Kenza eBookz

Triplets book 4 Complete - Chapter 81

Triplets book 4 Complete - Chapter 81

Triplets book 4 Complete Chapter 81: Triplets book 4 Complete Chapter 81. Kujera Mark ya kawo mashi ya zauna kusa da wutar yana gasawa. Ba dan tsananin…

3,321 words

Kujera Mark ya kawo mashi ya zauna kusa da wutar yana gasawa. Ba dan tsananin tsoronsa da su Mark ɗin suke yi ba, da yau babu abin da zai hana basu yi mashi video ba, dan ko a mafarki basu taɓa tunanin zasu gansa a kusa da gas na girki bama bare kuma itace, sam basu taɓa yin gigin irin wannan tunani ba, sai ga shi yau saboda babynsa ya zauna a gaban itace mai ci da wuta yana gasa kifi, gaskiya mace duniya ce, duk wanda ya ce maka mace bata isa ba, to wlh bai shiga hannun macen da ta kai mace wadda ake cewa mace ba mun rako mata ba, kun san akwai mace wadda ta amsa sunan mace, sannan kuma akwai mun rako mata, sune zaku gansu sai a hankali, amma cikakkiyar hamshakiyar mace, ai ko namiji baya so sai ta juya shi son ranta.

A takaice dai yau ga His Excellence of United States yana aikin gasa kifi a bakin ruwa........😂

Kai mata duniya ne, dole haka ya yi wannan aiki ba dan ya so ba, sai dan yana son farincikin matar tasa da kuma abin da yake cikinta, a can gefe guda kuma Sir Safwan ya ɗake a saman kujerarsa cikin office nasa dake white house, ya haye kujera yana ta aiki tamkar Lion ɗin ne, babu wanda ya iya gane cewa ba Lion ɗin bane, kowa a matsayin Lion yake ɗaukarsa, ba su san ga shugaban kasarsu mai mulkarsu a nan bakin ruwa shi ma ana mulkarsa ba, ya mulki al'umma, ya juya su son ransa, shi ma kuma under 15 years girl ta mulkesa ta juyasa son ranta, wannan abin ni PRINCESS FATEEMA ZAHRA yana mugun yi mun daɗi..................😂(Team Lion kada wanda ta ji haushina kun ji na gaya maku😂 ato daɗi nake ji yadda Rimsha take murza kanbun mulkinta😂 ya gasa mana kifi muci😂 dama ni ina da Maltina mai sanyi 🥱)

Haka ya gasa wannan kifi tsab, sannan ya bar wajen tare da komawa ta gefe guda yana turɓune fuska. A saman laps nasa Rimshar ta zo ta zauna tana faɗin ya bata kifin a baki to.

Idan baku manta ba tun a book 1 Aseef baya cin namar kifi, hakan yasa dukka TRIPLETS basu damu da shi ba, ya zamana suma basu so, so har yanzu Lion wari kifi take yi mashi, bai iya ci ba, baya son karninta kuma. Amma a haka ya daure ya rinƙa bawa Rimshar a baki, dan ya samu ta ci abinci, yasan ba komai take ci ba sai abin da ta zaɓa.

Shi dai Mark izuwa yanzu ya gama sadaukarwa da cewa babu abin da mace ba zata sanya namiji ba, mace zata iya juya namiji son ranta idan ta san menene ciwon kanta.

A takaice sun ɗauki tsawon lokaci a wajen wannan bakin ruwan, sun sha soyayya ba karya, Rimsha ta zuba sarautarta son ranta, abin gwanin birgewa, sai da lokacin da zasu tafi Nigeria ya yi ne gwaggo ta kira shi a waya a kan ya dawo zasu je Nigeria.

Okey ya amsa mata da shi, amma sai ana gobe zasu tafi sannan ya dawo gidan.

Wani irin kyau Rimshar ta kara, jikinta ya samu sauki sosai, dan ta samu hutu, ga kayan marmari da take ci sosai, sai ta kara fresh over. Sai dai kuma har yanzu babu wanda ya iya gane cewa tana da ciki, sam basu gane ba, dan cikin bai fito ba, kwata kwata 3 months ne cikin, domin two months suka yi a bakin ruwan kafin su dawo.

Sun shirya zuwa Nigeria gagarumin shiri, dan sun tsara idan suka je zasu yi ziyara sosai. Sai dai fa ko da suka je Nigeriar basu sauka a gidan Lion na Kaduna ba, a villa suka sauka, a fadar shugaban kasa, saboda yanzu in dai ba tafiyar sirri zasu yi ba, to babu in da zasu je su zauna a karamin waje, sun wuce wannan level ɗin, ku kanku kunsan matsayi ta ci uban na da.

Daddyn Rimsha bai zo Nigeria ba shi, shi suka tarawa aikin a matsayinsa na vice president, suka tara mashi aiki suka tafi suka bar bawan Allah, mummy ta so zuwa, amma ina ba hali, haka ta hakura ya zauna tare da mijinta.

Sun sha yawo a Nigeria sosai da sosai, sun yi ziyara wajen ƴan uwa da abokan arziki, har Bauchi sai da suka je wajen ƴan uwan Dr Salman, sannan suka je Katsina wajen su Maman Sadiq. Jehan ce ta sanya Areef ya yi wa Maman Sadiq da Sadiq ɗin gagarumin kyauta, katafaren dankareriyar gida na alfarma ya saya masu a cikin gari, ya ce su bar kauyen nan, sannan ya biyawa Sadiq da Yusuf school fees na tsawon su kammala karatun a wani katafaren school na ƴaƴan manya, ya bawa Sadiq jari mai tsoka da zai iya isar sa ya rike ahali guda, shi ma baban Sadiq ɗin ya bashi jarin sosai, da farko Jehan ta so hana shi ya bawa baban Sadiq ɗin, ta ce ai munafikin uba ne mugu, sai da Rimsha ta roketa, sannan ne ta yi shiru ta hakura Areef ɗin ya bashi 5m.

Daɗi kamar baban Sadiq ba zai mutu ba, nan take ya hau zuba masu godiya tare da godewa Maman Sadiq da ta rike su Jehan mutanen kirki. Ni kuwa nace ɗan banza, sai yanzu kasan da cewa su mutanen kirki ne ba, da yake anji maiko, kai amma wannan hali naka dai tirr da shi.

Lion kuma Rimsha ta ce to ya biya masu kuɗi su je Makka su yi ibada, Okey ya amsa mata tare da cika mata abin da take so, su maman Sadiq za'a keta hazo zuwa ƙasa mai tsarki.

Bayan sun kammala zasu bar garin Katsina su koma Abuja ne Aafia ta ce da Uncle T zata je wajen Ummin Dr Nawid a gidan sarki kenan.

Ba musu suka ɗunguma zuwa can, dan ziyara suka zo, sai dai fa Lion da Rimsha basu bisu ba, sun kama hanyarsu sun bar garin, Rimsha ta tsayar mashi da rigimar sai dai ya kaita garin Ilorin, dan tana son ta je taga Kausar, dama kuma idan baku manta ba ya taɓa yi mata alkawarin zai kaita can, dan haka sai ya ɗauketa suka nufi can.

Su Aafia kuma sun je su duba Ummin Dr Nawid tana nan lafiya, a nan ne suka sami labarin Abbo ya dawo bai mutu ba, sai dai ya haukace yana yawo bola bola, ga ciwon kafa da yake fama da shi, kafar ta ruɓe har tana tsutsa, an nemi magani har an gaji babu sauƙi, hakan tasa aka raba auren Ummi da Abbon, da da farko ma an ɗaure shi ne, daga baya da aka ga wannan fa ba samun lafiya zai yi ba, sai aka sake shi ya shiga duniya ɗan banza.

Nasan zaku yi mamakin jin cewa Abbo yana raye, to dama bai mutu ba, da ginin tazo ruguzowa a kansa sai ya ɓace, hakan tasa yake raye, sai dai kuma aljanun tsafin nasa sun ce ba zasu yafe mashi ba, dan sun bashi arziki mai tarin yawa, da alkawarin zai basu mata, sau uku kenan yana yi masu alkawarin basu ƴan mata amma yana karyawa, ya yi alkawarin basu Jelly, Allah ya kuɓutar da ita, sanan ya yi alkawarin basu Aafia, nan ma Allah ya kuɓutar da ita, sai Adiva kuma, ita ma Allah ya kuɓutar da ita, hakan ne ya arzuƙa dodannin tsafin nasa suka haukatashi, sannan suka sanya mashi ciwon kafa mai azaban zafi har tana tsutsa.

Sosai Aafia ta ji daɗin hakan, amma bata nuna hakan a fili ba, sai ta ɓoye murnarta ta taya Ummin Alhini kawai.

Sun samu tarba ta karamci da girmamawa a wajen ƴan uwan Ummi, hakan ya yi masu daɗi sosai. Cikin dabara Aafiar ta tambayi Ummin ina Oummunsu wato hjy Hadiza, nan Ummin take sanar da ita ai ita ma Oummu ƙwaƙwalwarta ya taɓu an kaita gidan mahaukata an ɗaureta.

Cikin ruɗu Aafiar ta tambayi me ya sameta, nan fa Ummi ta bata labarin cewa Hjy Hadizar ta yi aure a kan aure ne da wani Balarabe har sun haifi yara biyu, to ashe balaraben kam mugu ne, duk ya lalata mata yara, ba wanda yasan me yake aikatawa har sai da ciwo ya kama yaran suka mutu, to Hjy Hadizar ta zo ta gane gaskiya shi ne kwakwalwa ya taɓu saboda son da take yi wa yaran.

Sosai Aafia ta yi kukan jin abin da oummunsu ta yi, abin ya yi mata ciwo sosai, amma ya zata yi? Haka Allah ya ƙaddaro masu nasu kaddarar, dole kuma su rungumeta.

Sosai Ummi ta rinƙa rarrashinta tana bata baki tare da nasiha a kan yarda da ƙaddara. Jiki a mace ta rinƙa zubawa Ummin godiya. Haka suka cigaba da yin hira har zuwa karfi 2 na rana, bayan sun yi sallar azahar sai suka ɗauki hanyar komawa Abuja. Amma fa kafin su koma sai da aka ɗaura auren Uncle Herry da Ummin Dr Nawid ɗin, dan ta gama idda, kuma dama tun da ta je Washington time ɗin haihuwar su Jehan ya kamu da sonta da ya ji cewa mamar su John ta mutu, sai ya ji yana sha'awar ya auri ƴar Nigeria kamar yayansa Dr William kenan, duk da cewa shi Dr William kusan za'a ce ba ƴar Nigeria ya aura ba, dan gwaggo dai ƴar Russia ce, bata wani zauna a Nigeria ba koda suka dawo ɗin ma, kada ku manta da ta koma wajen daddyn Rimsha ma a Dubai suka zauna kafin daga baya su dawo gida Nigeria.

So a takaice dai sai da aka ɗaura auren Uncle Herry da Ummi kafin so dawo Abuja, kuma ya taho tare da matarsa, Ummi ta baro Katsina kenan, Allah mai kyauta mai kari, mai yin yadda yaso, tana son Aafia sosai, ga shi Allah ya sake haɗasu waje guda da Aafiar, sun sake curewa a family guda abin ya burge matuƙa.

A ɓangaren su Lion kuwa, kasancewar da jirgi suka tafi Ilorin ɗin, sai suka isa da wuri, kai tsaye gidan gwamna suka sauka, sai da suka ɗan huta kafin su bada sanarwar zasu je in da suka zo domin shi.

Dankara dankaran motoci goma sha biyar gwamna ya fitar dan a kai'su in da za su je ɗin.

Har kofar gidansu Kaunar aka kai'su, dan Rimsha bata mance da sunan unguwar ba, suna zuwa unguwar kuma ta gane gidan.

Tun da suka dimfaro unguwar jama'a suke ta kallon motocin, domin tsadaddun motoci a jere irin haka basu saba zuwa su wuce ba, ga kuma uban jiniya da motocin sojoji biyun da suka rakosu suka saki, jiniya ta karaɗe ko'ina tamkar filin yaki zasu tafi.

Ganin motocin sun yi parking a kofar gidansu Kausar ne yasa jama'a suka fara cincirindo suna fitowa daga gidajensu ne shagunansu ne, dan su kalli me yake faruwa.

Rimsha sarkin kauɗi, har ta kai hannu zata buɗe kofar motar ta fita Lion ya riƙota.

Da mamaki take binsa da kallo, ɗaure fuska sosai ya yi yana faɗin ina zata je?.

Ganin babu alama sauki a tattare da shi ne yasa ta nutsu, cikin sanyin murya ta bashi amsa da cikin gidansu Kausar.

Kallon driver da yake tuƙasu ya yi, cikin bada umarni ya ce. "Go and call Kausar for her".

A hanzarce bodyguard ɗin ya amsa da okey sir, sannan ya fito da sauri ya nufi cikin gidan.

Sojojin da suka rakosu kuwa, suna yin parking na motocinsu suka diro kasa daga saman bayan motocin, cikin ƙanƙanin lokaci suka kewaye arear wajen da bindigunsu dan tabbatar da tsaro, da gwamna ya so a tashi helicopters ne ma dan bawa Lion ɗin tsaro mai inganci, amma sai Lion ɗin ya ce mashi a'a baya bukatar hakan, iya motoci biyu na sojoji sun wadacesa, dan shi ba rago bane ba........😌

FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA CE.....✍️🔥

❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️❤️🔥

*KINDADE KINA NEMAN ABUN DA ZAI SANYAKI QIBA,QIBA MEKYAU KIYI DIMIMI DUK INDA KIKA SHIGA BABU RAINI KINYI TA SIYA KINA ASARAR KUDINKI🤔 ALBISHIRINKI NAZO MIKI DA ABUN DA ZAKISHA BA TARE DA KINYI ASARAR KIDINKI BA 💃 Yana da matiƙar kyau sosai ko'ina naki zai chiko ki xama abar sha'awa duk mai buƙata ta nemeni ta wannan number 09067614054, kada ki bari ayi babu ke, kayanmu tested and trusted ne, guarantee ne*.

*KINDADE KINA NEMAN ABUNDA ZAI SANYA KISAMU XAMAN LFY TARE DA KWANCHIYAR HANKALI? TO BABYN HABIBI KIXO UMMU AFFAN TAXO MIKI DA SHAHARARRUN KUMA INGANTATTUN MAGUNGUNAN MATA, KAMA TUNDAGA KAN HUMRA, TURAREN WUTA, INFECTION KILLER, COLACCA, SAI KAYAN GYARA PAGE. KACA KACA. YALLAGWADA. JIGIDA. RUWA RUWA. BANI BANI. WOMEN JELL BATA BATA. DAFIN KAXA. TANTABARA. XABUWA. CICCIƁI. AND EXCLUSIVE, XUMA TASTED AND TRUSTED INA FARIN CHIKIN SANAR DA KU MUN FARA RAMADAN PROMO GAME BUQATA XA A IYA TUNTUBA NA TA WANNAN NUMBER 09067614054 JIGAWA STATE MUNA AIKAWA KO'INA CIKIN AMINCI DA YARDAR ALLAH, BABYN HABIBI KARKIMANTA DA KAYANMU FIRST CLASS NE, DAGA KANSA AN RUFE KOFA, YANA DA INGANCI NA WUCE TUNANINKI*.

❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥

https://whatsapp.com/channel/0029VaMOfZZI7BeKXPU9gK2S

❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥❤️🔥

TSARAWA DA RUBUTAWA......✍️

❤️FATEEMA ZAHRA MUSA (💫PRINCESS TEEMA💋)

*Domin samun damar karanta littafin nan daga farko har karshe zaki iya nemana ta wannan number 08161390581*

E55

"Noorish a kirata kuma? Tom ai ba ita kaɗai bane, ina son in ga Iya ma".

Jawota jikinsa ya yi yana faɗin. "Koma waye kike son gani za'a kirasa ya zo nan, ba zaki shiga wannan local wajen ba, da na san a irin wannan kazamin wajen suke ma ai da ba zan kawo ki ba, sai dai nasa a ɗauko maki su ki gansu, amma saboda rigima irin taki sai da kika wahalar da ni kika kawoni dirty place ɗin nan".

Wai shi Lion bai san cewa ita Kausar ji da kanta take yi a matsayin big girl bane da zai zage masu unguwa?😂

Shiru ta kwanta a jikin nasa har bodyguard ɗin ya fito daga cikin gidan a tare da Kausar da kuma Iya, Kausar ɗin tana rike da wani baby boy mai kama da boda Jami'u, bakin kirin da shi.

Ganinsu yasa Lion ɗin yasa aka sauke mata glass ɗin motar ta side ɗinta, sannan ya ce ta tashi su gaisa dan shi ya gaji da kallon wannan kazamin unguwar, yana son su tafi.

Cikin zumuɗi ta tashi daga jikin nasa tana ambatar sunan Kausar ɗin.

Sam Kausar ɗin bata iya gane ta ba, saboda ba karya Rimsha fa ta canza gabaɗaya, ba zata taɓa cewa ita ɗin bace.

Sai da ta yi wa Kausar ɗin bayani, sannan ne ta iya gane ta, abinku da yarabawa, ihu Kausar ɗin ta fara zundumawa tana ambatar Rimsha! Rimsha!.

Sai murmushi Rimshar take yi, taso ta fita su gaisa da kyau, amma Lion ya hanata, wai ba zata sauka a cikin dattin nan ba, dole ta hakura suka gaisa tana daga cikin motar.

Kausar ɗin taso bata labarin bayan rabuwarsu da komawarta Daular Mutuwa da ruguje Daular Mutuwa da wasu bayin Allah suka yi suka sa ta fito, da cikin shegen da boda Jami'u ya yi mata ya gudu Lagos ya barta da yaro wai ya tafi neman kuɗin da zasu yi aure, da dai sauransu. Amma ina Lion ya ce su wuce, dan shi bashi da lokacin tsayawa shirmen matan nan, Rimsha ta so jin labari, amma ina ba dama, haka dai ta ji labarin sama sama.

Ta taya Kausar ɗin alhinin abin da suka faru, sannan ta ce Lion ya basu kuɗi mana, yana ta aikin latsa wayarsa tun lokacin da su Kausar ɗin suka zo, ba tare da ya ɗago kai ba ya ce ta ɗeba ta basu mana.

Sai ɗaga mashi gaisuwa Kausar da Iya suke yi, amma ina ko kallo basu isheshi ba, tamkar bai san da sun zo wajen ba, sai ya kama aikin latsa wayarsa kawai, sai kallonsa Kausar take yi, tana son ta yi wa Rimsha gulma ta tambayeta waye shi, amma tana tsoron shi, saboda bata ga fuska ba, kun san yadda face nasa take ai? Babu alamar wasa, ga kwarjini mai rikitar da mutane, hakan yasa Kausar ɗin ta sha jinin jikinta ta haɗa malaman jikinta ta nutsu.

Cikin zumuɗi Rimshar ta ɗebo maƙudan dollars daga aljihun Lion ɗin ta miƙawa Iya, sannan ta sake ɗebowa ta miƙawa Kausar ɗin. Abin ku da yarabawa, har kasa iya ta zube gwiwowinta tana zuba uban godiya.

Umarnin Lion ya yi wa drivers ɗin a kan su tafi. Ba ɓata lokaci suka tashi motocin a dubu suka bar unguwar.

Har suka ɓacewa ganinsu Iya da Kausar suna zube a saman gwiwowinsu suna aikin zuba godiya, iya har da kukanta da hawaye, dan ba kuɗin wasa Rimsha ta basu ba, idan zasu canza wannan kuɗi a kallah zai kai 5m, dan dollars ne, Lion bashi da wani kuɗin da ya wuce dollars, ga shi dama suna cikin halin babu, abinci ma idan sun sami na safe basu sa ran zasu sami na rana, sai ga shi yau Allah ya aiko masu Rimsha ƴar albarka ta zo ta basu kuɗin da basu taɓa tunanin zasu same shi ba a rayuwarsu, ai dole su yi kukan murna.

Suna barin unguwarsu Kausar kai tsaye airport suka nufa, dan su koma Abuja.

Su Akila kuma sun je Kaduna gidan Abbanta, a nan ne Ammienta take sanar da ita ɗan uwanta Duna ya dawo, ashe dama bai mutu ba, kuma ya musulunta shi ma, ya bar harkar tsafi, sannan ya gaya mata gaskiyar cewa Queen ba Mahaifiyarsu bace, yayarsu ce da suke uwa ɗaya uba ɗaya, dan haka ba Queen ce ta haifesu ba, sosai Ammien ta yi mamaki jin hakan, dama ita ta ra'ina girman Queen ɗin nan a ce uwarsu ce, ashe uwarsu ta mutu tun kanwar Ammien tana jaririya, kwananta uku da haifar kanwar Ammien ta rasu, Queen kuma ita ce babbar yayarsu, shi ne yasa ta rikesu tamkar ita ce uwarsu, dan ta girmesu sosai. Alhaji Mustapha mijin Hjy Zainab ma ya dawo, ashe bawan Allah yana a tare da Duna, tare suka gudu daga Daular Mutuwar lokacin da Queen ta yi ƙoƙarin kashesu, sun samu sun kuɓuta da kyar, sai dai ita Hjy Zainab kam ta mutu, Queen ta kasheta kamar yadda ta kashe Amarya matar Dr Salman, sai dai muce Allah ya sakawa Hjy Zainab kasheta da aka yi bada hakkinta ba, ita kuma Amarya dama mugun iri ce, sai dai muce masu hali irin nata su yi ƙoƙari su tuba su dai'na, ko kuma suma karshensu ta yi irin ta amarya ko fin haka.

Sosai Akila ta yi murna da jin cewa dan uwan mamanta Duna ya dawo, kuma ya musulunta, ko ba komai yanzu tana da uncle guda ɗaya musulmi.

Sun je gidan Abbin Irfan ma, a nan Abbi ya sanar da Aafia cewa kidnappers sun sako kawarta Rufee ta dawo gida, shi ma last week ya samu labari, amma sun yanke mata kafa guda ɗaya, dan kafar ta ruɓe, da kyar ma suka sakota, dan sun mayar da ita parkarsu ce, bada aure ba suke kwanciya da ita, kuma ba mutun ɗaya ba, wannan ya yi ya bawa wannan, tamkar wata karya haka suka mayar da ita, kawai Allah ya kaddara tana da rabon fitowa daga hannunsu ne ma yasa ta fito, badan haka ba da ai ita kam shikenan tata ta kare, yanzu ma cututtuka kala kala ta ɗauko, sai dai muce Allah ya bata lafiya ya kawo mijin aure, masu hali irin na Rufee ishara gareku, ku tuba ku da'ina.

Aafia ko a jikinta da ta ji wannan labari, sai ma cewa da ta yi Allah ya kara.

Sosai Aunty ta kara yi mata nasiha a kan ta zauna ta rike mijinta da kyau, ga shi ta samu miji jarumi ɗaya tamkar da dubu, ga kuɗi, mulki, ga shi soja, sannan ba karo mata kishiya zai yi ba, dan su mata ɗaya suke aura, dan haka ta kula da shi sosai su mori kuruciyarsu, ita ma Aunty ta haifi ɗanta namiji ɗaya. Godiya sosai Aafiar ta yi mata.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull