Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 - Chapter 52
Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 Chapter 52: Zafin kai complete by mamuhgee wps office 1 Chapter 52. Wani mummunan faduwan gaba da zufa ne ya…
3,365 words
Wani mummunan faduwan gaba da zufa ne ya keto mata sbd Safnah taci gaba da binta akwai babbar matsala zaa iya kamasu duka tare Dan haka suna sake ficewa daga mutane ta tsayar da motarta tana kallan motan Safnah datai parking bayanta.
Fitowa mota Safnah tayi cikin tsananin baqin ciki da takaici tareda tafasan zuciya sbd har lokacin ta kasa Gane me momyn ke Shirin aikatawa.
Tana tahowa momy sai dataga ta fito motar ta nufota kafin tayi gaba kadan da motarta tayo reverse cikin Wani mummunan gudu ta taka Safnah din da motarta Bata tsayaba ta buga da mugun speed tayi gaba tana Hawa titi sosai da gudu.
Cikin mummunan yanayi na karywar qafarta Daya da fita fit a take jamian tsaron suka iso kan Safnah wadda ke cikin halin Rai ko mutuwa Dan hatta fuskar kusan tayi dameji suka kwasheta sauran motacin kuwa suka bi bayan momy.
Asibitin da aka Kai Ababa Wanda tini Shima gurin cire bullet an qarasa lalata qafar acan aka kaita itama da qafarta Daya Bata hayyacinta sbd fuskarta datai damage.
Momy gudu takeyi sosai tana qarawa hankalinta na tashi tana waya da qaninta dazai Siya mata ticket a Daren ta wuce Lagos daganan zata Bema visa tabar qasar gaba Daya.
Checking point na sojoji ne suka tsayar da ita ganin yanda take gudu sosai tana mace.
Jakar kudin dake qarqashin qafafunta suka fara gani take suka buqaci tayi parking.
Parking tayi tana Dan kame kame tana murmushin karfin hali kafin tafara magana saiga ledan qwayoyin abayan motarta.
Koda jamian dasuka biyo motarta suka iso gabaki Daya kamanninta sun sauya daga hannun sojojin Dan haka take case dinta ya girmama aka fara daukanta hotina mutane ana korarsu sbd harda bindiga a Jakarta.
Kamata Akai babu tausayin halinda take ciki da mummunan dukan datasha da kan bindiga a hannun sojojin aka saka mota ko tafiya Basu fara ba itama ta sume kaman matacciya hancinta da bakinta suna jini hakama idonta Daya ya tsiyaye.
Same Asibitin itama aka kaita inda su Ababa da Safnah suke babu Wanda yasan inda Kansa yake haka itama aka Bata gadon batasan inda kanta yakeba jininta na tsiyayewa. saisun farka su samu Daman karban hukuncinsu. ##MAMUH#
*_Arewabooks@Mamuhgee_* 91 Familyn Kaantes sai alokacin da sukaji Safnah da momy na hannu Daman shi Ababa tini yana hannun hankalinsu ya Dan kwanta suka dawo da sabuwar damuwarsu akan ta inda zaa fara Neman Bena da Anne yanzu.
Ta bangaren Umme kuwa da alh Bulama rasuwar hajiya sabuwa ta dawo musu sbd ganin yanda su Safnah suka kasheta cikin rashin Imani da tausayi.
Kowa ya shiga jimami tashin hankalin Jin wannan masifar, Umme tayi Kuka fiyeda lokacinda suka rasa hajiyar, Alh Bulama kuwa bayan ciwo da baqin cikin rayuwar dasuka samu kansu aciki harda baqin ciki da radadin rasa 'ya dayayi sbd Safnah tashiga cikin tsakiyan zuciyansa fiyeda yanda ake tinani ashe ita din ba tsatsonsa bace.
Umme itace ta ringa tausan Dan uwanta tana Jin radadin sa na rashin 'ya ko 'dan Kansa.
Matansa kuwa murna da Jin dadi suka hau Yi sbd har ga Allah sun azabtu da Safnah sbd itace take jiya rayuwar Alh Bulama din da matansa yanda takeso haka akeyi babu wanda ya Hana.
DD kwana daya da wuni Daya yayi a Asibiti kafin ya Dan warware ya dawo gida lokacin labarin rasuwar hande yazo musu babu Wanda yaji komai akan Hakan saidai suka bita da Allah yaji qanta tinda musulma ce Kuma mutuwa na kan kowa hakama kowa Yana fatan idan ya rasu ya sadu da malaikun rahama.
Bayan dawowarsa daga Asibiti Kai tsaye kaantes ya koma sbd highbridge din ana gyara na sauya komai na gidan Daya buqata.
Zuwa wannan lokacin Amnah ta fahimci mummy dinta batanan baa San inda take ba Dan haka ta kwanta rashin lafiya sbd rigima da kukan data ringa yi musu ba kakkautawa.
Shi Kansa Daddyn nata Dake Neman yin kukan Sam qin yadda tayi da rarrashinsa Dan haka Shima kusan Neman komawa kwance jinyar yakeyi sbd Yana gab da rikicewa gaba Daya Shima idan ba gano inda matarsa take akai ba.
Cikin tashin hankalin Rigima da ciwon Amnah sukai kwana biyu Shima a lallabawa kawai yakeyi sbd baida lafiyan,
Bincike kuwa tini aka bazama babu kama hannun yaro dukiya me yawa ake zubarwa Dan tsananta binciken Amma shiru.
*******Nafisat dake kwance tareda Amnah tana shafa kanta datai bacci jikinta da zafi sosai sbd rigima data gama kafin baccin.
Wayarta ce tayi haske alaman shigowan kira Dan haka ta Zame Daga jikinta ahankali tareda nufar toilet ta shige ta kunna ruwa ta dauki wayar cikin nutsuwa da sanyi tace
"Hello Ina wuni Yaya sulaiman?"
"Lfy kalau alhmdllh,kina jina ko Nafisat?,Yaya Amnah?ya jikinta?"
Numfashi Nafisat ta sauke ahankali tareda Dan zaunawa gefen bathtub tana cewa
"Lafiya kalau,Amma ta kasa yarda da rashin Anty Bena ko yanzu rashin lafiya ce sosai a jikinta.
Shiru sulaiman yayi kafin ya Dan gyara zamansa cikin napep din da yanzu Janta kawai yakeyi sbd batar da tinanin mutane da kamanni yace
"Inshallah ta kusa kasancewa tareda mahaifiyarta Amma dai yanzu Mummyn tata batada lafiya duk lokacin Nan fama akeyi da ita Dan haka yanzu Abinda mukeso dake passport dinta da id cards dinta duka Zaki tattara guri Daya ki samu yanda zakiyi ki fitomin dasu anjima idan anshiga sallan ishai masallacin kaantes.
Shiru Nafisat tayi tareda Dan Nazari duk da Bata taba musawa duk Abinda yace kaman yanda Shima Bai taba musawa Bilal Abinda yace ba Dan haka tace
"Zanyi kokarin yin Hakan anjima Amma Dan Allah Yaya sulaiman kada ku bari Amnah ta Dade a Hakan babu mamanta wlh zata iya kamuwa da Wani ciwon,yarinyar nada qawa zucin mamanta sosai, Dan shiru tayi na sakanni kafin ta qara da cewa
"Shima daddynta Yana cikin mummunan halin"
Gyada Kai sulaiman yayi Yana cewa " wanna duk sai yanda Sir Bilal yafada zaayi"
Sallama sukai ya kashe wayar itama ta kashe tana kashe ruwan tareda fitowa daga toilet din.
Tana fitowa ganin DD a dakin ya sakata rudewa sbd Bata taba tsammanin shigowarsa ba Dan haka tai saurin qasa da Kai tana gaidasa a girmame.
Kaman bazai kalletaba qafafunta kawai idanuwansa suka kalla zai nufi 'yarsa dake kwance kan kujeran dakin Bena din zai dauka sai yaga babu alaman ruwa ko kadan a qafafunta bayan daga toilet ta fito.
Mayun idanuwansa da duk suka fada a kwanakin na rashin matarsa ya dago ya zuba mata Yana kallan hannuwanta Suma ya gansu a bushe tsaf babu ruwa ba alamansu bayan yaji qarar ruwa shigowarsa a toilet din.
