Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul - Chapter 125
Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 125: Ajiya a duhu book 1 & 2 complete by billyn abdul Chapter 125. .........Gaba ɗaya wajen ya…
3,354 words
.........Gaba ɗaya wajen ya rikice da kai-kawon yaran mabera. Dan danan suka shiga fito da mashina da motoci dake lulluɓe da yayin ciyawa. Harda nasu Abah guda biyu da akazo da su jiya har sun ɓoyesu shegun. Mabera da Sille sai faman kai-kawo sukeyi suma hankalinsu a masifar tashe. An gama fiddo motoci da mashina zasu fara saka su Abah kawai suka fara jiyo ƙarar jirage masu saukar angulu na tunkaro jejin. Koda suka fara dube-dube sai suka fahimci ai takowane bango ne zobe ake shirin yi musu. Mabera ya wani cije baki yana mai yarfar da hannayensa irin na ta ƙwaɓe ɗin nan. Babban yaron su ya kalli Sille da gaba ɗaya ma ya gagara cewa wani abu shi kam. “Boss mutanen nan sun riga sun cimmana fa, mafita ɗaya ce damu a yanzu da zamu iya tsira a hannunsu”. Mabera da ya kallesa da sauri yace, “Wace irin mafita ce? Kasan da mafitar amma ka zuba mana ido tun ɗazun muke neman rikita kammu!!”. “I'm sorry Sir! Nima yanzu dabara yazo min, inaga mu koma da mutanen nan cikin gida kawai. Wannan shine plan a ”. Wannan fa shine mai neman nutsewa a ruwa ko maciji aka miƙa masa zai kama a matsayin igiya domin ceton kai. Babu wanda ya tambayi minene plan b suka tattara kowa suka maida cikin gidan, suma duk suka shige suka zagayesu da bindigun. Kawai sai Mamy ta hau dariya kamar zararriya. Cikin takaici Sille yasa ƙafa ya kwasheta sai gata wanwar a ƙasa, ya ja kunamar bindigarsa kawai ya danƙara mata harbi a kan ƙafa. Zai ƙara wani Mabera ya hana... Wani irin gigitaccen ihu Mamy ta saka, hakama su AA a tare sukai shirin zabura yaran su Sille suka riƙesu. Cikin matsanancin zafin rai Sille yace, “Baa! Ka barni na kashe azzalumar na huta. Da bataje ta haifeni a titi ta yarda a bola ba da ban zama haka ba. Wlhy in har yau zan mutu a jejin nan kema anan zaki mutu wulaƙantacciyar baiwa. Ya sake ƙoƙarin gwada harbinta... “Son barta barta, ai babu abinda ya rage ma wannan sai jiran mutuwa. Amma bazata mutun ba sai waɗanda take taƙamar da su a yanzu sun san ita ɗin wacece. Ku tattara waɗan nan mutanen da basu da alaƙa da wannan case ɗin ku maida min su gefe.” Hakan kuwa akayi, asalin waɗanda akai kiddinapping tuni aka tattare su aka maida can gefe. Iya Abah da zuri'arsa ne kawai a wajen. Gaba ɗaya Mamy ta jiƙe sharaf da zufa, Oum kam sai share hawaye take yi, su AA idanu sun gama kaɗewa jazur tamkar an watsa musu wuta. Mabera dake kallonsu ya ce, “Koda ace zan mutu a yau bazanyi baƙin ciki ba, dan ko yanzu na nunama Kamila tabbacin alƙawuran dana ɗauka mata na zan dawo na cika su. Na dawo mata da AJIYA A DUHUN da tayi daya ruguzata a gaɓar da take ganin ta gama cin nasara. So hakan kuma yamun daɗi dan koba komai za'ayi komai a gaban shari'ar da take ganin itace ƙarfinta a yanzu, al'amarin kunga ai zaifi romon daɗi ma. Zan dawo da baya domin wanda basu san ni wanene ba anan su sani. Musamman alaƙata da amini na kuma ɗan uwa. Dan ban taɓa amini ba a rayuwata sai Darma, bayan shi kuma ban ƙara yi ba dan bamma sake yarda da kowa ba hatta kaina. Sai abota kawai” “Da farko dai sunana Junaid Abubakar Mabera. An haifeni a cikin garin Kano, anan na tashi, anan nai karatun primary na, nayi Secondary school boarding a garin Bichi local government. Anan ne na haɗu da Darma. Dan muna shekarar ƙarshe, wata shidan ƙarshe ma da muke shirye-shiryen fara ssce aka kawoshi shima zai zana jarabawa damu. Ni ne shugaban ɗalibai na wannan shekarar dan haka vice principal ya damƙa Darma a hannuna akan na kula da shi saboda ta hannunsa aka kawo Darma. Na amsa da hannu biyu, domin Darma dai ƙyaƙyƙyawane, a kallo ɗaya zaka fahimci ɗan masu kuɗi ne. A lokacin bawai dan kwaɗayin shi ɗan masu kuɗin bane yasa naji ina sonshi, nima daga gidan kuɗin na fito, kawai dai ina ganin abotarmu zata kasance ta ƙwarya tabi ƙwarya ce. A cikin sati guda sabo da shaƙuwa ta shiga tsakanina da Darma. Har ina kiransa My Darma shi kuma yace My Mabera. A yanda mukai gaggawar ƙullewa kowa a makarantar sai ya ɗauka dama can muna da alaƙar sanayyar juna ko zumunci ma mai ƙarfi na jini. Bamu taɓa musama kowa ba muka bar abin a haka. Ba wani isasshen lokaci ne da mu ba muka fara exam. Cikin ikon ALLAH har muka kammala. Tun zuwan Darma bashi da labari sai na ƙanwarsa Fateema. Duk motsinsa zai ce Zarah kaza, da yanzu Zarah tai kaza. Tun sunan Fateema na shiga kunnena da labarinta muyi dariya kawai harya fara tasiri a cikin zuciyarta, dan nasan dai bai wuce ƙanwarsa ba. Bawai ina nufin tasiri na soyayya ba, a'a nima dai ina mata so irin na ƙanwa. Tare da Darma muka tafi gida, duk da anzo ɗaukata nima amma sai na shiga motar gidansu drivern gidanmu ya bimu a baya. A'a mizai faru, cikin ikon ALLAH ashe anguwarmu ɗaya, layi ne kawai ba ɗaya ba. Hakan ya mana daɗi sosai, mun kumayi farin ciki. Har gida na shiga na gaida su Baba da Umma, na tambayi Fateema akace tana makaranta. Da yake nima ina zumuɗin son tafiya gida ne ban daɗeba na fita drivern gidanmu daya biyo mu a baya ya ɗaukeni sai gida. Dawowarmu gida ta sake ƙulle abotarmu, a gidansu Darma kowa ya sanni, hakama a gidanmu kowa ya san Darma. Nakan je gidansu na yini wani lokacin ma har kwana. Yakan je gidanmu shima sai dai bai taɓa kwana ba. Nine auta a gidan mu, dan haka nake matuƙar son ƙannen Darma musamman Fateema. Haka ni da shi zamuyita goya ƴan biyu, hatta Mahmud ma mune komai nasa dan lokacin shima yana Secondary. Jarabawar mu ta fito, muka kuma ce makaranta ɗaya muke so dan haka babana ya amshi takarduna mu kasancewar yana da alaƙa da harkar ilimi ya nemar mana makarantar tare. Bamu sha wahalar komai ba kuwa komai ya daidaita, da farko dai zuwa muke mu dawo, daga baya muka koma hotel. Kowa ɗauka yake munada alaƙa ta jini, duk da bama kamanni sam. Sannan halayyar mu ta banbanta sosai. Babu ruwan Darma da mata, hasalima baya sakar musu fuska sam, niko gaskiya ina son mata, ina huɗɗa da su sai dai ban taɓa taɓa ƴar kowa ba. Amma ni kaɗai nasan hakan, dan yanda nake mu'amula da su hatta shi Darma bai yarda bana bin mata ba. Duk da nasha yi masa rantsuwa da ALLAH idan yana mun nasiha ko faɗa amma sai yace bai yarda ba. Tun ma ina damuwa da masa bayani da son ya fahimta harna haƙura na ƙyalesa muka cigaba da karatunmu, ban kuma daina shiga cikin mata ba ayi shewa da arerewa. Sai dai a duk lokacin daya zauna yana tuhumata abin na ƙona min zuciya, dan ina ganin kamar yana son ƙasƙantar da ni ne ko nuna min ya fini sanin ALLAH da tsoronsa. Sai kuma yanda matan kullum suke roƙon na haɗasu da Darma, gashi fa ina a cikinsu ina ƙyautata musu amma su hankalinsu nakan Aliyu da ko kallon su bayayi. Wata ma a cikinsu bai taɓa magana da ita ba. Da naga abin nasu fa na gaske ne sai kawai na fara business da su. Idan kikace kina son Darma na dinga tatsarki kudaɗe kenan akan zan daidaitaku. Haka na dinga haɗa kuɗin matan nan ina ci tun abin ina yinsa a raha har ya fara tasiri da mun daɗi a zuciyata, kun san dai kuɗi da shiga rai. Yanda nake damun Aliyu akan ya dinga kulasu ko kaɗan ne sai muka fara samun saɓani da shi, ya fara janye jikinsa daga gareni, bana son rabuwa da shi dan tarayyarmu na kankaro min mutunci saboda nutsuwarsa, gashi da ƙoƙari akan karatu, sai kawai na daina masa maganar matan na koma jan ra'ayinsa akan business ma. Wannan shine sanadin da muka yanke shawarar fara business ni da Darma, batare da sanin kowa ba muka haɗa ƴan kuɗaɗenmu muka fara saro yadika, takalma, da ƙananun kaya muna kawowa cikin makaranta. Al'amarin kamar wasa sai cinikin ya ɗaukaka, takai har malamai sayen kayanmu sukeyi. Hakan nama wasu zafi ganin anƙi hanamu, bayan kuma dokane yin business ɗin a cin makarantar. Takai wasu har suna ganin dan iyayenmu nada kuɗi ne kawai. Surutunsu bai sa an hanamu ba, mu kuma bamu fasa ba. Ikon ALLAH kafin mu kammala sai ga jari ya zauna mai nauyi saboda kuɗin da dana yanzu darajarsu ba ɗaya ba. Mun kammala karatu mun dawo gida, ga jari mai tsoka a hannunmu, sai dai bamu sanar da iyayenmu ba muna son muyi surprise ɗinsu. Kwatsam mun dawo gida da sati biyu kacal kamar saukar aradu sai naji wai an ɗaurama Fateema da Aliyu aure. Babbar magana, taya haka zata faru bayan iyayensu ɗaya. Hankalina ya tashi mamaki ya kamani nazo ina tambayar Aliyu, bai ɓoyen komai ba ya gaya min alaƙarsa da Fateema. Al'amarin ya zafeni, ya kuma dakeni a zuciya dan ban taɓa tunanin Darma bai ɗaukeni yanda na ɗaukesa ba gaskiya. Kufa gane ba son Fateema nake ba sam. Amma sai kawai na samu kaina da jin haushin auren nasu. Dama ga wani kaffa-kaffa da Aliyu keyi da Fateema tunda muka fara jami'a like baya son na raɓeta saboda yana min kallon mazinaci.........✍️
*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*
*+234 805 568 7449*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
*_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣5️⃣9️⃣
______________
.........A'a al'amarin fa ya fara damuna da min zafi, ya mutum ina tare da shi yasan halina sarai amma yaƙi yarda dani. Bafa gidansu sunfi gidanmu kuɗi bane ba balle yace maula nake masa. Sannan ba ilimi ya fini ba balle tarbiyya balle yace gidansu sunfi namu iya tarbiyya. Gefe ga wani abokina yanata sake zugeni akan wulaƙancin da Aliyu ke min na hantara da nuna ƙyamatar halayena a gaban kowa har baya iya barina na sake da ƙannensa ma musamman Fateema, duk iya ƙyautatawar da nake ma yarinyar sai kaga yana gwaleni. Kawai wataran anyi ruwa muna tare da abokin nawa sai ga su Fateema da ƴan biyu sun taso islamiyya, tanata fama da su ƴan biyu suyi sauri wani hadarin na tasowa amma sunƙi sai ma wasansu suke. Ni uban ƴan gwaninta sai na daukar mata Hussain abokina ya ɗauki Hassan ita kuma na kama mata hannu dan iska ta taso mai ƙarfin gaske har ba'a iya ganin hanya da ƙyau. Taso kwace hannunta sai naƙi saki, nai mata tsawa akan bata ganin iska ko so take ta tafi da ita. Fateema nada tsoro sai ta nutsu, sai dai sai hawaye takeyi alamar dai bata so ko kuma tsawar dana matan ce ta mata zafi oho mata. Mun shawo kwanar layin su sai ga Aliyu a motar gidansu zaije ɗaukar su Fateema. Mun tsaya ina cema yaran yauwa ga yayanku nan ma zaije ɗaukarku kawai naji saukar naushi a fuska, kafin na dawo hayyacina na gama tantance wanda yay min hakan an kwace Fateema da Hussain kawai an hau dukana. Kafin wani dogon lokaci Aliyu ya kaini ƙasa, abokina daya kawo min ɗauki ma ya nausheshi dole ya koma gefe yana ƙoƙarin tare jinin dake zuba masa ta hanci. Ga mutane nata gudun wucewa gida saboda hadari. Sai ƙalilan suka tsaya rabamu faɗan da Aliyu ne kecin nasara a kaina dan ya wanke min fuska da ruwan dagwalon ruwan farko da akayi, ya nannaushe min fuska harda idanu ya fitar min da haƙori ɗaya. Da ƙyar da ƙyar aka ɗaga Aliyu a kaina, yana huci da tabbatar min sai yay ajalina”. “Wannan kalma itace ta fusata mamana da yayyuna sukace bazasu yarda ba, ga raunikan daya jimin. Munje gidansu kawai muka samu har lokacin ana fama da Aliyu akan shi sai ya biyoni har gida ya kasheni wai na taɓa Fateema bayan ni mazinaci ne. Ai nasan matar aure ce, miye-miye. Wannan abu yamin ciwo, ya kuma daki zukatan iyayena, suka tsareni akan kalmar mazinacin da Aliyu ya kirani babana harda marina, na dinga rantsuwa ban taɓa aikatawa ba, na kuma ce aje ayi bincike. Yayuna ne sukai dukkan binciken daya dace, suka kuma tabbatar ban taɓa aikatawa ba sai dai ina huɗa da matan a zamantakewar yau da kullum, a jami'a kam wannan normal ne ai, sai abun yay musu ciwo basuyi shawara da kowa ba suka ɗauki ƴan sanda sukaje har gida aka kama Aliyu, sai da yay kwana biyu a rufe sannan muka sani. Hakan baima iyayenmu daɗi ba, amma ni sai naji farin ciki, koba komai yanzu Aliyu yasan nafi ƙarfinsa, kuma wlhy sai na rama dukan da yay min da abu mafi ciwo a rayuwarsa da zan bar masa tabon tunawa na har abada. Bayan an fito da shi kusan da wata guda na gama shirya dukkan abinda zan masa na ramuwa na zagaye naje na sameshi na bashi haƙuri. Da farko yaƙi saurarena, dan nafi wata guda ina binsa kafin na samo kanshi. Na masa bayanin komai daya faru ya fahimta daga ƙarshe muka sasanta har ya kaini wajen su Baba suma na sake basu haƙuri na kuma yi musu bayani hatta na rufe shi da akai a police station nace babu wanda ya sani a gidanmu ma sai su Yayun nawa da sukayi. Ban san miyasa suka yarda dani ba kai tsaye a lokacin, har Baba ya shirya yaje ya samu Abbana shima suna sasanta. Wannan shine dalilin sake dawowar tarayyarmu sai dai ba kamar da can ba dan Aliyu baya taɓa barina da Fateema, yayuna kuma idan suka ganni da Aliyu sunta zagina kenan da kirana mara zuciya. Kai cikin gidansu ma yakan daɗe bai bari mun shiga ba. Haka dai muka kammala karatu muna cigaba da Business ɗin mu, dukkanin kuɗaɗen kuma na hannuna, bayan dawowar mu gida sai komai ya tsaya, maganar business kuma na cinye kuɗin bai mun magana ba nima ban masa ba. Matsalar da muka samu a result ɗinmu mu duka yasa sai da muka sake komawa makaranta mukai gyara na shekara ɗaya, bayan nan ma munfi shekara ɗaya a gida kafin mu sake komawa makaranta mu jona Masters ɗinmu. Lokacin da muke kammalawa ne kuma Fateema ke kammala tata secondary ɗin, kawai sai ga batun wai tana da cikin Aliyu. A zahiri na tayashi murna, amma a ƙasan zuciyata kishi da ɗacin hakan nake ji, sai kawai naji a raina ga hanyar dazan rama abinda Aliyu yay min kenan. Abokin nan nawa daketa nuna min illar tarayyata da Aliyu na samu da shawara, aiko ya bani mai ƙyau ya kuma nuna min hanyar dazan aywatar. Budurwarsa na aikin asibiti, ita yasa ta kawo mana wasu ƙwayoyi, yace nayi duk yanda zan yi na canja maganin da Fateema kesha da wannan maganin. Nace masa na miye? Yace bana komai bane sai na lalata mahaifar Fateema, kuma a hankali maganin zai dinga aiki baza'a taɓa farga ba sai ya gama mata illa ta fara zubar jini.......” A wannan gaɓar a mugun firgice, a kuma tsorace Abah da Oum ke kallon Mabera. Abah daya gama kaiwa wuya zai yi magana Mabera ya katse shi da faɗin, “Ai bakaji komai ba, da zakai haƙuri dana kaika fiye da inda kake son ji.” A hankali AA ya riƙe hannun Abah, Yaya Fawzan kuma na Oum da take kuka sosai. Ita kanta Mamy zancen ya daketa, dan Junaid bai taɓa gaya mata shine ya aikata hakan ba. Cikin rashin damuwa Mabera ya cigaba da faɗin, “Wani irin daɗi naji a raina, haka na amsa cikin farin ciki, na kumayi duk yanda ya dace har sai da na saka maganin nan a maganin da Fateema ke sha na asibiti da suke bata akan rainon ciki. Shiru-shiru zanji wani sakamako banji komai ba har abin ma ya ban haushi na zazzagi wancan abokin nawa da kiransa maƙaryaci. A dalilin haka muka rabu da shi. Kullum cikin ɓacin rai da tunanin hanyar dazan rama abinda Aliyu yay mun nake har akace Fateema ta haihu kuma ƴan biyu ma, sai dai ɗaya ya rasu. Naji farin cikin mutuwar ɗayan, na kumaji baƙin cikin haihuwar ɗayan, amma na saka a raina yanda ubansa yay iƙirarin kasheni nima sai na kashe shi. Inata ƙullawa da kwancewa ban samu hanya ba sai da sukaje saudia wajen iyayenta dake zaune a can suka dawo sannan. Naje yi musu sannu da zuwa na shaƙama yaron abinda ya sanadin kawo masa murar da ta zama ajalinsa....” Babu wanda a wajen nan baya ma Mabera mugun kallo da tashin hankali. Kai ita kanta Mamy baki ta saki da hanci tana kallon Junaid ɗin. Shi ko babu wani damuwa a tare da shi ya cigaba da faɗin, “Bayan mutuwarsa mukai shirin tafiya hidimar ƙasa. Har lokacin kuma ban huce ba, dan a ganina shima dole Aliyu yaji a jikinsa, amma sai nai shirin barin komai har sai mun kammala saboda anyi rashin sa'a shi Aliyu an turashi kudancin ƙasar, ni kuma anan Kano aka barni saboda tsayawar babana. Burina akan Aliyu akan dukiya ne kawai, amma kwatsam sai aka sake cewa Fateema nada ciki, tashin hankali wanda ba'a saka masa rana kenan, ai anyi ba'ai ba kuwa. Aiko sai na bazama neman mafita. Sai dai kafin ma na samota sai labari ya sameni akan Fateema babu lafiya, an kaita asibiti kuma sunce sai an cire mata ciki da mahaifa gaba ɗaya dan tana da wani ciwo har ma Babanta yazo Nigeria shima Aliyu ya dawo Kano, amma ko sanar min baiyi ba. Farin cikin dana tsinta kaina a lokacin baida misali, nan fa na shiga neman abokin nan nawa amma na gagara samunsa a ko'ina. Daga ƙarshe ma akace min yana Lagos ai. Nayi takaici, abinka da babu waya, nai masa wasiƙa dai na bayar akai masa dan kuwa dai magungunan wancan karon ne suka jawo hakan ga fateema. Bayan cirema Fateema mahaifa da ciki babu jimawa muka kammala hidimar ƙasa. Inda a hidimar ƙasar ne kuma lokacin da Kamila ta shigo rayuwata sai naji a raina zata min amfani ta min aiki musamman ganin ba ƴar kowa bace ba, sannan ita a karan kanta makwaɗaiciya ce, gata dai ƴar ƙarama kuma a fuska shiru-shiru amma shaiɗaniyar kanta ce. Kamar yanda a baya Aliyu kemin zargin ina bin mata kuma banyi haka akan Kamila ban taɓa sakama raina zan lalata mata rayuwa ba, ita da kanta ta bani kanta ta hanyar zuba min abu a lemo nasha. Koba haka ba!!??”. Yay maganar a tsawace yana kallon Kamila. Ganin bata da niyyar amsa masa Sille ya take ƙafar dai-dai inda ya harbeta. Wahallen ihu ta saki zufar azaba na sake keto mata tako ina a jikinta. “Zakiyi magana ko sai na sake fasa ɗayar ƙafar”. “Zanyi-zanyi. Wlhy zan faɗa musu komai nima bazan ɓoye ba”. “Oh da kikace ke shegiya ce”. Cewar Sille yana komawa ya zauna. Sai da Mamy taja mintuna biyu hankalinta ya ɗan dawo jikinta sannan ta fara faɗin,...........✍️
*_AJIYA A DUHU na kuɗi ne, 500 ne kacal, ƴar uwa bazaki ragu da komai ba dan kinzo kin sauke hakkin wahalata ta rubutu. Dan ALLAH magana ta WhatsApp kawai 😀🙏_*
*+234 805 568 7449*
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
*_WhatsApp channel_*
https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
*_BOOK 2_* 🅿️➖1️⃣6️⃣0️⃣
______________