Kenza eBookz

Kaddarar ramlah book 1 complete - Chapter 31

Kaddarar ramlah book 1 complete - Chapter 31

Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 31: Kaddarar ramlah book 1 complete Chapter 31. Wasu 'yan daba daga kauyen makwabta sun shigo sun buge wani…

4,474 words

Wasu 'yan daba daga kauyen makwabta sun shigo sun buge wani dattijo, wai saboda ya tsallake hanyar su a kasuwa. Gaba ɗaya jama’ar garin suka rude.

Na fito na tsaya bakin ƙofa ina kallon hayaniyar da ke tashi. Sai ga su Aliyu da wasu 'yan daba guda biyu suka nufi gidanmu da masifa. Na ja baya cikin tsoro.

“Bashari... ka bamu shawara jiya! Yanzu fa su suna jin kana tare da mu!”

Na jiyo Aliyu yana ihu.

Bashari ya fito rike da farin riga a hannu yana fadin,

“Dallah ku rufemun baki Ina kokarin gyara rayuwata. Banason tashin hankali yanzu. Ku tafi.”

Sai Aliyu yayi dariya mai ban tsoro, “Kaji Bashari! Wanda muke ɗauka uban yan daba! Kamar yadda muka zaburarka lokacin da babu kowa, to yanzu ba mu buƙatarka.”

Kafin su juya, sai daya daga cikinsu ya buge kofar gidanmu da sanda. Ina tsaye gefe da kwanon shara a hannu, numfashina na karanci, zuciyata na bugawa da karfi.

Bashari ya tsaya cak, yana kallon kofar. Na leƙa gefe na ce masa,

“Dan Allah kada ka yarda su jawo ka baya. Ka tuna da maganar mu. Ka tuna da yadda kake son canzawa...”

Sai ya juya ya kalle ni.

Wallahi kallon da ya yi min a lokacin, ya bayyana cewa zuciyarsa na cikin ruɗani. Amma sai ya dafe kansa da hannaye biyu, ya rufe ido ya furta,

“Allahu Akbar… Ya Allah Ka ba ni ƙarfin zuciya.”

Na matso na riƙe hannunsa cikin sanyi, nace

“Zaka iya, Bashari. Ka tuna da abinda kake faɗa min.”

Sai ya sauke ajiyar zuciya, ya ce

“Ramlah… idan har zan tsira daga wannan hali, Sai na dage, sai na zama wani.”

Bayan kowa ya watse, sai muka zauna a cikin dakinmu. Ya juyo yana kallona.

“Na gode da kika tsaya tare da ni.”

Na girgiza kai nace

“Ni dai ina so ka canza. Ka zama wanda zaka iya tsayawa da kansa.”

Sai ya kama hannuna, yace

“Ni kuma ina so ki zama matar da zata nuna min cewa har mazan da aka watsar da su za su iya komawa mutane.”

Na lumshe ido cikin shiru. Amma zuciyata sai bugawa take da sabuwar ƙauna, sabuwar fatan rayuwa.

Kwana biyu kenan Bashari na yawan zuwa birni. Ranar Laraba da daddare, nayi mana danwake da daddawa sai kawai na ji “Assalamu alaikum” daga ƙofar gida. Ashe Bashari ne. Ada shigowarsa ba sallama, amma yau sai da murya mai nutsuwa ya shigo da sallama, hannunsa ɗauke da ledoji na kayan miya.

Na kalle shi cikin mamaki da murmushi, nace

“Sannu da zuwa Bashari.”

Yayi murmushi, yana cewa,

“Ƴar kwalisa ta... nayi missing dinki wallahi.”

Yayi kamar zai rungume ni, nima na rungume shi a hankali kamar yadda na saba da shi yanzu. Sai yace

“Kinsan yanzu idan zan kwanta, sai nayi wanka. Na saba da tsafta saboda ke.”

Na murmusa nace

“Lallai kayi kyau.”

Sai yayi dariya ya ce

“Na gaji da zama kamar kura. Yanzu na samu mai rarrashi, mai gyara.”

