Wata kishiya complete by sa'adat - Chapter 6
Wata kishiya complete by sa'adat Chapter 6: Wata kishiya complete by sa'adat Chapter 6. securities din duk bakin ciki ya rufesu ganin an fito da yarinyar…
3,424 words
securities din duk bakin ciki ya rufesu ganin an fito da yarinyar wato de ba a dauke ta ba, aiko sunyi bakin ciki ganin ga dadih iya dadih kuma ze wuce ya barsu musammanma salisu tantiri shifa yariga dayasa ran har room and falo din gindin yarinyar nan seya kutsa ya shiga tako ina kmr de yadda ake brushing teeth musammanma in yayi datti, haka yaso yayi da burarsa a cikin gindin yarinyar nan duk yafi kowa sa rai, aiko yafi kowa bakin cikin ganin hajiya kande da yarinyar sun fito,Allah yasani a lokacin dasukazo ficewa a get na farko ji yadingayi kamar ya jawo yarinyar jikinsa dan wallahi seda bindinsa dake cikin wando ya mike zumbur ya fara ambaliyo da ruwan zallar sha'awar yarinyar. Suna shirin isa ga get na uku wayar hajiya kande ta shiga vibrating din neman agaji, tsuki hajiya kande taja ga dare sunyi yanzu tasan ko fita daga anguwar ma aiki ne ja, kafin su isa bakin ti-ti se sunsha tafiya, duk haushi ya rufe kande na kiran da aketa mata a wayar, ba tare data duba ba, suka fice a bakin get na ukun securities din suka bisu da Allah ya tsare kande ta amsa da Amin kai kace abin fada ne, sbda a hasale take zuciyarta dugume take. Cikin sassarfa suka fara tafiya a kn layin yayin da haske ya haska ko ina bakace dare bane sede ba motsin rai ko daya a layin ba jama'ah, kasancewar GRA ne kuma ga dare ya farayi dan 8:50pm ake nema, kusan tafiyar 20mnt sukayi kafin suka fito titi Allah yaso sukayi sa'ah suna tsayuwa a bakin titin sega yar kurkura wato (napep) hajiya kande ta taresa hadi da gaya masa ''hayin rigasa zaka kaimu..." Jin ta ambato anguwa me nisan tsiya yasashi wucewa ba tare dayace komi ba. Hajiya kande tabishi da tsinuwa sbda wucewar da yayi be daukesu ba. Ba jimawa wani me napep din yazo kande tasake gaya masa hayi ze kaisu me napep din yayi jim sannan yace "gaskiya hayi tayi nisa.." kande tashiga hadasa da Allah da manzansa kanya ya temaka mata saboda dare ne ke karayi. Me napep din yaji tausayinsu kunsan namiji da mace, shi saboda ganin kyakyawar yarinyarnan yasashima ya tsaya amma ya tashi a aiki, amma daya ganta se yaji tamkar mashi akasa a baka aka harbo masa a kirjinsa. Dan matashin me napep din wanda a kalla baze wuce 30yrs ba Yace "Toh mama ku shigo..." Kande tace "toh dannan nawa za a baka?" Ta karashe maganar hadi da marairaicewa Me napep din da idanuwansa ke kan yarinyar nan dake tsaye kusa da kande ita ma shidin take kallo a zahiri amma hankalinta na can ga wani tunanin da batasan ma meyeba. "Bakomai ku shigo mama ai baze gagara ba..." Cewar me napep din. Kande ta washe baki danta kula tin tsayuwarsa yaketa kallon yarinyar. "Wallahi yarnan da babu kullalliya a kasa dani na ajeta a gidana na dinga hadata da manyan masu kudi mazannan kawai ana service da ita ana mikomin kudade abina...amma wane mutum wane kayansa!" Hajiya kande ta fadi hakan a ranta yayin da tasa kai cikin napep din kana yarinyar ma tashigo ta zauna still yar jakar ghana most go dinta na jikinta ta kankameta gam kai kace za a kwaceta a hannunta. Me napep yaja suka fara tafiya hajiya kande ta ciro wayarta daga bag dinta taga uban miss calls shiga tayi gun miss calls din tana fadin "yauni kande na shiga uku har miss call 80, ohh ni jikar mas'udu me yalo, uwar dan kande! wannan jarabar kira ya isheni...." Kande ke surukatanta ita kadai, yarinyar de se binta takeyi da ido. Idanuwan hajiya kande suka sauka a kan miss call din hajiya saude wadda ta mata kusan kira uku,, jikin kande har rawa yakeyi tayi dealing number din hajiya saude ttana me tunanin ko meyasa ta kirata kuma oho, a zuciyarta de tana adduarh Allah yasa hakarta ta cimma ruwa. hajiya saude dake zaune har lokacin bakin bed dinta tanata tunani tunani bayan ta kira hajiya kande har kira uku bata dauka ba kawai seta rike wayar a hannunta tanata nazarirrika gabaki daya ganin yarinyar nan ya gama dagula mata guntun lissafinta, ta rasama wani tunani zatayi,, tana cikin nazarirrikan ne kiran Hjya kanden ya shigo wayar ta, hannu takai ta katse kiran seta kirata back, bugu daya kande ta dauka yayinda hajiya saude ta fara magana "Ina kika ajiye wayar ne ana kira baki dagawa..." Kande tace " Wallahi Hajiya bansan kinata kira ba, wayar ce take cikin jaka kuma na cire karar shiyasa banji ba ranki ya dade tuba nake..." Saude tace "Okay kunyi nisa ne?" Kande tace "Aah ranki ya dade, amma de harmun hau abin hawa .." Saude tayi jim harga zuciyarta bataso tace su dawo amma ta yanke hukuncin kawai ta amshi yarinyar ko nan da 1month ne kafin kanden ta kawo mata wata... Jin tayi shiru kuma tana kan wayar yasa kande tunanin ko wani abinne dan haka tace "Ranki ya dade ko wani abinne ya faru?'' Saude ta dawo daga duniyar tunanin data afka hadi da sauke ajiyar zuciya tace "kande kawai ki dawomin da yarinyar..." Jin abinda tace yasa kande farin ciki a tsakiyar zuciyarta har seda ya bayyana a kan fuskarta. "To shikenan ranki ya dade gamunan dawowa..." Saude tace "Okay .." Ta katse wayar. Kande ta cusa wayar a bag dinta hadi dacema me napep din " d'ana dan albarka maidamu inda ka dakkomu dan Allah..." Me napep din daketa aikin tukinsa yace "toh hajiya kin fasa zuwa hayinne?'' Kande tace "aah ba fasawa nayi ba, inka kaini can inda ka dakkomu zanshiga wani gida in fito seka dawo ka kaini hayin, uzurine ze maidani..." Me napep din yace toh hajiya..." Ya juya kn napep din daman basuyi wani nisa ba, yana tuki yana kallon yarinyar ta cikin madubinsa, har suka isa inda ya daukesu hajiya kande tace ya shiga dasu cikin layin..ba musu me napep din ya shiga layin ammafa dabadan yarinyarnanba wallahi da bazeyi wannan tafiyar ba saboda shi a ka'idarsa 8:pm yake tashi a aiki...hajiya kande keta ma me napep din kwatance har suka isa bakin get din gidan yayi packing. Kanden ta sakko yarinyar ma sakkowa tayi duk tanajin me sukacewa ta waya kande da sauden, dan hatta da Maganar saudenma tanaji ta cikin wayar saboda wayar bata da sirri. Hajiya kande tace dame napep din tana zuwa yanzu zata fito insha Allahu me napep din da idonsa ke kan yarinyar yace "Toh bakomai hajiya..." Kande ta masa godiya kana suka nufa get din gidan, Securities din na ganin sun doso ba bata lokaci suka barsu suka shige get na daya, zuwa na biyunma har zuwa get na ukun salisu tantiri na ganinsu ya washe baki ya taso ya iso inda suke idonsa na kn yarinyar se tande harshe yakeyi yace yana fuskantar kande "Hajiya segaku kun dawo kuma..." Hajiya kande data gimtse fuska tace "Ehh wallahi hajiya ce tace mu dawo..." Salisu tantiri ya washe baki, red teeth dinsa suka bayyana, kana yace "Madallah hajjaju kice de nan zaki bar mana wannan kyakyawar..." Kande ta dago ta kallesa taga irin kallon dayakewa yarinyar daman tin sadda sukazo gidan. Hjya kande ta kara hade rai tace "Eh nace ehh a nan za a barta sede wannan ba hurumin dazaka lasa bace,... dan wallahi karkaga kaci yar ficikar me Aikinnan ladiyo dana kawo kwanaki na rufa maka asiri wallahi wannan rufin asirinka karka koyi magana da ita dan ba sa'arka bace, ruwa fa ba sa'an kwando bane, ka kiyayi duniya salisu tantiri.." Salisu tantiri yayi mamakin yadda ta ganeshi yashafa ta mantasa ne, sbda an dade dayinnabin. kwanaki hajiya kanden ta taba kawo me aiki wata yar mitsila wadda bazata fi 14yrs ba, tantirin salisunnan ya dinga lallabata yana cin yar mutane har yayi mata ciki ciki yakai 3month sannan tantiri yagane danya saba harkar cin matan mutane, shine yasamu kande sukayi settling ya bata 10k yace tazo ta dauke yarinyar a gidan da kyar kande ta dauketa bayan sunyi cikini na tsadar tsiya duk wata ya dinga bata 20k a albashinsa harya bata kudade 140k da kyar shima dan tace zata gayawa hajiya saude ne, yasan maganar taje gun saude to tamkar me gida ne yaji maganar kuma yasan in har megida yaji mgnr ze amshi hukunci shiyasa yasamu asirin ya rufu ruf, aka zubda cikin daya dirkawa yar mutanen, sannan suka rabu lafiya shida kanden. "Haba hajiya kande kefa tawa ce kn mance ne..." Cewar salisu tantiri dake mana yana kashe ido se shafar tumbinsa yakeyi da wayau da wayau yana shafo gabansa. kande ta daka masa tsawa cikin matseefa tace "Kai dallah rufemin baki bakin shege kawai gantalalle, maye, kaide damuwarka daya ce kasa bura a gindi, gindinma bana halak malak ba sena zina, dan iska kawai!..." Kande ta masa tass-tass. Ganin hajiya kande tana neman ta tara masa mutane yasa salisu tantiri rufawa knsa asiri ya kyaleta dan inya biye mata se uban kowa yasan sirrinsa dake boye tin tini, dan hk ya koma ya zauna hadi da basarwa danma Allah yasoshi basu san kn zancen ba yan uwan aikin nasa sundeji kande na masa tsawa. Kande tayi kwafa kawai taci gaba da tafiya yarinyar na biye da ita a baya, har suka isa kiching din ma'aikatan na nan inda ta barsu sukayi mamakin ganin dawowarta, ta kara binsu ta wankesu da zagi tass-tass, kana suka nufa cikin falon hajiya saude, a falon suka tadda hajiya sauden zaune ta daura kafa daya kan daya table din gabanta cike da kayan marmari na motsa baki. "Barka da hutawa ranki ya dade..." Hajiya kande ta fadi murya cike da maula. A takaice saude ta amsa da "yawwah...ku karaso..." Ta musu iso zuwa gabanta. Suka karaso suka zazzauna a kasan carpet din, kallo daya yarinyar tama hajiya saude tayi kasa da knta haka kawai taji kiyayyar matar a zuciyarta tin sadda ta daura idanuwanta a kan picture din matar. Hajiya saude ido tabi yarinyar dashi still se take tajin bugun zuciya amma ta dage tunawa datayi da maganganun hajiya Abulle itama da knta tasan ko tsirara mijinta zega mace baze taba ko kallontaba, dan tasan kishi ne kesata jin bugun zuciya a kn yarinyar. "Toh hajjaju gamunan mun dawo..." Cewar kande ganin saude ta tasasu a gaba ba tare datace komi ba. Hajiya saude takai apple bakinta ta gutsira ta jijjiga kafarta dake kan daya cikin isa kana ta fara magana. "Zan dauki yarinyarnan kafin de zuwa ki samar min wata, nan bada jimawa ba..." Kande tace "toh hajjaju..." Hajiya saude taci gaba da magana "Amma sede akwai sharruddan dazan kafa mata ai kince tana jin magana kou?'' Kande tahi wankan tsarki tayi carab ta amshe da "Eh tanajinki hajjaju gimbiyar mata..." Hajiya saude ta kara gyara zama tana fuskantar yarinyar cikin kallon tsana hadi da bakin cikin kyaun da Allah ya tara ma yarinyar. tace "Ke kina jina Kou?'' Yarinyar ta dago ta kalli hajiya Saude hadi da daga mata kai alamar ehh. Hajiya sauden taci gaba da magana "Zaki dinga dafawa mijina abinci ai kn iya girki sosai kin iya farfesun busashen kifi hkou?'' Yarinyar ta daga mata kai alamar eh. Saude tayi jimm idanuwanta na kn yarinyar tunani takeyi ta ina za ayi aiki da bebiya wadda bata magana sekace de duk duniya an rasa masu aiki, ita da gogan ze Amince dame aikin kamfani ma aka daukar masa wadda ta iya girki sosai ba wadannan locals din ba, amma ina shi locals din yakeso. dan guntun tsuki taja kana taci gaba da magana idanuwanta na kan yarinyar "Kin iya karatu da rubutu na hausa?" Yarinyar ta daga mata kai alamar ehh hajiya saude ta dawo da dubanta kan kande tace "Wai haka ta iya karatu da rubutu? Ko karyarsu ce dasuka saba dan masu aikinnan duk makarya tane'' Kande ta amshe da "Kwarai ma kuwa hajiya...ai tayi makaranta fa ta gwabnati irin ta bebaye tayi makaranta sosai nan har rubutu da karatun turancin dana hausa kakarta tace ta sosai, tafa gama sacandari, sannan uwa uba tayi karatun Allo saukarta biyu na alqur'ani ne girma, bakin talauci nefa yasata fitowa aikinnan hajiya,..." Cewar kande data kara da fadi ba a tambayekaba. Hajiya saude tace "okay to abin zezo da sauki tinda ta iya karatu da rubutu,,, za a baki komi na abinda zaki dinga dafawa mijina a rubuce kama daga kan abinda zeci dasafe zuwa kan abinda zeci da rana da daddare da time din da ake ajiye masa komi da komi a kn dinning, ki tabbatar da kinyi komi in time banasan abinda ze batawa mijina rai sannan becin gishiri a abinci duk de za a baki a rubuce ki tabbatar kinyi komi a kn ka'ida kinajina kou?" Yarinyar ta daga mata kai alamar Toh.. Hajiya saude dake kallonta har zuwa lokacin kiyayyar yarinyar nata yawaita a zuciyarta, taci gaba da magana "Ka'idojina sune na farko karki kuskura wata magana ta shiga tsakaninki da mijina bayan gaisuwa, kin ganni nan dago ki kalleni da kyau!'' Yarinyar ta dago ta kalleta hajiya saude ta nuna knta da yatsanta hadi daci gaba da mana "Kin ganni ko banda mutumci inde a kan mijinane babu irin abinda bazan iya aikatawa ba a kan mijina, dan wallahi har kisan kai zan iyayi a kan mijina..." Yarinyar ta kure hajiya saude da ido sosai zuciyarta cike da firgici yayin da idanuwanta suka bayyana abinda ke zuciyarta wato tsoro da firgici. Hajiya saude ta daga mata kai alamar tabbatarwa. Hajiya kande ma seda ta firgita dajin furucin hajiya sauden batasha halin nata ya wice inda take tunani ba se yau. Saude taci gaba da magana cikin isa " banda kirki a kan mijina amma in kika kiyayemin mijina zakiyi aikinki ba ruwana dake saboda bani kikewa aiki ba mijina kike yimawa sede a karkashina kike, amma ko haduwa ba kullum zamu dinga yiba, sede kullum a ka'ida se duk ma'aikata sunzo sun gaisheni dasafe da daddare, kinji ni da kyau kou?'' Yarinyar dake kallonta da saurarenta ta daga mata kai alamar "eh.." Har zuwa lokacin firgici da razana basu barta ba. Hajiya saude ta kara ballar apple din dake hannunta tana masa wata iriyar tauna ta rashin mutumci a cikin bakinta kana taci gaba da magana. "Sannan Kullum ki kasance cikin tsafta, duk sanda zaki shiga kiching yima mijina girki ki tabbatar dakinyi wanka kinga sau uku zaki dinga wanka a rana kenan kou?'' Yarinyar ta daga mata kai alamar eh. Hajiya saude ta mata wani kallon dayasa yarinyar yin kasa da knta ganin zallar rashin mutumci a cikin kwayar idonta. "Banasan kiyi kwalliya ko kadan a wannan fuskar taki, kullum ki kasance cikin hijjabi dare da rana da safiya, ki dinga sa hijjabi har kasa kinadasu ko a tsiyace kikazo kema?'' Yarinyar ta dago ta kalleta zata girgiza kai hajiya kande tayi saurin cewa "Ai a tsiyacen tazo hajjaju sede in a bata hijjaban ade temaka kmr yadda aka saba..." Saude ta taba baki tace "Okay zansa laraba ta bata, sannan za a nuna mata dakinta na kwana,..ki kara ja mata kunne a kan mijina kafin ni na mata babban jan kulle, Dan banda mutumci hanyarma da mutumci yabi ni ban bi ba, karta kuskura ta dinga jimawa a side din mijina, inta kai masa abinci fita zatayi inya gama zuwa kmr 3h se taje ta kwashe komi ta gyara inda ya bata domin besan kazanta haka itama ta tabbatar da tana tsaftace knta, tanasa turare kwalliya ce kadai baza tayi ba, sannan a dinga brush dan bamusan kazanta nida mijinnawa,, in bnda ma kaddara dashi abinda yakeso megidan ai wannan yafi karfin ta dafa masa abinci.. " saude ta karashe maganar tana yatsina fuska. Hajiya kande ta amshe da "Dama mana hajiya yo Allah na tuba Ai mijinki babban mutum ne yau ko yan indian yakeso su dafa masa abinci ai ze samu, Allah na tuba kudi nefa tako ina Allah ya baku.." Saude ta yamutsa fuska tace "kundeji sharuddana kou?" Kande ta amsa "Anji ranki ya dade kuma dole abi ko ince anbi ma tini..." Hajiya saude tace "Yafi de...ynzu ku tashi kuje side din masu aiki kice larai tazo inasan ganinta dan dole wannan dund'um din seda waya sbda ta nan za a dinga mata messages din abinda zata dingama mijin nawa..." Kande ta karbe da "Dundum ma haka take wannan ai tafi dundum..." Saude ta yatsina fuska kana tace " nan zaki kwana ke kande ?'' Hajiya kande tace "Aah hajiya tafiya zanyi me napep ma na can yana jirana..." Saude tace "Okay ba dmwa ku tafi ki turomin laran de inajin yau yarinyar zata fara Aikinta mugani ya nata hannun yake..." Kande da tini suka mike tsaye ita da yarinyar ta kara amshewa da "Dama mana ta fara hajiya to meye amfaninta ai daman aikin tazoyi ba hutu ba, hutu aise ku dakukaci kuka tara..." Hajiya kande ta fadi zuciya cike da rashin imani. Saude ta tabe baki hadi da lalubar Aljihunta ta lalubo kudi yan dubu dubu kusan dubu talatin ta mikawa kande, kande ta tsugunna ta amshe jiki na rawa ta shiga antayo mata godiya ruwa ruwa, hajiya saude bata bi ta kanta ba tace "Sannan kudin aikin yarinyar nawa za a bata?'' Kande da bakinta yaki rufuwa saboda farin cikin kudin da saude ta bata tace "toh hajiya a bata abinda kikaga ya dace..." Hajiya saude tace "Okay...ya sunan yarinyar ne?" Kande tayi jim tace kai na mnta sunanta da wahala gaskiya. Saude ta daga kafada irin ko a jikintannan daman ita ko tasan sunanta ba amfani ze mata ba dan sunan duk ma'aikatanta daya ne a gunta Wato Ke\kai. Hjya Kande ta karama hjya saude godiya kana suka fice a falon, ta kai yarinyar gun sauran masu aikin nan wajen kiching sannan ta gayawa larai hajiya saude nason ganinta cikin hanzari larai ta tafi amsa kiran madam dinta. kande ta tafi cikin murnar abinda take bukata ya tafi dai-dai ko tace abinda aka sata,se hamdala takeyi a zuciyarta tana tafe tana waiwayon yarinyar , haka kawai kuma taji zuciyarta na cike da tausayin yarinyar, bata taba kawo me aiki taji tausayintaba kmr yadda taji tausayin wannan yarinyar har zuwa kasan zuciyarta, a hk ta fice a gidan zuciya cike da murna data fito tasha bazataga me napep din ba se kuma akaci sa'ah taga be tafi ba ashe yana nan yana jiranta hakuri ta bashi na barinsa datayi yanata jiranta, bakomai yace yana me jiran fitowar yarinyar danshi sbda ita ya tsaya jira da baze ma jirataba a wannan uban dadewar datayi, ganin hajiya kande ta shiga bega yarinyar ta fito ba. yasashi tambayar ina dayar dasuke tare. Hajiya kande tace " daman ai aiki na kawo ta tana cikin gidannan..." "Allah sarki..." Cewar me napep din, a zahirin gaskiya Sam me napep din ba haka yaso ba, yaso ya sake ganin yarinyar haka kawai yakejin san yarinyar na ratsashi. Wayarta dake cikin jaka ta dauko tayi dealing wata number wadda bata da suna se J kawai aka rubuta a kn sunan, hajiya kande tayi dealing number din bugu daya aka dauki wayar, hajiya kande tace "wasikarnan a gayawa me aikenta ta isa inda akeso ta isa fa akwai yar matsala ..." Daga cikin wayar akayi murmushi muryar wata dattijuya wadda a kalla zata girmema hajiya kandenta fara magana. "Alhamdulillahi karki damu da matsalar tinda tasamu mazauni kawai shikenan... muna fatan wasikarnan ta isa inda akeso ta isa domin aji dadin karatunta..." Hajiya kande murmushi tayi tace "Insha Allahu damo ze isa ga harawa...ai matsalar dama ba babba bace, tinda mun kaiga ci, a fari kin amsar wasikar akayi..." Daga cikin wayar dattijuwar tace "Alhamdulillahi kice ansha gwagwarmaya?'' Kande ta amsa da "Ai kadan ya rage wasikarnan ta yage ba tare da an karan tata ba....ammafa insha Allahu zama daram, wai me nakuda tasamu katifa..." Dattijuwar dake cikin wayar ta kara sautin murmushinta hadi dacewa "Bi izinillahi...yanzu zan idda sakon zuwa inda akayi aikensa , kema kuma taki wasikar na nan tana jiranki, domin kuwa zakisha tukuicin hidima..." Hajiya kande ta washe baki zuciyarta cike da zallar farin ciki tace "Godiya nake kuma a mikamin godiya bisa godiya...fatanmu de yanzu muji iska ta dauki farar takaddar nan ta isar da ita inda mukeso..." Daga cikin wayar dattijuwar matar tace "Inde kere na yawo zabo na yawo ai dole ne wata rana a hadu mujede zuwa..." Hajiya kande tayi yar dariyar nasara kana sukayi sallama da niyar kome ake ciki in an idda sako ga wadda tayi aiken takaddar kande zataji komi.