Kenza eBookz

Triplets book 4 Complete - Chapter 36

Triplets book 4 Complete - Chapter 36

Triplets book 4 Complete Chapter 36: Triplets book 4 Complete Chapter 36. Kusa da gwaggo Areef ya zauna, ita kuma Jehan ta koma saman bedside drawer ta…

3,326 words

Kusa da gwaggo Areef ya zauna, ita kuma Jehan ta koma saman bedside drawer ta zauna, dan bata son hawa saman bed ɗin, tana hawa zasu fara yin faɗa da Rimshar, yanzu kamar wuta da audiga haka suka zama, basu haɗuwa waje guda, ba komai ne yasa hakan ba face ita ma Jehan tauraronta yana da nisa, ba'a banza ta cika faɗa da zafin ran nan irin na Lion ba, su ƴan baiwa ne, taurarinsu yana da nisa sosai, wanda taɓasu a wajen matsafa abu ne mai matuƙar wahala, ita ma Rimshar sai da suka ci bakar wahala tsawon watanni suna bibiyarta kafin su sami galaba a kanta, sun wahala fa fiye da tunaninku kafin su cinwa Rimshar. Kun tuna lokacin da Jehan ta gayawa fake William magana a palo? Kuma babu abin da ya iya yi mata, to hakan ce, ita sam sam bata taɓuwa, duk bala'i haka za'a ganta kuma a barta, kamar Lion take, shi ma dai nan gani nan bari, Rimsha ce dai mai ɗan rauni baiwar Allah, kuma duk wata gaskiya ta wajenta yake fara bankaɗowa, ita take zama sanadiyar bayyanar abubuwa da dama, baiwarta ya wuci tunanin mai tunani, ita ta je Daular Mutuwa, ita ta zama sanadiyar bayyanar Dr Salman, yanzu kuma kusan ita ce ta zama sanadiyar bayyanuwar wannan lukutar matsalar da suke a ciki!!.

"Good morning momma". Ya faɗa yana kallon Rimsha dake ta faman kallon wajen mirror.

"Good morning or good afternoon?". Brr Naurat ce ta tambayeshi. Ɗan murmushi ya yi yana faɗin "Kai ƴar tsohuwarnan, kin iya sa ido, to ai ni yanzu garina ya waye".

"E ba shakka yanzu garinka ya waye kam, ga alama nan na gani". Ɗan zaro idanu ya yi yana faɗin "Ina alamar kuma?". Shiru ta yi bata yi mashi magana ba. Gwaggo ce ta ce "Areef ina Aseef? Ina autana? Ko dai bai tashi daga barcin bane?".

"I think bai tashi ba, our Rimsha what are you thinking? Naga hankalinki gabaɗaya baya a kanmu ne". Ya kai karshen maganar yana ƙoƙarin kai hannu zai taɓa face nata.

Dakatar da shi gwaggo ta yi ta hanyar cewa "Kaga ne wlh ka rufa mana asiri, yadda take kwance shirun nan barta a haka, idan ka taɓota, kamar ka kwanto bana gidan rina ne! Idan ta fara bala'i sai mun rasa me yake yi mana daɗi".

"Momma like how? I didn't understand anything, yi mani bayani, Rimshar ce mai faɗa? Ita da take so silent". Cike da mamaki ya yi maganar.

Ba ɓoye ɓoye gwaggon ta bashi labarin duk abin da yake faruwa, da tafiyar Lion, har kiran da Lion ɗin ya yi mata ɗazun ya ce mata ga abin da yake faruwa, dan haka sai su kara taka tsantsan, dama wannan dalilin yasa ta ce Jehan ta kira mata shi, dan ta gaya mashi halin da ake ciki.

Shiru ya yi yana tunanin wasu abubuwa, maganganun Josephine ne kawai suka fara dawo mashi cikin kansa, a koda yaushe idan ya je wajenta kai mata ziyara, maganarta ɗaya shi ne tana taya su da addu'ar samun gane gaskiya cikin ƙanƙanin lokaci tun kafin komai ya kure masu, to shi a lokacin yana ɗauka ko gaskiya tsakaninta da Dr William ne take son su gane, bai san cewa ba haka abin yake ba, ga gaskiyar da take magana a kai yau sun fara ganewa, Allah sarki kullum baya taɓa sauraronta idan ya je, da ta fara kawo mashi labarin baya zai dakatar da ita, ya ce mata shi gaisheta ya zo yi ya kuma tambayeta me take da buƙata, dan ya saya mata, idan kuɗi take so ya bata, shi baya son wani dogon magana, bai san cewa ga abin da ta jima take son sanar da shi ba.

Duk sai ya ji jikinsa ya yi muguwar sanyi, ya shiga damuwa sosai, tunaninsa ɗaya yanzu ina ɗan uwan nasu, cikon QUADRUPLE nasu yake? Yana raye ko ya mutu? Ina ainahin daddynsu yake? Hakika ya tausayawa daddyn nasu da kuma momman nasu, sun sha wahala, an cutar da su, uncle Herry da Josephine suma an cutar da su matuƙa, ga Tga a gefe, wannan wani irin rayuwa ne?, Ga Rimsha baiwar Allah da bata san komai ba ita ma an jefata cikin bala'i.

Gwaggon ce ta katse shi da cewa "Saif ya ce kada kowa ya ɗaga hankalinsa, kada mu yi kamar akwai wata matsala, mu yi rayuwa kamar kullum, nan da lokaci ƙanƙani komai zai zo karshe, dan haka kada ka ɗaga hankalinka kai ma".

Nisawa ya yi tare da miƙewa, zuciyarsa na yi mashi kuna na rashin kashe William ɗin da bai yi ba, abin ya baƙanta mashi rai, ji yake yi kamar ya yi ta buga kansa da jikin bango ko zai sami sukuni, hanyar fita daga cikin ɗakin ya nufa yana faɗin "Momma am coming". Ya kai karshen maganar tare da ficewa.

Bin shi da kallo suka yi har ya fita, sannan gwaggo ta ce da Jehan "Jeki ki kai mashi abinci, nasan bai yi breakfast ba". Okey ta amsa tare da miƙewa ta bi bayansa.

A ɓangaren Lion kuwa, yana zaune a wajen da yake zaune tun ɗazun, bai motsa daga wajen ba, yana aikin latsa waya ga Tv tana magana, kamar daga sama ya fara jin wani ɗan jarida daga cikin Tvn yana bada rahoton wai GENERAL OF THE ARMY'S ROMEO ya kashe wani babban ƙusa a gwamnati babu gaira babu dalili, wanda kuma ya kasance kakansa ne, har gida ya shiga ya yi poisoning nashi, yanzu ƴan'sanda sun sami damar garzayawa gidan, suna kuma bincike a kan gawar, su kasance kusa da Tvnsu dan jin yanda komai zai na wakana.

A hankali ya ɗago idanuwansa izuwa kan makeken Tvn nasa, gawar kakan nasu ne aka hasko tare da hotonsa a zaune a saman bedside drawer kakan yana ta kallon kakan nasa. Sam bai yi mamakin ganin hakan ba, dan yasan da akwai CCTV camera a cikin ɗakin, tun time da ya shiga ya gani, kuma da gangan ya bar camerar a kunne ta naɗi komai, dan dama yasan ba zasu faɗi gaskiyar komai ba, zasu yanke video ne ba zasu nunawa duniya ainahin abin da ya faru a tsakaninsa da kakan nasa ba, sai dai su nuna iya in da kakan nasa ya fara fafutukan mutuwa, shi kuma ya fice daga gidan, su suna jin daɗi sun kafa mashi tarko, basu san cewa ya jefawa kifi namane a cikin bakin ruwa idan ta zo kamawa shi kuma sai ya capkota ba, sun shirya hakan suna son ruguje shi ta kowace hali, shi kuma ya shirya yi masu rubdugu, yasan cewa kakansa His excellence zai ma iya shiga ya fita ya sanya a cire mashi kayan aikinsa, ma'ana a karɓi mukaminsa na wajen aiki, saboda yanzu ya yi fito na fito da su, amma sam hakan ko a jikinsa bata damesa ba, saboda shi kaɗai yasan abin da ya ƙulla masu, shi kaɗai yasan abin da zai jijjigo, sai ya tashi kansu. BABBAR MAGANA, YAU AKE YINTA, YANZU WASAN ZAI FARA A TSAKANIN TSOFAFFIN NAN GUDA UKU, WATO HIS EXCELLENCE, ANDERSON, UWARGIJIYARSU, DA KUMA LION SHI KAƊAI, ZAMU GA WAYE YA IYA BUGA WASAN A CIKINSU, ZAMU GA WAYE ZAI ZAMA ZAKARAR GWAJIN DAFI A CIKINSU, SU UKU SHI KAƊAI! BA SHAKKA AKWAI YAKI BA KAƊAN BA, YANZU DAI GA SHI SUN YI MASHI SHARRIN YA KASHE BABBAN ƘUSAR GWAMNATI, SANNAN GA SHAIDA ƁARO ƁARO JAMA'A KOWA YA GANI, KUNGA KUWA DOLE LION YA FITO YA YI WA DUNIYA BAYANIN MEYASA YA KASHE BABBAN ƊAN SIYAYSA KAMAR WANNAN, DUK DA YAKE KAKANSA DOLE YA YI WA DUNIYA BAYANI, DUK DA YAKE GENERAL OF THE ARMY'S DOLE YA YI BAYANI, DAN BA ZAUNA GARI BANZA AKA KASHE BA, BARE ACE KILA ƁARAWO NE KO WANI MAI LAIFIN, BABBAN MUTUN MAI MURYAR FAƊA AJI AKA KASHE, AKWAI KALLO!! YANZU WASAN ZAI ƊAUKI ZAFI.

❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥

*KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*.

*KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*.

❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥

https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S

❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥

TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️

❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋)

*Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581*

E20

Date: 30/4/2024

Mikewa ya yi tare da ɗaukar wayarsa ya nufi cikin bedroom nasa. Ko'ina a cikin ɗakin a gyare fes fes, tamkar ba'a taɓa taɓa komai na cikin ɗakin ba, makekekiyar katafen gadonsa a shumfuɗe da white bed sheet na alfarma, mai matuƙar kyau da tsada, sai tashin daddaɗar kamshi air freshener mai kwantar da hankali tare da sanyayya zuciya bedroom ɗin nasa yake yi. Toilet ya nufa, wanka ya yi tare da fitowa ya shirya cikin wata kyakkywar farar jallabiya tas da ita, ya zo ya shumfuɗa dadduma ya tada sallar azzahar.

Bayan ya idar ya jima yana addu'a tare da kaiwa Allah kukansa, bayan ya shafa addu'ar ya mike ya nufi saman shumfuɗaɗɗiyar bed nasa.

Mikewa ya yi ya kwanta, yana tsananin kewar Meeshansa, a hankali ya lumshe idanuwansa, ba jimawa barci ta yi awon gaba da shi.

A gida Nigeria kuwa, Areef yana fita harabar gidan ya ci karo da motar Donal ya dawo daga airport, ya je ya ɗauko Sheikh Sultan, wato limamin masallacinsu na Washington. Iso ya yi wa Sultan ɗin izuwa cikin gida. Kai tsaye bedroom na Lion ya kai shi, sannan ya fita ya je ya sanar da su gwaggon zuwan Sultan ɗin, daga nan ya fito ya nufi waje, mota ya je ya shiga ya bar gidan mai gabaɗaya.

A ɓangaren Mark kuwa, an yi nasarar ɗaura mashi kafafun nasa, sai dai anci bakar wahala, sai da ma aka wuce da shi babban asibiti, a gida abin ya ci tura, Lion ya ce su shirya shi ya dawo Washington ya yi jinya a can, dan sun fi kwararrun likitoci da zasu kula da shi sosai, so yanzu ana shirye-shiryen ne, Brr Naurat ta ce yakamata kafin Mark ya koma Washington, to a ɗaura aurensa da Anaya, ya karɓi kalmar shahada, sai a ɗaura auren kawai su wuce tare da ita, wannan shawara da ta yanke kowa ya yi na'am da ita, dan ita ma Anayar ta damesu da kukan ciwon Mark ɗin, kukan yanzu daban na anjuma daban, ga shi daddynta ya hanata zuwa asibiti wajen Mark ɗin, sau ɗaya ta je ta rinƙa yi mashi kuka, yana fama da ciwo kuma ga kukanta, da wanne zai ji? Shi ne suka hanata zuwa kawai, sai dai ta yi ta takura masu da kukan a gida.

Abba, Abbi, daddyn Anayar, daddyn Jelly yau dukkansu za su koma gidajensu, sai dai za su bar Anaya a wajen Brr Naurat, Lion ya ce su bar Brr Naurat da Dr Salman a gidan nasa, shi ne yasa suka barsu, an bar Anaya, Aafia kuma zata tafi da Abbinta, baiwar Allah har yanzu dai sauki bai samu ba, yanzu haka asibiti zasu fitar da ita waje, tana jin duk abin da za su faɗa, bata manta kowa ba, magana ne dai bata yi masu, shiru shiru ta koma.

Sai misalin karfe 1:20 Aseef ya farka daga barcin da suke ta zubawa tun bayan sallar asuba. A hankali ya waro idanuwansa, idanun nasa sun yi jajir da su, har sun ɗan kumbura, saboda barcin da ya rinƙa zubawa kamar ba gobe.

A hankali ya kai kallonsa gefensa, har lokacin Akila tana zuba barci bata tashi ba. Nisawa ya yi tare da yunkurawa ya mike zaune, cikin wani irin kasala jikinsa duk zafi yake yi mashi, a hankali ya zuro kyawawan fararen kafafunsa kasan bed ɗin. Da kyar ya iya mikewa tsaye, a hankali ya fara jan kafafun nasa ya nufi toilet, sai aikin turo baki yake yi kamar wanda aka yi wa dole ya tashi. Ita kuwa Akila barci sai abin da ya ci gaba, dan ita ta fi shi gajiya.

Wanka ya yi tare da fitowa ya shirya cikin pajama launin maroon color, sannan ya shunfuɗa dadduma ya gabatar da sallar azzahar, bayan ya idar ya fito dan ya je wajen gwaggo.

A nan ya isko Sheikh Sultan yana yi wa Rimsha addu'a, ta kwanta shiru kamar bata a wajen, a zahirin gaskiya ba shiru ta kwanta ba, Malika ce ta danneta, dan bata son ta ɗaga masu hankali, amma banda haka wannan tofin da ake yi mata ɗin ba karamar haukata matsafan da suke tattare ita ya yi ba, da Malika ta kyaleta, tsab zata shake Sultan ɗin ma da kansa, amma ta ruketa gam, ta ki barinta ta yi borin.

Bakinsa ɗauke da sallama ya shigo cikin ɗakin. A tare suka amsa mashi da gwaggo da Brr Naurat. Waro idanu ya yi yana kallon Sultan dake ta faman yin tofi. Cike da mamaki ya ce "Shaikh is it you?" Ya yi maganar yana kara waro idanu waje.

Sultan ɗin bai amsa mashi ba sakamakon yana addu'a, sai bai amsa ba. Kusa da gwaggo ya zo ya zauna yana faɗin "Momma am feeling hungry". Hannu ta kai ta ɗan shafi kansa, cikin sanyin murya ta ce "Sannu da tashi, let me bring food for you ko?".

"No momma just leave it, I can't eat anything without my heartbeat, bari ta tashi sai muci a tare, zan jirara".

Jinjina kai ta yi, rigimar Aseef tana da yawa, shi fa ya ce yana jin yunwa, za'a kawo mashi abinci kuma ya ce sai da Akila zasu ci a tare, ya iya rigima kala kala.

"Momma what happened to Rimsha?". Ya yi maganar yana kallon Sultan da ya dafa kanta yana yi mata karatu a fuska.

"She isn't feeling fine". Ɗan zaro idanu ya yi tare da cewa "What? Momma kuma shi ne ba'a gaya mani ba? What is wrong with her?".

A takaice gwaggon ta ce mashi aljanune suka taɓata. Shiru ya ɗan yi yana maimaita kalmar aljanu, shi sai yau ma ya taɓa jin wannan suna, wai aljanu, abin ma dariya ya bashi, ko meye aljanun? Ya tambayi kansa. Da yaga dai shi ba wani ganewa zai yi ba, sai ya miƙe yana faɗin "Let me go and see uncles".

A takaice gwaggon ta ce mashi "Is good, suna ma shirye shiryen wucewa gidajensu yanzu ne". "Why zasu koma gidansu?". Ya tambaya da mamaki a saman face nasa.

Brr Naurat ce ta ce "E mana zasu koma gidansu, shi ne dai'dai, a nan sun takura sosai ne". Turo baki ya yi yana faɗin "Amma without uncle Hossain ko? Dan ni Allah ba zan yarda ya je ko'ina ba, dole duk in da zamu je mu tafi da shi tare, i don't want him to stay out of us". Ya kai karshen maganar kamar zai yi kuka.

Da sauri gwaggo ma ta ce "You are right! Nima gaskiya ba zan iya yin nisa da Nawazuddeen ba, dan haka shi dole ya zauna a tare da mu, dole na gayawa Saif, ina son mu kasance a tare da Nawazuddeen".

Juyowa ya yi ya dawo ya sumbaci gwaggon a kumatunta yana faɗin "That's my momma, that's why I love you, uncle babu in da zai je, we are together with him". Ya kai karshen maganar tare da wucewa ya fice daga ɗakin.

Ita dai Brr Naurat da idanu kawai take binsu, Aseef ɗan rigima.

A takaice sai da Sheikh Sultan ya shafi kwana uku yana yi wa Rimsha addu'a tare da magunguna irin na addinin musulunci, sannan ne suka sami nasarar cetota ta dawo dai'dai, amma fa anci kwakwa, an wahala ba kaɗan ba, tsayuwa zayyana maku irin wahalar da aka sha ma sai mu cike wannan book 4 ɗin fam, da akwai sauran story a gaba, so ba zan tsaya ɓata lokaci na sosai a wajen zayyano maku ba, just ku yi imagine ya bakar wahala take a ranku, akwai abubuwa da yawa a gabana, ba zan tsaya ɓata lokacina ba!.

A cikin waɗan nan kwanaki ukun fa abubuwa da dama sun faru, wanda suka haɗa da dawowar Tga Nigeria, dan Lion ya ce mashi ya dawo Nigeria zai biyo shi, sannan su Abba kowa ya koma gidansa lafiya lou, yanzu gidan ya rage daga gwaggon, Brr Naurat da Dr Salman, sai Jehan, Rimsha and Akila, matan TRIPLETS kenan, sai Sheikh Sultan mai yi wa Rimsha magani, ita kuma Anaya sun wuce Washington da Mark ɗinta, Lion yasa an mayar da shi can, dama already kunsan Brr ta ce ya karɓi kalmar shahada sai a aura mashi Anayar su tafi a tare, to hakan aka yi, su Abba ne suka ɗaura auren a cikin palo bayan ya musulunta, yanzu sun wuce Washington yana asibiti bawan Allah, yana shan wahala sosai da sosai, sai daddyn Rimsha, shi ma yana nan a gidan bai koma gidansa ba, dan gwaggo ta ce babu in da zai je ya barta gaskiya, shi ne Lion ya ce to ya zauna sai ya dawo kawai, Aylar daddyn Jelly kuwa tana asibiti a kwance, saboda ta samu matsala a cikinta har sai da aka yi mata aiki, ta sha wahala ne, cikinta ya zube, ta zubar da jini, sannan ta ɗauki tsawon kwanaki a sume, ga kuma wahala da jijjiga da cikin nata ya sha, abin dai ba'a cewa komai, Allah ne ma ya kaddara tana da sauran numfashi a gaba, ai da ta jima da mutuwa, yanzu dai shi ne yasa sai da aka yi mata aiki, yanzu haka tana gadon asibiti tare da Aunty matar Abbi, dama kunsan sun koma gidansu. A ɓangaren su Aafia kuma, Abbo ya dawo, ya sakata a gaba, tun da ya dawo ya makale yana zarya a tsakanin gidansa da gidan Abbi, Ummi tana Katsina wajen ƴan uwanta, bata san ya dawo ba baiwar Allah, kuma bai bari ta san ya dawo ɗin ba, dan ba ta ita yake yi ba a halin yanzu, hankalinsa ya karkata a kan Aafia, dan ita ya dawo dama, ana buƙatar ta a wajen tsafin nasu, shi ne ya dawo ɗaukarta, sai safa da marwa yake yi a tsakanin gidajen biyu, sai dai Allah da ikonsa, duk zuwa gidan Abbi ɗin da yake yi baya samun ganinta, ko sau ɗaya bai haɗa idanu da ita ba, shi kuma burinsa kawai su haɗa idanu, suna haɗa ido shikenan ya sami kaso 60 a cikin ɗari na abin da yake so, Allah sarki, so suke yi su hallakata kamar yanda suka hallakar da Dr Nawid, Abbo shi ya bada Dr Nawid, sai dai ba'a son ransa ya bada shi ba, dole suka tilasta mashi, da farko ma ya ce ba zai bayar ba, sai da ya ji matsa da wahala ne ya yarda ya bayar, abin da yasa suka ce sai ya bada Dr Nawid ɗin kuma shi ne, idan baku manta ba Dr Nawid ɗin ya hana shi yin amfani da Jelly, to shi ne abin ya ɓata masu rai, suka ce tun da ya rushe masu shirinsu a kan jelly, to za su yi amfani da shi a madadinta, shi ne yasa suka kashe shi.

To a takaice dai Abbo ya dawo, yana neman ta yadda zai yi ya ɗauki Aafia ido rufe.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull