Tarko complete novel - Chapter 45
Tarko complete novel Chapter 45: Tarko complete novel Chapter 45. Tashin hankali wanda yafi karfin furta zance shi Yaya Abubakar ya shiga ciki, Don sai…
3,636 words
Tashin hankali wanda yafi karfin furta zance shi Yaya Abubakar ya shiga ciki, Don sai gumi ke feso mashi da kafafen jikin saboda irin yadda ya ke ji, a lokacin, Allah kawai ya tsare su don tuki kawai yakeyi batare da yasan may yakeyi ba, Tunane kala kala sun zo mai a lokaci guda batare da yasan yana yi ba, Sun iso gida sun samu Baba Wadda ya iso a lokacin don har yaci abinci yai sallah ko, Nan suka zauna da Baba Wadda a falon gaba dayan su a na gaisawa, Ina kitchen ina yan aiyu kana tare da kara rusa abincin a cikina, Jin shigowan su yasa na fito don in masu barka da dawowa, Kallo guda naiwa yanayin Yaya Abubakar nagane cewa yana cikin tashin hankali, A take naji banji dadi ba don gabadaya a rude yake sai faman mazurai da idanu yakeyi yana kallon ko wani sashe nagidan kamar mai nemqn wani abu, A lokacin da naji Baba Wadda zai fara mashi bayanin akan Sakon da yazo dashi sai na bargurin zuwa part dina, Ganin irin halin da Sadiya take ciki ne Baba Wadda wanda yaro ne sosai amma ya kawo shawaran cewa ya kamata fa asanar da yan uwan Sadiya don a samu wanda zaizo jinyar ta, Cikin murya mai nuna damuwa da kasala Yaya Abubakar kecewa saida nai tunanen hakan nima, Don kaga wanan tsohuwa dai tai muna mutunci sosai gaskiya, Ba kuma zatai ta zama a nan haka ba, don ita ma tana da nata laluran ai, Matsala guda yanzu shine ai kasan halin irin na Sadiya, ba kirki ne gare ta ba, Ba ruwan ta da yan uwanta bakajin tana zancen kowa daga cikin yan uwan ta, Ba ta damu sam da yan uwan ta ba balle wani daga cikin su yaji dadin zuwa gurin ta, Ai akwai wata wace ta taba zuwa lokacin da nafita karatun wata shidda amma kafin in dawo matar ta wuce saboda irin zaman da su kayi, Baba Wadda yace amma dai duk da haka ni sai nake gani da dai a sanar dasu zai fi, Don kada daga baya su zo su ce ai ba,a fada masu ba, Gaskiya ne kuma inji Yaya Abubakar wanda ya fada cikin bata rai, Yana cewa zan kirasu in sanar da su idan sun zo to idan babu wanda yazo kuma shi ke nan,
A lokacin Salawatu ta shigo gidan saye da wani dogon riga sai dan wani yalalon gyale daidai wuyan ta, Gaba dayan su kallon ta sukeyi kowa da irin kallon mamakin da yake mata, Duk da ta sheda Baba Wadda amma sai batai masa sannu da zuwa ba tasa kai zata shige, Cikin wani murya Yaya Abubakar yace, Salawatu da karfi abinda yasa ta juyowa tare da dawowa baya, A cikin bacin rai yace baki ga Baba bane zaune ko baki san shi bane ? Kunya taji amma sai ta dake tana cewa, gaskitan kula dashi ba don ban kalle gurin ba, Sannu da zuwa ya hanya tace tare da wuce wa çiki, Yaya Abubakar ya dan rintse idon shi don shima halin shi kaman namune don bamu kaunan a taba yan uwan mu, Baba Wadda bayan shigewan wata ya dubi Yaya Abubakar yace Maisunan malam wanan matar taka ai ba sa,an yin ka bace, don da alama zatai wuyan saitituwa, kamar sauran mata, Murmushin yake kawai Yaya Abubakar yayiwa Baba Wadda don jin abinda yace, Ya san halin Baba Wadda shi bai boye zancen