Kenza eBookz

Triplets book 2 complete - Chapter 8

Triplets book 2 complete - Chapter 8

Triplets book 2 complete Chapter 8: Triplets book 2 complete Chapter 8. Ganin Kausar yasa suma suka fara na su ihun murnan, su Rimsha sun tsorata sosai da…

4,469 words

Ganin Kausar yasa suma suka fara na su ihun murnan, su Rimsha sun tsorata sosai da jin yadda suke ihu, basu san yarabawa bane, yarabawa idan suna magana cikin kwanciyar hankali ma sai ka ɗauka faɗa ake, saboda Allah ya zuba musu murya mai sauti, har sama idan suna magana, ina ga kuma abun murna ya samu, ai shikenan kuma sai dai wanda bai saba ji ba ya toshe kunne

Gaba ɗaya sun cike anguwar da ihun Kausara ta dawo Kausara ta dawo, wannan ya ja Kausar ta nan wannan ya ja ta ta can, farinciki a wajen su ba'a magana, babu wanda ya kula da Rimsha da Ayla, Allah sarki bayin Allah sai bin su kawai suke da ido, sun ga abun da yafi karfin su.

Almost 20mins ana wannan ihun murna na dawowan Kausara kafin iya Kausara ta jata zuwa cikin gida tana faɗin suje tayi wanka taci abinci sannan tazo ta basu labarin ina ta ɓata, suma makotan kowa ya wuce gidan sa, suka bar su Rimsha tsaye sun rasa madafa, sai zare ido suke gwanin ban tausayi.

Har sun shige cikin gida, Kausar ta fito da gudu tana faɗin "Iya friends ɗina" bin ta da ido iya Kausara tayi tana kallon ta, har ta fito wajen palon.

In da ta bar su Rimsha tsaye wajen ta fito ta same su, sun kasa ko motsawa Allah sarki, tunanin nasu iyayen kawai suke, ita Rimsha tana tunanin ita ma idan ta koma gida kila haka su Jehan za su yi mata, ita kam Ayla ƙoƙarin ɓoye hawayen dake ƙoƙarin zubo mata take, dan ganin Kausar cikin yan uwan ta, ya jefa ta cikin tashin hankali, dan ita ba ma ta da yan uwan bata da kowa sai maman ta kawai.

Suna tsaye sunyi jugum jugum babu wanda ya kula su, Kausar tazo ta jawo hannayen su tana faɗin "Kuzo muje?" Bin ta su kayi zalalau-zalalau zuwa cikin gida, duk jikin su a mace, ji suke kamar su yi ta kuka kada su dakata

"Kausar su waye wayan nan?" Iya Kausar ta tambaya cikin harshen Hausa "Iya friends ɗina ne tare muka zo ai" kallon tsab iya Kausar ta musu kafin tace "Ban gane tare kuka zo ba? Ina za su je?"

Saman sofa dake cikin palon Kausar ta zauna tana faɗin "Iya nan mana suka zo, basu da kowa ne shiyasa" tsawa iya Kausar ta daka mata "Dan basu da kowa, sai ki kwaso su ki kawo ma na su? Tukun nan ma daga ina kuke?" Cikin sauri Kausar tace "Daga Daular Mutuwa muka fito"