Na karɓi kayan miya daga hannunsa na kai cikin kitchen. Yana zaune yana kallona da murmushi mai taɓa zuciya, har na dawo da abincinsa. Yana ci yana hirar kirki da ni ba irin hirar dan daba ba. Sai naji yana fadin

“Kamin na manta, ga wasu takardu nan.”

Na karɓa na dubasu, takardu biyu ne. Na kalleshi cikin tambaya

“Takardun me ne ne wannan?”

Sai yayi shiru kadan sannan yace

“Lokacin da zan aure ki, mahaifinki ya bani 5 million. Ya ce inyi miki jere ko kuma wani abu da zai amfaneki.

Ni kuma nace tunda ina Sanaa sosai, kuma shagunana biyu ne a birni, da kudin da nake samu da kuma ƙwazon da nake da shi, sai nayi amfani da wannan kudin na saya miki ƙaramar gida a birni.”

Na ɗaga kaina cike da mamaki ina kallonsa, sai yace

“Wannan takardar mallakar gidan ne. Gidan ki ne Ramlah. Ba hayar da za ki biya ba, sai dai ki dinga karbar haya idan kina so. Harkar gidan yana kawo kusan 1 million a shekara.”

Nayi shiru, zuciyata na bugawa, idona na cika da hawaye.

Bansan lokacin da nace masa

“Kana nufin wannan gida nawa ne? Wallahi Bashari ka bani abin da zuciyata bata taɓa tsammani ba. Allah ya saka maka da alheri.”

Ya girgiza kai yana murmushi, ya ce

“Ƴar kwalisa... wannan duk saboda ke. Daga ranar da kika ce min in gyara rayuwata, na fara hangen wani haske a cikin duhu na. Ina jin ki da zuciya.”

Na ɗan sunkuyar da kaina ina jin wani sanyi a jiki. Kalaman Bashari sun fara karade ni da wani irin soyayya da ba daga baki ke zuwa ba, daga can cikin zuciya take fitowa.

Yana kallona yana dariya yace

“Kada kiyi kuka fa. Ki murmushi. Ameen da addu’arki... Allah ya saka.”

Na daga kai na kalleshi da idanu masu sheƙi da hawaye nace masa

“Allah ya saka da alheri. Na gode.”

Ya kai hannu ya share hawayena da yatsansa, yana kallona da wani kallo da ba na daba ba, ba na barkatai ba, amma na mutumin da ke ƙoƙarin zama mafi alheri.

Cikin baccina naji ana kiran sunana cikin sanyi da murya mai rauni, kamar daga zuciya. Na ɗago idanuwana da dan tsoro, zuciyata na bugawa. Idanuna suka sauka a kan Bashari, tsaye yana kallona da idanu masu launin dare danun da suka saba da duhu, amma yau sai suke kamar suna nema su haskaka cikin duhun da ke ransa.

Sai yace cikin murya mai laushi

"Ƴar kwalisa... dan Allah in rungumeki? Wallahi bazan miki komai ba.

Nayi wanka, nayi brush, bansha taba ba... ban sha giya ba. Kawai... runguma nake nema daga gareki.

*****************

Nana hadiza

09030569336ƘADDARAR RAMLAH

SHAFI NA TAMANIN

Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!

Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!

Domin biyan kuɗi:

Acc Name: Bilkisu Sani Kaura

Acc Number: 7040402435 (OPAY)

Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:

09030569336 ko 07040402435

Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a

Arewabook @nanadiso10

https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693

********

Gabadaya hankalina ya tashi. Ban gane ko mafarki nake ba, ko kuwa wani abu mai girma ne ke shirin faruwa. Jiƙinsa yana rawa, idanuwansa kuwa sun canza launi daga irin yadda na saba ganinsu zuwa wani, kalar gaba daya jiƙinsa rawa yakeyi.

