Kaddarar ramlah book 1 complete - Chapter 22
Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 22: Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 22. “Yanzu ki fada min gaskiya taya za ki zauna da namiji wanda kullum…
4,477 words
“Yanzu ki fada min gaskiya taya za ki zauna da namiji wanda kullum gantale yake, wanda babu motsi, amma kullum kalaman soyayya yake jera miki? Ke fa ba budurwa ba ce, Wallahi da nice ke da tuni na duba gabana. Maza nan sun cika, babu lokacin jira.”
Ayshatu ta zuba mata ido. Idonta ya yi ja.
“Fatima… ki saurare ni.”
Ta matso da kujera gaba, ta furta cikin sanyi da karfi a lokaci guda
“Kin san me nake da shi da baki da shi? Ni ina da abin da ku baza ku gani ba zuciya mai kyau Kauna ta gaskiya. Fahimta. Karɓa. Tausayi. Kuma da duk abinda kika lissafa sha’awa, jiki, motsi –babu wanda ya fi waɗannan daraja a soyayya.”
Fatima ta dan ja bakinta gefe. “Zuciya dai bata cire kishirwa ba.”
Ayshatu ta dafe kirjinta. “Amma zata hana mace zama tamkar rakumi mara ruwa. Ni fa bana son abun sosai yarana fa biyu shekarar mu nawa yanzu? Nazama shi yazama ni Ina sonsa saboda yana kula da ni a lokacin da maza da dama ke wulakanta mace idan ta ce ‘ban ji daɗi ba’. Yana sauraren kuka na. Yana tuna lokacin da nake fara karatu. Yana tuna ranar da muka haihu. Me zai hana in kasance da mutum wanda ya ba ni komai face ɗaya lafiya, wanda kuma yana kokarin dawo da ita?”
Fatima ta ɗan sauke murya. “Toh, ina nufin fa… ki lura da kanki.”
Ayshatu ta ce, “Ina lura. Kuma na gane ba kowane abu kike samu a gado ba. Wasu abun sai ka nema a gwiwa, cikin addu’a da hakuri. Shi yasa ni bazan canza wannan soyayya da duk masoya ‘tsala-tsala’ ba.”
Fatima ta ɗan sunkuyar da kai. “Ki yafe ni, Aysha. Kawai na damu da ke.”
Ayshatu ta ce da murmushi mai zafi, “Idan kina damuwa da ni, ki tsaya a gefe kina duba yadda ƙauna ke ƙarfafa wanda duk duniya ta ce ‘ya kasa’.”
Fatima ta ɗan ɗaga kai, idonta cike da tunani. Ita daman baƙin cike takeyiwa kawartata so takeyi takashe auren dan duk ciƙinsu tafi kowa samu da wadata.
*****
Yana zaune a cikin wani shahararren café da ke tsakiyar Casablanca. Gaban sa akwai ƙaramin kofin Moroccan tea, tururin shayin na tashi yana haɗuwa da kamshin mint.
Cikin shigar farar riga da wando ruwan toka, yana ta danna wayarsa da yatsu masu tsabta.
Ya gama kira da Mai Martaba, wanda ya masa magana “bana jin daɗin jinkirin ka. Kana buƙatar dawowa. Cikin satin nan ka bayyana a gabanmu. Ina buƙatar ganinka da kaina.” ya sunkuyar da kai. “Na'am, ranka ya daɗe. Zan shirya, insha Allah.”
Ya ajiye wayar. Zuciyarsa bata da nutsuwa. Ba don kira daga Mai Martaba ba. Kafin ya iya miƙewa daga kujera, sai wayarsa ta sake ɗaukan karar kiran Ayshatu.
Ya kalli sunan Habibiyata Sai murmushi ya bayyana a leɓensa, ya dan latsa “accept”.
“Assalamu alaikum, Aysha.” “Wa alaikum salam, Habibie. Na gaji da ganin hoton ka inason ganinka kusa dani.”
Murmushin da mai tsada yayi yace “Ina jinki, masoyiyata.” “Nace ko zaka iya kara ganin likitanka a nan Morocco. Ka san fa bana jin daɗin yadda ka ke yawan shiga damuwa yanzu.” Yayi dariya mai taushi.