zuciyar shi sam Wayan shi ya jawo daga aljihun shi inda yafara neman layin wayan mahaifiyan Sadiya,, Kamar bazata daga wayan ba amma sai yaji muryan ta tana cewa Salamu Alaikum, Sun gaisa acikin mutunci sai dan shiru ya biyo baya, Can Yaya Abubakar yace Mama dama Sadiya ce ba lafiya yau kwana biyu ke nan, Gaban Hajja ne ya fadi don itama kwana biyu kenan da take fama da Dodon ta wan da ya dawo duk jikin shi ya salle saboda tabin da Sadiya tai masa, Amma karfin hali irin na Hajja sai cewa tayi yanzu may zan yi mata nida ke nan, ku kuna can, Allah dai ya bata lafiya Daga haka ta kashe wayan ta tabar gurin cikin kunan rai don a lokacin taji hamman Dodon ta wanda idan yai hamman zakaji wani irin wari, mai doyi, yana tashi, a guri, Wani irin mamakine ya kama Yaya Abubakar a lokaci guda, Yadade da sanin cewa,Sadiya halaiyan uwar ta ke gare ta, na rashin mutunci, Bai kara gaskan tawa ba sai yau din ya tabbatar da hakan , Ace yar ki ga halin rayuwan da take ciki amma sai ki cewai, ke ya zakiyi babu Allah ya sauwa sai kawai ki kashe waya don rashin imani,, Baba Wadda wanda ke daga gefe yana nazarin yadda suke waya da Hajja yace, Ya ce tayi ma halin nata ko ? Murmushi mai kama da yake Yaya yayi kawai tare da hade wasu miyau masu zafi, Daga gurin da yaya Abubakar yake zaune, kasan carpet, ya jingina bayan shi ga kujera, Ya sanya hannayen shi guda biyu ya dafe goshin sa da su, Zuciyar shi sai wani harbawa takeyi tana masa ciwo, da radadin saboda duk, abin duniya yai masa yawa, Falon na shigo da sallamana, ganin yanayin sa yasa na gaishe shi a sanyaye, Cikin dauriya Ya Abubakar ya cire hannu daga goshin shi ya,dago idon shi da,suka rine sukayi ja, Yake ce min a hankali Meenat kina kuwa shan maganin ki ? Na ansa ma shi da cewa ina sha yaya har sun kusa karewa ai, Baba Wadda wanda ke gefe sai cewa yayi Meenatu malam na cen duk ya tayarwa mutane da hankali yana cewa wai kina garin mutane babu mai kula da ke, Daga gurin da nake na sake wani irin murmushi ya subuce min, har ina yar darawa, nace malam ho, Ya Abubakar ya ce, daga gurin da yake zaune ai kasan malam baida kamar meenatu duk gidan nan, Ina fada mashi cewa ta yi bari ya na batun fasa min dodon kunena da wani irin salati, Wani irin duban wasa na sakewa yaya Abubakar ina cewa amma dai kowa yasan cewa kaine dan gaban goshin sa bani ba, Ni da watarana muke fada har ya hana min fura, ko zuman cin masa, Abin mamaki sai kiran malam din ya shigo a wayan yaya Abubakar, a lokacin, Cikin dan ya mutse fuska yaya Abubakar yace ga dan rigiman nan ya bugo ai, Nace, Allah sarki malam yana dai ji da kai Baba nasan ya bugone yaji ko ka iso, Bayan sun gaisa ne yake tambayan ma su jiki yaya Abubakar ke masa da,sauki, Sai kuma yafara mashi bayanin yadda zai da maganin da aka kawo mashi, Sai yake cewa yaya Abubakar ya tabbatar da cewa yai sadaka da masa mai zuma ranan jumma, Sai kuma gyadaw wanda akasoya, suya ruwa wanda zai ba wa yara kanana sadaka,, Sai sugar na kwali cubes yaraba yara kana shima yace duk wani abu wanda zakaba yaro yasha har yaji dadi dashi zaka hada ka basu sadaka, Amma ka tabbatar da duk yadda nai bayani kayi da wa yan nan sakon kayi Godiya sosai ya Abubakar yayiwa malam tsoho tare da fara mashi bayanin abinda malam dake kauyen da suka tafi yace masu, Malam tsoho ya kira sunan yaya na kwarai da cewa, ABUBAKAR, yaya ya amsa mashi da cewa na,am malam, Malam yace ba sai ka fada min ba don ni nasan komai ko, Don tun bayau ba nake hasashen wasu abubuwa da dama a gidan ka, Yanzu ne zargina ya tabbata cewa aike ne ake maka daga nesa, Don ni tun auren ku da Aminatu nagane cewa akwai wani bakon al,amari a tare da kai, Amma mutun karya yayi saidai Allah badai mutum ba wallahi, Tun lokacin da suka fara zancen abinda malam ya fada masu hankalina yai mugun tashi, Muryan Baba wada ne suka ji daga inda yake zaune yana cewa cikin dan kwantar da murya, Ai wanan mace muguwa ce yanzu mutane ko da kudi basu bi hanyan gidan ta, Yaya Abubakar ya ke tambaya da crwa wake nan ? Ba wani shakka ko tsoro a fuskan shi ya Hajja mana, Da sauri naga yaya Abubakar ya dan juta gurin da nake yana kallo na, Baba Wadda wanda bai san may ba sai ci gaba yayi da fadin Ai tun ranan da ta shigo gida da nufin gaida Maman mariya (Mama Ladi) Iskokin mata yai ta tashi harda mariya wace mun koma daga nan ba,a wani dade ba Mariya nada iskane ? Yaya Abubakar ya tambaya cikin jin haushin hiran shirmay da Baba Wadda keyi, Nan Baba Wadda yashiga zaiyana muna tiryan tiryan yadda al,amarin ya faru a ranan, Dagani har yaya Abubakar shiru mukayi tankar ruwa cimu muna sauraren abin al,ajabi, Idan hankalina ya kai dubu babu wanda bai tashi ba a ranan don tsoro, da fargaba, Don tun ina karama nake tsoron Hajja muna ji a,na cewa muguwa ce, Wanan labarin yasa na shiga wani irin hali wanda har na kasa boye, Ya Abubakar wanda sai Innalillahi yake maimaitawa, don mamaki, Duk da ba wai yarda da zancen yaya Abubakar yayi ba amma sai zance ya sosa mashi zuciyan shi sosai, Shigowa Sallawatu cikin wasu matsatsun kaya tana taunan chewing gun, da wani irin kara, wanda ya dawo masu da hankalin su gare ta,, Cikin wani irin murya take cewa Yaya Abubakar sweet Oga, na son,ganin ka ne fa , A hankali ya dan dago kai ya dubeta sai yake ce mata, naji ina zuwa, Bai wani dauki lokaci mai tsawo ba ya mike tare da dan tsuki, ya bi bayan shu,uman,,,
Wani irin ajiyan zuciya na sauke, tare da kallon gurin dashupba Wadda yake zaune, a cikin mamaki, Nan nake tambayan shi zancen al,amarin Hajja ya ke bani labarin irin muggancin ta da takeyi,, Tsoro ya kara kamani sai naji ba ma zaman gidan ba duk garin gaba daya ya fita raina,,, Nace gaskiya Baba ni zan koma sokoto ne don duk garin nan ya isheni wallahi Baba Wadda yace Meenatu in sha Allahu babu abinda zai samay ki, Don Allah ya natare da bayin shi , ke dai kawai ki rike ibada da addu,oin neman tsari daga sherin mutun ko dabba ko, aljan ko kwaro, Nace ina yi duk wanda malam tsoho ya umurce ni da yin tun da farko, Yace Allah ya tsare ni kin ga wanan matar ta mai sunan malam batai min ba sam, Don duk take taken ta na ya zauna da ita ce ita kadai don wanan bata kaunar ta bude ido ta ganshi da wat mace daga cikin ku, Baba Wadda yace tun dai ke Meema don baki gari a lokacin zuwan ta gidan nan ida ta dage adole sai dakin ki, zata zauna wai yafi kyau da girma, Sai da,na nuna,mata ni da Hamza cewa mun fisu iya,iskanci, sannan aka zauna daidai... Nace Baba har yanzu bawai tabar ni bane ji take kamar ta daina ganina agidan nan kwata kwata wallahi, A hasale Baba Wadda yace sai dai tabar maki gida wallahi don babu inda zaki, Auren ki da mai sunan malam mutu ka raba bana rabuwane in ta sawa ran ta sauki ta, Nace cikin yar tausa murya wallahi Baba ka daina zancen ta don zaku iya batawa da Yaya a kan ta wallahi, Ai shi yasan cewa bani kaunar wanan matan a rayuwa na wallahi don ni sam batai min ba,, Saboda kallon yan Togo nike mata, knga waya dai ta taho tai mashi, Dariya sosai Baba Wadda ya bani nace cikin dariya Baba So ne fa haka na, son ta ya ke yi shinasa,, Baba Wadda yace kai wani irin So Meena son yaudara ko ? Yanzu fa debo tahowa dai tayi ta ce mai ya taso yatashi ya bita kamar Rakumi, Yanzu ke kina iya cewa Taso kazo ya taso zuwa inda kike haka kai tsaye, Sod di ya,i gwalmad,diya,i,,,, Dariya yasani shigewa dakina don Baba Wadda a cikin serious yake zancen shi, Na shiga don gabatar da Sallah nakai wani lokaci kamar kullun ina kai kukana ga Allah, Daga inda nake zaune zancen labarin Hajja da Baba Wadda ya bamu yazo min a rai, Nan gaba na ya shiga faduwa don nasan cewa tunda malam tsoho da kan shi har ya furta cewa da matsala a gidan to da matsala ke nan, Wani irin tsoro ne ya kara ziyara na yadda baba ya fada muna cewa wai mata nata ihu suna ce ga dodo da diyan shi na lasan mutane, Tsab na mike nadauko wayana dake caji a gefe guda, Noban malam tsoho na kira duk da nasan kila yana cikin masallaci yanzu suna wuridi, Cikin ikon Allah sai naji ya dauki wayan yana cewa Aminatu ke ta, Na ansa da wani irin murya na damuwa nace nita malam, Mun wuni lafiya ya ansa da fadin wallahi lahiya lau Aminatu, Ya jama,an wajen ku,? Suna lafiya malam, sai kuma nai shiru ba tare da nace komai, Aminatu Yaya ankayi na nace malam naga sako gurin Baba, Wadda nagode Malam yace kai haba babu komai ki dai yi amfani da suwa kinjiya, Nace to malam, Amma malam, ni gaskiya hankali ya daga ga gidan nan yanzu sosai gaskiya malam bazan iya zama ba zan dawo gida ne ni, Sai kawai kafin yai magana nasaka mashi kuka mai tsuma zuciya, Subbahanallahi naji ya na fadi, yana cewa ashha Amina , Mi zai tayar maki da hankali haka nace maki ki kwantar da hankalinki don Allah,, babu abinda zai samay ki insha Allah, Nace cikin kuka wallahi malam duk kwanakin nan bana barci a tsorace nake don da idona naga wanan abin sihirin da ya shigo dakin Sadiya lokacin da yake fita, Abin mamaki maimakon malam tsoho ya nuna damuwan shi sai naji ya yi murmushin manya yana cewa Amina kwantar da hankalin, ke jiya, insha Allah babu wani sihiri da zai yi tasiri akan ki, Ke dai ki tsare adduan da ke gaban ki don babu abinda zasuyi da ke, Wanan abin da kike gani ai bai isa yazo gare ki ba sai dai in Allah ya bashi iko hakan ? Don ke ba jinin su bace sai dai yazo gurin wace adda alaka da shi, Amma ke mi kin ka hada da suwa ? A,buguda da yanzu ka damuna, shine mijin ki Abubakar ina tsoron kada su illanta shi a sanadin zaman da yake dasu, a gida, Nace cikin muryan kuka kaman mai tausayi may ya faru da shi malam ? Yace, babu komai Meenatu kwantar da hankalin ki Zaman da yake yi da yar gidan Hajja na ke dan jiyewa don kin san mace shu,umace,, Saboda haka ki kwantar da hankalinki kamar yadda na fada maki tun farko ki dinga karanta, Lahaula wa,la,quwati, illa billahi aliyal,azeem kafa 41 Kafin ki fito waje, duk safe, sai hasbunalah shima 450, Babban makami wanda zai sa har basu kaunar hada ido dake shine, Kalman shahada,,,kamar yadda na fadi a baya, Idan kuma kin fita anguwa ko kin dawo kafin ki shiga gida kikaranta, Alam tarakaifa, kafa uku ahannuwan ki, sai ki shafe jikin ki, Naji yace hummm Amina bazasu iya komai da,ke ba wallahi, muddin kika tsare wanan abin , Ke wallahi ko shi Abubakar sai ya koma ya shakkan ki, Daga gurin da kika idar da Sallah magrib ki karanta Basmsla kafa 21 a kulun, Na ansa da cewa to malam nagode, Yace kin san kanufari na amsa da eh malam ina dashi, ma, ai, Ya ce masha Allah to wanan KANUN FARIN zaki kirga guda 41 sai ki nika su ya zama gari, A kullun sai kina lasawa a hankali har ya kare , Insha Allahu zai maki amfani ta hanyoyi daban daban Amina, Don tsarine mai amfani sosai don zai maki tarei dakuma gyaraki, Watau Amina,abinda ku yaran yanzu baku sani ba shine, Wa yan nan abubuwan da akai amfani dasu a da can baya sunfi aiki bisa ga wanda kuke yi yanzu, Don da mace zata tare yin su wallahi zataga fa,idan su so,sai don haka ki yi hakuri ki zauna tare da dan uwan ki,, Sauran bayani sai ki bari duk ranan da Allah ya kawo ki sai muyi shi a fayyace, Yakare zancen da tambayan yadda na kara jin karfin jikina, Na,ansa dafadan cewa Alhamdullahi malam naji sauki sosai,,, Bayan mungama waya da malam na mike don zuwa gaida Anty Sadiya, Na samay ta zaune tana hawaye ita kadai a daki, ta,na jin sallamana tai wani irin firgigit tana cewa Meenatu don Allah kizo ki taimakamin don tun dazu na ke son in kewaya babu wanda zai kaini, Tausayi tabani sosai irin yadda na sa may da kuma yadda tai min magana, Na kamata har zuwa bathroom na kuma samo leda nace ta da ita ta tura hanayen ta kadan daga cikin ledan , Sai dai ta kasa yin hakan sai da na kama hannun ta na saka a ledan da kaina, Wanka nai mata don ta danji daman jikin ta, sai faman yi min godiya take yi idon ta na zubar da hawaye, Na gyara mata inda zata kwanta, da kuma duk abinda ya dace da dakin nata, Ina shafa mata mai Yaya Abubakar ya shigo dakin cikin mamaki yake kallon mu, Tambayan Anty Sadiya ya jikin nata ya keyi sai take ce mai da sauki don yanzu ma Meenat tai min wanka, Tare da Yaya Abubakar muka shafa mata magani a jikkin ta, muka bata na sha, Ina kokarin yi masu saida safe ne Mama Bi,u ta shigo da sallamanta, Na tsaya muka gaisa da ita sanan nai masu sai da safe,na juya zuwa daki na, Ba Yaya Abubakar ba har Maman Bi,u ba taji dadin yadda taga yanayina ba, Don kallo guda mutun zai mun ya iya fahintar cewa ina cikin yanayin damuw daga fuska na, Ina shiga dakina na fada wanka don bazan iya kwanciya haka na ba, Ina fitowa sai naji wani irin yunwa ya ziyar ce bama zan iya kwantawa batare da naci wani abu ba, Ina shiga kitchen na samu inda na aje abinci an kwashe ko ban tambaya ba nasan cewa Salawatu ce, Raina yai matukar baci na fita zuwa part din ta inda na samu tana shafa man shafi jikin ta ma , saboda duk ashe wani dabbara dabbara jikin ta ya ke dashi , Nace Salawa ke dan Allah kika juye abincin kula dukka ? Sai cewa tayi cikin wani irin kashe ido wani ya aiko ki ki tambayeni,? Na ce eh to kaman hakane don bake, ce kika dafa ba ko ? Ok to shine akace don ban dafa ba kada inci ko ? Na murmusa kai nace Salawa ke nan ashe kina son ci kika ki tsayawa ki dafawa muna, Bayan kin san cewa kece da alhakin bamu abinci yau agidan kika fita batare da kin sauke hakkin ki akan mu ba, Mikewa tayi tare da cewa ke Meenat wallahi rashin kunyar ki ya isheni don bazan daukar maki raini ba, Wani irin harara na watsa mata na ke baki isa ba wallahi, Na juya zan bar dakin ina cewa kindai ji kunya wallahi mace bazata iya tsayawa tayi girki ba sai an girka tazo ta cinyewa mutane, don rashin kunya, Nafito daga dakin fuuu muka hade da Yaya Abubakar wanda yafito kai Baba Wadda masauki, Da mamaki yake kallon na ya na cewa a zuciyar shi may yakawo ni dakin Salawa a wanan lokacin haka ? Itace tafito bayana tana cewa wallahi ni sai in maki dukan tsiya, Ganin Ya Abubakar a tsaye tai saurin cewa yauwa Sweet Oga dama ina son in fada maka cewa Wallahi kajawa yarinyar nan kune, Don muna auren ka a tare, does not means raini da rashin mutunci zai shiga tsakanin mu, Yace cikin daga murya wai may ke faruwa ne haka duk kun kasa yi min bayani, Salawatu tace, wai kawai sai gata tafado min daki tana tambayana cewa ina abincin da ta aje a cooler, Ni ce har don samun guri zata zo har daki takawo min, rashin mutunci wai naci abinci, Ya Abubakar yace to ke kinci ne ? Tace na ci mana tunda angirkane don aci, Kece jika girka da zakici au dear don bani na girka ba kenan bazanci ba, Na fito daga kitchen ina cewa kawai na girka abinci sai ki zo min kamar shonike ki kwashe abincin, gaba daya batare da ma kin raga mun ko da kadan ne,, Wani tsawa Yaya Abubakar ya daka min yana cewa ke Meenat ban son hayaniya fani a gidan nan, Don kin dafa abinci taci shi har zai kawo fitina haka ? Nace to ai yaya itace ya kamata ta girka muna muci amma tasa kai tafita tabar gidan, Nima don zuwan Baba wadda yasani girkawa kada yazo aji kunya, Ya Abubakar yace OK shine, kuma akace bayan shi kada wani yaci abinci ko ? Nace yaya abinci na ne fa da nake son ci insha magani Look Meenat bana son fitina for god sake kubarni in huta please ban so banso Ban iya çewa komai ba sai idona da yakawo hawaye a lokaci guda, nake jin wani irin baci rai da mamaki suna cimin zuciya, Na juta kitchen ina hawaye tare da dan sharewa a hankalo da bayan hannuwana, Gashi bazan iya kwantawa ba banci ko mai ba saboda irin yadda nakejin cikina yana min, Na dafa tare da kwashewa na nufi dakina dasu, Sai da naci nasha sanan na kwashen kayan zua kitchen inda na samu ankashe wutan falon gaba daya , Haka ya tabbatar min da cewa maigidan ya kwanta ke nan a lokacin, Wani irin tsoro naji don duhun da ya mamaye falon gaba daya a lokacin, Da saurina aje kayan na juya zuwa dakina don sai ina ganin kamar wanan abin zai iya fito min a lokacin,