Ban iya cewa komai ba. Kawai sai na ji ya rungume ni da ƙarfi, kamar wanda zai fasa ni saboda yadda zuciyarsa ke bugawa. Na ji numfashinsa masu zafi, masu nauyi suna saukowa a wuyana da kafadata, suna tafiya cikin fata ta tamkar wuta. Wani shock ya ratsa ni tun daga kaina har ƙafata. Na kasa motsi. Na kasa magana. Amma zuciyata na harbawa da wani irin yanayi da ban taɓa sanin yana cikina ba. Wani abu ne daban, ban sanshi ba ban taɓa jinsa ba sai yau tsigar Jikina tashiga Amsawa sosai Yanayin da har kwallah sai da naji ta cikamun idanuwa na.

Kafin na gama mamaki, sai na ji bakinsa a fuskata. Sumbatar da ba zan iya kwatanta ta da kowacce ba. Ba sumbatar da za ka iya ce "so kawai" ba a’a, sumbatar da ta shige hanu, ta shige ido, ta shige zuciya. Ta tsaya a tunani kamar ana ƙoƙarin rubuta wani sabon labari a jikina. Sumbatar da ta motsa wani irin kuka daga cikin raina kuka mai nauyin gaskiya da tsoro da soyayya da ƙauna. Sai na fashe da kuka. Kuka mai sauti, mai daci, amma kuma mai natsuwa.

Yayi shiru. Sai na ji ya dakata. Amma yana ta harhada kalmomi da bakin da ke rawar jiki.

“Na bari… na bari… amma ina so, dan Allah.”

Ya faɗa da wata irin murya mai nutsuwa, irin wadda ko a mafarki bai taɓa yi min da ita ba. Muryar da ta gama karya rigar zuciyata.

Na dago kaina na kalleshi. Idanunsa har yanzu suna da wannan yanayin da na gani a da, amma yanzu suna cike da hawaye hawaye da ke zawarci ba da karfi ba. Ya kama hannuna. Hannunsa yana rawa sosai, amma kuma yana da dumi.

“Me kake nufi?” Na tambaya a hankali, kamar wata murya daga cikin ni'imar da ke yawo a jiki na.

Ya kalle ni, sannan ya saki wani irin numfashi. “Na tsaya. Na tsaya saboda ban san ko zan iya dawowa ba idan na ci gaba. Amma bazan iya ɓoye ba ina jin ki fiye da yadda ya kamata. Ba ina son ki ne kawai ba. Ina jin kamar idan ban ce miki ba, zan mutu gaba daya jikina ya saƙe ƴar kwalisa muradinki yakeyi.”

Na rasa me zan ce. Kalmomin sa sun shige kaina, sun shiga zuciyata kamar wani ƙarfi da ke zuga wuta. Na ji kamar ni ma na shiga wani hali. Ba son rai ba. Ba wahala ba. Ba jin daɗi kawai ba. Wani abu daban ne cikakken ɓacewa a cikin wani wanda ya karanta jikin ka fiye da ka karanta kanka.

Ya matsa kusa, yana kallon kaina, kamar yana jiran izini daga wata duniya. Idanunsa sun dawo kamar yadda na saba daidai, masu haske, masu ban tausayi. Yana fadin

“Kiyi min afuwa idan na wuce gona da iri. Amma bana neman gafara ne saboda kuskure, bana neman yafiya saboda jin haushin kai ba bani da haushi, bani da hujja, sai dai gaskiya. Ina so ki sani cewa tun ranar da na fara kallon ki da zuciyata…”

Wani irin sanyi da dumi suka gauraya a kirjina. Na kasa hana hawaye zuba. Kuka na ya dawo, amma wannan karon kuka ne na fahimta. Na fahimci kaina, na fahimce shi.

Ya ɗora kaina a kirjinsa. Numfashin sa har yanzu yana nan sama masa mai nauyi. Amma wannan karon na ji dumin sa kamar garkuwa. Na ji kamar a cikin duminsa akwai amsa ga tambayoyin da na taɓa yi wa kaina ba tare da furta su ba.

Muka zauna haka na wani lokaci, babu wanda ya ce komai. Sai jikinmu ke magana, sai numfashinmu ke musayar zance. Sai zuciyoyinmu ke faɗin kalmomin da bakunanmu suka kasa furtawa.

“Idan kika ce min mu tsaya anan, zan tsaya,” ya ce cikin sanyi. “Amma idan kika ce min mu ci gaba, ba zan taɓa ja da baya ba. Zan tsaya tare da ke har karshe.”

Sai na dafe hannunsa, na ce

“Ka tsaya.”

Bansan lokacin da bacci ya dauke ni ba, amma kafin hakan, sauke ajiyar zuciya kawai nake, ina jin motsinsa a jikina. Numfashinsa mai zafi da nauyi yana bugawa gefen wuyana kamar yana karantar zuciyata ne, yana sauke wani salo da ke tayar min da dukkan tsigar jikina. Sai dai haka bacci ya saceni, cikin nutsuwa, zuciya cike da mamaki da tausayi.

Da safe farkawa nayi a hankali, idanuna sun fara bude ido ne akan shi. Na hangoshi zaune a gefen gado, yana karatun Alkur’ani. Wannan abu ya bani mamaki sosai, har na tashi nayi alwala nayi sallah. Bayan na dawo, na karasa kujerar da yake zaune a kai, nace da shi da fara’a, “Ina kwana?”

Ya juyo da murmushi mai cike da nutsuwa, sai ya sumbaceni kadan sannan yace, “Zan fita yanzu, ƴar kwalisa. Zan tafi birni. Ki rubuto min abubuwan da kike bukata, zan siyo miki inna dawo.”

Na tsaya da mamaki ina kallonsa, sai na dauki takarda da biro na rubuta masa jerin abubuwan da nake so. Na mikamasa, sannan na dafa kafadarsa nace, “Allah ya dawo da kai lafiya.”

Ya juya yana saka takalmansa, sai nace masa da tausasawa, “Yaya Bashari, dan Allah kadaina tafiyar nan ashagiɗe.”

Ya tsaya ya juyo, kallon tausayi ya saukar min da shi, sannan yace da wata murya mai natsuwa, “Sai a hankali ƴar kwalisa. Zan rage, insha Allah. Ki kara hakuri, kinji? Yar albarka .”

Sai ya juya ya fita, yana cewa “Bari naje, yau bana son kwana a can, yau nakeson dawowa.” Na bi bayansa da addu’a, “Allah ya kiyaye hanya.”

Bayan ya fita...

Na dauki tsintsiya, na gyara gidan tsaf. Na dora ruwa, nayi shayi, nasha da ragowar bread din da ya kawo jiya. Ina gamawa wayata ta fara ringing. Maryam ce, na daga da fara’a. Mun sha hira sosai, tana cewa

“Wallahi Ramlah, duk mijin da Allah ya bani yanzu, hannu biyu zan rikeshi. Mazan nan yanzu ba su san darajar aure ba, son lalata kawai suke. Kin ga dama Allah yayi ki da miji kamar Bashari da ke kokarin canzawa ki rikesa da gaske.”

Na yi dariya, na ce mata, “Ai hakane Maryam, komai sai da hakuri.”

Bayan mun gaisa sosai, sai mukayi sallama. Nace bari in kira Mumy ko zata daga. Na sake kira, sai naga blocked. Hatta wayar Abba ba a daga. Wannan abu ya sosa min rai sosai, sai na daure zuciya naceTo ba komai, Allah ya fi komai. Zan ci gaba da hakuri da addu’a. Lokaci zai nuna komai.”

Na ajiye wayar a gefe, na shafa fuska da ruwa, zuciyata cike da tausayi da fatan alheri.

Daga can sai naji an buga ƙyaurena. A firgice na tashi, na nufi ƙofar. Da na buɗe, sai ga Babah ce tsaye da farar hijabinta, tana kallona da wayam.

Nace mata, “Sannu da zuwa Babah,” tana shigowa cikin ɗaki na kawo mata ruwa, muka gaisa da dan sakin fuska, koda kuwa na lura da kallon bincike a idanunta.

Sai tace min, “Ramlatu, naji kwana biyu Bashari bai buge ki ba. Kamar ma baya gidan?.”

Na dan tsaya, zuciyata ta bugawa da ƙarfi. Mamakin tambayarta ya girgiza ni, amma da kyar na danne kuma na ƙirƙiro murmushin karya nace,

“In shaa Allahu Babah, ai yanzu ya shiryu. Wallahi har shaye-shaye ya bari, yana kokarin gyara kansa.”

Sai ta gyara zama tana fadin, “Inji uban wa? Dan shaye-shaye yana daina wa? Shi ne yazo yayi miki karya kin amince? To ai karya yake miki .”

Mamaki ya sake kamani. Baki na na kasa rufewa, na kasa amsawa kai tsaye.

*****************

Nana hadiza

09030569336ƘADDARAR RAMLAH

SHAFI NA TAMANIN DA DAYA

Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!

Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!

Domin biyan kuɗi:

Acc Name: Bilkisu Sani Kaura

Acc Number: 7040402435 (OPAY)

Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:

09030569336 ko 07040402435

Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a

Arewabook @nanadiso10

https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693

********

Ke yarinya ce, ba lallai ki fahimci abinda nake nufi ba yanzu, amma bari na faɗa miki gaskiya, wayagamiki dan shaye-shaye ba abokin amana ne, makaryata ne, ko da ya ce ya daina, kada ki gaskata shi, domin babu wani shiryuwar gaske da suke yi, kalmomin Babah kenan, matar da kullum ke shigowa cikin gidana da sallama da nasiha, tana bani hakuri, tana ce min in dage da addu’a saboda mijina zai sauya, itace yau a zaune take kallona tana furta kalmomin da suka fi kowane zafi a gare ni, ita ce yau take fadar zancen da zai iya fasa min zuciya da hawaye saboda kawai nace mata Bashari yafara shiryuwa Nakasa rike takaicin dake zuciyata nace mata"Babah, wallahi Bashari ya daina shaye-shaye,” daga nan kuma sai zuciyarta ta canza, sai magana ta koma daga fatan alheri zuwa zargi, daga tausayi zuwa gaba, daga kulawa zuwa cin mutunci, kai wannan duniya ba a gane mai kaunar mutum, wallahi tamkar a mafarki nake, ban san yadda zan fassara wannan sauyi daga mutum ɗaya ba, sai kawai na ji wani zafi a zuciyata, kamar ana watsamin garwashi, nayi shiru ina kallonta.

Sai ta ce “To banda abunki yarinya, ni ba ni ce nake gaya miki kullum ki dage da addu’a ba? Na ce maki zai canza ? To me yasa yanzu kike kokarin kare shi? Wannan ai ba addu’a bace, wannan ruɗi ne,” ni kuwa na kasa rike bakina, sai nace mata da damuwa, “Babah, dan Allah ki fahimce ni, me yasa a duk lokacin da aka nuna alamun canji sai a fara masa zargi? Kin fa san yadda Bashari ya ke da halin rashin mutunci, amma yanzu yana ƙoƙari, kin dai sha ganinsa yana zama da Qur’ani yana karatu ko? To me yasa sai kike ganin duk wannan wasa ne?” amma ina, kamar ta ƙi jin kowace kalma tawa, kamar kalmomi na na fita ne daga kunnen da ba ya ji, ta kalle ni da fuska ba yabo ba fallasa tace

“Ni na gaya miki gaskiya, ba zai yiwu ba Habu ya sake shigowa wannan gidan, Na tsorata kar Bashari ya koya masa shaye-shaye. ni bana so habu ya koya halaye marasa kyau daga wajen ɗan daba, ki dinga aikinki da kanki, ki dinga girki da kanki, abinci kuma ai ba zai rasa ba agurina, tun kafin ki zo ni ke basa,” sai naji zuciyata ta karye gaba ɗaya, ba don komai ba, sai domin irin yadda kalamanta suka juyamin komai, matar da ke bani hakuri kullum, tana gaya min in dage da addu’a, yau ita ce ke min kallon wadda ke kare ɗan daba, sai kawai nayi murmushi cike da takaici nace da kwantar da murya

“Ai hakan da kika yi Babah nagode, Allah ya saka da alkhairi, Habu kuwa Allah ya rayashi,” tana kallona da idon da babu wata alamar juyayi sai ta juya da sallama Ta daka tsaki kadan, tace:“To madallah sai anjima”.

Tana barin gidan zuciyata kamar zata fashe, sai naji duniya tayi min kama da wata matsatsiyar ƙasa da nake tsaye a cikinta, na juya na shiga daki ina jin kamar na fashe da kuka, amma sai na runtse idanuwa na, na kalli sama cikin zuciya nace “Ya Allah, kai kadai ka san abin da ke cikin raina, kai ka fi kowa sanin zuciyar wanda ke ƙoƙarin sauyawa, idan da gaske Bashari yana neman gyara, ka ba shi ikon hakan, idan kuma da zambo ya ke, kai kadai ne shari’a, ka hukunta shi bisa gaskiya,” daga nan na sauke numfashi, na zauna ina tunani, me yasa ake jin tsoron canjin mutum? Me yasa mutane basa yarda da sabon shafi? Me yasa ake cigaba da ƙyamar mutum duk da cewa yana neman barin duhu? Zuciyata cike take da tambayoyi, amma babu wanda zai bani amsarsu sai Allah.

Ina cikin zurfin tunani da nauyin zuciya, wayata tayi kara. Numba ce ban sanshi ba, amma saboda yadda zuciyata ke bugawa, sai na daga. Amma kafin na iya cewa komai, naji muryarsa “ƴar kwalisa...”

Na danne wani abu mai nauyi a ƙirjina, nace da sanyi, “Baka yi sallama ba.” Sai naji yace, “Afuwan tawa... ya gidan?” Amma saboda takaicin da nake ciki, musamman kalaman Babah da suka tsaya a zuciyata, sai kawai na kashe wayar kai tsaye.

Ina jefar da wayar gefe, sai wani kuka ya kufce min kamar wanda aka yanka da wuka. Ko shakka babu, kalaman Babah sun fara ratsa zuciyata sun fara barazana ga irin tunanin da nake dashi game da Bashari.

Ina zaune, zuciyata cike da ɓacin rai da ruɗani, na duba wayata ya kirani fiye da sau ashirin. Amma duk da haka, ban ɗaga ba. Ba don bana son jin muryarsa ba, sai dai bana bukatar jin wannan muryar tashi yanzu muryar da take neman rushe ƙoƙarin da zuciyata ke yi don ta fahimta.

Wani irin bakin ciki ne ya taso min tamkar toka a wuyana ya toshe zuciyata ya hana ni numfashi. Bansan sanda na ɗauki mayafi ba, jikina kamar ba nawa ba. Kai tsaye na nufi gidan Uwani, aminiyar Malam Zakari, domin in nemi nutsuwa, ko sauƙin zuciya. Amma a maimakon haka, na tsinci kaina cikin wani sabon rikici.

Na yi sallama ina shigowa, muka gaisa. Tana ta murmushi irin na wayo, can sai ta kalle ni da idon tuhuma tace

“Ƴar birni, me ke haɗaki da munafukar matar gefen gidanku?”

Na zaro ido cike da mamaki, nace, “Wacece? Babah? Kakar Habu?”

Ta gyada kai tana dariyar gulma.

“Eh ita mana. Tsohuwar hegiya ce ai. Ni dama nace wa Malam, wallahi ita ba ‘yar kirki bace. Wai fa tana yawo da ke a kauyen nan, wai kuna saka mata jika a ɗaki kuna kunna masa sigari... Ke kuma kina kallon haka kina murmushi.”

Na ji wani zafi ya ratsa ni, na kasa magana. Jikina ya dau rawa. Nace cikin muryar da ba ta da ƙarfi

“Ban gane ba Uwani… ta baya kuma? Meye hakan?”

Ta kalle ni tana wani sauke numfashi na gulma tace

“Ta baya mana… wato bashari yana bin Habu ta hanyar da bata dace ba.”

Nayi sallati cikin firgita.

“Innalillahi wa inna ilayhi raji’un! Wallahi Karya ma take yi wa Bashari. Wannan wacce irin mummunar zuciya ce haka?”

