Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 - Chapter 53
Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 Chapter 53: Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 Chapter 53. Kasa motsawa tayi sbd kalmominsa dasuka…
3,371 words
Kasa motsawa tayi sbd kalmominsa dasuka shigeta jikinta ya sake mutuwa ta dago hannuwanta ta zagayesa dasu tareda qanqamesa tana sake shigewa jikinsa.
Kaman daga sama Bilal ya fito daga hanyar bedroom dinsa sanye cikin jallabiya fara da wayarsa a hannunsa Yana qarasowa cikin palon Abinda ya fara girgiza zuciyarsa shine qamshin da babu Wanda ya sani dashi sai mutum Daya a rayuwarsa shine DD kaante,shine ya fara shiga hancinsa shigowansa palon tareda girgiza masa zuciya a tsanake ya qarasa cikin palon ya tsaya cak daga inda yake Yana zubawa DD idanuwansa da tini suka sauya zuciyarsa na mummunan harbawa da bugawa.
Naseer Daya fara lura da Bilal din Shima kusan wutace ta daukewa jikinsa sbd jiya ya kasa yarda da cewan da gasken Bilal ne ya Gani, Ya dauka idanuwansa ne,kenan tabbas shine, Bilal kaante na Raye kenan?
Da sauri cikin tashin hankali ya Maida kallansa kan DD Wanda yasan zai iya samun bugawan zuciya ya sume idan yaga Dan uwansa Bilal a gabansa a Raye Dan haka ya Dan Tako kadan ya matso kusa da DD din Dan Incase kafin ya Dan Bude murya dake rawa ya danyi gyaran muryar daqyar tana yankewa ya Bude baki cikin yayyankewan kalamai ya ambaci sunan D din ya nuna nuna masa bayansa.
Budewa idanuwa DD yayi tareda dagowa batareda ya saki Bena ba hannunta na cikin nasa qanqame ya juya ya Kalli inda Naseer yake nuna masa idanuwansa suka dauka cikin na Bilal kaante dake tsaye bayansa Yana kallansa cikin firgici da tsananin so da kaunar Dan uwansa me tsananin gaske tareda Kuma tsananin mamaki da tsoron ya Akai yasan Nan din har yazo.
DD kuwa da farko dakatawa yayi dakyau Yana kallan mutumin dayake tsayen a gabansa idan Bilal ne kokuwa shine yake ganin Hakan,
Hannunsa dake riqe Dana Bena sakewa yayi ya rasa kuzarin kama komai bare iya riqewa Nan take,
Lumshe idanuwansa yayi ya sake budesu akan Bilal Wanda hawaye suka cika idanuwansa dakyau sbd yasan yanzu DD zai iya somewa idan ya tabbatarda shine sbd Kansa baya daukan shock masu girma be sababa da tashin hankali.
Motsawan Bilal ahankali tareda yowan taku daya Yana kokarin nufo DD tareda Bude baki zai kira sunan D din take DD ya fahimci tabbas Bilal ne a gabansa, Daqyar ya iya waiwayowa ya Kalli Naseer dake gefensa Yana kokarin ganin DD din Bai shiga shock da yawa ba, Gyada masa Kai Naseer yayi da alaman "yes Bilal dinne a gabansa Shima yana ganinsa.
Kasa riqe Kansa DD yayi Kansa yayi Wani irin sarawa qafafuwansa suka sare lokaci Daya Naseer da Bilal dasukasan zaayi Hakan dama suka taresa batareda ya Kai qasa ba Bilal ne Kai tsaye da kansa ya cirasa da qarfi yayi kan kujera dashi Naseer na gyara masa pillows na doguwar 3 seater Turkish sofa set din aka Kwantar dashi.
Momyn Abdul kuwa na ganin Hakan tayi kitchen da sauri ta dauko ruwa me sanyi ta kawowa Bilal ta miqa masa karba yayi tareda ajiyewa gefe sbd sunyi sanyi ko babu sanyi ana saka masa su yanzu sai ya tashi da shiga Wani ciwon kan kokuma Wani abin Kuma Dan haka Naseer ne ya kalleta yace ruwan dumi zata kawo.
Bena datasan itama Daman zai iya shiga firgicin ya shiga wannan halin hawayen dake idanuwanta ne suka gangaro kan fuskarta ahankali taji qafafunta na qasa daukanta da sauri sumayyah da Anne dasuke kallan iKon Allah sukai saurin riqota a tare suma sumayyah na rungumeta jikinta Anne Kuma na riqe da hannunta Daya tana Dan shafa bayanta da hannun Daya.
Daki sukai da ita suka zaunar bakin gado Anne ta Kalli sumayyahn tace taje ta kawowa Bena din ruwan dumi na tea itama Tasha da sauri Dan zata iya Amai da wanna firgicin sbd babu komai a cikinta.
Sumayyah kan Bena ta shafa cikeda kulawa kafin ta miqe ta fito daga bedroom din ta nufi dining ta fara kokarin hada mata tea sukuwa su Bilal na kan Dan Umme har lokacin.
Tana gama hadawa Bena din tea ta nufi dakin da sauri itama sbd Suma kokarin taimakawa tasu sukeyi.
Tana Kaiwa Anne ta karba tafara bawa Bena din wadda ta girgiza Kai tana cewa bazata iya saka komai acikintaba batajin buqatan Hakan.
Tilastata Anne tayi tareda sumayyahn suna rarrashin Tasha tea din sai alokacin sumayyah da Anne suka Kalli juna sumayyah ta zauna kan kyakyawan kujeran Dayake dakin ta Kalli Bena cikin kulawa sosai da tausasa murya tace
"Shine DD kaante din???
Anne ma shiru tayi tana jiran amsar da Bena din zata bayar sbd kansu na duhu da ganin wannan Dan madarar mara qarfin jini.
Numfashi ta fara saukewa kafin ta Dan dago ta Kalli Anne da itama ita take Kallo Dayake sun Saba ahaka suka taso basuda Wani abokai ko qawaye bayan Annensu da junansu.
Gyada Kai tayi a kasalance tareda bude baki ta furta "eh shine" ahankali tareda rufe idanuwanta hankalinta baya kanta Yana palo kan Wanda zuciyarta ke tsakanin bugawa a lokacin akansa.
Numfashi Anne da sumayyah suka sake lokaci Daya sai alokacin Anne taji kanta yayi Wani irin qato da sanyin jiki sbd kunyar kasancewarta a Palo lokacinda wannan abin ya faru, Data sani Tim farko Hakan ze faru da yau bazata fita daga Dakinta ba zata zauna ta kame kanta acikinsa, Daman Bilal ne keta ganin Basu takura ba ko kame Kai sun saki jiki sun Saba dashi sosai yakeso sbd su zama ahali me kusanci da shaquwa da jina sosai.
Sumayyah kuwa shiru tayi sbd itama kunyar abin ne ya rufeta lokacin sbd da farkon lamarin duka shock ya hanasu Gane komai bare tinanin komai sai yanzu ne kunya da takaicin suna gurin ya shigo ke dabaibaiyesu.
Ita kanta Bena Jin yanda sukai tsit kowannensu Kansa a qasa yasata Jin kunyar komai Daya faru sbd harga Allah Bata tsammaci ganinsa ko a mafarkinta ba yanzu,hakama tasani kome zatayi a daidai wannan lokacin ko waye a gurin zai iya aikata Abinda ya aikata batareda yaji komaiba sbd Bai dauka baayin hakan ba a gaban mutanen.
A Palo Naseer ne yayi dubarunsa da ruwan dumi Yana saka qaramin sabon towel da yanzu aka fasashi Dan bazai yiyu a saka masa Wanda ba sabon ba zai iya Basa matsa a skin ya ringa sakawa a cikin ruwan zafin Yana matsewa kadan da sauran ruwan yan goga masa a tafin qafarsa da tafin hannuwansa.
Cikin zafin jikin Daya kamasa take ya Bude idanuwansa ahankali Yana kallan fuskar Bilal dake gabansa Yana shafe masa yan qananun zufan dasuka firfito daga lafiyayyar farar fatar fuskarsa.
Qurawa Bilal din idanuwansa yayi ya kasa ko qyaftawa tsawon lokaci Yana shiga tinani da abubuwa kala kala na yanda rasuwar Bilal din ta kasance da yanda daga baya yake sanin akwai yiyuwar ba gawar Bilal bace Daman aka samu a mota Ashe.
A yanzu Neman hawayensa yayi ya rasa idanuwansa sukai jajir Yana kallan bilal har lokacin ya kasa tashi daga kwancen Dayake Saida Bilal yaga shock da nauyin zuciyan na Neman yiwa DD din yawa ya ajiye tissue din hannunsa tareda Kai hannunsa biyu ya dago DD din zaune ya rungumesa jikinsa atake suka qanqame juna da qarfi kaman mata wannan Karan Bilal ne ya fara hawayen kewan Dan uwansa da yayi fiyeda yanda yayi tsammanin zuciyarsa zata riqe.
Shi DD kuwa Wani nauyi da radadin rashin Bilal da yayi tsawon shekarun ne suka danne kirjinsa idanuwansa sukai jajir baya iya ko hawayen farin cikin ganinsa sbd Wani abin busar da hawaye yakeyi.
Naseer ajiye towel din hannunsa yayi ya miqawa momyn Abdul robar yace takai kitchen tabasu guri.
Tana barin gurin Shima wayarsa ya fidda daga aljihunsa Yana nufar kofa sbd yakamata yayi magana da Zeenah Dan babu Wanda yasan sun Abuja gashi yasan tayita kiransa jiyan Bata samu sbd kashe wayarsa da yayi.
Yana fitowa daga palon tana daga Kiran nasa cikin sanyin murya da mutuwar jiki sallama kawai tayi masa tayi shiru sbd fushin datakeyi akan kashe wayarsa da yayi batareda ya nemeta ba.
Yanajin muryanta sauke ajiyan zuciya ya fara Yi sbd nutsuwar Daya samu tareda Jin kaman zazzabin kewanta zai kamasa saidai yasan Kuma muryan nata akwai fushi aciki dan haka tausasa muryarsa yayi tareda Bude mota ya zauna ciki ahankali yafara rarrashinta cikin tasa kalan soyayyar da kusan irin ta ubangidansa ce Dan kuwa tinda ya fara soyayya da Zeenah daga zaman jinyar da sukai ya mace gaba Daya akanta kallanta kawai kashe masa dukkanin jiki yakeyi. ##MAMUH# #TOO HOT #ROMANCE #LOVE #CRAZY IN LOVE #DD LOVE #BILAL/SUMAYYAH
*_Arewabooks@Mamuhgee_* 93 ZINNIEE’s SECRET (One stop shop for a new sensation)
Kina Neman kamshi mai sanyaya zuciya❓ Shin kina Neman kamshi da dada❓ Ko kuwa kamshi mai ratsa zuciya kikeso❓ko Kayan gyaran jiki kike nema dry skin ne dake ko hard skin tabbas kinzo inda za’a share maki kukan ki
Tabbas Zinniee’s secret ya gama da damuwarku Ina mata masu aji mace mai aji ai Sai da gyara .tabbas Zinniee’s secret sun gama da damuwarki Hajiya ta.
Zinniee’s secret sun tanadar muku Kaya kamar…… Room freshener Toilet spray Bed spray Dish wash Mopping mist Kai har ma da Feminine wash Akwai Glowing soup dinmu mai kyau da inganci. Glowing cream Face cream da kuma body scrub.
domin samun dadadan Kayan kamshi.da Kayan gyaran jiki maza garzayo Zinniee’s secret Zinniee’s secret DUNIYA ne !!
Zaku iya yi mata magana a wadannan kafafan sadarwar kamar su—IG-@Zinniee’s secret TIKTOK@ Zinniee’s secret Ko ku tuntube su a wannan number 08080840567 za kuma ku iya mata magana ta hanyar Watsapp da wannan number. Zinniee’s secret suna nan a kano Hadeaja road Kano state.
Zinniee’s secret one stop shop for a new sensation.
Zinniee’s secret got u covered,a trial will convince you.
********** DD da Bilal su kadai ne a Palo zaune bayan sun jima rungume da juna cikin yanayinda baya fasaltuwa na tsananin kewa da kaunar juna kafin DD ya kallesa da idanuwansa dasukai laushi har lokacin ya kasa hawaye ma bare, Da taushin murya me sanyi da nutsuwa yace
"Meyasa ka boye kanka daga familynka bayan kasan Muna cikeda da radadin rashinka?? Meyasa??
"Kasan irin gwagwarmayar da Akai before life ya kawo mu inda mike a yanzu? Rayuwana ya shiga Wani mugun hali ni banma San yazan fada Maka ba Amma dai meyasa ka zabi Hakan??"
Numfashi Bilal ya sauke ahankali tareda Dan sauke Kansa yayi shiru tsawon mintina tukuna ya dago ya Kalli DD dayayi Wani Kalan tausayi cikin qanqanin lokaci ya Bude baki a hankali cikin nutsuwa yace
"Na zabi boye Kai ne na Dan Wani lokacin bawai na har abadaba, Zuciyarta tana tsananin son sumayyah da bazan taba iya komawa da ita gida a halinda take ciki kafin ta warke sbd nasan family na bazasu taba karbanta su barmu tare ba,
Nine asalin dalilin rusa yar rayuwar da suke lallabawa da ita a hannun mahaifinsu Tayaya zan barsu a cikin wannan halin bayan nasan a wancan lokacin ba karban sumayyah din zaayiba da Abinda zata Haifa anfada ne kawai Da wata manufar da bansan mecece ba, Ban baro kaantes ba a wancan da niyar tafiya nabar gida kwata kwata ba Amma a halinda na Tarar da sumayyah din aciki lokacinda na Isa gidansu ban yarda Dana barta ahakan ba shiyasa na dauketa da niyar tafiya nesa da ita Dan nemar mata lafiya,
A halinda na fito da ita ni kaina ban dauka a kwai sauran Rai a jikinta ba Dan haka Kai tsaye Wani private hospital dake hanyar fita gari sosai nakaita Kuma aka karbeta cikin gaggawa aka tabbatarda Bata mutu ba da ranta sedai tana mummunan hali.
A wannan lokacin na shiga mafi munin tashin hankali sbd ban dauka zata rayu ba,na dauka rasata zanyi.
Ta dayan bangaren Ina ganin Kiran dukkaninku a wayata Dan haka na sakawa Raina maganar dd babba ce akan kada na taba dawowa kaantes Dan haka a cikin wannan halin na kira driver Dina nace aikasa yake kaantes ya dauko mun password da duka sauran id cards Dina da cards Dina da wasu abubuwan da zan buqata batareda sanin kowaba sbd banason Umme ta shiga damuwa da tashin hankalin bazan dawo kaantes ba.
A cikin Daren na karbi komai hannunsa nace ya mayar da motar kaantes.
Mun rabu dashi bansan sun a akaiba da safe Abinda na fara cin Karo dashi a labarai shine labarin rasuwata daya yadu cikin qanqanin lokaci, Driver na yayi accident ya rasu an dauka nine Dan haka babu Abinda yazo Raina kawai bayan na tafiyata inda zan samu nutsuwan jinyar sumayyah Dan samar mata lafiya tinda har Hakan ta Riga ta faru.
Boyon kaina na fara tareda taimakon sulaiman me napep din Dayake kaisu makaranta, A gidansa muka koma bayan sumayyah taji sauki kusan kwana ashirin Muna jinya,
Acikin kwanaki ne na samu labarin aurenka da Bena, Banyi mamakin Hakan ba sbd yanda Ababa bai fidda zancen yarsa ta rasu ba ga kowa bare batan gawarta.
Sanin daga Kai har Bena zaku zama iyayen da kusan zasu Fi mu son 'yar da aka Haifa dakuma ganin Bena ta samu Damar da zata fita daga hannun mahaifinsu da tsananin quncin rayuwarta ya sakani Yanke shawarar dauke sumayyah mutafi inda zan nema mata lafiya sbd bayyanarmu zai dakatar da aurenka da ita Ta tabbata a gidan Ababa hakama nasan bazaa taba karban sumayyah a halinda take ciki ba na rashin cikakken hankalin.
Da kaina nayiwa Nafisat hanya a sirrance ta hanyar Bata complimentary card Dina nafada mata Wanda zata Kaiwa wadda yake da iKon Kai ma'aikatan kaantes Kuma cikin iKon Allah ya dauketa sbd tausayin nayi alqawarin inganta rayuwarta kafin rasuwata Dan haka aka miqata cikin sa'a a matsayin nanny Kuma me aikin Bena.
Sulaiman ne ya rakoni har Abuja da sumayyah tareda momyn Abdul wadda itace take yiwa sumayyah wanka da sauransu.
Dawowanmu Abuja da farko Badan Sha fama da gwagwarmaya sbd yanayin sumayyahn dayake da wahala da wuyan shaani Dan haka muka na Nema malamai aka daura mana aure.
Bayan aurena da ita ko watanni bamu rufa ba muka bar qasar na koma Canada da ita.
Acan na fara Aiki Kuma Ina kulawa da ita Kuma Muna ganin likitoci kan matsalarta Akai Akai.
Bana tareda kowa Amma na Samu nutsuwa da farin cikin rayuwar Dana Dade bansamuba a cikin family na, Sumayyah itace nutsuwa da farin cikin rayuwata, Batada kowa sai ni,batasan kowaba sai ni, Nine uwa,Uba,aboki,miji da komai nata.
Aikina Yana sake daukan tsanani da buqatan mayar da hankali sosai Dan haka na tura komai sulaiman ya turo min da momyn Abdul sbd ta taimaka gurin kulamin da sumayyah.
Sumayyah ta sake sumun ciki so Daya Tasha wahalarsa sosai wanda kusan yaso qara juyar mata da Kai Dan haka muka ciresa babu sake samun Wani ba na aje maganar haihuwa sai lokacinda ta samu dawowa daidai,
Duk Abinda yake faruwa kaantes ina sane Ina ji Kuma Ina farin ciki sbd ganin kunsamu kwanciyar hankali,
Munfara bibiyan Safnah ne batareda munsan ita din asalin yar uwar Bena bace sai lokacinda ta Kade Anne Kuma suka so kashe Bena Wanda sulaiman yagansu Kuma shine yafara Kaiwa Bena Doki kafin Zeenah ta iso ta Tara mutane, Daga wannan lokacin sulaiman yafara bibiyarta,
Ranar data zubarda Abinda sulaiman ya dauko muka duna muka Gane Abinda suka baka se washe gari mukaji Ashe Kai suka bawa wainnan qwayoyin shine dalilin Daya sakanin dawowa qasar tareda Sumayyah da momyn Abdul Kuma a ranar na barsu Abuja na wuto sbd kunbar qasar a wannan lokacin nasan komai zasu iya aikawata Bena tinda ba kowa.
Kai tsaye Asibiti na Isa ta tararda Bena tabar Asibitin Koda muka kira Nafisat itace ta sanar damu Bena din Takoma da napep da alama gidansu zata tafi Dan Nafisat taji maganar Ababan ta waya.
Kafin na Isa sulaiman ya rigani Isa gidan Kuma ya leqa ya tabbatarda suna ciki Kuma duk Abinda suka fada yaji komai Dan haka bayan fitowarsu Bena shine ya nuna inda suka bi Ina Isa kuwa na samesu a hanyar na daukesu na taho dasu sbd hadarin Safnah da matar Alh basheer bulama yanada yawan gaske da zasu iya sake canja hanyar kawar da ita matiqar Bata bar garinba kwata kwata na lokaci.
A yanzu dinma rashin lafiya take fama dashi tinda ta baro ta kasa cire tinani da damuwa a ranta Wanda tana buqatan cirewan kada Wani ciwon ya shigeta shiyasa na buqaci passport dinta Dan fita da ita na Dan lokaci.
Shiru DD yayi Bai iya cewa komaiba sai ja da idanuwansa suka qara tsananin ciwo da nauyin Kansa na qaruwa, Shidai irin wainnan abubuwan jirkita Kansa sukeyi,baya daukan Hakan, Bai sababa, Duka wannan abubuwan akan sumayyah da tsananin son da Bilal din ke mta yayisu?
Idan shi Bilal zai iya Hakan akan sumayyah shi dayafi Bilal din Jin mafiyin wannan son akan Bena to Yaya zeyi idan Wani Abu ya samu Bena, Yaya zaiyi idan da sun samu fita qasar da Bena batareda ya gano inda suke ba, Da haka zai zauna babuta? Tayaya zai iya dauka? Zuciyarsa bazata iya daukaba.
Juyawa yayi ka Kalli koina cikin palon yana Neman inda zai ganta ko zuciyarsa zata dawo saitin daidai sbd wannan tinanin ya sakasa da zuciyarsa cikin tsananin rashin nutsuwa.
Ajiyan zuciya bilal ya sake Yi sbd yasan Shima kalan halinda zuciyarsa take shiga akan soyayyar 'yar gidan Anne,ga Kuma DD Wanda da alama shi Kansa bazai iya dauka ba sbd baisababa haka Bai iya boye Abinda yake zuciyarsa ba game da komai.
Sarawa kan DD yakeyi sosai da duka Abinda yaji Dan tausayi da tsananin son Dan uwansa sabo fil ya dawo masa Yana Kuma farin cikin dawowarsa rayuwarsu sbd babu Wanda ya Isa ya raba Bilal da sumayyah a yanzu Dan ko shi bazai bari a rabasu ba yanda yasan Yaya akeji dinnan.
Sake rungume juna sukai zuwa lokacin tsananin ciwon kan DD din yayi yawa sbd ga rikice rikice, ga abinci Daya dena ci,ga damuwa, ya abubuwan Dayake taji da yakasa yarda da suna faruwa a duniyar Dan haka abin yayi masa yawa,
Bilal ne ya miqe da sauri ya dauko wayarsa ya kirawo likitansa Wanda yake Kuma kaman aboki hakama a cikin estate din nasu yake Shima Dan haka cikin qanqanin lokaci sai gashi ya iso.
Naseer na ganin shigowar likita yayi sallama da Zeenah Yana nufo ciki batareda ya fada mata komaiba gameda Bilal dasuka Gani sbd sai DD ya Bada umarnin abari kowa ya sani tukuna.
Dubasa likita yayi babu Wani Abu face damuwa da gigita datai masa yawa cikin Kai so Hutu kawai yake buqata da isashen bacci zai samu Kansa ya sake inshallah.
Bayan tafiyan Dr kallan sumayyah yayi wadda hankalinsu ya Dan tashi sun dauka Wani abin ne Kuma ya samesa Yace ta hadowa DD din simple breakfast yaji kafin ya samu hutawan Daya kamata.
Kallan sumayyahn yayi kafin ya mayar da kallansa kan Bilal har lokacin Kansa na sarawa yace Bena yakeson Gani.
Shiru sumayyah tayi tana juyawa ta Kalli kofar dakin da Bena take ciki tareda Anne Yana ganin Hakan ya miqe a hankali zai nufi dakin Bilal ya riqosa cikin Dan basarwa yace masa Anne na ciki fa.
Kallan Bilal din yayi kafin ya girgiza Kansa a hankali yace ok a kirata ita tasan Abinda yake iya ci.
Murmushin da sumayyah batasan yazo mata bane ya subuce mata take shikuma Bilal jikinsa ya mutu da Hakan Dan haka ya saki DD yabarwa Naseer shi yabi bayan sumayyah zuwa kitchen Yana saka Kai yaga momyn Abdul tana Kitchen din Dan haka ya juyo Ya dawo Yana Dan fuskewa.
Gaba Daya hankalin DD na kan kofar dakin da Bena ke ciki basarwa kawai yayi Yana daurewa sbd Bilal da Naseer sunce baa shiga idan mahaifiyar mata ne aciki Amma shi ko Umme na Nan ai Yana shiga.
Simple instant noodles da boiled eggs da sausage sumayyah ta dafo ta ajiye a dining Daman already akwai kayan breakfast dake Jere Wanda babu Wanda yayi breakfast din a cikinsu Dan haka cikin kulawa Bilal ya Dan tilastawa DD yayi breakfast din kafin ya tafi masaukinsu ya huta,
Sam bayajin cin komai tinda ba Bena zai ganiba kawai baya buqatan cin komai sai ya dawo anjima din Amma dole Bilal yai masa.
Zaunawa sukai a dining din harda Naseer, Sumayyah ce tayi serving nasu ta koma kitchen ta dauko musu ruwa marasa sanyi sosai ta ajiye.