Kenza eBookz

Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 - Chapter 28

Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 - Chapter 28

Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 Chapter 28: Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 Chapter 28. Idanuwan dd babba akan Benazir tin…

3,375 words

Idanuwan dd babba akan Benazir tin shigowansu Kuma acikin mintina qalilan ya Karanto nutsuwa a tattare da ita Kai tsaye Dan haka ajiyar zuciya ya sake saukewa a Karo na biyu tareda amsa gaisuwar datai masa kanta qasa cikin tsananin girmamawa da ladabi.

Numfashi ya sauke tareda sakar mata a fuska cikin kauna da kulawa ya tambayeta Yaya baquncin sabon guri.

Kanta ta sake yin qasa dashi cikin sanyin murya da nutsuwa tace lafiya kalau.

Amnah ya tambaya itama tace lafiyan kalau.

Cikin hikima da nutsuwa yayita yan mata tambayoyi har akan karatunta yaji inda ta tsaya take ya yanke shawarar zata koma makarantarta tinda ashema hutun ya qare tin last 3 weeks.

Tariga ta cire tsammani daga komawa makaranta Dan haka tana Jin zancen nasa ta dago ahankali Amma Bata iya kallansa ba tayi godia cikin sanyin jikin yanda zatayi karatu da Amnah, Kwatsam mutane su ganta da haihuwa ba aure.

Dd babba hanata tafiya yayi Saida yayi mata tambayoyin Daya gamsu da tafara samun sabo da kwanciyar hankali a Kaantes Dan haka ya sallameta ta tafi.

A Karan farko itama data samu nutsuwa da sanyin kwanciyar hankali da Wani Kai tsaye a cikin Kaantes din bayan Zeenah da Umme.

Jin tayi kaman ta samu Wani sabuwar nutsuwa da yanda dd babba ya mata nasiha tareda Bata tabbacin ta Kwantar da hankalinta a qarqashinsa babu Wani Abu dazai sameta ko Annenta duk da Bai fito ya nuna mata yasan komai ba.

Tana dawowa tini Zeenah ta shige hakama umme Bata ma sashen tana gurin dad kaante Dan haka itama shigewa tayi tayi Shirin bacci ta sallami Nafisat ta tafi sashen masu aiki ita Kuma ta shige bargo da Amnah dake bacci sosai har lokacin.

Washe gari suna cikin breakfast hajar me aikin Umme ta shigo har dining room ta sanar dasu Abbakar ya Aiko cewan Bena ta shirya za'a kaita makaranta.

Daga Umme har Zeenah sosai sukai farin ciki da Hakan Dan haka sama sama ta qarasa breakfast din ta miqe taje ta shiryo ta fito cikin wata Kuwait jallabiya me tsadan gaske maroon Bada mayafi bare hijab Dan haka dole kaman yanda Zeenah ta fada mayafin rigar ta Tayata nadowa suka fito gabanta na tsananta duka sbd yanda zataje school da 'ya Amma Kuma hankalinta zai rabu biyu bazata taba samun nutsuwan karatun ba matiqar ba da Amnah taje ba Dan haka tini ta shiryata fes cikin designer kayan babies masu taushi da rashin ado aka nadota a pink shawl sai qamshi takeyi suka fito Nafisat na bayanta dauke da baby bag dinsu ta kayan Madara da komai na buqata da amfanin Amnah din.

Daga takalmin qafarta har chanel handbag din Dayake hannunta batasan kudinsaba Amma a yanda nutsuwarta yake Zaka dauka komai na jikinta ta San kudinsa Jan ajine takeyi Amma ha Hakan bane.

Bayan kwallin cikin fararen idanuwanta babu komai a fuskarta sai facemask Wanda Zeenah ta Koya mata amfani dashi ko acikin gida wasu lokutan, Ita kuma Zeenah ta dauki dabi'an ne Daya yayan nata da babu inda zashi Bai sakasa sbd baya San ana yawan kallansa sai gashi Allah yayi masa wata irin haiba da kwarjinin da duk inda yaje zaa kallesa din sbd Wani nutsatsan kyau da ajin kamewa ne dashi.

Har mota Zeenah ta Rakata Driver ne sabo aka kawo yau din sbd kawai Kai Bena makaranta Kuma a Daya daga cikin motocin dd babba ya ware mata Dan kaita kawai da daukota.

Driver na ganin isowarsu ya fito da sauri ya budewa benazir din mota Yana mata barka da fitowa.

A mutunce cikin fargaba da tsoro ta amsa har Saida Zeenah a ta Bata qwarin gwiwa ita fa kaante ce yanzu ba buqatan Jin fargaba ko Jin nauyin girman da zaa ringa Bata.

Nafisat a gaba ta zauna Dan haka benazir din ce kawai a baya ita kadai sai Amnah dake jikinta.

Wayarta ta fidda tana son Kiran wayar Anne Amma tasan wayar na hannun Ababa lokacin Amma tinda ance driver ya biya da ita ta dauki takardun makarantar Datake ganin tana buqata wainda duka ta baro gida sai takejin gabanta na tsananta faduwa duk suka qara kusanci da Isa gidan.

Tsoro ne da rawa hannuwanta keyi sosai na Ababa Daya dasa musu a cikin ransu da har abada bazasu iya goge wannan tsoron ba.

Id card dinta kawai take buqata daga takardun makarantar data bari gidan Amma zuwan nata Sam Badan Id card din zatayisa ba sbd buqatan ganin Annenta ne da suka Dade Basu ga juna ba saidai a waya.

A kofar gidansu lafiyayyar motar tayi parking sai Data sauke ajiyan zuciya da numfashi a Jere kusan ba adadi zuciyarta na bugawa da qarfi cikin tsananin tsoro da shiga tashin hankali.

Tana cikin wannan firgicin ne Driver ya Bude mata kofa bata ma saniba Saida ya kira sunanta cikin girmamawa da a nutse.

Fitowa tayi qafafunta na Dan rawa tana damqe hannuwanta dake rungume da Amnah.

Kai tsaye kofar shiga ta nufa Nafisat na bayanta kaman jela dauke da jakar kayan madarar Amnah. #MAMUH# #ROMANCE #LOVE #HOT #DBENA #AMNAH #BABY MAMAH

*_Arewabooks@Mamuhgee_* 49 Daqyar sallamarta ta fito daga maqoshinta lokacinda ta shigo tsakiyar gidan sbd tsoron da zuciyarta take ciki.

Duk da ba Wani sosai ta saka tirare ba Amma tsadansa ya sakashi sauya iskan tsakan gidan ahankali da sanyin qamshi hande dake daki bataji sallamar ba qamshin taji iska ya Dan kado mata shi daga waje take ta fito sbd tasan dole baqine suka shigo gidan.

Anne kuwa zaune take tsakar gidan tana Yanke farcenta da wata tsohuwar Reza wadda da benazir dince ta Saba Yanke mata farcen

Har cikin tsakiyan zuciyarta sallamar benazir din ta ratsa sbd take tasan Bena dinta ce Dan haka ahankali ta dago jikinta na sanyi da mutuwa wasu hawaye masu zafi suka ciko idanuwanta dake bushe tana kokarin maidasu kada Benazir ta gani.

Benazir kuwa ganin Annenta kadai tsakar gidan ya sanyata qarasowa da wuri ta nufeta qafafunta na rawa Basu tsaya janye Amnah a tsakaninsu ba Benazir ta rungume mahaifiyarta tana Jin dukkanin qarfin zuciyarta na karyewa.

Hande data fito salati me qarfi ta sake ganin su a Hakan Wanda ya saka Ababa Dayake shirin fitowa fitowan da sauri Yana cewa hande saita kashesa wata Rana da wainnan salatin nata masu daga hankali.

Yana fitowa idanuwansa akan Anne ya fara sauka Saida ya duba dakyau ya tantance Benazir ce Gyaran murya yayi suka saki juna ahankali suna tsayawa gefen juna kan benazir qasa tana hadiye yawun zuciyarta dake bugawa da karfi.

Da sanyin murya me taushin data fara samu na nutsuwan rayuwar data fara samu ta Bude baki muryarta na Dan rawa ta gaidasa.