Fuskarta ya kalla itama ruwa sai ya Dan Kalli wayar hannunta take ya tabbatarda waya tayi ta sirri idan har babu ruwa hannuwanta da qafafunta da fuskarta Kuma ta kunna ruwa to Hakan na nufin tabbas waya tayi.
Bai furta komaiba ko gaisuwanta be amsa ba ya dauki Amnah din ya fice daga dakin.
Kai tsaye dakin Zeenah ya kaita Dan fasa tafiya yayi da ita ya fita Yana fidda wayarsa ya kira Naseer sbd shi yanzu kowa baya yarda dashi akan duk Abinda ya shafi Bena da 'yarsa Dan haka take yace Naseer ya saka qaqqarfan bincike akan me aikin Bena Kuma Nanny din Amnah.
Naseer na Jin Hakan yafara kokarin bincikar masu aikin gidan ma gabaki Daya.
DD gaba Daya yanzu ko mutane bayason shiga bayason suna nemansa Kuma, Kadaice Kansa yakeyi sbd baya buqatan kowa atareda shi matiqan ba matarsa ce ya dawo qarqashinsa ba.
Ranar ma haka ya wuni cikin tsananin zafin jiki da ciwon Kai Dana kirji me tsananin gaske Wanda ya saka hankalin dd babba ma nasa hankalin b kwance yakeba da batan Benan,
Wainda dake asibiti kaf acikinsu babu me sauran amfanin da zai iya magana bare yasani ko ma ya fada inda Bena ta tafi.
Safnah ma dai har tsawon kwanakin Bata farfado ba sbd ba qaramar buguwa kanta yayi ba.
Ababa duka qafafunsa biyu babu me Aiki dayan bullet ya lalata dayar itace ta karye tin gidan DD babban baqin rayuwarsa da quncin Daya dabaibaiye rayuwarsa shine yau ko qafafun da zai iya daga Kansa tsaye baida, Hande ta mutu ta bar duniya, Ga hukuma na jiran su warke ayi gidan yari dasu ita momy ma da Safnah akwai yiyuwar ratayesu zaayi da ransu suna ji suna Gani su mutu Subar duniyar,shi kalan nasa hukuncin kuwa Kila life in prison ne sbd dumu dumu ansaka sunansa cikin tare suka maumalan qwayoyin da aka kama momy dasu Dan haka shi tasa mummunan qaddarar ta qarew yari ce har mutuwa da qafafu biyu babu ko Daya. Daya Tina Hakan Wani irin Kuka yake fasawa wanda ke saka jikinsa daukan rawa Yana Rasa ta yanda wannan mummunan kaddarar ta samesa,Jin yake dama shine ya mutu ba hande ba ya huta da wannan biyu babun.
*********Koda Akai sallan magrib Saida likita yazo ya duba DD sbd jikinsa dake tsanani, Bayan tafiyan likita daqyar Anne ta sakasa yaci abinci yasha magani.
Hakanan ya daure ya fita sallan magrib masallaci daga can Bai jiraba kaman yanda dd babba keyi wasu lokutan na tsayawa jiran sai anyi ishai ya baro masallacin gaba Daya.
Bedroom dinsa ya nufa Kai tsaye ya tube tareda sakarwa Kansa ruwan sanyi sbd ciwon Kansa ya rage ya samu Jin sassauci.
Ya jima Yana cikin ruwan kafin ya gama ya fito daure da towel fatar jikinsa tana Wani irin kyallin daukan Ido sbd duk yanda yake cikin tsananin damuwa da quncin zuciya fatarsa da kyansa suna Nan saima daukan Ido Dayake qarawa sbd rashin fita.
Yau jallabiya ya saka da hula ya Kalli time yaga lokacin sallan ishai yayi har na fara ya fito a natse cikin kamewa Yana nufar hanyar fita.
Yana kawowa sashen ummensa da a hango fitar Nafisat daga sashen tana nufar gate zata fice.
Kallawa yayi a natse ya Gane ita din ce Dan haka wayarsa ya fitar Kai tsaye ya kira Naseer yace yabi Nafisat gatanan ta fita Kaantes.
Naseer alwala yayo zashi masallacin Amma ya juya ya nufi hanyar babban gate na fita Kaantes Yana fita ya hanga har tayi Dan nisa Dan haka bicycle din securities na gidan da ake zagayen gidan da ita da daddare sbd tsaro ya janyo ya hau yabi bayanta Yana kafe idanuwansa akan inda tabi.
Dap da zai cimmata can nesa da kaantes ta baya yaga napep tazo gabanta ta tsaya sukai kaman sunyi magana inda ze kaita cinikin beyiba ta jefa masa jakar dake hannunta a bayan napep din yaja y wuce ita Kuma sai datai tsayuwar mintina kusan biyar kafin ta juya ta dawo gida.
Naseer bayan napep din ya ringa bi da Keke Yana hanasa Gane ana binsa.
Dagowan tafiya sukai har sulaiman ya Isa gidansa yayi parking din napep dinsa ya fito ya shiga baya ya Ciro jakar da Nafisat ta jefa masa tambayar ta passport din Bena ya shige gida dasu.
Naseer da ba qaraman gajiya yayi ba da tuqin keken tini ya hada uban zufa guri ya nema a nesa da gidan ya ajiye kekan ya fara sauke numfashi tsawon lokaci kafin ya dawo daidai ya fidda wayarsa tukuna ya turawa DD sakon inda yake kawai.
Yana gama tura masa sakon ya saka wayar aljihunsa ya nufi masallacin anguwar ya sake alwala yashiga sallan da beyiba.
Kaman Wanda yayi gudun fitar Rai Yana sallame sallah DD ya iso gurin Dan haka Shima motan ya shiga suka zauna suna gadin gidan sbd koma menene Nafisat ta bawa me napep din dole akwai inda ze Kaisa sbd nan gidan Daya shiga matarsa da 'yayansa biyu ne a ciki a yanda Naseer ya tambaya cikin masallacin.
Kaman ma barayi haka Suka dasa zaman Jira a motar ga zazzabi sosai a jikin DD Dan haka dole Naseer ya mayardashi gida ya dawo shi ya dasa zaman Jira.
Har asuba Yana gurin a gabansa sulaiman ya fito sallan Asuba Shima ya fito suka shiga masallaci a tare sukai sallah da zasu fito ne sulaiman ya fidda wayarsa yakira Wani yaronsa Dayake napep yace yazo ya karbi napep dinsa yakaisa Tasha zaiyi tafiya zuwa Abuja yau.
Naseer na Jin Hakan ya dakata cikin masallacin Saida sulaiman ya shige gidansa.
Kallan man Dayake cikin motarsa yayi yaga tabbas ze Kaisa Abuja Dan haka wayarsa kawai ya dauka ya turawa DD sakon zaibi Naseer din Abuja tukana yaga wane abune Nafisat ta Basa kuma waye zaa Kaiwa.
*****Qarfe 7 sulaiman ya fito daga gidansa rataye da jakar matafiya tareda matarsa data biyosa har waje tayi masa Allah ya tsare hanya ta koma Shima ya shiga napep saurayin Daya kira yazo suka shiga napep din ya jasa zuwa Tasha.
Sai dasukai Nisa sosai Naseer ya tada motarsa yabi bayansu har cikin Tasha Yana kallo ba jimawa motan da sulaiman ya shiga ta cika ta tashi ta fito zuwa Abuja.
Naseer Kansa ya manta yaushe rabonsa da tuqin doguwar tafiya sbd jirgin dasuke Hawa sai yau din.
Sosai yake tattare da gajiya sbd ga kwanan mota ga tukin keken da yayi hakama ga doguwar tafiyar Dan haka Koda suka Isa Abuja yamma tayi hakama ya matiqar gaskiya sosai Shima kaman zazzabin yake ji Amma haka yayi karfin halin bin motar har ta sauka passengers duka firfito harda sulaiman ya dauki drop ya kama hanyar gidan Bilal.
Saida Naseer yaga har gidan da sulaiman yayi ringing kofa ba jimawa aka Bude Wanda ya Gani je ya sakasa kusan somewa a motan Daman ga yanayin Dayake Dan haka da qyar ya Ciro wayarsa ko Gani bayayi sosai ya turawa DD address da house number na gida tareda saka sunan Bilal kawai karshe.
DD da tinda ya samu sakon Naseer yake kiransa baya samunsa har yamma tayi Jin yakeyi kaman zai qarasa zaucewa Yana fitowa sallan magrib sakon Naseer na qarshe ya shigo masa dakatawa yayi cak da inda yake tareda qara Karanta sakon kusan so uku kafin ya juya kawai ya nufi sashensa ya dauko Abinda zai dauka ya fito da Kansa yakai Kansa airport ya Siya ticket cikin dare Saida ya Bata kusan awa biyar zuwa shiga a airport din kafin ya samu jirgin zuwa Abuja.
Duk yanda yaso Bai samuba sai qarfe 7 na safe Shima ya samu iso masaukin Naseer Wanda ya kwana cikin matsanancin halin zazzabi me qarfin gaske Amma ba laifi lokacin ya warware.
Qaramar tsadaddiyar luggage dinsa ya ajiye a dakin Naseer din alwala da sallah kawai yai bugun zuciyansa na qaruwa sbd har lokacin be Gane sakon Naseer ba sosai hakama babu Wanda yasake maganar komai acikinsu Yana idarwa karfe 8 suka fito Kai tsaye da mota Naseer ya nufi gidan.
*******Jikinta yayi Dan sauki sosai akan jinyar datasha ta kwanakin,jinyar jiki data zuciya wadda har yanzu ta kasa cirewa ko kasa tinaninsa a zuciyarta sbd mutuwace kawai tasan zatayi yafita ranta.
Anne da sumayyah harma da Bilal duk Wani kulawa da tattalin dasuke Bata Basu iya cirota daga damuwa da radadin zuciya ba saidai suna iya kokarinsu gurin ganin sun kula da ita din musamman sumayyah data San duk Abinda ya faru Bena ta fada mata Dan haka Suka taru suka boyewa Anne maganar Safnah din Dan gwara abarta akan yarda da Safnah ta Dade da mutuwa kawai akan baqin cikin dazata shiga idan taji Abinda yake faruwa.
Shikuwa Bilal ya yanke shawarar su tattara su dukan su koma Canada ne sbd tashin hankalin rikice rikicen da aketa Yi a Kaantes kafin hankali ya kwanta Bena din ko zata samu sassaucin halin Datake ciki shiyasa ya buqaci passport dinta.
Da safen sumayyah da momyn Abdul ne kawai a palon suna hada dining se Anne data fito da Bena wadda tayi fari fayau ta Dan rame Sosai,
Sanye take da Riga da wandon bacci masu tsantsi da hula qarama akanta Anne ta kamota cikin kulawa riqe da hannunta ta fita da ita Dan ta daure tayi breakfast tareda su sbd tsoron kada yunwa Kuma tai mata illa.
Knocking kofar Akai kafin momyn Abdul taje ta Bude Kai tsaye aka Murda kofan aka Bude Kai tsaye daidai fitowan Bena da Annenta daga bedroom din Dayake na Bena din yanzu.
Akanta idanuwansa suka fara sauka ita kuwa abinda ya Saba sanar mata da wanzuwarsa a guri ya shiga hancinta cikin Wani mummunan sanyin jiki ta juya ta Kalli kofan idanuwanta suka sauka kansa.
Shikam tsaban Abinda zuciyarsa ta kasa riqewa bare yarda dashi ya Tako cikin rufewan idanuwa batareda damuwa da duk Wanda yake gurinba Kai tsaye yana isowa ya kamota ya hade fuskarsa da tata cikin tsananin budewa da fallasa zuciyarsa ya hade bakinsa na nata hawayen Daya kasa riqewa kaman Wani baby suka fara gangaro matsa.
Daga Anne har su sumayyah da Momyn Abdul din dake palon mummunan tsoro ne ya kamasu ganin Abinda Basu taba ganiba. ##MAMUH#
*_Arewabook@Mamuhgee_* 92 ZINNIEE’s SECRET (One stop shop for a new sensation)
Kina Neman kamshi mai sanyaya zuciya❓ Shin kina Neman kamshi da dada❓ Ko kuwa kamshi mai ratsa zuciya kikeso❓ko Kayan gyaran jiki kike nema dry skin ne dake ko hard skin tabbas kinzo inda za’a share maki kukan ki
Tabbas Zinniee’s secret ya gama da damuwarku Ina mata masu aji mace mai aji ai Sai da gyara .tabbas Zinniee’s secret sun gama da damuwarki Hajiya ta.
Zinniee’s secret sun tanadar muku Kaya kamar…… Room freshener Toilet spray Bed spray Dish wash Mopping mist Kai har ma da Feminine wash Akwai Glowing soup dinmu mai kyau da inganci. Glowing cream Face cream da kuma body scrub
domin samun dadadan Kayan kamshi.da Kayan gyaran jiki maza garzayo Zinniee’s secret Zinniee’s secret DUNIYA ne !!
Zaku iya yi mata magana a wadannan kafafan sadarwar kamar su—IG-@Zinniee’s secret TIKTOK@ Zinniee’s secret Ko ku tuntube su a wannan number 08080840567 za kuma ku iya mata magana ta hanyar Watsapp da wannan number. Zinniee’s secret suna nan a kano Hadeaja road Kano state.
Zinniee’s secret one stop shop for a new sensation.
Zinniee’s secret got u covered,a trial will convince you.
******** Yanda yayi mata kyakyawan rungumar da yanda ya hade fuskansu da yanda yake kissing nata hawayensa na gangarowa daga cikin kyawawan idanuwansa tini ta kasa hanata Kansa ko kwacewa daga garesa sbd ita kanta ganinsa ya zo mata ne kaman a mafarkin da Bata taba kawowa a kusa ba, Ta Riga ta cire Rai daga ganinsa har abada sbd tinanin ya haramta gareta, Ganinsa da jinsa a jikinta yanzu ya tabbatarwa da zuciyarta bazata taba iya rayuwa babusa ba a ynzu shi din wani tsoka ce a kirjinta da bazata taba iya fitaba.
Ita kanta hawayen ne masu sanyi suka gangaro mata idanuwanta na rufewa ahankali hakama jikinta na sakewa gaba Daya a jikinsa sbd kasa yarda da ganinsa ya taho gareta.
Sake rungumeta jikinsa yayi dakyau Yana qanqameta tareda zare bakinsa daga nata Yana sake qanqameta dakyau Yana jero ajiyoyin zuciya hawayensa na kasa tsayuwa sbd sai alokacin ykejin kaman zai tsaga kirjinsa ya mayar da ita cikinsa gaba Daya ya boye ya Hana kowa da komai ko taba ta bare a sake rabasa da ita.
Shiru palon ya dauka babu Wanda ya iya magana babu Wanda ya iya motsawa Anne dake gefenta tsaya tini ta saki hannun Bena din dayake riqe a hannunta tareda matsawa gefe kadan sbd kaman bema lura da kowa a palon ba bare ita Datake riqe da Bena din,
Sumayyah da momyn Abdul Kallo dai sukai masa tin Sako Kansa palon suka fahimci shine DD qanin Bilal sbd kamarsu datai yawa.
Naseer daga kofar ya tsaya bayan shigewarsu Yana tura kofar palon ya rufe ya tsaya Yana Dan dauke Kansa daga kansu Bena din sbd Daman yasan zaayi Hakan sbd DD shi Sam baisan Yaya akeyi ko control na Kai akan lamarin da duk ya shafi Bena.
Ita kanta Bena din sai da suka jima a Hakan tsaye kafin ta Tina da akwai mutane palon ta Dan bude idanuwanta da sukai jajir tana zamewa daga jikinsa ta dago ta kallesa gabaki Daya idanuwansa dasukai laushin rashinta ya zuba mata tareda sake Kai bakinsa yayi kissing idanuwanta ahankali kafin ya dawo yayi kissing hancinta da kumatunta duk a hankali daga qarshe ya sake mayar da ita jikinsa ya rungume Yana Bude baki cikin Wani raunannan sauti yace
"Karki sake barina ko me Wani zai fada Miki,zan baki kariya ke da Annen ki, please karki sake barina,I love you,I love you"