Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 - Chapter 14
Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 Chapter 14: Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 Chapter 14. Hande dataji shiru dagowa tayi ta kallesa…
3,358 words
Hande dataji shiru dagowa tayi ta kallesa taga yayi shiru kaman baiji abinda ta fada masa ba dan haka ta miqe tsaye tana kallansa cikin dan daga sauti takira sunansa tana cewa
"Kaji abinda na fada kuwa?
Nace Ciki ne a jikin sumayyah gatanan na haihuwa,
Da alama kuma zekai wata uku koma fiye,
Kuma wallahi tallahi bansaniba sai yau dinnan nake kamasu suna maganar,
Duk ciwon datake ta fama dashi duk tsawon lokacin nan ashe laulayin ciki takeyi bamu saniba daga uwarta sai yar uwarta suka sani sunata boyan abinsu da saidai idan an haihu munji kukan jariri a gidan mu ankara.....
Ledar lemun hannunsa data subuce masa ce yasata yin shiru tana kallan lemun dasuka watse tsakar gidan kowannen na ganganrawa nasa gefen.
Rintse idanuwansu dasukai jajir dukkaninsu sukai suna sauke numfashi mai dumi.
Ababa ma numfashin ya ringa jerowa yana kokarin sanyaya wutar data kunno cikin zuciyarsa tana cin jininsa sbd yasamu fahimtar komai daki daki akan abinda handen ke fada sbd yasan dai ciki a gidansa ba magana me yiyuwa bace sbd soyayyama ya fada musu sun sani bame yiyuwa bace haka hukuncinta me girma ne,yanzu kuma yaji ana maganar cikin haihuwar dan mutum a gidansa,
Wannan ba labarin da zai taba yarda dashi bane sbd bame yiyuwa bane acikin gidansa dai Kuma a tsakanin yayan nasa.
Gyara tsayuwa yayi yana sake calming kansa sbd Kai tsaye zancen Mai shigesa ba kafin ya kalli hande yaga lafiyarta kalau da alama ba soki burutsun zancen take ba,amma ai akwai tsufa a tareda ita Kuma tsufa nasaka zance mara kan gado,
Da Annensu ce ta fada masa da sai yace haukartace ta tashi.
Benazir dayasan gidan kaf ita kadai ce me cikakkiyar lafiyar qwaqwalwa ya kalla kai tsaye yace
"Ke Benazir fadamun meye hande take fada,kuma komai nakeson ji dalla Dalla ba irin wannan rikicin zancen data fada ba yanzu Kuma idan kika yiwa kowane zance kwaskwarima gurin fada wlh saina karya wuyan uwarki gatanan a tsaye gefenki."
Mutuwa jikin benazir yayi ta sake boyayyan numfashi mai zafi sosai ta dan dago kanta kadan batareda ta kallesa ba ta bude baki muryarta na rawa ba wahalarda Kai Kai tinda komai ya Riga ya fito Kai tsaye tace
"Eh ciki ne wata uku".
Shiru gurin ya sake dauka suna jiran wata tambayar saidai tsit ababan baice komaiba sbd har lokacin dai Bai yarda da abinda kunnuwansa suke jiba Dan kuwa ko Anne ta dauka cikinsa a yanzu dukan tashi Kisha ruwan gishiri zai mata bare,
Sai daya Dan gyara tsayuwa ya sauke numfashi Yace,
"Annen ce da ciki kuke magana kokuwa"??
Shiru sukayi zuciyar kowannensu na kokarin Faso kirjinsu ta fito har handen wadda take sake qarewa cikin na sumayyah kallo ranta na tafasa.
Jin shiru yasa shi dagowa kallo daya yayiwa Benazir tayi qasa da Kai qafafunta na sake daukan rawa tace,
"Aa ba Anne ba"
Cikin zafi da tafasan Rai a hasalce Yace
"Waye yake da cikin Dan a gidan Nan ita kadai Ce aure"
Saida Benazir ta fixgi numfashinta Dake Neman daukewa sbd tsananin tashin hankali da tsoron dasuke ciki na tinanin Ko Basu rasa ransu duka ba Kila sai daya ko biyu sun tafi lahira sun bar daya muryarta na fita da karyewa tace
"Sumayyah Ce ta.... Bata qarasa ba sai jin tayi ya shaqurota da hannuwansa biyu yana kokarin rabata da numfashinta da karfin gaske cikin wani irin zafi da fushin da basu taba ganinsa dashi ba da murya me qarfi da zafi yace
"Zaki fadamun komai danace kokuwa uwar taki kike jiran na balla,
Cikin mutane ne kokuwa na aljanu?
Dan kuwa sai dai na Aljanu suka shafeta sukai mata shi.
Cikin azaba da neman cetan ranta dayake neman rabata dashi tafara wintsila qafafu tana Neman barin duniya idanuwanta take suka firfito suna neman rufewa.
Wurgi yayi da ita qasa tareda saka qafarsa daya ya take cikinta cikin masifar data saka Sumayyah sakin qaramin fitsari jinin dayake zubar mata yana dan qara gudu sbd masifaffen masifar datafi qarfin balain da sika saba gani.
Cikin wahalalliyar muryar da bata fita sosai Benazir tace
"Na mutum ne a makarant ta hadu dashi,
Yace ze aureta,bamusan da cikin ba sai daga baya.... Marin daya saka bakinta fashewa da jini ya sakar mata na bayan hannu, take ta kife a gurin kunnuwanta na dauke ji kwata kwata haka idanuwanta na ganin wasu irin taurarin wuta jinin bakinta kuwa kaman wadda ta fasa kai.
Sumayyar ya damqo yana kallan cikinta zuciyarsa na wata irin tafasar da shi kansa bai taba jin wuta irin wannan na ci a jini da zuciyarsa ba,
Kallan cikin ya tsaya yi yana rasa me zai mata sbd zafin da kansa keyi bayajin idan ya daga hannunsa ya dora akanta zai barta da rai.
Wlh Bai yarda mutum yayi mata ciki ba saidai Aljanu Dan kuwa Wanda ya taba ta kawai ma bare ciki ai bindigarsa zaisa ya fasa Kansa wlh saidai yayi prison,
Jikin bango ya jefata da qarfi tareda binta ya rufe da masifaffen duka yana nanata kalman cikin tareda qin yarda da cikin mutum ne a jikinsa.
Dukan dayake mata ne shi kansa bayaji baya gani yasa Anne da hande yunqurawa dan cetan ta sedai suna isa ya kama Annan itama ya rufe da dukan yana nanata kalmar ciki har wata uku a cikin gidansa.
Hande data ga 'dan nata ya zauce da gudu cikin tashin hankali tayi cikinsa ta riqesa tana fashewa da kuka tana cewa Anne da 'yayanta sun zautar mata da 'da da baqin cikinsu.
Tinda yake a rayuwarsa bai taba ji ko haduwa da abinda yake neman sakar masa bugawar zuciya ya mutu ba sai a wannan ranar.
Rawa jikinsa keyi yana fizga kaman dan taurin da aka kadawa gangar kirari.
Kuka hande keyi sosai sbd ganin halinda yake ciki ga Sumayyah da Anne kaman sun mace ba rai a jikinsu.
Benazir kuwa har lokacin jinta bai dawo daidai ba sama sama take jin ihunsu da hayaniyarsu hakama ganinta bibbiyu take gani.
Daki hande tayi dashi ta zaunar jikinsa na wata irin rawa Kansa na Neman juyewa yana cewa wlh gobe asibiti zai kaita sai an auna yagani zai yarda da cikine a jikinta na mutum tukuna yasan ma kalan matakin da zai dauka akanta da duk Wanda yakeda sani akan cikin aka boye masa da yanda ma aka samu cikin,saiya kashe wanda yayi mata cikin nan ko dan uban waye,
Sai ya daure zuriarsu kaf a gidan yari,
Sai ya buga musu tambarin da har zuriar su qare a duniya sai sun ringa tinasa da abinda sukai masa.
Hawaye hande keyi tana tsinewa koma waye da zuriarsa tareda tsinewa karatun nasu Sumayyah da sanadinsa suka hadu da wannan muguwar kaddarar.
#MAMUH#
#BENAZIR ABABA#KAATES#DD#DAWOOD DAUDA#CONTRACT#HOTLOVE#ROMANCE
ZAFAFA BIYAR🔥
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR 'KASHI
Safiyya Huguma
-FURAR DANKO
Billyn Abdul
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Send your Shedan biya Anan👇
09032345899
MTN VTU/MTN CARD/AIRTIME TRANSFER👇👇
09033181070
Yan Nijar kuma ga inda zaku biya👇👇👇
+22799643131
Zafafa🫶🔥🔥
23
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
23
Mintina kusan goma Sha wani Abu suka share a tsakar gidan yashe Babu Wanda ya dawo hayyacinsa acikinsu bare yataimaki Dan uwansa,
Benazir datasan itace komai dadewa zata taimaka musu tafara kokarin miqewa ta rarrafa tana Dan bubbuga kanta sbd kunnuwanta su dawo daidai da Ganinta.
Gurin Anne ta fara nufa Amma Annen ita Kuma kokarin motsawa takeyi ta nufi gurin sumayyah datake kaman ba Rai jikinta.
Ganin haka itama benazir din ta nufi sumayyahn tana dagota jikinta tana Kiran sunanta da qaramin sauti sbd bakinta daya kumbura a take baya iya buduwa sosai.
Anne ma sumayyahn take Kira murya a shaqe tana Jin zuciyarta na karyewa idan wani Abu ya samu sumayyahn,
Ba zasu iya rayuwa Babu ita ba,
Benazir din ta ma zata iya rasa tata qwaqwalwan idan suka rasa sumayyahn,
Idan benazir datake jinsu da ganinsu tareda zama kaman itace uwarsu ta rasa kanta Yaya ita zata kasance?
Hawayen da zafinsu yasa take tinanin na kukan jini ne da ake fada anayi Idan balai da masifa sukai yawa anayi suka gangaro mata tareda benazir data dago sumayyahn gabaki daya sai alokacin taga jini a jikin sumayyahn tana zuba Sedai ba sosaiba take hankalinta ya tashi sai alokacin ta fashe da wani irin kuka mai qarfi dayasa Anne rikicewa tana qanqame benazir din hawayenta na gudu tanacewa
"Bena ta karki haukace kece gatanmu ni da sumayyah,
Idan wani Abu yasameki kaman yanda muke bamuda sauran Saka Rai daga sauki,
Kasa motsi benazir din tayi kukanta na tsananta tana sake rungume sumayyah.
Inama Ababa zai Basu mahaifiyarsu su tafi ko bolar ce su bi,
Zata zabi arawa kanta haukan itama tabi uwarta da yan uwanta subi bolan yafi musu Wannan masifar,
Zuciyarta tafara raunanan da Kila bazata iya daukaba,
Tabbas idan suka rasa sumayyah itama kanta juyewa zaiyi sbd bazata iya kallan mahaifiyarsu a cikin Hali na haukan rasa sumayyah ba.
Anne ganin benazir din na cikin tsananin halin kukan sai kawai ta daure ita ta miqe tsaye da qyar qafarta na wani irin radadin azaba da tsami Amma a haka ta kama sumayyahn daga jikin benazir din suka kamata zuwa can bangaren dabbobi benazir ta rungumeta Anne ta aro jarumta da dauriya wadda Benazir ke tinanin bama a hayyacinta Annen take ba kawai dai girman soyayyar uwa da 'yayanta ne yasata rikicewa tana Neman ganin sumayyahn ta tashi.
Ruwan ta debo takawo dukkaninsu jikinsu na rawa suka hau wankewa sumayyahn jiki Wanda sanyin ruwan yasata Bude idanuwanta a wahalce tana kallan sararin sama sbd bazata ma iya kallan mahaifiyarsu da Bena dinta ba sbd wahala da baqar kaddarar data janyo musu,
A yanxu da cikinta ya bayyana sunsani Babu ranar sauki ko kadan daga rayuwarsu sai Kuma yanda Allah yayi dasu,
Inama ta mutu da cikin ta tafi ta rage musu wahalarsu musamman Bena sbd Anne da qwaqwalwanta yajuye bazata tantance komaiba bare ya tsaya zuciyarta Amma Bena komai na rayuwarta tsayawa zaiyi,
Acikinsu kowa ya cimma tasa qaddarar ita idan duka suka barta batasan ya nata kaddarar yake ba.
Benazir data San tinanin da sumayyahn keyi rungumeta tayi ahankali bayan sun wanketa tas kaman gawa sbd ko motsi Bata iyawa da kanta.
Annensu sai alokacin take Jin zuciyarta na nauyi Bata ko iya Jan numfashi daidai Saida benazir itama ta rungumota sukai shiru a hakan tsawon lokacin kafin suka taso suka shige dakinsu har lokacin hande na gurin Ababa tana fama dashi sbd shi Kansa kaman qwaqwalwansa Neman juyewa takeyi sbd a rayuwarsa Bai taba Jin tashin hankali da masifar wuta na cin zuciyarsa kaman yau ba,
'yayansa datake tinanin ko tirelar qwaya mutum yasha bazai tinkaresu bama bare har kebewa Harma da ciki,
Ko waye wannan tsautsayi yakaisa tabbas ya jawa Kansa da kaf danginsa da kuwa wlh kafin hukuma ta shigo ciki su zuba muguwar makauniyar shariar da sai ya tabbata an rufesa kafin can saiya fasa masa gaban wando da bindigarsa idan ya warke ayi shariar sbd lokacin ya rasa lafiyar wandonsa ta yanda shi da mace sai kallo.
Hande kuwa tsinuwar datake rafkawa akan me cikin da karatun nasu da ma Anne data bi bayansu aka boye cikin gashi suna Neman cinnawa 'danta hauka kokuma tace sunma cinna masa.
Gari kawai yake jiran ya waye yakaita asibiti a auna masa ita a duba a fada masa cikin idan na gaske ne Kuma watansa nawa ta yanda zaizo yayi dalla Dalla dasu yasan ta inda zai fara karya qafar uwarsu kafin ita me cikin Dan kuwa ko watansa daya saita haifesa a ranar batareda anbata komai na fitowar tasa ba.
Benazir ruwan zafi ta fito ta Dora a sace ta zubo a roba tazo ta gasa jikin sumayyahn koina
Kafin ta gasa Anne itama data fara kokarin birkicewa Amma benazir ta dage tana shafata da adduoi har ta lafa sai Kuma ciwon jiki da zafin jiki a haka har tayi baccin wahala.
Sumayyah ma baccin wahala ne ya fizgeta
Sai a lokacin benazir ta zauna ta dasa kukan dayake cinta tanata dannewa sbd Anne data rude da kukan nata.
Kasa bacci tayi tana gadinsu idanuwanta jajir sbd tsoron kada suyi bacci Ababa yazo ya rufesu da duka kokuma fushi yasa ya cinnawa dakin wuta.
A zaune ta kwana tashin hankali da tsoro Bai bari ta iya ko rintsawa ba sai gab da asuba ta fito tayi alwala ta ringa nafila tana kuka cikin sujjada tana fadawa Allah kukansu.
Anne da sumayyah dayake ba lafiyar sunyi baccinsu cikin wahala jiki duk yayi tsami ko motsawa sukai ciwo jikin ke musu koina.
Sai datayi sallan asuba ta tayar dasu Anne tayi sallah sumayyahn Kuma suna Saka ran cikin ya qarasa zubewa Amma a mamakinsu Jininma ya tsaya Babu ko alamansa Dan sai jikinsu ya sake sanyi dole tayi sallah jinin da alama na tashin hankali ne ya zubo.
Bayan gama sallar su Saida benazir ta sake gasa musu jikinsu harda ita sbd idan ba hakan ba ko miqewa tsaye daidai Babu Mai iyawa a cikinsu.
Ita da Anne dole suka daure suka fito suka hau aikin gidan a tsorace sbd sunsan baayi komaiba jiyan tinda bai tambayi komaiba sai yanzu ne zai tambayi komai yasan yanda zaiyi dasu.
Tsit tsakar gidan yake daga hande har Ababan babu Wanda ya fito Kuma da alama duk sun tashi kawai dai kowa baqin ciki da tinanin yanda zaayi dasu akeyi.
Suna gama aikin qafafun benazir na rawa zuciyarta na tsalle takaiwa Ababan abincinsa saidai ko dagowa baiyi ya kalleta ba sbd kaman yanda sukai kwanan zaune Shima yau shi yai sbd an shammacesa Tako Ina,
Anci Amanarsa,
An yaudaresa duk a cikin gidansa,
An lalata masa komai,
Duk Wanda ya sakasa wannan baqin cikin da ciwon ran wlh Shima sai yayi uban ubansa,
Ita sumayyahn naqudar dole zai sakata a yau din tasan me ake nufi kame Kai dayace suyi daga kula uban kowa.
Hande da Benazir takai mata abincinta harara da fada Mai zafi ta rufeta dashi harda jifanta da maficin roba dayake hannunta tana kiransu da sunaye.
Bata iya dagowa ta kalletaba bare tankawa harta gama ta Korota ta fito da nasu da handen ta Basu takawo musu daki.
Babu Wanda ya kalli ruwan Lipton din da biredin sbd damuwa da rashin sanin mezai faru.
Anne daga baya ta takurawa sumayyah Tasha kafin Suma suka Sha suna gamawa hande ta leqo dakin tana kallan sumayyah da Benazir tace su shirya su fito inji Ababa asibiti zasu.
Tana fada musu ta bar gurin tana cewa suyi sauri karsu Bata lokaci Aljanun masifarsa su tashi.
Shiru sikai dukkaninsu tareda sauke numfashi Mai sanyi jikinsu na sake sanyi tareda saddaqarwa suna barin komai ga ubangiji.
Anne kaman wadda zata rabu da 'yayan nata haka takeji zuciyarta na sanyi tareda jikinta,
Da kanta ta taya sumayyah shiryawa bayan tayo wanka jiki mace,
Benazir ma jikin nata a mace yake har suka shirya suka fito Anne Bata iya fitowa dakinba har suka fice tana Jinsu.
Ababan ne a gaba sai hande a bayansa sai benazir din da sumayyah kaman marayu Babu Mai kuzari da qwarin jiki.
Taxi ya Tara ya shiga gaba hande tafara shiga kafin tace su shigo,
Sumayyah Ce ta fara shiga benazir na taimaka mata kafin itama ta shiga ta rufe suka bar gurin.
Babu Mai magana a cikin motar tsit ake kowa da yanda zuciyarsa ke bugawa da kalan tinaninsa,
A motar kaf idan aka cire direban kowa fatan yakeyi idan anje a auna aga bakomai cikin ace Babu ya fice.
Shi kansa Ababan dayake Jin Yana ci da wuta Kansa na zafi fatan yake cikin ace Babu.
Wata private asibiti sukaje sbd bazai juri zuwa Inda zaa masa aikinda zaa kasa basa cikakkiyar bayani yanda yakeso.
Kudin yankar kati da komai ya cire ya biya zuciyarsa na sake daukan zafi sbd kusan wata dubu goma ya kashe.
Zaunawa sukai zaman jiran layi duk da Babu wani layi mutum biyu ne gabansu,
Gabaki daya fuskar Ababa da dukkaninsa Babu annuri ko kadan a tare dashi,
Wani zafi Kansa ke sake dauka har lokacin Babu kalma ko daya data hadasa dasu har Handen datake ta masifa qasa qasa tana zungurar Sumayyahn ta qafa.
Sumayyah kuwa hannunta Yana cikin na benazir sun qanqame hannuwan junansu kaman zasu hade junansu,
Da ace ana cire cikin wani a Maida na wani tabbas da tin kafin asirinsu ya tonu zata dawo da cikin sumayyah jikinta, ta dauki duk wata wahala da ukuba Harma da azabar Ababa a maimakon Sumayyahn.
Yanda zuciyoyinsu ke bugawa cikin fargaba da tsoro kaman lokacin ne zaa fada musu cikin,
Hande ma sai zare Ido takeyi tana qarawa ta matsu ayi musu bayani suji su koma su San yanda zasuyi da cikin tin wuri.
Kiran sunan sumayyahn Akai take gabanta yai mummunan faduwa ta sake qanqame benazir tana kallanta idanuwanta na cikowa da hawayen.
Ababa ne yayi mata wani kallo daya fuskarsa Babu sauki ko kadan,
Sakin benazir tayi tareda miqewa tsaye tabi bayansa suka shiga dakin likitan.
Kallansu likitan Dake zaune yai Yana mamakin shigowarsu su biyun.
Ababa da Bai tsaya jiran komaiba ya zauna Kai tsaye ya korowa likitan bayanin 'yarsa Ce Kuma budurwa Amma suna tinanin ciki ne jikinta a duba masa ita dakyau idan da gaske ne.
Kallanta Dr yayi take ya hangi nutsuwa a tareda ita Amma Kuma yasan baka shedan mutune yanzu Dan haka Yace Ababan ya fita yabasu guri.
Fitowa Ababa yai Dr ya dubata tareda tambayoyi duk abinda suka dace kafin ya turata office din kusan dashi ya biyo bayanta yayi mata scanning da Kansa ya duba duk abinda yake buqata suka fito.
Office dinsa suka koma ya Kira Ababa Kai tsaye ya miqa masa takardar ya sanar dashi ciki ne Kuma kusan wata uku Harma da kwanaki.
Yanda Ababa yayi shiru yasa likitan yayi tinanin tawakkali ne mahaifin nata yayi sai kawai ya Basu yan shawarwari tareda nuna musu ilolin cire ciki Harma da nasiha sosai kafin ya sallamesu suka fito.
Suna fitowa hande fuskar Ababa takalla tasan masifa ta qullu kenan Dan haka suka taso itada benazir Dake kallan 'yar uwarta ta qarasa suka kama hannun juna suka fito Ababa na gaba suna bayansa.
#MAMUH#
#HOTLOVE
#DD KAANTE
#BENAZIR#MARRIAGE#ROMANCE#
#ZAFIN KAI
ZAFAFA BIYAR🔥
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR 'KASHI
Safiyya Huguma
-FURAR DANKO
Billyn Abdul
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim
Send your Shedan biya Anan👇
09032345899
MTN VTU/MTN CARD/AIRTIME TRANSFER👇👇
09033181070
Yan Nijar kuma ga inda zaku biya👇👇👇
+22799643131
Zafafa🫶🔥🔥
24
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
24
A motarsu ta dawowa tinda suka shigo hande Ce Mai magana cikin takacinsu Dana uwarsu sai fada takeyi tana qarawa Amma Babu Mai iya ko dogon motsi a cikinsu bare dagowa su tanka,
Hankalinsu da tashin hankalinsu Yana kan Ababa ne da yake shiru har lokacin Bai Ce qala ba,
Idanuwansa sun kada sinyi jajir sbd tafasar zuciya da bacin ran dayake fal cikinsa.
Suna isowa nesa da gida aka ajiyesu ya biya Mai taxi suka nufi hanyar gida.
Duk taku daya dasu benazir keyi na hanyar zuwa gidan bugun zuciyarsu da numfashinsu sauyawa yakeyi har suka iso.
Annensu da tin bayan fitarsu kowane second daya shude fargabarta da tsoranta qaruwa yakeyi,
Aikin girkin da aka barta tai na Rana har suka je suka dawo Bata iya aikata komaiba sbd Bata cikakken hayyacinta matiqar ba yayanta taga sun dawo mata ba,
Tsoro da tashin hankalin datake ciki Mai girma ne sbd tinaninta da sanin Ababa zai iya Kai mata yayan wani guri ya barosu akan wannan laifin dasuka aikata.
Suna shigowa ta miqe tsaye daga zaunen datake tsakar gida tana jiran tsammani,
Idanuwanta akan Yayanta suke saidai kafin tai yunqurin Isa garesu Ababa ya dago fuskarsa yana zama kan kujerar robar zamansa Dake tsakar gidan.
Numfashi ya sauke tsawon mintina kafin ya dago ya kallesu daya bayan daya ya zare hular Kansa ya ajiye gefe tareda nade hannuwan rigarda daga zaunen cikin kwantar da hankali yace
"Wannan cikin zaa min bayaninsa Dalla Dalla,
yaushe aka samesa,
Dan gidan uban waye yayisa kokuma uban waye yayisa,
Tayaya aka Sami wannan damar,
Yaushe kuka San dashi aka boye min Kuma ubanwaye a cikinku ya Bada shawarar a boyemin,