Bai amsa ba ya Tako ya qaraso gabansu ya tsaya cikin sake tsuke fuska ya miqa hannu ta miqo masa Amnah dake bacci ya karbeta.

Kallan babyn yake Yana Jin farin cikin ganinta, Bai taba kaunar ko nasa 'yayan ba Amma ita cikin ransa yake jinta sbd ta zama silar arzikinsa da 'yayansa suka kasa zama sanadin.

Dagowa yayi ya kalli Benazir murya a zafafe ya tambayeta metazo Yi

Shiru tayi kanta a qasa

Cikin zafi ya sake cewa

"Me na fada Miki? "Babu ziyara matiqar ba nine na buqata zuwan naki ba Kuma ba yanzu zan buqata Hakan ba sai kin zaunu cikin Kaantes kin jiqu yanda ya yakamata, Annenki zata biya duk Wani hukuncin laifin ki wlh sbd bansan hakuri ko asara ba.

Rufe idanuwanta tayi ahankali kanta na sake Yin qasa hannuwanta na Dan tsananta rawa.

Ahankali ta Bude baki ta sanar dashi Abinda akace tazo dauka makaranta zata.

Gyara tsayuwa yayi cikin Jin Wani lissafin na Hawa Kansa Jin anfara considering dinta as kaante itama tinda aka ware mata mota da drivern kanta.

Hana farin cikin fara samun Abinda yake Neman yayi ya Dan daure murya yace taje ta dauko ta fice daga gidan.

Juyawa tayi qafafunta na Dan rawa da sanyin jiki ta nufi dakinsu ta shige Anne na bayanta.

Suna shiga ta dakata tareda juyowa ta Kalli Annenta da itama ita take Kallo zuciyarta na wadata da sanyin ganinta tareda farin cikin ganin dd babba ya dauko hanyar inganta rayuwar Bena dinta kaman yanda yayi mata alqawari Dan haka itama zata qara juriya da hakurin kowace irin ukuba da wahalar gidan har lokacin da dd babba zai gama bincikensa akan rasuwar su sumayyah tukuna ya dauki mataki akan Ababan da dalili.

Hannuwanta ta daga ahankali ta zaunar da Anne qasan tsakiyar dakin da tini aka dauke katifar ciki.

Rezan sake hannun Annen ta karba ta durqusa ta Yanke mata duka farcenta cikin kulawa da sauri.

Tana gamawa suka miqe tare Anne da kanta ta dauko mata id card dinta inda yake ta kama hannunta ta saka mata cikin murya Mai bayyanarda jarumta da kauna tace

"Karki sake dawowa Nan ki zauna gidanki kiyi ingantacciyar rayuwa, Ki nutsu kiyi karatunki ki inganta kanki ki samu Daman Gina taki rayuwar da Zaki samu Daman samun 'yancinki, Inshallah zanyi dauriya nayi juriya Zamu tsira da yardar Allah, A baya Banda qarfin zuciyan fatan rayuwa me nutsuwa Amma a yanzu inadashi sbd ke Bena Dan haka kije na yafe karki dawo Nan din saikin Gina rayuwarki me kyau Allah ya sadaki da dukkanin Alkhairi da farin cikin gidan ki.

Duk Wani gabar jikin benazir Saida yayi sanyi ya sake da maganar Annenta hawaye ya ciko idanuwanta Amma ya kasa saukowa sbd Wani irin sanyin jiki Dana zuciya da zantikan suka sakar mata tare Kuma da qwarin gwiwa.

Sake rungume Annenta batareda ta iya cewa komaiba sbd zasu iya fashewa da kuka su dukan idan ta Bude baki Dan haka ita kadai ta fito Anne tayi zamanta daki.

Hande na daki tana jiran shigowar benazir din dakin har ta fice bata saniba a waje ta tadda Ababa Yana lissafin motar da aka bawa benazir din zata fi miliyan Dari.

Tana fitowa driver ya Bude mata motar ta shige ya rufe.

Ababa da Kansa ya Kwantar da Amnah gefen benazir ya rife kofar motar Yana Jin zuciyarsa fal haske da lissafi.

Suna barin kofar gidan Benazir ta lumshe idanuwanta ahankali hawayen Datake riqewa suka gangaro mata ta Ciro handkerchief me taushi daga Jakarta ta share fuskarta ahankali tana Jin zuciyarta na sanyaya da rabata da mahaifiyarta da Akai Wanda takejin zatayi karatu inshallah tuquri ta inganta rayuwarta ba iya zaman kaantes ba tana buqatan yiwa kanta nata sunan bayan na kaantes Dan samun iKon karban mahaifiyarta, Zatai karatun da zata Tara arzikin da zata Siya mahaifiyarta daga mahaifinta ko nawa ne inshallah. Sake share hawayenta tayi tana sauke numfashi Mai zafi da ajiyar zuciya.

Kai tsaye jamia suka Isa hankalinta na kwantawa daga tinanin duk Wanda zai ganta da baby, Basa muamala da mutane ko a baya Dan haka babu damuwanta ga duk Wanda zai ganta da babynta.

Parking driver yayi Bata Jira ya Bude mata ba ta Bude ta fito rungume da Amnah ta wuce Nafisat na bayanta suka nufi inda zata samo tabbacin komai na hutun da aka dawo su timetable da lectures da Akai da sauransu.

Cikin sa'a yau din sunata lectures in the next 20 min masu zuwa Dan haka taje duba results dinta na last semester data San ba lallai ma taci ko Daya.

A sa'arta taci courses uku ta fadi sauran 5 Dan haka Bata Wani damu ba tinda tasan yanzune zata dage tayi karatun Kaiwa matsayawa.

Da zasu shiga lectures Nafisat ta goyawa Amnah bayan ta Bata Madara Tasha Takoma bacci.

Mota Nafisat suka koma sbd babu inda driver ya tafi Yana Nan saita gama idan dare zata Kai zai Jira tinda aikinsa kawai shikuma na ta ne.

Suna fitowa 12 to 2 kai tsaye mota ta nufo tana Isa wayarta dake jaka kira ya shigo Cikin Wani irin sanyi ta Ciro wayar sbd bayan Su Anne babu Wanda take magana dashi a wayar.

Sunan Umme tagani ahankali ta sauke ajiyan zuciya sbd wannan shine Karo na farko data fito kaantes tin kaita shiyasa ummen duk ta Dan damu sbd Amnah da Bata fita Rana.

Daukan wayar tayi cikin nutsuwa da sanyin murya tace

"Umme Ina wuni"

Ajiyan zuciya ummen ta sauke daga can bangaren tana cewa

"Bena Yaya makarantan? Akwai Rana da yawo ko? Ga Amnah tanata rigima Kila ko?

Ajiyan zuciya Bena ta sauke tana lumshe fararen idanuwanta zuciyarta na na'am da kaunar Umme akansu Dari bisa dari Dan haka tayi kokarin gwada Sakin murmushi me sauti tace

"Amnah a mota na barsu tin dazu Nima yanzu na fito daga lectures din Amma zamu sake shiga 2 zuwa 4."

Ajiyan zuciya ummen ta saki tana cewa "ok ki kula da kanki da Amnah akwai Rana sosai,saikin dawo."

Ahankali ta iya Bude bakinta dayayi nauyi sbd mutuwar jikinta ta furta "Nagode Umme Allah ya saka da Alkhairi."

Murmush kawai ummen tayi tareda kashe wayar daidai shigowan DD palonta Yana amsa wayan Safnah da kusan kullum take kiransa ahankali,ita wannan dake gabansa baimayi noticing nata ba hakama Bai taba tambayar ta ba sbd baisan Tayaya zai fara kulawa ko Neman matan yayansa daya rasu tinda dai Amnah dinsa zai ringa ganin babynsa Hakan ma is ok.

Sallah Bena tayi a mosque na mata Ta bawa Amnah Madara ta canja mata diaper da kaya zuwa Versace overall marasa nauyi da qamshi kafin suka koma ta shiga lectures suka zauna mota.

Sai 4 har da Rabi suka baro makarantan suka nufi gida.

Suna Isa driver yayi mata Saida safe ta wuce Nafisat na biye da ita gajiye duk da Bata ciki yunwa sbd akwai biscuits da drink da Umme ta sako musu cikin jakar kayan Amnah.

A gajiye suke sbd sabon da suka fara samu daga ita har Nafisat me aikin nata na zama guri Daya cikin hutu.

Babu kowa a palon Dan haka Kai tsaye dakinta ta wuce ta tube ta fada toilet Saida tayiwa Amnah wankan tayi tayo alwala ta fito ta shirya cikin Riga da straight skirt na atampar super wainda kusan duka atampopinta babu qarama bare laces da baa maganar kudadensu.

Sallah tafara Yi kafin ta shirya Amnah cikin guntayen overall blue da safa Mai taushi itama suka fito zuwa dakin Umme Dan gaidata.

Suna zuwa tayi knocking ahankali ta Bude ta shiga ahankali ummen na zaune tana amsa waya cikin nutsuwa.

Tana ganinsu ta sake fuskarta da farin ciki tana miqa hannu ta karbi Amnah din tana ci gaba da wayarta.

Bena kuwa ficewa tayi ta nufi dakin Zeenah batanan Dan haka ta fito ta nufi kitchen acan taci Brown spaghetti da aka dafa Dan ita kawai da yamman.

Sama sama taci ta koshi sbd Sam batada cin abinci sosai hanjinsu sun Dade da tsukewa daga Horan da Akai musu tin tasowansu.

Ruwan sanyi Tasha kadan kafin ta kamawa su Madam beba aikin abincin dasuke Yi na dare.

Tuwon semovita sukai da Miya kala biyu sbd banbancin raayi kowa yaci wadda yakeso.

Ita tayi miyan fresh veggies da Alayyahu sai uban Naman Kazan da babu qashi da nikakken nama Madam beba kuwa miyan yauqi sukai da kifi da Naman rago.

Suna gamawa Zeenah na dawowa ta Kalli benazir din tana tambayarta me takeyi a kitchen.

Murmush kawai tayi ta sanar da ita Aiki sukai na abinci.

Sallar magrib tayi Bata fito ba sai bayan datai ishai dinta ta miqe ta fito.

Tana saka qafarta tsakiyar palon hancinta ya shaqar mata qamshin Daya sakata dakatawa sbd sanin Yana kusa kokuma Yana cikin palon Dan haka ta silale Takoma daki.

Koda aka Aiko kiranta cin abinci cewa tayi ta Kasho Bata Dade da cin spaghetti ba.

Kyaleta sukai sukaci abincinsu batasan DD baya part din ba shigowa yayi Kuma ya fita da Amnah.

Saida ta tabbatarda sun gama cin abinci ta fito Zeenah ta Rakata gurin dd babba gaidasa da masa godian komawarta makaranta.

Sun shiga Zeenah ko qarasawa batayiba ta juya sbd Kiran Daya shigo wayarta Dan haka ita kadai qafafunta na Dan rawa ta qararasa cikin palon da sallama a natse cikin siririyan muryanta me sanyi kanta a qasa.

Kallan Dawood da Bai dagoba dd babba yafara Yi kafin ya amsa sallamarta tareda Kiran sunanta

"BENAZIR? Qaraso ki zauna kinji.

Sunan da dd babba ya ambata ya saka DD dakatawa daga kallan datakewa Amnah cikin nutsuwa da tsananin kauna Amma Bai dagoba duk da sunan ya tabbatar masa da Mummyn Amnah dince ake nufi.

Itama Bata dago ba bare ta iya kallansu batama San waye da waye a palon ba Dan haka kanta a qasa ta zauna natse kaman yanda dd babba ya umarceta. ##MAMUH# #LOVE #HOT #DBENA #BABY MAMAH

*_Arewabooks@Mamuhgee_* 50 Bude baki tayi nutsuwar muryanta a bayyane ta gaida dd babba cikin ladabi da sanyi.

Murmushi me sanyi dd babba ya sake cikin kulawa ya amsa tareda tambayarta Yaya school.

Sake Dan qasa tayi da kanta tana damqe hannuwanta dake Dan rawa cikin nutsuwa tace "lafiya kalau."

Dawood da kaman baya gurin dd babba ya kalla kafin ya Maida kallansa kan benazir din da ita Kuma batasan ma da waye a gurin ba ya Dan sauke numfashi Mai sanyi da kulawa sosai yace

"Benazir ga mijinki Nan a zaune ki gaidasa."

Faduwa Mai tsanani gabanta yayi kirjinta ya fara bugawa da qarfi ahankali ta Dan karkata gefensa batareda ta dago ba kanta a qasa ta Bude baki muryarta na Dan rawa sbd sanyi tace

"Ina wuni."

Shi Kansa DD din shiru yayi na seconds sbd kalman dd babba ta cewan ga mijinta a zaune yasa ya Tina da auren mata biyu ne a hannunsa wainda babu wadda yasan ta inda zai iya sakata a mizanin lissafin rayuwarsa harma da matsayi na matar da ake tinanin yayi rayuwar Jin dadi kwanciyar hankali da nutsuwa da ita.

Batareda ya juya ya kalleta ba ya amsa Kai tsaye tareda miqewa ya fice Yana Ciro wayarsa da kiran Lizz ya shigo.

Bayan fitarsa dd babba ajiyan zuciya ya sauke tareda numfashi kafin ya saki qayataccen murmushi mara sauti ahankali Yana jinjina Kai.

Benazir data kasa motsi ya kalla yace

"Jeki benazir ki saki jiki kiyi karatunki ki qarasa wannan session din a gwada sauya Miki gurin karatun " Godiya ta sake masa cikin sanyi tareda masa fatan Qarin lafiya tai masa seda safe ta fice.

Ita kadai ta Isa sashensu Dan haka tana Isa babu kowa a palon tana dap da Isa dakinta taji kukan Amnah ta juyo Kai tsaye sbd mantawa a hannunwa Amnah din take tintini.

Juyowanta yayi daidai da shigowansa palon Shima Yana kokarin riqe Amnah din dakyau sbd kaman zata Fadi da motsin kukan datakeyi.

A kyakyawan farar fuskarsa idanuwanta suka sauka gabansa a yayi mummunan faduwan Daya saka hannuwanta rawa da fitan numfashi da sauri tayi saurin dauke idanuwanta zata shige daki taji muryarsa me nutsuwa da kamewa yace

"Karbeta."

Saida ta damqe hannuwanta ta tattara nutsuwanta guri Daya kafin ta iya dago qafafunta ahankali ta iso gabansa ta tsaya

Ya dago Amnah ya miqa mata tasaka hannuwanta dake Dan rawa ta karbeta tareda juyawa Kai tsaye tayi bedroom dinsu ta shige

Shi Daman tin kafin ta juya ya juya Yana cigaba da amsa cikin rashin daga hayaniya.

Bayan shigarta daki Hana kanta zama tayi bare dadewa acikin rawar hannuwanta da faduwan gaba ta hau kintsa Amnah hannuwanta na Dan rawa har lokacin.

Tana gama shirya Amnah itama tayi Shirin kwanciyar ta kwanta tareda rintse idanuwanta.

***Washe gari morning lectures take dashi Dan haka da wuri ta shirya tayi breakfast a dining tareda Umme da itace ta hada musu kaya a jaka yau ma Zeenah Kuma tana bacci suka fice yauma cikin wata tsadaddiyar Noriea Abaya ash da Rolling.

Sai yamma ko yau din ta dawo a gajiye sosai, Sallah magrib tayi tayi wanka tea kawai Tasha ta kwanta bacci ya dauketa tabar Amnah a can gurinsu Umme sallar ishai ma sai cikin dare ta farka tayi taga Amnah kwance gefenta an Kwantar mata tasan Umme ce ko Zeenah suka kawo mata ita.

******Ahankali rayuwar makarantan da Amnah ta sabo da ita tin tana Jin stress da gajiyan Hakan harta Saba Bata Jin komai yanzu musamman Mai aikinta Nafisat na kokari sosai gurin kulawa da Amnah Bata wasa da lamarin Amnah ko kadan,. hakama drivernta Ahmed Yana mata biyayya kaman Bai girmeta nesa ba kusa ba Amma sbd a qarqashinta yake biyayyarsa tayi mata yawa take Gani.

Rayuwar gidan ta Saba a yanzu da ita kusan ta ko Ina,

Readers Also Read