Har wani bonsin iya Kausar tayi jin an ambaci sunan Mutuwa, dafe kirji tayi tana zare ido tace "oloni Kausara Mutuwa kuma?" Gyaɗa mata kai Kausar tayi tana faɗin "Eh iya Daular Mutuwa" "kaiii Kausara ki dai na kiran Mutuwar nan, wannan suna mai sanya tashin hankali haka, tukun nan ma ai na kuka samu wannan suna?" Tana magana tana zare ido ta dafe kirji "iya gaskiya na faɗa miki daga Daular Mutuwa muka fito, Daular da ba'a shiga a fito a raye, mu Allah ne ya tsare muna da sauran kwana" hannu biyu duka iya Kausar ta ɗaura a kan ta, ta kara zaro idon nan waje, nan take ta birkice musu kamar wadda notir ɗin kan ta ya kwance, cikin sauri ta dawo kusa da Kausar ta zauna, kun san dai yadda yarabawa suke idan suka tsorata "Yanzu Kausar Mutuwa ma har da Daula yake da shi? Na shiga uku ni jummai, Kausara anya kinji me kika faɗa kuwa?" Gyaɗa mata kai Kausar tayi, sannan ta fara bata labari cikin Daular Mutuwa da yadda suke yanka mutane, a zabure iya Kausar ta miƙe da karfi tace "Kai kakai kakai Kausara bari bani wannan labari, bar shi kada ni ki kashe ni, ke basu kashe ki a Daular Mutuwa ba ni kuma zaki kashe ni a nan da labari, ni wlh bana son ji, ya isa haka, bayin Allah sannun ku eyeee wannan bala'i haka, gaskiya na tausaya mu ku" tana magana tana zare ido kamar idon ta zai faɗi kasa, dariya Kausar tayi tace "Iya wannan fa baki ji ko kwata daga cikin labarin abun da muka gani a Daular Mutuwa ba, har da masu canza ido fa" ihu iya Kausara ta kurma tana faɗin "oloni Kausara zan wurgaki waje idan baki dai na kiran wannan bala'i ba, ki dai na kira mun Mutuwa tsirarar ta a nan" abun ma dariya yaso bawa Rimsha da Ayla, ganin yadda iya Kausar ta birkice musu lokaci guda, daga jin sunan Daular Mutuwa, wanna da ita aka kai Daular Mutuwa tsoro da fargaba ne za su kashe ta, mata sai bala'i tsoro, ji yadda take zare ido, tana bahaushiya amma zaman ta da yarabawa yasa ta dawo sak su, ta koyi ɗabi'un su da komai nasu, idan ba kaga fuskar ta na hausawa ba, bazata taɓa cewa bahaushiya bace, duk wani attitude nata na yoroba ne yanzu.

Iya Kausar kam daga jin zancen Daular Mutuwa sai ta nitsu tayi hankali har da yiwa su Rimsha sannu. "Iya ina boder Jami'u?" Cewar Kausar "Baki tambayi dadyn ki ba, kina tambayar boder Jami'u ko?" Dariya Kausar tayi kafin tace "Ai zan manbaye shi ina suke?" Tayi maganar tana miƙe wa ta nufi wani ɗaki mai kama da kitchen "Daddy'n yana Lagos, Jami'u kuma yana cikin Ilorin" iya Kausar ta bata amsa, already Kausar ta shige cikin Kitchen abun ta.

Tukunyar abinci ɗungurungum na shi ta ɗauko , ta dawo palon ta yi zaman yan bori a kasan carpet, ba wanke hannu ba komai ta fara dumbulan abincin tana kai loma bakinta,

"Kausar ba zaki kira friends na ki su zo ku ci bane?" Cewar iya, kallon su Kausar tayi, duk sun yi tsuru-tsuru da su, kamar wasu marayu, kamar biri yana jin matsanancin yinwa, haka suka yi da fuskokin su "Ayla kuzo kuci abinci mana" ta faɗa tana tura abinci a baki, jolof rice ne ya ji kayan haɗi sai kamshi yake, dan ba karya yarabawa sun kware wajen iya girki

Haushi yasa Rimsha tace bazata ci ba, dan a ganin ta Kausar ta wulakanta su ne, ga shi tana jin matsananciyar yunwa saboda jiya ma bata iya cin abincin da matar sarki ta ba su ba, amma ba zata ci abincin nan dake gaban Kausar ba, dan Kausar ta raina su, kuma har ga Allah ita Rimsha bata ɗaukan wannan wulakanci, karku manta duk da Rimsha take shiru-shiru mai sauƙin kai, jinin Nawazudden ne ke gudu a jikin ta, kanwar DPO Jehan ce, family Nawazudden basa ɗauran raini da wulakanci ko kaɗan

Ita ma Ayla ganin Kausar taƙi cin abincin yasa ita ma tace ta ƙoshi, Kausar ko a jikin ta dan sun ce sun ƙoshi, ta ci-gaba da ɗura abincin ta kawai, dan ita bata da burin da ya wuce taci ta ƙoshi, bata wasa da abinci, sannan ko wani irin wulakanci zaka mata, ka mata in dai zaka ba ta abinci to zata ɗauka

Ita ma iya Kausar ba ta wani damu ba, dan su Rimsha sun ƙi cin abinci, haka suna ji suna gani, suna jin matsanancin yunwa haka Kausar taci abincin nan iya cin ta ta mai da sauran kitchen bayan ta ƙoshi, sai wani ƙugi cikin su yake, musamman idan suka shaƙi kamshin abincin sai ka ji cikin su na kulululu saboda bala'i yunwa, Allah sarki bayin Allah.

Bayan Kausar ta mai da sauran abincin Kitchen ne ta dawo tace su tashi su je ɗakin ta su ɗan huta, ba musu suka ta shi, tayi gaba suka bi bayan ta

Ɗaki ne mai ɗan girma, dan ginin yarabawa suna yin sa da girma ɗakunan su, ƙaramin gado ne guda ɗaya a ciki, sai yar drawer saka kaya shikenan. Saman gadon Kausar ta haye tana faɗin "Yau zan yi barci mai daɗi Alhadulillah" gefen gadon Ayla da Rimsha suka zauna suna bin ɗakin da kallo.

To masu karatu sai Allah ya sa da mu bayan na dawo hutu, ku ci-gaba da yiwa Rimshan daddy addu'a, dan har yanzu da sauran ta, bata fita ukubar rayuwa ba, baiwar Allah [11/11, 8:52 PM] +234 906 579 6460: 💞💞TRIPLET'S💞💞

🌹🌹Episode 11-12🌹🌹

Ɗaki ne mai ɗan girma, don ginin Yarabawa suna yin sa da girma ɗakunansu, ƙaramin gado ne guda ɗaya a ciki, sai 'yar drawer saka kaya shi ke nan. Saman gadon Kausar ta haye tana faɗin, "Yau zan yi barci mai daɗi Alhadulillah!" Gefen gadon Ayla da Rimsha suka zauna suna bin ɗakin da kallo.

"Kausar ina ne toilet naku? Ina son in je in yi wanka." Cewar Rimsha. Miƙewa zaune a tsakiyar gadon Kausar ta yi tana turɓune fuska ta ce, "Idan kin fita falo ta wannan hanya da na bi na je na ɗauko abinci, to ta nan za ki bi toilet na wajen."

Miƙewa Rimsha ta yi tana faɗin "Ayla bari na je na yi wanka." Ayla kam ta kasa magana baiwar Allah saboda tsananin yunwa da take ji, haka ta zuba wa Rimsha waɗannan idanun nata da suƙa ƙanƙance saboda wahala tana kallon ta har ta fice daga ɗakin, shiru suka yi daga ita har Kausar ɗin, kowa da abin da yake tunani.

💞💞After some minutes💞💞

Ɗaure da towel nasu da ta ɗauko a toilet ɗin Rimsha ta shigo cikin ɗakin Kausar, yadda ta fita ta bar su haka ta dawo ta same su, tana shigowa Ayla ta miƙe tana faɗin, "Ni ma bari na je na yi wankan ina zuwa." To, kawai Rimsha ta amsa mata da shi, sannan ta zauna a gefan gadon tana kokarin mayar da kayan dattin ta da ta cire kafin ta yi wanka, duk bala'i datti ya canza wa kayan launi, ba za ka taɓa gane cewa wannan pink blouse gown ɗin nata mai bala'i kyau da ta fita da shi gida ba ne, saboda tsananin dattin da ya yi, ya zama launin kasa, har wani maiƙo-maiƙon datti jikin rigan yake.

"Meesha kada ki saka kayan dattin nan kin ji? Ki tashi ki duba kayan da kike so a cikin drawer kayana ki saka." Cewar Kausar, da kamar Rimsha za ta ƙi, sai kuma ta tuna kayan nata warin datti yake sosai, don haka sai ta hakura ta miƙe ta nufi drawer kayan Kausar.

Mafi yawancin kayan dake cikin drawer wandunan Jeans ne da T-shirt, sai gown na kanti da na materials, atamfofi ƴan kwaranni ne a ciki, duk wanda ya san Yarabawa ya san su da sanya ƙananan kaya, daga yaransu har manya, kai har tsofaffi, ba su damu da atamfa ko leshi ba, idan ka gan su da atamfa ko leshi to biki za su je, ko Walima ko dai wani shagali, amma ban da haka za ka ga jibgegiyar mata ga tsawo ga ƙiba, sai ka gan ta da wandon Jeans ya matse ta kamar cinyoyin ta za su fasa wandon su fito waje, kana ganin komai na daga halittarta, a haka suke yawo a cikin gari, a haka suke rayuwarsu ba ruwansu, ba ruwan kowa da kowa, sai wanda ka shigo da shi cikin rayuwarka.

Da kyar Rimsha ta laluɓa ta fito da wata doguwar riga mai faɗi kaɗan, ita ta sanya a jikinta, duk da Kausar ta fi su jiki, rigar ta zauna wa Rimsha sosai a jikin ta, saboda Allah ya mata wata irin halitta wanda Hausawa ke cewa karuwan jiki, komai ta sa zama yake a jikinta ɗas kamar don ita aka yi shi.

After some hours💞💞

Sun gama shirin su tsab, har ita ma Kausar ta yi wanka, ta sha wandon jeans da T-shirt, kayan sun matse ta sosai, sai wani washe baki take, ta ci ta ƙoshi ta bar su Rimsha da jin bala'in yunwa.

Suna zaune a falo, yayin da ita kuma Iya tana cikin kicin tana ƙoƙarin girka abincin rana. Kamar wadda aka tsikara Kausar ta miƙe tana faɗin, "Ku zo mu je ku ga garin Yarabawa yau kam, tunda Allah ya kawo ku." Da farko Rimsha ta ce, a'a ita ba za ta je ba, sai da Ayla ta sa baki sannan ta hakura ta miƙe suka fito a tare, sai wani murmushi Kausar take kamar ba lafiya ba.

Miƙar hanya suka yi zuwa Eyankorin Junction, sai surutu Kausar ke zuba musu, ban da um da uhm ba abin da suke bin ta da shi, saboda yunwa suke ji, ba bakin yin magana sosai, gara ita ta ci ta ƙoshi.

Duk wanda suka wuce in ma mace ko namiji sai ya kara waigawa ya kalli Rimsha, ga shi yanayin yadda take ta fi kama da mai jin barci saboda kasalar da yunwa ta sauke mata, sannan kuma ta sanya takalman Kausar mai ɗan tudu kaɗan a kafarta, hakan yasa take jan kafa a hankali. Jama'a sai tambayar Kausar suke yaushe ta dawo, ina kuma ta samo yar Indiya, wasu ta ba su amsa wasu kuma ta share su

Sun zo za su wace wasu gidaje da ke jere kamar tagwayen gida, komai na ginin iri ɗaya, wata yarinya dake zaune a tsakanin gidajen tana wasan ƙasa ne ta ce "Kausar iya Ganiyu ta fara zane, masu kyau." Ƴar yarinya ba za ta wuce shekara bakwai ba, cikin sauri Kausar ta ce, "Da gaske kike Waliya?" Gyaɗa mata kai yarinyar ta yi tana duƙe tana wasan kasarta.

Cikin sauri Kausar ta juya tana faɗin, "Meesha ku zo mu je Iya Ganiyu ta yi mana zane." Girgiza kai Rimsha ta yi tana faɗin "Ni Kausar ba na son yawon nan mu koma gida." Ƴar dariya Kausar ta yi kafin ta ce, "Kada ki damu idan mun je wajenta, ta mana zane sai mu dawo gida." Shiru Rimsha ta yi ba ta sake yin magana ba, wucewa gaba Kausar ta yi suka bi bayanta, kamar raƙumi da akala, duk in da Kausar ta yi haka suke daurewa ga yunwa suna jan ƙafa su bi bayanta, ita kuwa Kausar har wani taku take ta ci ta ƙoshi abinta.

Kafin su kai gidan iya Ganiyu suka iso ko wani shagon kanti. "Kausar bari na sayi drinks a nan shagon kin ji?" Cewar Rimsha ta yi magana tana fito da wannan ₦2,500 ɗin da sarki da matarsa suka ba su.

Kausar ko a jikinta, wai an yakushi kakkausa ta ce, "Ki saya mana Meesha, duk abin da kike so ki saya." Miƙa wa Ayla dubu ɗaya Rimsha ta yi tana faɗin, "Ayla ke ce babba ki riƙe wannan, ni da Kausar kuma sai mu raba ragowar ₦1,500 ɗin." Cikin sauri Kausar ta ce, "A'a ni ba na so, ni da na dawo gida, na bar muku tunda ni na iso gida." Kallon Ayla Rimsha ta yi, abin gwanin ban tausayi, murya a raunane saboda yunwa ta ce, "To shi ke nan Ayla ga ɗari biyar ɗin nan, ki haɗa ni kuma zan riƙe 1k Kausar mun gode." Girgiza kai Ayla ta yi tana faɗin "Ai yanzu tsakanin mu babu zancen raba kuɗi, ki bar kuɗin duka a wajenki, ki riƙe mana, idan buƙatar su ta taso sai mu yi amfani da su." To, kawai Rimsha ta ce tare da karɓar kuɗin ta haɗa, sannan ta shige cikin shagon bakinta ɗauke da sallama.

Sai kallon ta mai shagon yake, da Yarabanci ya ce da Kausar "Kausar ina kika samu wannan ƴar Indiyar?" Kallon banza Kausar ta masa ta ce, "Sadudin amma kamar na ce kada ka sake yi mini magana kafin mu yi tafiya da Iya ko?" Shi ma kallon sama da kasan ya mata kafin ya wuce ya je ya ɗauko wa Rimsha Coca Colar gora biyu, masu sanyi daga fridge ɗinsa, sannan ya haɗo mata da biscuits guda biyu, kamar yadda ta buƙata.

Karɓa Rimsha ta yi tare da miƙa masa 1k da ke ɗayan hannunta, karɓa shi ma ya yi ya ɗauko canjin 400 ya miƙa mata, ta karɓa ta fito, ta zo ta miƙa wa Ayla Coca Colar guda ɗaya da biscuit ɗaya, ita Kausar ta ce ba ta buƙata, karɓa Ayla ta yi, suka wuce suna hira

"Ku sha lemon mana Meesha." Cewar Kausar, kallon ta Rimsha ta yi kafin ta ce "A'a ya za a yi mu ci abu muna tafiya a kan hanya?" Dariya Kausar ta yi tana faɗin, "Meesha nan fa ƙasar Yarabawa kuke, ba cikin Hausawa ba ne, mu a nan babu ruwanmu da kowa, ko a tsakiyar titi kika ji za ki iya cin abin da kike so za ki ci, ba ruwan wani da ke, ke ba ki ga wancan gidan da muka wuce in da Waliya ke zaune tana wasan nan ba ne? Ba ki ga a waje suke girkinsu ba ne? Ku Hausawa ku ne kuka san wani abu wai sai an shiga gida ake wasu abubuwa, mu ba ruwanmu da hakan, a nan kowa yana da ƴancin ya yi abin da yake so." Shiru suka yi dukansu, don daga Rimsha har Ayla babu wanda zai iya cin abinci a kan hanya, don ba su saba ba, ita ma Kausar ɗin da ta ga ba su da ra'ayi cin abu a kan hanya, sai ba ta takura musu ba, don ta san Hausawa ne su, ta sha zuwa garuruwansu ta san yadda suke rayuwar daban da ta Yarabawa, su Hausawa suna siririnta abubuwansu da dama, amma su Yarabawa babu ruwansu, abin da suka yi ra'ayi za su yi kuma ko a ina ne a cikin garinsu.

Da sallama suka shiga wani gida, wanda ba za a iya ce masa gida kai tsaye ba, sai dai a ce ɗaki, domin babu katanga gidan, ɗaki ɗaya ne a wajen kamar shago, sai wani waje daga ɗan nesa da ɗakin wanda aka kewaye da bulo, ba gini aka yi ba, an ɗaura bulon ne ɗaya kan ɗaya, kuma ba har sama ba, iya rabi aka yi shi kawai, kana tsaye daga ɗan nesa ma kana iya hango abin dake cikin wajen, murhun girki ne da gingima-gingiman tukane da sauran kwanuka, da alama shi ne kicin na masu gidan.

Ganin ba kowa a wajen yasa Kausar ta sake kwaɗa sallama, wata mace ce mai ƙiba ta fito daga cikin ɗakin wadda da ka gan ta ka ga asalin Bayerabiya. Cikin harshen Yarabanci ta yi musu sannun da zuwa, sai murmushi take saboda ta san Kausar, da fara'a ita ma Kausar ta amsa mata tare da gaishe ta.

Bayan sun gama gaisawa ne Kausar ta sanar da ita abin da ya kawo su. To matar ta ce tare da wuce wa ta koma cikin ɗaki, su kuma suna tsaye, Rimsha da Ayla sai faman bin garin da kallo suke, ita kuma Kausar sai wani murmushi take kamar ba lafiya ba.

Jim kaɗan matar ta fito hannunta riƙe da wata baƙar gora mai ɗauke da wani baƙin ruwa kamar tawada, ɗayan hannun kuma ɗauke yake da wata ƙatuwar kujera.

Ajiye kujerar ta yi a ta gefe da bakin kofar ɗakin nata, sannan ta zauna tana faɗin me za ta zana musu, Rimsha ta ce ita kam ba ta so, ganin Rimsha ta ce ba ta so, ya sa ita ma Ayla ta ce ba ta so, kuma da ma ita Ayla ba ta sa a ranta za ta yi wani zane ba, da ma dai ta ce idan Rimsha ta yi, ita ma za ta ce a mata, idan kuma Rimsha ba ta yi ba, to ita ma ba za ta yi ba.

Kausar kam cike da zumuɗi ta miƙa hannunta ta bayan hannun ta ce a zana mata sunan boda Jamiyu, kama hannun nata matar ta yi ta fara zana mata da wani abu mai kama da fensir. Duk wanda ya san asalin Yarabawa ya san mafi yawancinsu da irin wannan zane, na zana sunan miji a jikinsu da wannan abu kamar tattoo ɗin amma ba tattoo bane.

Su Rimsha sun zuba ido suna ganin yadda matar take zana wa Kausar sunan boda Jamiyu a hannunta, lokaci guda Rimsha ta ji sha'awar abin har cikin ranta, cikin sauri ta ce "Kausar ki ce ni ma ina so a zana mini."

Murmushi irin na mai jin matsanancin yunwa Ayla ta yi kafin ta ce, "Me za a zana miki to? Kin ga dai ita Kausar boda Jamiyu ta ce kuma daga gani wannan boda Jamiyu shi ne mijin da za ta aura, don tun da muka zo nan ba ta da wata magana sai boda Jamiyu, ko dai ke ma boda Jamiyun za a zana miki ne? Ko kuma sunan ki Rimsha? Don na san dai ba ki da saurayi." Cool murmushi Rimsha ta saki, wanda sai da ya sanya kyawawan haƙwaranta bayyana, sannan wannan kyakkyawan dimple ɗin nata ya lotsa gwanin ban sha'awa, a nutse ta ce, "Yanzu Ayla sai ki rasa waye za ki ce a zana mini sai boda Jamiyu? So kike Kausar ta sumar da ni ne yadda take ji da wannan boda Jamiyu, ni har na ƙosa ya dawo na gan shi, in ga waye wannan Kausar ta dame mu da zancensa." Ƴar dariyar yunwa Ayla ta yi kafin ta ce, "To ai na ga ke ba ki da saurayi ne, to ko dai sunanki za a zana miƙi ne?" Shiru Rimsha ta yi tana ta murmushi ita kaɗai, kamar ba lafiya ba, ba ta sake ce da Ayla ko uffan ba, shiru ita ma Ayla ta yi, suka zuba wa Kausar da matar ido kawai suna kallon zane. Duk hirar da suke yi Kausar na jin su sai dai bata tanka su ba.

Bayan an gama yi mata zanen, Rimsha ta miƙe ta je gaban matar ta tsugunna tana faɗin "Kausar kin faɗa mata ne?" gyaɗa kai Kausar ta yi alamar e.

"A ina za a zana miƙi? Kuma me za a zana miƙi?" Cewar matar, ta yi maganar cikin harshen Yarabanci, juyowa Rimsha ta yi tana kallon Kausar tana jiran Kausar ta fassara mata, fassara mata abin da matar ta ce Kausar ta yi, wani haɗaɗɗen murmushin Rimsha ta sake saki a karo na biyu, sai kallon ta su Kausar suke Ayla kam mamaki irin murmushi da Rimsha take ya hana ta yin magana

Miƙa wa Ayla Coca Colar da biscuit dake hannun ta Rimsha ta yi, bayan Ayla ta karɓa, sai ta sanya hannunta, ta cire mayafin kanta, ta ɗan zuge zip ɗin rigarta, ƙasa kaɗan, ta zamo da hannayen rigar nata zuwa kafaɗar ta, su Ayla dai sun zuba ido suna ganin ikon Allah, suna jira suga me Rimsha za ta yi ne wai.

Bayan ta gama zamo da hannun rigar ta zuwa kafaɗar ta sai ta matsowa da matar kirjinta, ta ce a rubuta mata "The General Of The Army Romeo'', Tashin hankali babbar magana, kallon-kallon su Ayla suka fara yi wa junansu ita da Kausar, tunani suke anya Rimsha ba ta samu matsala a ƙwaƙwalwarta ba kuwa? Ta rasa sunan da za ta ce a zana mata sai sunan wannan kafurin Bature da bai san da zamanta a duniya ba, kuma ma ta rasa a ina za a zana mata wannan suna sai a kirji, kai lallai ya tabbata Rimsha ba ta da hankali.

Suna can suna zancen zuci su ba su sani ba Iya Ganiyu ta gama zana wa Rimsha rubutun nan a kirjinta, da kananan rubutu, saboda tsawon sunan.

Su Ayla ba su ankara ba sai jin muryan Rimsha suka yi tana faɗin "A kasan The General Of The Army kuma a rubuta mini, GAR." Tana magana tana kara sauƙe wuyan rigar nata zuwa saman breast nata, tashin hankali da ba a saka maka rana, Rimsha fa da gasken-gaske take, babu wasa a lamarin nata ko kaɗan, haka kuwa matar nan ta rubuta mata sunan Romeo kamar yadda ta buƙata, ga shi ruwa baya wanke abin, idan aka zana maka, tofa ya zauna ke nan, idan kana son gogewa sai an maka aiki a wajen, yau ga ikon Allah.

"Ayla me za a zana miƙi?" Cewar Rimsha, girgiza kai Ayla baiwar Allah ta yi tana faɗin, "Ni jikar mutumin da ban san shi ba, ku rufa mini asiri, ni ba na so, to waye ma nake da shi da har zan zana sunansa a jikina? Sai dai idan sunanki ke da Kausar za a zana mini." Zaro dara-daran idanu Rimsha ta yi ta ce, "Ba mu gane ba? Kamar yaya sunana ni da Kausar? Ki yi mana bayani."

Murya a raunane Ayla ta ce "Da kuke gani na ɗin nan, mamata kawai na sani a duniya, ita ma ban san asalin sunanta ba, don tun da na girma take cikin ciwo har na bar wajenta, babana ko alamar mai kama da shi ban taɓa sani ba, sunansa kawai nake ji, a takaice ma ƴan unguwarmu ce mini suke ba ni da baba wai shegiya ce ni." Ta kai karshen maganar tare ta miƙewa tana kokarin goge hawayen da ke zubo mata, Allah Sarki!

Cikin sauri Rimsha sarkin tausayi ta miƙe ta nufe ta tana faɗin, "Ki yi hakuri Ayla, ki yi wa baba addu'a Allah ya jikan sa kawai." Rungume Rimsha ta yi ta saki kukan da ta jima tana ɓoyewa, "Don Allah Ayla ki daina kuka kin ji ko, addu'a kawai za ki yi wa baba Allah ya jikan shi da rahma."

Cikin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro Ayla ta ce, "Meesha waye ya ce miki babana ya rasu ne?" Hawaye ita ma Rimsha ta fara yi tana faɗin, "To idan bai rasu ba yana ina? Me yasa ba ki san shi ba?" Matsowa ita ma Kausar ta yi ta rungumo Ayla tana ɗan bubbuga bayanta alamar rarrashi, ita dai iya Ganiyu kallon su kawai take, da yake ba ta jin me suke faɗa sai ta bi su da ido kawai, don wannan al'adar Yarabawa ce, in dai ba kai ka kira su cikin magana ba, tofa ko kana yi ba za su saka maka baki ba, musamman ma idan ba da yarensu kake yi ba sai su yi banza da kai.

"Rimsha babana yana nan da ransa, bai mutu ba, amma jama'ar unguwarmu suna ce mini ni shegiya ce, na tambayi mamana ina babana ta ce mini yana nan kuma ba ƙaramin mutun ba ne, babba ne a kasar nan, babba mai faɗa a ji ma kuwa. Sai dai kuma ban taɓa ganin shi ba, ban taɓa sanin inda yake ba, jama'a shegiya suke kira na, mun rayu cikin takaici da ukubar rayuwa, na yi fama da mamana ta faɗa mini me yasa ta rabu da babana, amma ta ki faɗa mini, ta ce babana yana da kuɗi sosai amma kuma ni da ita mun rayu cikin talauci babu cin yau bare na gobe, babu makaranta, wahala kan wahala, wani lokaci ma sai na ji gwara mutuwa da wannan rayuwata" Ta kai karshen maganar tare da sakin kuka mai sauti.

Ganin sosai Ayla take kuka ne yasa iya Ganiyu ta miƙe ta fara rarrashin ta, duk da cewa ba ta san a kan me suke magana ba, ta lura yaran da suna cikin damuwa.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull