Wata kishiya complete by sa'adat - Chapter 27
Wata kishiya complete by sa'adat Chapter 27: Wata kishiya complete by sa'adat Chapter 27. wasu daga yawancin mutane da dama, na zargin tana hakan ne saboda…
2,819 words
wasu daga yawancin mutane da dama, na zargin tana hakan ne saboda danta yaci shugaban kasa a nigeria, nan ko Allah kadai yasan zuciyarta, ita dazata rasa komi a batta da d'anta dase tafi farin cikin hkn a kan wannan yalwar arzikin da Allah ya mata....jiri taji yana neman kwasarta, dan haka ta koma ta zauna daga tsayuwar datake, nan take taji kanta yayi wani dum-dum kawai kamar an saukar mata da ruwan azabar ciwon kai, nan da nan kawai taji idanuwanta sun lumshe, cikin hanzari ta mike a daddafe kmr makauniya, hajiya Binta, wato wadda tafi kusanci da ita, jakadiyarta,, na ganin ta mike ta biyota a baya sauran masu taka mata baya sukayi kokarin biyosu hajiya binta ta dakatar dasu domin tini ta fahimci chanjin yanayin uwar gijiyarta. Karasowa hajiya binta tayi ta dafeta ganin tana niyar faduwa saboda ko gabanta bata gani, sosai. "Ki kaini part din baban jalalu..." Itace kalmar data fito daga bakin hajiya salma da kyar. "An gama ranki ya dade..." Cewar hajiya binta, ita ta kamota, suka nufo part din me martaba Sarki, tin kafin su karaso ya fito daga part din nasa cikin hanzari sanye da jallabiya. ya tarbeta domin yana daga window tin sadda take tsaye baking get tana kallon masu raba sadaka, yana kallanta har zuwa yanzu. Karasowa yayi ya amsheta daga rikon da hajiya binta ta mata wadda a kalla zata kai 60yrs. Dukawa tayi har kasa ta korowa me martaba gaisuwa, ina be samu damar ansawa ba, hankalinsa na kan iyalinsa farin cikinsa. "Salmanah ya akayi? Ko jikinne?'' Ya jefowa hajiya salma tambayar, saboda yau daman ta tashi batajin dadih, dama seda yace mata ma yau ta dakatar da bada sadakarnan ta bari se next friday amma taki. "Kaina ke ciwo..." Ta fadi idanuwanta na ciccikowa da kwallah, cikin hanzari ya nufa babban falonshi da ita, yanata mata sannu, ya tabbatar ciwonne ya matsa mata sosai, da bazata taba gaya masaba, tafi karfin 2weeks tana rashin lafiya a tsaitsaye ya tambayeta meke damunta tace masa bakomai, yayi-yayi a kira dr amma taki amincewa, to tabbas yanzu data bayyana ciwon yacita sosai ne. binta ta juya ta koma bakin get tana me jimamin halin da hajiya salma ke ciki, binta tasan komi, kuma kullum cikin adduarh suke a kan Allah ya karkato da ran Farin cikin uwar gijiyarsu gareta wato JALALUDDEN.
A kan kujerar 3st suka yada zango, yayinda hajiya salma ta kwanta ta daura knta bisa cinyoyinsa, kwance take kn cinyoyinsa amma yana jiyo heart beat dinta, dan haka hnklinsa ya kuma tashi, ya dauki wayarsa ya lalubo lambar Dr, bugu daya dr rabi'u ya dauka zuciya fal mamakin yau Sarki ne da knsa ke kiransa, be taba kiransa da knsa ba, sede yasa na hannun damansa wazo Zakinsa wanda shine aminin sarki kuma me masa hidima Umar sunansa,. Yana daga kiran Me martaba yace "kazo gida ynzu,.." Yana fadar hkn ya katse wayar. Yadda yayi maganar ya kara tabbatarwa da rabi'u ba lafiya. Ba bata lokaci ya iso gidan, direct part din me martaba ya iso, ya nemi iso aka masa iso, ya shigo bakinsa dauke da sallahma yana me karewa aljannarh duniyar falon kallo, an narka dukiya ainun a falon. Karasowa dr rabi'u yayi cikin hanzari ganin hajiya salma kwance kan cinyar me martaba kallo daya ya mata ya fahimci itace ba lafiya. Ba bata lokaci dr ya dubata kasancewar akwai kebantancen asibiti da komi na bukatuwa a cikin gidan, dr yayi mata allurori nan da nan tasamu bacci. Dr ya juyo ya kalli Me martaba wanda ke zaune gadon da hajiya salma ke kwance, yayinda dr ke zaune bisa kujera. "Dr meke damunta?'' Itace Kalmar data fito daga bakin Me martaba zuwa ga dr, cikin tsananin tashin hankali me martaban yayi tambayar. Dr ya fara da kwantar masa da hankali, dukda be fahimci meke damuntaba saboda ba fanninsa bane amma ya tabbayarda akwai matsala. Me martaba yace "rabi'u, kanata kwantarmin da hnkali dan Allah ka gayamin meke damun matata.." Me martaba ya fadi cikin zallar damuwar tashin hankali, yayi mgnr tmkr ba babban mutum ba,. Dr rabi"u ya fara magana cikin muryar kwantarda hankali me dauke da tambarin girmamawa. "Insha Allahu ba wani babban abu bane, ranka ya dade, ku kwantarda hankalinku ynzu zan kira wani dr ya kara dubata,..." Hnkalin me martaba ya kara tashi yace "Kana nufin baka fahimci meke damuntaba..." Dr rabi'u yace "Ba fanni na bane, amma insha Allahu ba wata matsala bace bari in kira dr hassan yazo ya dubata inkun bada permission ranka ya dade.." Ya karashe mgnr cikin girmamawa. Ba bata lokaci me martaba ya bashi izinin kiran dr hassan. Dr rabi'u ya kira dr hassan, ba jimawa yazo ya dubata sosai, kasancewar sunada kayan aiki kwararru be wani bata lokaci ba gun gano meke damunta, zuciyartace ta kumbura,. Cikin dabara dr hassan da rabisu suka gayama me martaba, ba karamin tashin hankali me martaba ya shiga ba, dr rabi'u da dr hassan suka shiga kwantar masa da hankali, hadi dace masa ai warke insha Allahu inde aka daurata a kn magani da temakon Allah.... Haka akayi aka dorata a kn magunguna, yayinda Me martaba yake kwantar mata da hankali akoda yaushe, amma ina taki ta kwantar da hankalinta, seda aka hada da Addu'ur'i hadi da amsar mata rubutun ayoyin ubangiji kana jikin nata ya farayin sauki amma ta gaza komawa dai-dai, tunaninta da zancenta a halin ynzu duk na jalalu ne,...temakon ubangijine yayi tasiri a knta tasamu ta mike amma badan ta cire tunanin Jalalu ba, yana nan ga ranta, tasan har ta komawa mahaliccinta , jalalu shine kaf tattalinta da tunaninta a halin yanzu.
USA..... Babbar asibiti ne, wanda su knsu turawan kasar keji dashi fiyeda kowanni asibiti a kasar, har zuwa kasashen dake makwabtaka dasu, duk sunaji da wannan asibitin. asibiti ne wanda sukeda kwararrun likitoci masu aiki kmr yankan wuka da temakon ubangiji,, wannan asibitin duk wanda kagani a cikinsa ba karamin miliyoyin kudade ya sauke ba, domin kuwa zuwan asibitinma bako wanni me kudi ba na kasar balle na kasashen nigeria, duk wani me karamin karfi yayi kuskura yazo asibitin nan kaf kudadensa zasu kare ba tare dayaga Koda dr ba. 10:pm Wata dattijuwa nagani kwance bisa gadon majinyata, hannunta makale da drib hancinta makale da na'u'rar zuko mumfashi wato oxygen, gabaki daya gadon da take kaima na'ura ce ke aiki a jikinta, tako ina a lullube take fuskarta ce kawai a bude, kanta sanyeda hula blue. Fans Gadon majinyatan dakin ma kawai abin kallo ne, ko ina so perfect, akwai komi na bukatuwa a dakin tamkar kana gida. Wata mace nagani zaune bisa kujerar dake facing gadon da matar ke kwance wadda a kalla zatakai 50yrs, black beauty ce, tanada kyau dukda ta manyanta, tanada matsakaicin tsayi a kallah bazatafi 56 ba lent dinta. Ita kuma wadda ke kwance gadon majinyatan a kalla zatakai 55yrs wato mara lafiyar tanada tsayin da a kallah lent dinta zekai 60, kaf tsawon nan nata ta mikeshi a kan gadan da take kwance, kai ka rantseda Allah matacciya ce. alamomin wahalar jinya dukya bayyana a tattare da jikin wadda ke kwance a kn gadon majinyatan, farace dattijuwar matar sosai tamkar a tabata jini ya bullo, gabaki daya zubin kalarta ba irin na yan nigeria bane.
Matar dake zaune tana facing wadda ke kwance kan gadon asibitin, ta Tsureta da ido sosai fuska ba walwala, a kallah yau kusan watanninsu biyu kenan, anata mata aiki kusan karo na uku kenan, an mata juyan jini amma har rana me kamar ta yau bata farka ba, tana nan kwance tamkar matacciya, Kullum jiya iyau, abin de sede du'a'i. Ajiyar zuciya matar ta sauke, zuciyarta cike da tausayi da tausayawa wannan baiwar Allah. "Allah ya tashi kafadunki dan martabar Annabi SAW..." Cewar dattijuwar matar datayi adduarh fuska dauke da dumbin damuwa. Wayarta dake kan jikinta ce tayi vibrating, dubata tayi, taga Sunan Director ya bayyana wato me bada umarni, hanzari tayi gun daga wayar, hadi da mikewa ta nufa can cikin wani daki, saboda ba asan ayi hayaniya a kusa da ita kwata-kwata. Tana shiga ta daga wayar ta kara a kunne hadi da rage volume din wayar kasa sosai, ta yadda ita kadai ce zata iya jin me yake cewa. "Barka da dare ranka ya dade..." Cewar dattijuyar se tayi shiru batare danaji mena cikin wayar kecewa ba, zuwa can dattijuwar matar ta karbeda "eh toh dasauki de saukin musulunci,,,doctor's de sunce zasu shiga wani aikin a kanta, shine last and last in bata mike ba toh sede fa ayi hkri..." ta karashe maganar murya cike da sarewa hadi da fargaba,, tayi shiru tana sauraren na cikin wayar kana daga bisani ta amshe da "Amin ya rabbil izzati..." Tayi shiru again tana sauraren na cikin wayar kana tace "Alhamdulillahi bama bukatar komi kayi hidima iyakar hidima ranka ya dade, Allah yasa Aljannarh tazamar maka makoma kuma, Allah ya tabbatar da Alkhairi a kan wannan babban sako dake kwance yana dabo, Allah yasa muji kyakyawan result..." Daga cikin wayar akayi magana ba tare danaji ba, matar tace "Toh shikenan ranka ya dade bari in kirata yanzu ma kuwa..." Ta katse wayar,, kana ta shiga calls dinta nan da nan ta nemo number me Alamar K, wato da dukkanin alamu suna yawan waya dame wannan number din, dealing number din tayi bugu daya zuwa biyu aka daga, ta kara Volume din kiran a wannan karan. "Allah ya temakeki jarida..." Daga cikin wayar wannan kalaman suka fito. Wadda aka kira da jariya wato dattijuwar matar nan ta amshe da "tare da ke Hajiya kande...to ya maganar wasika?'' Hajiya kande tayi murmushi tace "ina me tabbatar miki da wasika ta isa har an karantata karatu me kyau irin wanda muke da bukata, jaridar ta tafi yadda aka tsarata..." Dattijuwar matar tayi murmushin nishadi, hadi da sauke ajiyar zuciya. Kana tace "Alhamdulillahi, Hajiya kande kina bibiyarsu kenan? Ma'ana kuna waya ko kina zuwa gidan....'' Daga cikin wayar Hajiya kande tace "Aah ko kusa, hasalima banda ta inda zanjita, inada ido ne a gidan, na riga nasa matakin tsaro saboda jin kome ke tafiya..." Murmushin fara'ar dake kan fuskar matar ya karu ta jinjina kai hadi da cewa "Ina me miki jinjina hajiya kande da wannan namijin kokarin..." Hajiya kande ta amshe da "Ai na dole ne ranki ya dade, wadannan makudan kudi da kuke bani ai dole in tafiyar da aiki yadda ya kamata..." Dattijuwar matar tace "Hakane wannan...ga lada ga kudi, domin kuwa wannan aiki ne na ceton rayuka da dama, da kuma fidda rayuka a cikin dumbin bakin ciki..." Hajiya kande ta jinjina kai tace "tabbas hakane...amma fa jarida ina tunanin anya za a cimma manufa kuwa, ina tsoron randa asiri ze faso fili,..." Dattijuwar tace "me kika gayamin a kan maganar wasikar a yanzu?" Hajiya kande tace "Wasika fa an tabbatarmin data isa kuma karatunta ma ya wuce yadda kuka tsara, ko ince ya wuce da sanin ku gaskiya, dan ba wanda besani ba a gidan zuwa ynzu shiyasa nake kara hango matsala..." Dattijuwar matar tayi shiru hadi da nazarurruka kwakwalwarta tashiga thinking tabbas itama tasan akwai gagarumar matsala na kwance tana dabo, amma sede inta gayawa me gayya me aiki se yace mata bakomi ai magana ta riga ta tafi yadda ya kamata ko ansamu matsala a halin ynzu ba damuwa, saboda an riga anyi digi me kyau.... "Karki damu da matsalar tinda akwai cigaban ai shikenan...bari in gayawa gimbiya, in akwai wata matsala kina iya kirana ki sanar dani tin wuri, ko in an samu ci gaba kina iya kirana..." Hajiya knde ta amsa da "Angama jarida kanun zance..." Daga hk sukayi sallahma, jarida tayi dealing number din director, a memakon tace bari ta kira gimbiyar, ina tsammanin ta kira mace se tasake kiran lambar Director, haka tsarin yake. Ta sanar dashi duk yadda sukayi da hajiya kande, bansan meyace mata ba, saboda ta kara rage volume sosai, haka tsarin yake, saboda tsaro. "To shikenan yallabai, Allah ya kara doramu a kan ci gaba,,dukda bansan meye tsarinka ba, da kakeda tabbacin ba matsala...." Bansan meyace ba, kawai ta amsa da amin daga haka sukayi sallama ta koma dakin da mara lafiyar take, ta zauna ta tsura mata ido, zuciyarta na cike da nazariririkan kalaman me bada umarni, amma fa itama zuciyarta na ciccike da tsoro, saboda gabaki daya a hatsari wasikarnan take. "Wannan shine bada rayuwa a kan rai....gashi takaddar aiken wasikar tanada nakaso..." Jarida ta fadi hakan a kasan zuciyarta,, tana tsananin san sanin meye advantage din hikimar me bada umarni, dan ita lokuta da dama bata fahimtar komi a kan lamarin, a kullum zuciyarta rauni takeyi a kan lamarin. "Ya ilahi kasa kada ayi d'a kwance uwa kwance haihuwar guzuma..." Itace kalmar data fito daga bakin jarida a wannan karan a bayyane tayi maganar hadi da sauke ajiyar zuciya tayi bending a kan kujerar datake zaune, nan take ta shiga nazarirrika kama daga bisani zuwa yanzu. "Komi sha'ani ne na mahalicci, ya riga ya gama tsara komi, kama daga farko zuwa karshinmu, mu duk muna namu ne, Allah na nashi, na Allah shine dai-dai...." Ta kuma fadi a bayyane da low voice, kawai seta rintse idanuwanta tana me tariyo abubuwa da dama.
Nagode masu kirana suji ya jikina, Jikin de Alhamdulillahi nagode kwarai wadanda sukamin message a chart bn reply ba kuyi hakuri mutanen sunyi yawane. Allah yasa mugama lafiya. Hakkinku na raina, naci gaba da posting insha Allahu amma se kun danyi hakuri har yanzu ina asibiti, kawai tunanin hakkinku ne ke raina. Ngde da So da kauna.
Vip 1k normal dari biyar (500). 0542703718 Saadatu Abdullahi gt bank shedar biya ta nan 08101626484 ko M.T.N card or VTU...pls banda kira only chart kawai ko kin kirani bazan dagaba.
SAADATU BINTU ABDULLAHI (writer of Kyautar Allah)
Paid Page22 Kwanci tashi asarar me rai kmr wasa watanni na tafiya tamkar ki daga ledar pure water a yayin da kikejin kishi,. Watanni biyu da kwanaki goma sha biyar suka shude, tuni Dr mus'ab ya dawo nigeria, sede basu hadu da Abdoljalal ba.
A bangaren Al-muqri'ah taja baya dashi a Sosai a watannin nan, so takeyi ya janye a jikinta ko kadanne, amma ina yaki, sema ya kara zame mata kmr ciwgum, batada yadda zatayi dashi. taso taki yarda suci gaba da fita zuwa office dinsa tare Amma yaki amincewa shi, dole sede taren suke tafiya suje su dawo, zuwa yanzu kaf ma'aikatan sun fuskanci meke wakana tsakanin me-gida da bebiya, sam shi hakan be damunsa, Ai meso ba a sanci da zama matsoraci ba. kwayoyin idanuwansa a kullum kara bayyana abinda yakeji a kan yarinyar sukeyi, ya gaza boyewa, gabaki daya rayuwarsa ta kuma canzawa saboda zuwan yarinyar cikin rayuwarsa, ya zama wani iri duk cikakken me hankali inze kallesa seya fuskanci halin da yake ciki na SO, dabi'unsa sun chanza rayuwarsa ta chanza gabaki daya, se yanzu yake fahintar yana cikin duniya. Fans Amma fa duk shagalin nan da akeyi ita gimbiya Drum batasan anayi ba, ko alama maganar bata isa ga ko kofar side dinta ba, ita fa zuwa yanzu tama manta da wata Al-muqri'ah, mijin nata ma bata takanshi, se azabar kishin banza. lamurranta sun kara tabarbarewa, kawai ta businesses dinta take, kudi kawai, ina zaki kudi me kikeso kudi, a kullum yunwarsu take, itafa ko kudaden accounts dinta ne suka fara low se tayi kamar zatayi hauka, tana bala'in tsoron yankewar kudadenta tamkar yadda take tsoron mutuwarta, tanasan Kudi sosai, Kwata-kwata hajiya saude batada wadatar zuci, ko miskhalazarratin. In har kaga ta dauki waya ta kira Abdoljalal to kudi take bukata, in ba dan hakan ba ko kallan number dinsa batayi, gabaki daya ta gama sakankancewa da duniya, duk monthly boka nada kudin da take biyansa na Ayyukan da yake mata a kullum a kan Abdoljalal shiyasa ta kara sakankancewa, ta riga ta kudirtawa ranta ba wanda ya isa ya rabata da Abdoljalal a doron duniya. Hajiya saude batasan komi ba se sihira, se in dare yayi aljanu suyi bidiri a kan mararta, a kan jalalu babu Abinda bazata iya aikatawa ba.
Kwata-kwata Abdoljalal Ya dena fita da securities kullum shi kadai yake fita dagashi se glashinsa (al-muqri'ah), Ubangiji ne Kawai ke tsaresa daga magauta. tin Abdoljalal yana ganin wahalar tuki da kansa harya saba zuwa yanzu, kwata-kwata bayasan abinda ze shiga tsakaninsa da yarinyar, shiyasa dayaga ta fara janye jikinta daga garesa hankalinsa in yayi dubu seda ya tashi, ya sanar da ita ya riga ya zamar mata karfen kafa, ko bata sanshi , shi yana santa kuma dole seta zauna dashi a cikin halarar soyayyarsa gareta. Bata wani bari yana tabata, daya fara tabata zata gudu, shi kuma yanasan kasancewa da ita, dan haka yake dannewa ransa yabawa zuciyarsa hakuri sede yayita kallanta yanajin sanyi a ransa, amma sha'awarta na manne da jijiyoyin Azzakarinsa. A kullum Al-muqri'ah a tsorace take dashi, saboda kalaman larai gareta, ynzu bata wani zama a side dinsa data kai masa abinci take barin side din nasa.