“Aysha, likitoci nawa kike so nagani? Gaskiya magunguna sun ishe ni. Kowanne likita yana bani kalma daya. Ki manta da wannan.”
Aysha ta dan yi shiru. Sannan ta ce da hankali “Habibie, ba a gajiya da neman lafiya. Koda ana da kwanciyar hankali, mutum yafi jin daɗin samun tabbatacciyar lafiya. Ka kara ƙoƙari mana, ka sake ganin wani.”
Shiru ya shiga cikin muryarsa. Ya dago idonsa daga kofin shayi, ya duba sararin sama, kamar yana karanta abinda ya kasa faɗa.
Sai ya ce da sanyi mai sosa rai “Toh, Aysha. Zanje nagani gobe… Tunda kema kin gaji da namiji da baya miki komai Kin gaji dani ne, ko Aysha? Kin gaji da rashin amfanina? Kin gaji da zama da mutum wanda ba zai iya biyan ki ba a matsayin miji?”
Kalamarsa ta tsaya a kunne kamar ruwa da aka zuba a cikin toka. Aysha tayi shiru. Kamar kalmar ta daki zuciyarta.
Ta buɗe baki a hankali. “Habibie… Ban ce na gaji da kai ba. Na ce… ka ƙara ƙoƙari, domin ina son ganin ka da ƙoshin lafiya.
Sosai ya sauke ajiyar zuciya. Murya ta fara canza launi. “Na san baki ce haka ba. Amma bana jin kaina yadda nake. Wani lokaci nakan ce a zuciyata Me yasa mace mai kyau, mai tsafta, mai haƙuri kamar Aysha zata zauna da ni har yanzu?”
Aysha ta ce da kwantar da murya“Ka fi gabanka daraja. Ka fi karfin jikinka. Ka fi karfin lafiyar da ta ƙi tsaya maka. Ni ina sonka saboda zuciyarka, kulawarka, fahimtarka. Ba saboda... gamsuwa ba. Na riga na daina buƙatar hakan tun ranar da na fahimci kai da ciwonka na buƙatar ƙauna fiye da komai.”
Sosai ya saki numfashi mai zafi. Ya zauna. Hannunsa na rawar jiki.
“Ina jin kamar na kasa zama namiji. Kuma kina ci gaba da nuna min cewa ni har yanzu ina da daraja… hakan yana min ciwo, Aysha.”
Ayshatu ta ce da sauri, “ Wai Habibie shekara nawa kana gamsar dani? Shekaru ma yakamata nace ni yanzu da girma yafara kamani bari ni in fada maka kai daraja ce a wurina. Kai mijina ne, uba ne ga yarana, aboki ne, garkuwa ce. Idan babu karfi, akwai ƙarfi a zuciyarka.”
A can bangaren Morocco, Sosai ya lumshe ido. Ya kama kansa da hannu daya.
A cikin duk shirin tafiya, da kasuwanci, da kira daga masu daraja wannan kalmar Aysha ce ta fi komai nauyi.
“Zan je. Zan je gobe. Ba don magani kawai ba. Don ke.”
*******************************
Nana hadiza
09030569336ƘADDARAR RAMLAH
SHAFI NA HAMSIN DA UKU.
Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!
Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!
Domin biyan kuɗi:
Acc Name: Bilkisu Sani Kaura
Acc Number: 7040402435 (OPAY)
Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:
09030569336 ko 07040402435
Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a
Arewabook @nanadiso10
https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693
********
Washegari bayan hirarsa da Ayshatu, Sosai Yashiga damuwa ya zauna cikin shiru a ɗakin hotel ɗinsa mai matakin “presidential suite” a Casablanca.Girman ɗakin bai dame shi ba. Tagogin gilashi sun buɗe zuwa ga teku, hasken rana yana shiga cikin ɗakin a hankali, amma duk da haka, zuciyarsa cike take da kalmomin Ayshatu
“Kai daraja ce a wurina…”
“Ni bana sonka saboda jikinka…”
Wannan kalmomi suna yawo a cikin kansa. Sun damesa ba don sun ci masa rai ba, amma don sun faɗi gaskiyar da ya daɗe yana ƙoƙarin guje wa. Sai ya ɗauki waya. Ya kira direbansa.
“please, ka kai ni Centre Hospitalier Universitaire.” Wannan asibiti ne mafi girma a Casablanca, inda manyan likitoci ke duba matsalolin da suka shafi hormones da lafiyar maza.
A VIP lobby ya zauna, cikin farar rigar linen da wando mai sauƙi. Likita Faouzi ya fito daga ofis. Dattijo ne mai kamala da nutsuwa.
“Yashiga?” ya ce da murmushi. “Please, shigo ciki.” ya shiga. Ofishin ya cika da kamshi da tsabta. Likitan ya zauna yana kallon takardun da aka aiko masa tun tuni. Ya fara da cewa, “Na duba gwaje-gwajenka. Matsalar da kake da ita ana kiranta androgenic decline raguwa ce ta testosterone da karancin jinin da ke kai kuzari.”
Sosai ya lumshe ido, ya ce da murya mai rauni, “To, likita… akwai mafita kuwa?”
“Eh,” Dr. Faouzi ya ce. “Amma tana ɗaukar lokaci. Maganin hormones ne, da sauya salon rayuwa, da kuma goyon bayan zuciya. Kana buƙatar hutu. Kana buƙatar ƙarfin gwiwa. Kuma kana buƙatar ka yarda cewa har yanzu kana da daraja.” ya sauke ajiyar zuciya.
“Ina tsoron kada in rasa jin kaina kamar da,” ya faɗa.
*****
Da dare…
Ya kira Ayshatu daga dakin hotel ɗinsa. Tana kwance a gado, rigar barci a jikinta, tana murmushi da ganin sunan wayarsa.
“Ka yi kuka ne?” ta tambaya da dariya kaɗan.
“Ban kuka ba,” ya ce, yana murmushi. “Amma na kusa hakan.”
“Likitan fa?”
“Yace akwai mafita. Amma sai da hakuri. Da magani. Da taimakon mace mai ƙauna.”
Aysha ta dafe zuciyarta. “Ni zan kasance tare da kai, Kullum. Ko daga nesa.”
Yace, “In na dawo, zamu tafi hutu. Ba Maldives ba. Ba Paris ba. Sai inda zuciyarmu za ta huta.” “Zuciyata tana tare da kai,” ta ce.
*********
PARIS
Zaune take a cikin ɗakin salon penthouse a kusa da Eiffel Tower. Glass na kofar balcony a buɗe, iska mai sanyi tana shiga cikin ɗakin a hankali. A gabanta, teburin shayi ne mai tsabta, akwai cup guda, sai tiren croissant da bata taɓa ba. Zuciyarta cike take da tunani kala-kala. A waje ana ta motsi motoci suna wucewa da sauri, mutane suna kallon shaguna, amma Ayshatu ba ta jin komai sai ƙaran zuciyarta.
Ta ɗauki cup ɗin shayi ta sha sip ɗaya. Sanyi da ɗan ɗaci ya cika bakinta, kamar yadda maganar Fatima kawarta ta cika zuciyarta.
“Wai yanzu ke Aysha, haka zaki zauna? Miji baya biya miki bukata, ba da jiki ba, ba da kulawa ba... Kuma kina jurewa haka? Kinada kyau, kinada kudi, ga maza nan da zasu iya yayemiki sha’awa. Be wise mana.”
Ayshatu ta haɗe gira. Kalaman Fatima suna yawo a kanta kamar an kunna speaker a kunne. Ta san Fatima ba muguwa bace. Tana faɗar gaskiyar da yawancin mutane ke tunani, amma basu faɗa ba. Amma kalmomin nata suna ƙara zafi saboda akwai ɗan gaskiya a ciki.
“Kinada right. Kinada iko. Kinada kyau da kudi. Kuma mijin me? Kalaman soyayya da hawayen da ba su da amfani.”
Ta ajiye cup ɗin shayin, ta ja numfashi. Tana zaune a kujera, kafa daya a kan ɗayan, tana kallon hoton Eiffel Tower daga cikin gilashi.
Wayarta ta ɗauka. Tana jin komai dai dai tana da komai, amma tana jin ba komai a cikinta.
Ta shiga Instagram.
Scrolling take, tana kallon hoton wasu ma’aurata suna dariya a gaban wani wuri mai kyau haka kawai ta danji wata irin gasa a zuciyarta. Sai ta shiga shafin wani guy mai kyau wanda take yawan gani a Explore.
Guy din yana sanye da kaya masu kyau, gashi mai tsabta, lafiyayyen jiki. Sabon hotonsa na bakin teku ya ja hankalinta sosai.
“Handsome guy,” ta ce a zuciyarta, tana dannawa like.
Sannan ta shiga DM, ta sanya "Hot man 🔥"
Ta fita daga shafin, tana dan murmushi kaɗan. Ba dariya bane, murmushin wace ta san me take yi, amma har yanzu tana jin nauyin zuciyarta. “Sosai As'ad yana sona. Amma yanzu fa, ya zama wani irin mutum mai tausayin kansa da kalaman da basa motsa jiki. Kalaman soyayya da hawaye? Me zasu canja?” Ta ɗauki jakarta Gucci, ta ajiye a kusa da kujerar window. Tana son fita, amma ba inda take so ta je. Paris na motsi a waje, amma zuciyarta na cikewa da shakku.
Ta girgiza kai. Wannan kalmomi suna da daɗi, amma “Ni kuma fa? Shin ina da haƙƙin jin daɗi? Ko dole ne in zauna ina jiran shi ya murmure ne?” Ta tashi, ta nufi mirrow. Tana kallon fuskarta, wacce take cike da kyau, amma idanunta cike da fargaba. Tana son a ce ta daure, amma zuciyarta na faɗin abu biyu “Jira.” Da kuma “Bari.” A waje, iska ta fara ƙaruwa. Clouds sun rufe hasken rana. Tana ji kamar Paris ma na jin abinda ke cikinta. Ta koma ta zauna. Ta ɗauki wayarta, ta shiga chat ɗin As’ad, ta duba message dinsa na karshe “Ina fatan kin ci abinci. Ina jin ki kullum.” Ta rubuta “Na ci.”
Sannan ta ɗora da“Kana tunanin wannan ya isa?” Ta ajiye wayar, bata danna send ba.
Ta rufe ido. Idanuwanta sun cika da hawaye, amma ba sa gangarowa. Sai zuciyarta take rawa. “Akwai lokacin da soyayya ke gina mace. Amma akwai lokacin da zata iya karyata ta. Na san bana mugunta, amma ni mace ce. Ina da jiki. Ina da zuciya. Kuma ina da burina.” Sai ta danyi shiru. Kamar tana sauraron zuciyarta tana yanke shawara. A hankali, ta sake buɗe wayar. Sai ta koma message ɗin da bata tura ba... ta share shi.
*************
MOROCCO
A Morocco, cikin wani katafaren ginin da aka lulluɓe da gilashi mai kyalli, zaune suke a babban ofis wanda aka tanadar don tarurrukan manyan attajirai.
Abokan As’ad kusan goma ne, kowa sanye da kaya masu alfarma, wasu cikin suit, wasu cikin babban riga na gida, dukkan su masu kamfanoni, kadarori, da sunaye a cikin manyan jaridu na duniya.
Sun zauna cikin ɗakin taro mai sanyi, yana ɗauke da kujera na fata, gilashi da coffee tables masu tsari. A tsakiyar tebur akwai kayan ciye-ciye na musamman daga Marakeshalmond-stuffed dates, saffron tea, da pistachio rolls.
Hira ta kaure. Sai dariya take tashi lokaci-lokaci. Abubuwan da ke gudana sun shafi mata.
Wani daga cikin su Alhaji Muqaddam mai shagunan zinariya a Istanbul, ya ce yana dariya "Wallahi mace sai godiya idan tanada matsala. A gida sai koke-koke. Kai! Shi yasa na karo aure kawai. Kamar famfo ne in ɗaya ta ƙafe, ɗaya tana aiki."
Daga can, wani ya ce "Kai, ba kai kaɗai ba. Wato matata kamar gwamnati ce. Yanzu nake shirin tura ta Ghana kawai ta huta a can." Dukansu suka sa dariya.
As’ad kuwa yana zaune a gefe guda, yana dannawa wayarsa. Sai dai ya ɗago kai lokacin da Alhaji Salisbury, abokin kasuwancinsa, ya tabo kafadarsa. "Kai, Young Billionaire! Ka yi shiru ma. Kowa yana tofa albarkacin bakinsa akan mata, kai ka ƙi cewa komai."
Dukkan su suka dubi As’ad. Ya ɗago kansa, yana sanye da kayan Versace, wristwatch ɗin Cartier yana sheƙi a hannunsa. Sai yayi murmushi irin nasa mai taushi da ƙima. "Me zan ce? Ni ban da korafi." Wani daga cikin su ya ce "Kai ba korafi? " As’ad ya sosa gemunsa, sannan yace "I have the best wife in this world. Wallahi idan zan roƙi Allah, sai in ce ya ƙashe mu tare. Mutashi tare, rayuwa tare. Ayshatu is the best woman I ever met."
Suka kalli juna. Wasu sun yi dariya, wasu suka girgiza kai da mamaki.
Wani ya ce "Kai abokina, wacce irin giya kauna ka sha haka? Matar da aka baka ba mai martaba ne yabaka ba? Kai fa har yanzu baka gane menene soyayya ba!"
As’ad ya dan lumshe ido, yana murmushi kamar wanda ya gama addu’a. "Kuna kallon ita mace ce da kyau da hankali. Amma wallahi Ayshatu itace salama ta. Da ita nake samun natsuwa. Ba sai na ce komai ba, zata ji abinda zuciyata ke so. Ina ganinta kamar wata zuma ce da Allah ya ajiye a duniya saboda ni."
Salisbury ya kwantar da kai. "Kai As’ad, ni dai kam sai na ce Allah ya tsare wannan soyayya. Saboda kalamanka ba na kasuwa ba ne. Na zuciya ne."
As’ad ya gyara zama. "Ina da komai kadarori, jirgi, har kamfanin crypto. Amma wallahi ban jin daɗin komai idan Aysha ba ta cikin farin ciki. Idan ta yi dariya, ina jin kamar kasuwanci ya ci riba kashi dari. Idan ta yi shiru, duk ginin da na tara, sai ya zama duhu."
Daya daga cikin su ya ce da mamaki "Kana nufin da gaske, baka taɓa tunanin wata mace ba bayan ta?" As’ad ya dan yi shiru. Sannan ya ce "Ina za ka kai zuciyar da tuni ka bar a hannun wani? Ko da mace ta fi ta kyau, ta fi ta jiki, ta fi ta ilimi ba zata iya gina abinda muka gina ba. Aysha ba matar gado bace. Ita matar rayuwa ce." Salisbury ya ce, “Kai, kai da ka zama Sheikh Romeo.”
Suka sake dariya, amma wasu daga ciki sai suka saki jiki da tunani. "Ni dai Allah ya bani irin zaman lafiyar da ka ke da ita," wani daga cikinsu ya faɗa a hankali.
As’ad ya ɗauki wayarsa, ya kalli hoton Aysha wanda suka ɗauka tare a lokacin da suke tafiya Spain. Tana sanye da farin hijabi, tana murmushi. Wannan hoton ke masa kwanciyar hankali fiye da signature din banki.Ya ajiye wayar, ya sha ɗan saffron tea ɗinsa.Sannan yace cikin nutsuwa "Ba laifi bane mace ta buƙaci soyayya. Amma laifi ne mu manta cewa su ma mutane ne. Idan mutum yana so a girmama kasuwancinsa, ya fara da girmama macensa. Saboda mace da bata farin ciki ba zata yarda ta rike gidanka ba." Dukkan su suka yi shiru. Wannan kalaman ba na kowane attajiri bane. Kalaman mutumin da ya gano sirrin rayuwa ne.