Uwani ta kara gyara zama tace

“Ai wannan kadan kika gani. Babah fa ba karamar fitina bace. Itace aminiyar matar uban Bashari. Dukkanin auren da yake yi su ke zuga matansa su rabu da shi. Sun kasance silar ɓarnatar da rayuwarsa. Ita kanta shaidaniya.”

Na rasa mai zan ce. Hankalina ya tashi kwarai. Nace a hankali

“Wallahi Bashari ba haka yake b. Kuma tsakanin Habu da Bashari babu komai gaisuwa ce kawai.”

Uwani ta tabe baki cikin raini tace ai haja tace “Ke ma ai karuwace... da haka kika auri ɗan daba. Iyaye naki sun yi miki baki. Ai in ba haka ba, ba za su aura miki shi ba.”

Kamar wuta aka kunna a zuciyata. Idanuna suka cika da hawaye. Cikin jimami da ɓacin rai na mike tsaye, ban ma yi sallama ba na fita cikin zafin zuciya da girgiza kai, kamar wata wacce aka karyar da zuciyarta.

Na dawo gida kafin magariba. Cikin damuwa da faɗuwar gaba, kasa girki nayi. Sai da na dan tattara ƙarfina sannan na dafa shinkafa fara kawai ba domin ina so ba, sai don kada ciki ya ɗaureni.

Bayan nayi sallah, na koma ɗaki. Na zauna ina dannar waya, amma babu isasshen caji da zai ba ni damar kiran kowa. Sai dai kawai na kunna game don in ɗan kwantar da hankali, kodayake tunani ya ƙi barin zuciyata.

*****************

Nana hadiza

09030569336ƘADDARAR RAMLAH

SHAFI NA TAMANIN DA BIYU

Wannan littafin kuɗi ne, ba kyauta ba!

Biya Naira 700 kacal ki karanta cikin salama!

Domin biyan kuɗi:

Acc Name: Bilkisu Sani Kaura

Acc Number: 7040402435 (OPAY)

Tura shaidar biya zuwa WhatsApp:

09030569336 ko 07040402435

Masu son vip 👇Sai ku bibiyeni a

Arewabook @nanadiso10

https://www.arewabook,vs.com/book?id=6813670d91815df57bc25693

********

Ina zaune a ɗaki, zuciyata cike da nauyi. Tunani na yawo ba tare da natsuwa ba. Cikin wannan shiru sai kawai na ji an tura kofa. Na ji murya yana sallama da cewa, "Assalamu Alaikum."

Ban ce komai ba. Sai na ji yana kirana, "Ƴar kwalisa… Ƴar kwalisa kina ina? Ina kika shiga? Fito mana."

Na ƙi magana. Raina ya ɓaci, na kasa ma kallonsa. Na ji ya ajiye kayan da ya shigo da su, sannan ya shigo cikin ɗakin ya tsaya yana kallona. Ya ce da mamaki, "Lafiya? Ina ta sallama baki amsa ba?"

Na ce da ƙasa da murya, "Ban ji ba ne shiyasa."

Bai sake cewa komai ba. Sai ya cire rigarsa, ya ɗauki tawul ya shiga bandaki. Bayan lokaci kaɗan ya fito, ya fesa turare ba irin wanda na sani ba. Ya tada sallah, ya yi cikin natsuwa, har ya gama. Ni kuma ko motsi ban yi ba, ina zaune kamar gunki.

Ya fita daga dakin. Bai dade da fita ba, sai ya dawo. Na ji yana waya yana cewa, "Aliyu ku bar su. Nifa yanzu na bar dabi'ar nan. Abin da na yi a baya Allah ya gafartamun. Ka daina binsu danAllah."

Sai ya yi tsaki ya kashe wayar.

Ya kalle ni da ido mai rauni. Ya zauna ya ce

"Ƴar kwalisa… laifin me nayi? Ki yafe min. Halina ba nan take ake gyara ba. Zaki ga zan gyaru. Na dade cikin munanan halaye. Ki cigaba da taimaka min dan Allah."

Nan da nan hawaye suka gangaro daga idona. Ba haushinsa nake ji ba, haushin maganganun da Babah ta fada ne.

Na ji ya zo ya rungume ni. Yana bani hakuri.

