu dafi dai wanan sai kin shanye shi tas yau, Haka akayi inda na shanye na tara kassuwan a wani plate, Anty ta zuba su cikin wani leda ta fita dasu waje wai zata rufe su ne a cewan ta, Tun da na gama cin wanan naman nasha ruwa sai nafara jin wanu irin kasala yana rufe min jiki a hankali, Kara kwantawa nayi don dama weather ranan Alhamdullahi, Anty ta shigo dakin tana cewa hajiya Mama ce ta bugo waya take tambayana cewa, nadafa maki tantabarun kuwa kin ci? Nace cikin wasa ni dai ki fadawa wanan tsohuwar ta barni haka dai please ? Yar murmushin jin dadin yadda na mai da mahaifiyar ta tankar kakana tayi,, Tace don kin samu bat sa kishiba har tana gyaraki aida tabar ki da wa yancan maguzawan kishiyoyin naki , Nace aiko in gudo in dawo dakin ta direct don wanan Salawan da kike gani anty nasan za a sha daga da ita, Cikin muryan na Anty tace gwada mata cewa ke ma fa yar Kebbi ce ba Sanya don kin san mu matan kasan hausa sai wace taso zama bora agidan mijin ta, Meenatu muda ka bude ido da hudubar zama da miji har kishishiya tun muna kanana, Zan kai kai saman pillow in gyara kwanci wayana yai kara, A zatona Babana ne yakira saboxa naga cewa, safiya ne rana batai wani yi ba a lokacin sosai, Wata nombace da ban san,ta ba, na dauka ina mai kwarara sallama, Muryan Yaya Abubakar ne naji yana amsa min cikin irin dakewan nan nashi na kullun, Yaya ina kwana nace cikin siriri yar murya na ahankali, Sai da naji sauke ajiyan zuciyar shi sanan ya amsa min da cewa lafiya kalau Meenatu, Sai yai shiru, nima a nawa ban garen dan shirun nayi masa, Sunana naji ya ambata cikin wani irin murya mai saukewa mutun kasala da cewa, Meenatu, ina hanyan sokoto yanzu haka zan zo in dauke ki zamu tagi Niger Reporblic, Ban san lokacin da na maimaita maganan ba da cewa Niger ? Murmushi naji yayi yace eh Niger, ko bakya zuwa ne yai maki nisa, Na saki a jiyan zuciya nace zan tafi mana yaya Yace don kawai mu biyo ta nan mu dauke ki nai wanan tafiyan ta mota, Na lumshe idona ina tunanen yadda zan tafi Niger, din, Murya Yaya Abubakar naji yana ceea ko Uncle bazai bari in tafi mashi da yar shi wani kasa ba, A hankali na sake wani murmushi mai fitar da sautin cool, nace ,a,a ai Uncle baida iko dani kamar kai, ko banza, Allah dai ya kawo ku lafiya ?' Nace cikin kara lumshe idona, saboda wani irin abu da naji a lokacin, Na sauke numfashi bayan mun kashe wayan tare da kurawa hanya shigowa dakin ido, Ina tunanen yadda zan fadawa anty zancen tafiyan nawa, Kayan wanki yaran ta da aka wanke ta shigo dashi dauke a hannun ta, dakin namu, Tambayana tayi cikin son jin may yace yai maganan ranan da zaizo kuwa? Sai da na sada kaina kasa san nan na ce a hankali cewa yayi wai yana hanya zamu tafi Niger ne, Itama Anty acikin mamaki ta maimaita da cewa Niger shin? Na kada mata kai alaman eh, Ba bata lokaci naga anty Amarya ta hau shirya min kaya da kanta, Sai zuwa karfe daya na rana yaya ya iso shi da driver shin , Sai lokacin da na tabbatar da cewa tafiya fa zamu yi ne hawaye yazo min tab ga ido na, A lokacin Yaya Abubakar suna tare da Uncle dina a folo, suna dan shan drinks, A falo inda suke zaune da Uncle na samay su inda nadan zagaya gefen Uncle din na durkusa a gaban shi idon yana fitar da hawaye, Na kasa magana sai dan sheshekan kukan da nakeyi, kawai, A hankali na iya bude baki ina cewa, Uncle zan tafi, Kamshin turaren dake jikina Yaya Abubakar yadan shaka abinda hakan ua saukar mai da yar kasala a take har takai ga ya dan lumshe idon shi a hankali, Ga kukan da nakeyi yana torching din zuciyar shi, Cikin dakewa ya mike tsaye, tare da yi wata irin murya yai magana da uncle cewa To zamu kama hanya sai dai in Allah ya dawo damu lafiya sai mu biyo ta dauki kayan ta, Cikin dan kuka na juya inda su Anty suke tsaye na ce, a sanyaye anty mun tafi, Wani iri yaji a zuciyar shi don jin abin yakeyi kamar ya jawoni zuwa jikin shi a lokacin ya rarashe ni,, Mutanen gidan mu na Uncle suna daga min hannu kamar kullun, suna min bye, bye motar mu ta daga,, Daidai muna fita kwanar layin mu naji hannun Yaya Abubakar a cikin jiki na, Idona na lumshe lokacin da naji hannun shi a cikin jikina, A tare muka sauke ajiyan zuciyan lokaci guda, Muryan shi naji yana cewa bakya son tafiyan ne Meenat,? A hankali nadago kai na dan kalleshi karo na farko tun zuwan shi, Yayi wani haske fatan jikin shi sai sheki yakeyi don kyau, Yar,Sajen faskan shi da ya bari ya dan kwanta mai lub a saman kyakyawan fuskan shi, A lokacin da yake min maganar ashe idon shi yana a lumshe, ya kara bayan shi a makarin kujera, Batare da na kara kallon shi ba na ce cikin tausa murya, Kawai dai, ina jin kewan rabuwa na dasu ne da zamuyi, A kara cewa amma kuma baki jin dadin kasancewa da yayan ki da zakiyi ko ? Hmmm kawai na iya cewa batare dai nai magana da baki ba, Shima din bai kara cewa komai ba sai ji nayi ya kara matse ni a jikin shi tankar wani zai kwace may ni, Driver sai kwarara gudu yaje a saman titin dake cikin sahara, abin shi,