*******************************
Nana hadiza
09030569336ƘADDARAR RAMLAH
SHAFI NA HAMSIN DA HUDU
Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!
Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!
Domin biyan kuɗi:
Acc Name: Bilkisu Sani Kaura
Acc Number: 7040402435 (OPAY)
Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:
09030569336 ko 07040402435
Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a
Arewabook @nanadiso10
https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693
********
Na dauki sati biyu ina jinya a asibiti. Ciwon ya kama ni sosai har sai da aka ƙara saka min jini. Likitoci sun yi min gwaje-gwaje da yawa domin su gano abin da ke damuna. Sun kara bani wasu magunguna masu ƙarfi, suka ce in huta sosai. Amma duk da haka, jikina na kara ramewa. Na rasa ƙwari. Ciwon kai da gajiya sun zame min tamkar abokan zama.
Mumy kam, bata ji daɗin hakan ba. Kullum cikin masifa take cewa ta gaji da wannan jinyar. Bata damu da halin da nake ciki ba. Duk lokacin da ta zo asibiti, sai ta yamutsa fuska, ta ce, "Ke ba kya gajiya da kwance ne? Me yasa ba za ki warke ki dawo gida ki yi aiki ba?"
Nakan juya gefe kawai, ban ce komai ba. Ban san me yasa ta ke ganin kamar ciwon nan da nake yi da wasa ne.
Yanzu kwana biyu kenan da aka sallame ni daga asibiti. Amma har yanzu jikina babu ƙwari. Ina jin gajiya ko da ban yi komai ba. Duk jikina kamar an daddage shi. Da na hau gado, sai na kasa tashi da wuri. Nakan kwanta har rana tana fitowa.
Ranar da muka dawo gida, Abba ya ce wa mumy, "Yakamata Billy ta dinga gyara gida, ko kuma ku samo yar aiki."
Mumy ta amsa da cewa,
"To, ai Billy taje gidan ya Abbas ne. Can take yanzu."
Bayan kwana biyu, Abba bai ga Billy ba. Yacewa mumy me isa baya ganin bilkisu ina tashiga mumy takara cemasa ai tana gidan yaya abbas ne shiyasa bai ganta ba har yanzu. Sai yakira ya abbas ya rufeshi da faɗs akan ya tabbatar Bilkisu tadawo sai yace masa ai bama tazo gidan ba nan ne fa yadinga faɗa yakirata yace maza taxo ko datazo sai tayi masa karya tace masa ai tana gidan anty luba ne ai kuwa yadinga faɗa,
"Ke ki fidda miji. Auren zanyi miki idan bazaki iya samowa ba Ni zan samo miki miji."
Wannan abu ya yaɓakantawa mumy rai sosai.
Na shiga cikin dakina na kwanta. Ban da ƙarfi balle in ce zan fita ko in yi aiki. Ciwon kai bai bar ni ba, jikina kuma sai zufa yake kamar wanda ya sha gudu.
Da sassafe, ina cikin bacci, sai na ji wani abu mai sanyi ya zubo min a kai. Na farka da firgita. Na ga mumy ce ta zubamin ruwan sanyi daga cikin fridge. Na ɗaga kai cikin mamaki na ce,
"Mumy me nayi?"
Ta ce,
"Tashi ki gyara gida! Ina gaji da kallon ki kawai kina kwance naga kin warke kokuma jakar uwarki ce ni da zan dinga yimiki girki da aiki?"
Na ce mata,
"Kaina ciwo yake yi... Wallahi bazan iya ba."
Sai ta hau masifa. Tana cewa ni ban da amfani. Tana zagi na, tana cewa ni ba zan taɓa zama abin kirki ba. Na tsayar da hawaye na da ƙyar, amma zuciyata tana kuka sosai. Wani lokacin nakan tambayi kaina Shin me nayi wa mumy? Me ya sa take ƙin na haka?
Daman munada lecture da safe. Na san ba ni da ƙwari, amma na fi son na fita fiye da na zauna a gidan da za a ci min mutunci.
Sai Maryam, kawata ta, ta zo ta zauna kusa da ni. Ta kalle ni da kulawa ta ce,
"Ke lafiya? Kin rame fa. Yajikin naki nazo gidanku ai masu gadi sukacemun kina asubuti kuma mamanku na can kinganki kuwa kamar ba ke ba."
Na so in fashe da kuka, amma na ɗan daure. Na ce mata,
"Zan faɗa miki... Amma ba yanzu ba."
Ta dafa kafadata ta ce,
"Ni ina tare da ke, ko me ke damunki. Kar kiyi kasa da addu'a ramlah Allah yana jinmu yana ganin komai."
Na juya gefe, hawayena gangarowa a hankali. Wannan kalaman nata sun shige min zuciya.. A wannan lokacin na fara jin sauƙi kadan. Ko da kuwa jikina yana rauni, amma zuciyata ta samu sauƙi saboda akwai wanda ya damu da halin da nake ciki.
******
Washegari da safe, na farka da ƙarfin jiki. Bayan jinyar da na sha a asibiti, yau ce rana ta farko da na tashi ina jin natsuwa da ƙarfi kadan. Na shirya na ɗebo jakata, na saka hijabi, na fita makaranta da sauri. Gobe za mu fara exam, kuma yau muna da lecture na “Public Policy” daya daga cikin muhimman darussa da muke dashi a cikin Public Administration.
A hanya, zuciyata tana tafasa da tunani. Na sha wahala a gida. Amma makaranta ce kadai wurin da nake jin kwanciyar hankali. A can ba mumy, ba masifa, ba faɗa.
Da na isa makaranta, na samu Maryam a wajen da muka saba zama ƙarƙashin bishiyar mangwaro kusa da theater 2. Tuni tana karatu. Na zauna a kusa da ita, ta ce,
“Ramlah yau kin yi kyau. Yau jikin na ki ya samu lafiya kenan?”
Na murmusa kadan. Na ce,
“Eh, jiya na dan huta sosai. Gobe fa exam... dole in dage.”
Maryam ta bude littafinta, ta ce,
“To, yau zan koya miki summary ɗin ‘Decision Making Models’ da malam ya koyar lokacin da baki zo ba.”
Na kafe ido ina saurare. Ta fara bayani kamar malama. Ta ce
“Kin san akwai Rational Model, Incremental Model, da Garbage Can Model. Wannan su ake amfani da su wajen yanke shawara a ofisoshin gwamnati ko ma'aikatu.”
Na rubuta a cikin not dina, ina jin dadin yadda karatun ke shiga min sauƙi. Karatun Public Administration ba sauƙi ba ne, amma idan kina da wanda ke taimaka miki kamar Maryam, sai ki ji kamar komai yana yiwuwa.
Malam Lawal ya shigo da class ɗin “Administrative Theories”. Ya fara magana cikin salo mai natsuwa. Ya ce:
“Za mu fara da Theory of Bureaucracy na Max Weber. Kowa ya buɗe shafi na 45.”
Na buɗe shafina. Duk abin da yake faɗa, ina rubutawa. Sai na lura da wani sabon nutsuwa a raina. Duk da ciwon da na sha da halin gida, yanzu ina jin kamar na dawo cikin duniya. Na dawo Ramlah da nake so mai burin ta zama mace mai ƙarfi a gwamnati.
Bayan lecture, muka fita waje da Maryam. Tana dariya tana cewa
“Ramlah, idan kika zama Permanent Secretary sai ki tuna da ni!”
Na ce,
“In dai kika ci gaba da koya min haka, sai na sa ki Chief of Staff!”
Mu kayi dariya sosai. A irin wannan dariyar nake jin dadi araina. A hostel, na zauna da littafina. Ina nazarin abinda muka yi a rana
Public Choice Theory,Bureaucratic Politics
Fiscal Federalism, Na daina jin rauni. Ina ji a zuciyata cewa wannan karatu na da ma’ana. Ina so in gama in samu aiki a ma'aikatar kula da jin dadin al'umma. In taimaka wa matasa, in bude shafi sabo a rayuwar mutane masu rauni kamar yadda ni nake ji yanzu.
Da daddare, na lumshe idona. Na yi addu’a. Na ce “Ya Allah, ka bani lafiya da ƙarfi. Ka taimaka min in gama karatu, in canza rayuwata. Ka bani damar zama abin alfahari.”
Idan nace bana cikin damuwa ko tunanin Khalil, wallahi nayi karya. Kusan kullum sai ya fado min a rai. Ina kwance nake ji kamar yana kirana da murmushin sa. Sau da dama nakan so in tashi in tafi gidan su kawai in ga babansa in ce, inyi masa gaisuwa" Amma duk lokacin da nayi niyar zuwa sai tsoron wulakanci ya rufe ni kada Maman khalil ta koroni.
Na san mamansa ba za ta iya yi min dariya ba. Yanuwansa kuwa? Ina jin kamar ba zan iya jure kallonsu ba. Allah sarki Khalil. Masoyi na kirki. Yayi mini abubuwa da ba zan iya mantawa da su ba. Amma yanzu... komai ya zama tahiri. Soyayyar da ta cika zuciyata, yanzu ta zama ciwo. Kullum idan na tuna da shi, sai na ji wani abu kamar bargo mai sanyi ya rufe ni... amma da ƙaya.
Yau lecture ɗin da muka yi ya matuƙar gajiyar da ni. Ina isa gida na tarar da hayaniya. Kafin in karasa parlour, sai na hango Abba yana tsaye Yana faɗa da karfi, fuskarsa cike da fushi. Yana yi wa Yaya Bilkisu masifa sosai.
Yana cewa "Ki fidda miji Bilkisu! Bazaki cigaba da yawo a ba! Na gaya miki sau nawa? Wallahi ba zan sake jurewa ba. Nace ki zo office dina kiyi aiki aa! Sai yawon banza kike! Ko to, bazan yarda ba!"
A cikin zafin zuciya, ya ɗaga hannu ya mareta. Na tsaya cak! Bilkisu ta zube tana kuka. Mumy tana gefensa, tana ƙoƙarin kwantar masa da hankali.
"Don Allah... ka yi hakuri. Ta dai shiga mawuyacin hali ne. Ka ba ta dama," in ji Mumy tana tsaye
Ni kuma, ba ni da abin cewa. Na kalli Bilkisu tana kuka, sai zuciyata ta cika.nashige dakina nakwata kawai nasan wannan fadan da akayi mata mumy zataso ni akayiwa Sai gashi halin yaya Billy yanata fitowa ana gani.
*****************
Nana hadiza
09030569336ƘADDARAR RAMLAH
SHAFI NA HAMSIN DA BIYAR
Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!
Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!
Domin biyan kuɗi:
Acc Name: Bilkisu Sani Kaura
Acc Number: 7040402435 (OPAY)
Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:
09030569336 ko 07040402435
Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a
Arewabook @nanadiso10
https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693
********
Yau wata rana ce mai sanyi a cikin birnin Paris. Iskar garin tana busowa da ƙamshi mai daɗi daga Jardin des Tuileries, kyakkyawan lambu da ke tsakiyar birnin. Rana na haskakawa, amma sanyi yana ratsawa da laushi mai sanyaya zuciya.
A cikin wani katafaren gida mai hawa huɗu da ke kusa da Champs-Élysées, wata mata ta tashi daga barci a cikin gado lallausa Ita ce Ayshatu mace mai shekaru 34, mai fata kamar madara, cikakkiyar mace mai kudi, kyau, da sirrin rayuwa. Tana cikin fitattun matan da kafafen sada zumunta ke magana a kansu.
Da ta buɗe idanunta, ba bacci ne ya isheta ba, sai wani irin nauyin zuciya da ba ta iya fassara. Duk da komai na duniya tana da shi, akwai abinda zuciyarta ke nema, kuma wannan abun ba komai bane face namiji. Namiji wanda zai cika wannan giɓin da dukiya ba ta iya rufe wa.
“Sha’awata yanzu tafi yadda take lokacin da nake ‘yar shekara ashirin da bakwai,” ta faɗa da ƙasa da murya, tana kallon hasken da ke ratsowa daga Eiffel Tower. “Sun fa ce mace tafi buƙatar namiji daga shekara talatin... yanzu na fahimta.”