Sai ya tambaye ni, "Me ke faruwa? Wani ya taɓa ki ne?"

Ya ce da murya mai ƙarfi, "Magana nake miki!" Fuskar sa ta nuna fushi. Jikina ya fara rawa. Na ce da shi cikin kuka:

"Babah ce. Ga abinda ta fada…"

Bai bari na karasa ba, ya fizgeni daga jikinsa, ya miƙe cikin fushi. Na miƙe shima cikin hanzari nace, "To kenan baka sauya halinka ba kenan? Ita fa tace bazaka taba canzawa ba!"

Ya shiga ɗaki yana neman wani abu. Na biyo shi da kuka, na rungume shi daga bayansa. Na ce

"DanAllah kayi hakuri. Ka saurare ni."

Ya tsaya, ya dafe hannuna yana sauke numfashi. Ya ce

"Me nayi wa Babah da zata min haka? Wallahi ban ƙara shan komai ba. Wannan makon ma na ware kaina daga abokai. Addu'a nake yi. Ina roƙon Allah ya kare ki dani. Amma ki barni na ɗauki mataki a kanta."

Na shafa fuskarsa nace, "Kayi hakuri. Koma me tayi, kanta tayi wa. Allah yana gani. Allah yana kallon komai."

A hankali jikinsa ya lafa. Ya kalleni cikin ido. Sai ya ce da murya mai sanyi

"Bani abinci."

Na ce, "Da me nayi?"

Sai ya ce da dan murmushi, "Na siyo kaza da kayan marmari. A waje kayan suke. Ki dakko mana." Na ce masa, “To.” Sannan na mike na fita daga ɗakin. A hankali na tafi na ɗauko abincin da ya ajiye kazar da kayan marmari da ya siyo. Na dawo na aje a gabansa.

Yayi murmushi yana ce min, “Matso kusa dani ki zauna.”

Na zauna a hankali a gefensa, zuciyata tana bugawa da raɗaɗin ƙaunar da ke ƙara samuwa tsakaninmu. Yana cin kazar cikin natsuwa, sai ya ɗago ya kalle ni da ido cike da tsantsar buƙatar kulawa.

“Ƴar kwalisa, danAllah ki dinga dan nunamin kulawa… kinji?” ya faɗa cikin muryar da ba za ta gaza motsa zuciya ba.

Na ɗan saki murmushi, nace masa, “To.”

Sai ya ɗebo abinci da cokali, ya ce, “Bude bakinki.”

“To kinji,” na ce ina dariya kadan, na ɗan rufe fuska da tafin hannuna, kamar wata yarinya mai jin kunya.

“Kitaimaka mana,” ya faɗa yana kallona da idanunsa masu dumi. “Wallahi, idan na ga murmushin nan a fuskarki, wani irin dadi nake ji a zuciyata… Ƴar kwalisa.”

Haka ya cigaba da bani abincin. Shi kuwa bai ci ba. Idonsa yana kaina, hannunsa yana ciyar da ni. Sai da na fara jin nauyin bacci.

Na yi wata hamma mai nauyi, sai ya ce, “To fa, sai munyi brush ko?”

Na ce da dariya mai rauni, “To… Amma kai fa baka ci abincin ba.”

Yayi murmushi yana kallona, “Kallonki da nayi da yadda kike ci… wallahi hakan ya isheni. Na koshi da kallonki kawai. Allah ya baki albarka matata. Allah ya baki Aljanna. Kuma ya saka ki fara sona da zuciya ɗaya.”

Na lumshe idanu cikin jin daɗin kalamansa. Na saki murmushi, na gyara wurin da nake zaune, sannan nace masa, “Sai da safe.”

Na tashi na nufi ɗaki cikin nutsuwa. Na shiga na kwanta a kan gado, cikin shiru. Shi kuma ya cigaba da zama a kan kujera, inda yake kwana kullum.

A cikin duhun ɗakin, sai kalamansa ke yawo a kunne na kamar ana karanta su kai tsaye cikin zuciyata. Na juya a gefen gado, na lumshe idanu da murmushi, zuciyata cike da sabuwar fatan soyayya.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull