Kenza eBookz

Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 18

Triplets book 3 complete By teema princess - Chapter 18

Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 18: Triplets book 3 complete By teema princess Chapter 18. "Kai subhanallah Lion menene ya sami sister…

3,731 words

"Kai subhanallah Lion menene ya sami sister kuma?" Tamkar babu shi a ɗakin, bai amsa ba, sai ma yunkurawa da ya yi zai miƙe ya bar wajen, cikin sauri Areef ɗin ya ce "Please zauna bari ni nayi serving naka ko?". Ba musu ya koma ya zauna dan yunwa yake ji, ɗaukarta cak Areef ya fara yi yana ciza laɓɓansa alamar zafi kafaɗarsa ke mashi, dan akwai sauran ciwo sosai, ko sannu Lion bai ce mashi ba, ai shi ba ƙaramin yaro bane, yasan abin da ya dace da shi, da kuma wanda bai dace ba, idan ya yi wa kansa illah ma shi ya jiwo.

Saman sofa dake a cikin ɗakin ya kwantar da ita tare da dawowa wajen ɗan uwan nasa yana cizar lallausan laɓɓansa.

Abinci ya zuba masu suka ci a tare kamar ɗazun, bayan sun kammala ya kwashe kayan abincin ya ɗaura saman table dake cikin ɗakin.

A tare suka miƙe Lion ya nufi toilet shi kuma ya haye saman bed, ita kuma tana sume a samar sofa.

Wanka Lion ya yi tare da fitowa ya shirya cikin kayan barcinsa riga da wando masu shegen kyau ga laushi kamar auduga, ba su da nauyi ko kaɗan, kamar dai kullum launin white color ne, bai ɗaure kyakkyawar gashin kansa ba, ya barshi zube sai kyalli yake yi yana tashin kamshi.

Saman gadon ya dawo ya kwanta yana zuba uban kamshi, yana kwanciya Areef ya miƙe ya nufi toilet ɗin dan shima ya yi wanka, saboda ciwon dake a kirjinsa shi ba wanka yake yi kamar kowa ya yi ta zuba ruwa ba, no a hankali yake yi ta yadda ruwar ba zata taɓa bandejin dake wajen ba, har ta taba ciwon, hakan yasa idan ya shiga wanka sai ya ɗauki almost 1 hour kafin ya kammala, daki daki yake yin komai.

Shiryawa ya yi cikin kayan barcin Lion, a ƴan kwanakin nan ma kayan ɗan uwan nasa yake yawan sawa, dan kusan ya tare a ya dawo ɗakin Lion ɗin, idan ya shigo baya fita har sai idan zai yi wani abin, kayan barcin launin black color ya sanya, bai cika sanya farin abu ba a yanzu, sabida ciwon nan nasa, baya son ganin stain na jini a jikin kayansa, so ya fi sanya Black colar or brawn, wadda ba zasu fitar da shaidar abu ba, duk kaunar da yake yi wa white color ya hakura.

Saman gadon yazo ya kwanta kusa da ɗan uwan nasa, har lokacin Rimsha tana sume kwance saman sofa, da alama shi ma Areef ɗin ya mance da ita a wajen.

A kwanciyar tasu suna fuskantar juna, Lion idanunsa a lumshe, shi kuma Areef ya tsare shi da idanu yana kare mashi kallo tare da godiya ga ubangijin daya yi masu wannan kyakkyawar halittar haka, Lion kyakkyawar gaske ne kamar shi ya yi kansa, har ta ƴan uwan nasa yaba kyansa suke yi, da yake su basu ganin nasu kyau ɗin sai nashi, dama kuma haka ne, baka cika ganin abu ba idan a jikinka yake, kafi ganin kyaunsa a jikin wani, to suma haka ne sunfi ganin kyan juna, ɗaya yaga na ɗaya haka.

Daga karshe Areef ya juya tare da ɗauko wayarsa daya ɗaura saman bedside drawer ya shiga latsawa, dan kwata kwata baya jin barci, shi kuma Lion da alama barci yake ji sosai, Shiyasa ma ya yi barcinsa abinsa.

Ita kuwa Akila tana kwance tana chatting da masoyinta, bata wani damu ba dan Rimsha bata dawo ba, while shi kuma Imran yana ɗakinsa yana shirin barci.

☠️DAULAR MUTUWA☠️

A YAU DAULAR MUTUWA TAKE KARA SHEKARA GUDA A KAN SHEKARUN HASSASATA DA AKA YI.

Sai murna suke yi, an kawata gidan tamkar ba gidan ba, sun yi amfani da tsafinsu wajen sauya gine ginen dake a cikin gidan, sun fito da sabbin gine gine tare da sabon penti, ga wasu baloon da kayan kyalkyali da aka zuba, tamkar wajen party, kai idan ba ance maka nan DAULAR MUTUWA bane ba zaka taɓa ganewa ba, saboda tsantsar kyan da ya yi, su barbushi duk sun zama kyawawan matasa masu jini a jika, ma'ana sun koma aihanin halittar da Allah ya yi masu, kyawawan matasan kabilar Ebo ne, duk wanda ya san Ebo ya sansu da tsawo da kuma ƙiba, mafiya yawancinsu farere ne kuma kyawawa, to suma haka suke, fararene tas kyawawa, ga tsawo da ƙiba, suna da kirar karfi tamkar masu ɗaka karfe, ma'ana masu yin gym, kuma ba wani gym da suke yi, halittace kawai da mafiya yawan mazan Ebo haka suke.

Fadar QUEEN an kawata shi da wani irin mahaukacin kyakkyawar zazzafar kwalliya, komai na cikin fadar Navy blue ne, ga wasu tsala tsalar kujeru da suka yi amfani da tsafinsu wajen kyara su, idan ka kalli fadar QUEEN sai ka yi zaton wani katafaren Daula mai tarin arziki na wani hamshakin basarake ne.

A cikin fadar akwai wani hawa step 3 haka, a saman step ɗin ne a ka kawata wa QUEEN kujeran da zata zauna, sai dai kujerun guda biyu ne a wajen ba ɗaya ba.

Sai shagali ake yi, su baba da yake sun saba gani duk shekara sai basu wani damu ba.... WAI SHIN MENENE MAKASUDIN HASSASA DAULAR MUTUWA NE? kamar yadda na gaya maku a baya, ta kabilar Ebo ce, sun hassasata ne ma dan tsafe tsafensu na samun makudan kuɗaɗe, suna ɗebo yara daga arewa zuwa wajen, da wuya ka samu ɗan gudu a cikin waƴan da ke cikin gidan, ko da gigin wasa ba zaka taɓa gani sun yi kuskuren kamo ƙabilar tasu ba, suna tsafi sosai da jikin mutane, ba iya yara ba, har da manya wanda ya yi sake da addininsa, yanzu matsafa sunyi yawa a duniya fiye da tunanin mai tunani, sai a riƙe ibada dan a tsiranwa gaidinsu, suna shan jini sannan kuma suna cin namar mutane, suna sayarwa wasu gidan matsafar wani sassa na ɗan adam idan suka buƙata dan yin tsafinsu, a caf faɗin kasar nan da wuya a samu gidan matsafa da suka kaisu girma da komai da komai, sun shahara ta wannan ɓangaren ba kaɗan ba, duk wanda ya shiga wannan gida baya fita, an rufe babinsa.... MU KOMA KAN LABARIN MU.

Murna a wajensu ba'a magana, wata kyakkyawar halitta ce ta fito daga wani katafaren kyakkyawar ɗaki, wannan halitta mace ce, a shakaru ba zata wuci 22 years ba, tana da tsawo sosai, amma bata da ƙiba sosai, ga shape kamar ita ta yi kanta, fara ce tas, ga hancin nan ɗan siriri kamar karas, ya zauna sosai da kyau a saman kyakkyawar farin fuskar tata, ɗan bakin nan nata ɗan karami, lips nata launin dark purple, kyau iya kyau wannar matar ta yi, sanye take da doguwar riga launin black color, rigar tata tana ja har kasa, rigar irin weeding gown ɗin nan, kanta babu ɗan kwali, ta zuba gashin nan nata har gadon baya, tamkar ita ta bawa kanta wannan kyakkyawar gashin, ga shi irin gashi mai gazar gazar ɗin nan ne, sai ya kwanto mata har baya. Wannan mata ba kowa bace fa ce QUEEN.

Saman ɗaya daga cikin kujerun da aka tana da mata ta nufa, ga wasu kyawawan fararen samari guda biyu suna take mata baya, sai kasa da kai su barbushi suke yi alamar girmamawa, a gabaɗaya cikin fadar QUEEN ɗin ita ce karama, amma kuma ita kowa yake durkusawa dan girmamawa, har sai da ta zauna a saman kujerarta suma suka zazzauna a nasu kujerun.

Tana zama bai fi da minti 5 ba, mahaifiyarta ta fito, wadda ita kuma dattijuwa ce da a kalla zata iya kai 45 to 50 years haka, da kallo ɗaya zaka yi mata kasan cewa yes tabbas ita ta haifi Queen, ba komai zai sanya ka yi tunanin hakan ba face muguwar kamannin dake a kan fuskokinsu.

Tana takawa bodyguards guda biyu suna take mata baya kamar dai yadda suka rako QUEEN, har sai da ta zauna bodyguard ɗin suka juya zuwa ta bayansu suka tsaitsaya dan tabbatar da tsaro a kansu.

Cikin yarensu mahaifiyar QUEEN ta buɗe musu taron, kowa yana zauna saman tsadaddun kujerun, sun sha kwalliya na ƙin karawa, suna da yawa sosai, a kallah sojijin ko in ce dakarun QUEEN zasu iya kai su 50 haka, dukkansu babu wani yare na daban a ciki, duk yarensu ne, hakan zai tabbatar maka da ba ƙaramin shiri suka yi wa wannan bakin azzalumin gidan ba.

Cikin yaren su suka gudanar da komai, sun ɗauki tsawon lokacin suna magana, wadda a kallah zai kai awa uku zuwa biyar haka, sai tattauna suke yi, da alama suna kara yin shawara ta yadda zasu kara buɗa gidan ne, ta yadda zasu inganta shi ya kara girma fiye da tunanin mai tunani, shi ne abin da suke tattaunawa, kowa yana kawo shawararsa a kan ga yadda zasu yi.

QUEEN dai shiru bata ce ko uppan ba, mahaifiyar ta ke magana, daga karshe ma mahaifiyar tata ce ta yanke shawarar ga matsayar da zasu tafi a kan shi dan su kara faɗaɗa gidan nasu...... BASU SAN CEWA ALLAH BAI YI ALKAWARIN TALLAFAWA AZZALUMAI BA, ALLAH BAYA BARCI, YANA GANIN KOMAI DAKE FARUWA, WANNAN TSINANNEN GIDA BA ZAI CIGABA BA, YA DAI CIGABA A BAYA, SUN CI LOKACIN SU DA DAMARSU A BAYA, A YANZU IN SHA ALLAH SAI YA RUGUJE, BA ZASU SAKE YIN MASARA BA, BA ZASU SAKE KASHE KOWA BA, BA ZASU SAKE TSAFI DA KOWA BA, AZZALUMAI TSINANNU.

Duk wannan taron da suka yi babu Duna babu alamar sa, wai shin ina duna ɗin? Ina suka kai shi? To muje dai zuwa, koma me zamu ji a gaba.

Sai da dare ya tsala sosai suka tashi taron nasu, sun ci sun sha, sun ƙoshi sun yi hani'an, an cashe anyi murna sun sha sharholiya, abin ba'a cewa komai.

Sai bayan sun tashi taron mafiya yawa daga cikinsu suka koma kamanninsu na matsafan dan sun ce yafi yi musu daɗi, wasu kuma sun zauna a ainahin kamannin da suke da shi na kyawawan matasa.

QUEEN ma bata koma kamannin tsafi ba tukunnan, haka ita ma mahaifiyarta, da alama su kam basu son wannan tsiffa tasu ta matsafar, to koma yaya ne zamu ji a gaba,.

Da ainahin kamanninta Queen ta bar wajen zuwa katafaren daular yin barcinta, tana barin wajen taro ya watse, kowa ya wuce bakin aikinsa.

TO KUN JI ABIN DA YAKE FARUWA A DAULAR MUTUWA, BARI MU LEƘA WASHINGTON DC DAN JIN YA AKE CIKI NE.

WASHINGTON DC💋

Tafiya suke yi a cikin mota, Aseef da kansa yake tuƙa motar, shi kuma Musharraf yana gefensa suna hira.

"Kana ji uncle Hosain? Dama ai na gaya maka, sai na kwashi rabin kuɗin account ɗin uncle T na yi ta sadaka da su, ko Allah zai dube shi da idon rahama yasa ya musulunta, wannan kafurar zuciya ta ragu, to in gaya maka yau a account nasa na kwashi kuɗi na zuba a nawa, nan da anjuma zaka ji ya kirani akan me zan yi da uban kuɗin da na ɗeban nan, ai tun da suka sanar da ni sirrin bankin su, wlh ko ba su so sai sunyi sadaka, musamman ma uncle T da Uncle Herry, basu taɓa kyauta wa wani ba, sai pastor, shi kawai suke bawa kuɗin su".

Dariya Musharraf ya yi sosai kafin ya tsagaita ya ce "Wlh Aseef ka zama lashe money, ina ga nan gaba kaɗan sai sun canza gabaɗaya tsarin bankinsu saboda kai, duk sai ka talauta mutane ko? To kai ma dai Allah ya sanya ka gama karatun nan lafiya ka fara aiki ka tara naka kuɗin, sai ka fita daga layin lashe moneys".

Yana ƙoƙarin juya kan motar ya sauƙa daga kan titin da suke izuwa titin kasa ya ce "Uncle ba zaka gane bane, basu yin sadaka ne shiyasa nake yi masu, kuma ai kuɗin su ba zai kare ba tun da kullun wasu ne suke shigowa, duk cikin mu fa, daga Saif sai Areef ne kawai suke yin sadaka, shi ma daddy da kake ganin nan, wlh pastor kawai yake bawa kuɗinsa, bayan pastor kuma sai ni da nake cin kuɗin, ko suna so ko ba su so, kuma dole su bani na ci". Kara faɗaɗa murmushinsa ya yi "My Aseef ka cigaba da yi musu addu'a, In Sha Allah everything will be okey nan ba da jimawa ba".

Ɗan ɗaure fuska kaɗan ya yi. "Uncle Hossain wlh wannan bakar zuciya da kake gani, ni nasan daga wajen wannan Roshan ɗin suka gado shi, ko ban ji tarihin kakan nan namuba, nasan shi ne mai shegen bakar zuciya tamkar shaiɗanun farko, kai uncle Hossain baka ji sunansa bane? Wai fa Roshan, daga ji kasan anyi tsiya ba na wasa ba, ni ban ma son jin tarihinsa, ban son sanin komai, dan nasan bakin mugune da wani idanunsa a wajen, ya ma yi Sa'a Allah yasa idanunsa irin na Lion blue color, dan hakan yasa nake raga mashi, ba da ban haka ba, da sai na ce Allah ya kara mishi azaba tun da bai musulta ba ya mutu". Yana magana yana ɗaure fuska.

(Kai jama'a to me kakansu kuma ya yi mishi da ya kare mishi tanaji har haka?🤔 Allah ya shirya Aseef Wlh, wai da ya ce Allah ya kara mishi azaba🤣 to ai ka riga da ka faɗa sai dai kar a kara🤣)

"ASEEF abin da nake so da kai kana jina?" Gyaɗa mishi kai ya yi ba tare da ya yi magana ba. "Yauwa, musulmi ba zai taɓa zama cikakken musulmi har ya shiga aljanna ba sai yana kiyaye harshensa, Annabi da kansa ya yi wa duk wandan ya kiyaye abu biyu zuwa uku alkawarin shiga aljanna babu fashi, na farko, ka kiyaye abun dake tsakanin hakwaranka na sama da na kasa, wato harshe kenan, idan har kana iya kiyaye harshenka, to ana sa ran ka samu babban rabo, abu na biyu ka kiyaye abun dake tsakanin kafafunka, wato al'auranka, muddin ka kiyaye gabanka baka aikata zina ba, muna yi maka kyakkyawar zaton da samun Rahmar Ubangiji, abu na uku gani, ka kiyaye idanunka wajen zuwa lallai sai ka leƙa abin da ya zama haramun, misali kallon fina finan banza da tsiraicin wani, mutane biyu kawai Allah ya yafewa da su kalli tsiraicin juna, mata da miji, bayansu duk wanda zai zo a baya tofa akwai matsala, uwa tana iya yi wa ƴaƴanta wanka suna yara ta kalli tsiraicin su kafin sukai munzalin haramta ita ma a gareta, idan ba ya zama dole ba, Aseef ina son ka san wani abu guda wadda duk wanda ya sanya hakan a ransa dole ya tuba ya koma ga Allah, ina son ka saurareni da kyau, Ubangiji bai bawa kowa daman sanin aikinsa ya karɓu ko bai karɓu ba, ka kwana kana sallah, kana azumi, zakka, hajji, ba abin da baka yi a manya manyan ayyuka Alkhari, sadaka, amma kada ka kuskura ka saki jikin cewa wannan aikin naka tana karɓuwa, domin me? Saboda baka sani ba wata kila akwai in da ka tabka babban kuskuren da ya shafe dukkan ayyukan alkharin nan naka, idan bawa yana da hankali bai kamata ya saki jiki da duniya ba, saboda baka da tabbacin abin da aka turoka a duniyan ka yi shi mai kyau kuma an karɓa, Aseef muddin aikinka bai karɓuba ka shiga uku ka lalace, bari kaji Annabi da kansa akwai lokacin da Allah ya sauƙar mishi da aya ya daka mishi warning akan yana shiga abin da bai kamata ya shiga ba, a lokacin sai da annabi ya shiga tsananin tashin hankali na abin da ya faru, to shi kaga ɗan gata ne, Allah yana son shi da Rahma har hakan ta faru, zaka iya zuwa kana tapka babban kuskure da zai goge duk wani aikinka ba tare da ka sani ba, Sahabban annabi ban cire maka ko ɗaya ba, harta waƴan da suka san makomansu ɗin, waƴan da suka san aljanna zasu tafi irinsu Sayyidina Abubakar, Omar, Usman, Ali, ɗalhatu binu Ubaidullahi, abu ubidu binu zarrai da sauransu, su kansu idan aka kira lahira jikinsu kerma yake yi, kuka suke yi suna kara neman gafara da sassauci wajen ubangiji, wannan kawai bai isa yasa bawa ya kasance cikin tashin hankali a kullun ba? Manyan Sahabban da suka san yes aljanna zasu tafi, suna kuka idan suka ji annabi ya fara magana a kan lahira, to mu da ko rabin su a aikin Alkhari bamu yi ba, sai kaga bawa ya samu waje ya kwanta ana kiran sallah yana zaune tamkar wani kurma, ya ilahi ya lillahi, wlh bai kamata bawa ya zauna cikin kwanciyar hankali har ma ya yi tunanin cutar da wani ba, mutuwa gaskiya ce, tashin alkiyama gaskiya ce, yau ina kakaninmu? Wasu ina iyayenmu? Ina kannenmu? Wasu ina yayyunmu? Idan ka juya kaga matsalar dake a kewaye da kai ma kawan ya isa ya sanya ka kara jin tsoron Allah ka girgiza, ya isa ya sanya ka kara komawa ga Allah dan samun rabauta, kafin Annbi ya rasu, da Sahabbai suka tambaye shi ya Rasulullah yaushe za'ayi tashin alkiyama, ya ce da su sanin gaibu sai lillahi, Allah ne kaɗai ya barwa kansa sani, amma akwai misali da Ubangiji ya yi mini, zan yi muku shi dan ku kotanta, mikar da yatsun hannunsa gabaɗaya ya yi, kun dai san yatsun hannu ɗaya ta fi ɗaya, sai ya ɗauki babba ta tsakiya da kuma manuniyar yatsa, ya mikar da su sosai, ya ce da sahabbansa abin da ta regewa duniya ta tashi bai wuce ɗan wannan fifikon dake tsakanin yatsarsa ta tsakiya da kuma manuniya ba, ku duba ɗan ratan dake tsakanin yatsunnan, a lokacin annabi yace abin da ta ragewa duniya kenan, bare kuma yanzu da ya yi shekara 1445 da yin wannan maganar, to ku lissafa abin da ya saura kenan, a lokacin da Sahabbai suka ji wannan magana, hankalinsu ya yi mummunar tashi, masu kuka suna yi, annabi ya yi ƙoƙarin kwantar musu da hankali ta hanyar nunawa su sayyidina Abubakar cewa su fa ƴan aljanna ne, amma ina sunki yin shiru, suka ce idan ba sun ga kansu a cikin aljanna ba, sun karɓi takardansu da hannun dama, baza su taɓa daina kuka suna neman gafara da sassauci wajen ubangiji ba, ɗan adam ako da yaushe mai kuskure ne, tana iya yiwuwa su je su aikata wani abin da zai shefe musu aikin alkharinsu na baya, to su da suke Sahabbai ma kenan, ina ga mu da ba ɗaya kanwar biyu? Sai kaga mutun sai wani jiji da kai yake yi yana faɗi kamar ba nan da ɗan lokaci kaɗan cikin kasa zan koma ba, jama'a duk wasu masifa da suka zo a cikin Al Qur'ani mai girma da hadisan Manzon (S.A.W) da suke nuna almomin tashin alkiyama ne, to wlh sai bayyana suke yi, me ba'ayi yanzu? An maida zina abin kwalliya! An mai da luwaɗi gasa! An mai da lesbian sana'a! Saɓon Allah ya zama har tinƙawo da shi ake yi! Uba ya nemi ƴa ya kwanta da ita, yaya ya yi wa kanwarsa ciki, makwabci ya yi wa ƴar makwabcinsa ciki, mata su kashe mazansu a kan shirmen banza, ba'a ɗauki ran a bakin komai ba, matan aure suna zina, Maza na cin amanar matansu, namiji ya auri yarinya kuma ya zagayo ya yi wa kanwarta ciki, wasu ma tamkar a garin dabbobi suke, ka auri yarinya sannan ka kwanta da uwarta, ya ilahi ya lillahi, me ba'ayi?! Cutar mutane an mai da shi yanzu tamkar wani ilimi, har koyan danfara ake yi, karya na gudu kana bin shi a guje sai ka kamo shi, dole dole sai anyi karya, zalunci da hasada na gudu kuna binsu ku kamo su, dole dole sai an zalunci jama'a, kashe mutane kamar kiyashi ya zama contract! Gasa ta gina manya manyan gine gine a duniya ta bayyana, wadda annabi da bakinsa ya faɗa tana daga cikin manya manyan almomi na tashin alkiyama, masifu kala kala sai bayyana suke yi, shi kansa wannan faɗa ta yahudawa da musulmai ya zo mana a cikin Al Qur'ani mai girma? Kafin tashin Alkiyama sai anyi shi, duk wasu alamomi sun bayyana, jama'a muji tsoron Allah, mu tsaya tsayin daka dan gina lahirarmu, bai kamata hankalinmu ya kwanta mu saki jiki da duniya ba, har sai ranar da muka karɓi takardanmu da hannun dama, mu lizimci yin istigifari dan idan munyi laifi ma Allah ya yafe mana, a kowace rana ku rinƙa tuna mutuwa fiye da yadda kake tunanin abinci, dan mutuwa tafi abincin saurin zuwa, idan kwana ya kare ko tafiya kake zaka tsallaka babbar titi sai an zare ranka, second ɗaya mala'ika azarailu baya karawa bawa wajen zare rai, ko a ina yake kuwa, shi kuma abinci kana iya jira har sai an kammala, to dan haka mu lura, mu tuba mu koma ga Allah, zunubanmu ya yi yawa, Allah gafurun rahim ne, amma ku sani a yanzu ne kuke da damar tuba kafin lokaci ya kure, a lahira ko kabari ba'a tuba, iya duniya Allah yake karɓar tuba".... Yana magana yana hawaye bibbiyu, duk dakiyar zuciya irin na daddyn Rimsha sai da ya yi hawaye ba kaɗan ba, haka zalika shi ma Aseef, paka motar ya yi a gefen titi tun lokacin da daddyn Rimsha ya fara maganar, ya kifa kansa da jikin steering motar, hawaye yake yi sosai, wani na bin wani, duk sai ya ji duniyar ma ta ishe shi, ya ji jikinsa gabaɗaya ya mutu, me bawa zai nema a duniyar nan da ta wuce lahirarsa? Me zai tsayar da bawa yin wasu shirme a duniyar nan? Ya ilahi ya lillahi, gaskiya duk wanda ya zo duniya, ya mutu ya tafi wuta to tabbas shi ya so, shi yaga dama, kuma ya zama babban mai asara number ɗaya a duniya, dan Allah ya bamu lokaci da kuma dama, Allah Arrahaman ne, mai rahma a kan bayinsa, tabbas wannan hakane, Allah ne kaɗai zaka yi babban laifi ya kuma baka damar tuba ka koma gare shi, ka sake yi ya sake baka damar tuba, duk dan ka samu rahmarsa, ba wanda zai yi wa bawa haka sai mahaliccinsa, wani ma nan a unguwarku idan yana jin haushinka, haka kawai sai ya ɗauki gaba da kai ba gaira ba dalili, idan kayi kuskure yi mashi laifi kaɗan, to ka shiga uku, ba zai taɓa yafe maka ba, sai ya ɗau fansa, kunga ya tabbata idan ka mutu ka shiga wuta kai kaso.

Readers Also Read