Kenza eBookz

Asanadin makwabtaka book 1 by zee laluh - Chapter 36

Asanadin makwabtaka book 1 by zee laluh - Chapter 36

Asanadin makwabtaka book 1 by zee laluh Chapter 36: Asanadin makwabtaka book 1 by zee laluh Chapter 36. A daidai wasu jerin shagona ya parker Motar agefen…

4,255 words

A daidai wasu jerin shagona ya parker Motar agefen titi, wayarsa ya fiddo ya kira wani mai suna Kb yace mashi yana waje, ba 6ata lokaci ya fito daga wani shago acikin jerin shagunan wurin wanda na d'inki ne kamar yadda aka rubuta asaman shagon, matashi ne yana sanye da jeans da t-shirt yana zuwa bakin Motar Haisam ya bud'e kopar ya fito, cike da girmamawa ya shiga gaisar dashi yana tambayar ya ibada, bayan ya amsa mashi ne ya bud'e back door na Motar ya fiddo wata leda wadda yasa aka ware kayan da za'a dinka ma Fatuu, da sauri Kb ya kai hannu ya kar6a ya bud'e ledan ya duba kafin ya d'ago ya tambayi wa za'ai ma dinkinne kuma wanne iri, gaya mashi yay suna tare kafin ya lek'a ta gaba yace ma Fatuu ta fito, bayan ta fito yace ma Kb suje ya dau measurement nata sai ta za6i styles da take so, amsa mashi yay da to kafin ya nufi shagon yana zuwa saitin Fatun yace ta biyo shi, maimakon ta bishin sai ta kalli Haisam a rude tace "Ya tafi da abubuwan fa" cikin nuna rashin fahimta yabi Kb d'in daya kusa shigewa shago da kallo kafin ya maido kallon kanta, tana ganin hakan ta fahimci bai gane abunda take nufi ba hakan yasa da sauri ta sake cewa "Abubuwan da aka saka ciki nike nufi" still bin ta yay da ido kafin ya bude baki yace "i don't get u" jin hakan yasa ta d'aga hannu tana kwatanta mashi abunda take nufi harda d'an nuna chest dinta, wani kallo yabita dashi mai kaman harara aikuwa da sauri ta sunkuyar da kanta kasa, "Ki bishi" taji ya fada, juyawa tai sumi sumi ta nufi shagon haisam daya bita da ido yadan yi wani guntun Murmushi hadi da dan ta6e baki daga haka ya koma cikin Motar,

Tana shiga cikin shagon wanda babbane yana d'auke da manyan kekunan d'inki kala kala masu amfani da wuta Kb ya nuna mata plastic chair yace ta zauna, zaunawa tayi gaba d'aya hankalinta na akan ledar kayan tsoronta kar ace bras din na ciki, saida ya fiddo kayan ya duba taga babu su sannan ta samu natsuwa ta fara tunanin kilan suna acikin sauran kayan, wayarshi ya bata bayan ya bud'o mata inda styles suke yace ta za6i wanda za'ayi mata aikuwa hannu na rawa ta amsa ta fara dubawa, duk Wanda ta gani sai ta wuce bai yi mata ba can ta samu wadanda suka yi mata d'aya fitted gown d'aya kuma riga da skirt, koda ta nuna ma Kb d'in sai cewa yay ta dae sake wani wad'annan na Manyan yan mata ne ko kuma Amare aikuwa a harzuk'e tace ai itama yan matance, nan fa suka fara jayyaya har sauran yan shagon saida suka amshi wayar suka duba style d'in da ta za6an kowa ya duba sai yace da de ta canja, wani ma har shawara ya bata yace kayanta masu kyau ne kar ta lalata su amman ta nace ita dae su take so tunda ai a jikin mutane ta gansu sun sa lafiya lou balle ace wani zata lalata kayanta shidae Kb kafewa yay akan ta canja in ba haka ba zaije ya nuna ma yalla6ai Haisam, ganin taki canzawar yasashi nufar waje aikuwa zumbur ta mik'e tabi bayanshi suka nufi Motar sai faman wawwatsa hannuwa take tana fad'in ita da kayanta ba abunda take so zata za6a ba, suna isowa bakin Motar taja kopar ta bud'e lokacin ya d'age kanshi jikin headrest yana sauraron Radio, sauke kan yay ya kalleta ta Matuk'ar d'aure fuska tanata hura hanci,

"Miya faru" ya tambaya da kasalalliyar murya, hannu ta d'aga ta nuna mashi Kb dake gefe don shi baima ganshi ba, lek'o wajen yay ya zuro da k'afarshi guda ya kalli Kb d'in tambayarshi abunda ya faru yay, cike da girmamawa ya fara mashi bayani "Yalla6ai dama styles d'in data za6a ne naga kaman basu dace da ita ba don an fi yima Amare haka ko Manyan yan mata, ita in akayi mata karshe zasu takurata ne ma shine nace da ta canja wasu simple wanda zata mora sosae" tun kafin Haisam yace wani abu ta amshe a tsiwace tace "ai dae nima yanzu yar Matance ko, zaka wani ce na Manyan yan Matane to an gaya maka nima yanzu yarinya ce..." tsit ta dakata da Maganar ta juya tana kallon haisam daya d'an k'ank'ance ido had'i da d'an d'age gira yana kallonta lokaci guda tasha jinin jikinta ta fara d'an sussunnar da kai tana mashi kallon kasan ido, wani guntun bazawarin Murmushi yay tana ganin hakan ta turo baki tana kyakkyafta ido,

"Kai mata wanda take so" ya fad'a ba tare daya kalli Kb d'in ba, kallonshi tai tayi mashi gwalo shidae Murmushi kawae yay yace suje ya dauki measurement dinta tabi bayanshi tanata surutai tana fad'in "ai daman nasan cewa zaiyi kayi man don duk abunda nike so yi man yake gashi nan ai kasha wahalar banza" ta k'arasa tana mashi dariya, girgiza kai kawae yay ba tare daya ce mata komai ba don ya fahimci rigimamma ce, bayan ya gwadata atare suka fito har yan shagon na mata sai anjima, suna isa ta bud'e Motar ta shige shi kuma ya zagaya wurin Haisam ya fad'i mashi an gama komae yace zasuyi Magana daga haka ya tashi motar, zuge glass Fatuu tayi tana jaddada mashi ya d'inka mata su suyi kyau kaman yadda na jikin matan data gani suke, cike da zolaya ya d'aga murya yace bazai mata irinsu ba zani jaka tsaye(zani single) da riga zai yi mata, atsiwace tace " Wllh in kayi man su sai ka biya ni kayana in ba haka ba a kaika gidan yariii" daga haka Motarsu tabar wurin shi kuma Kb ya nufi shagonsu yana dariya da alama shima d'an barkwanci ne, lokacin da ya koma shagon hiran rikicin Fatun suka cigaba da yi har Kb din na cewa shi abunda ma ya bashi mamaki da yarinyar irin hips din dake gareta duk da ba wani girma ne da ita ba, gaba daya suka tambayeshi measurement din hips din, da mamaki duk suka maimaita daya fad'i masu awon har wani na cewa kodae bai yi awon daidai ba yace wllh daidai awon yake don da farko ita yaba ta zagayo mashi da tape d'in kamar yadda suke yi in zasu auna chest da hips sai suba mai dinkin suce ya zagayo masu dashi, da ya duba awon sai ya kasa yarda hakan yasashi kama tape d'in ya auna da kanshi amman sai gashi same abu ya bashi, gaba daya suka jinjina kai wasu na fad'in hutu ne da cin kayan dadi kawae, "Kunsan kuwa dangin Senator Ali zakee ce" Kb din ya fada, "Haba nifa nayi mamakin ganin an kawo maka dinki a wannan lokacin kuma ka amsa kai da kace ka rufe amsar d'inki ashe babbar harka ce" wani dake yin d'inki cikin yan shagonne ya fad'i hakan, dariya Kb yay "ai kaima kasan har dinkin wasu sai in aje akan wannan, daga fa gidan uwar d'akina ne Hajiya Hauwa Zakee mai Alkhairin ban mamaki yake"

"Waye ya kawo dinkinne ko wannan wanda take aikowa miye ma sunanshi?" wani daban ya tambaya, "Wai Tk, bashine ya kawo ba in shine ai shigowa zai yi jikinta ne Haisam dan Senator d'in" Kb ya bashi amsa, "Kace Balaraben nan ne, kai gaskiya mutumin nan wllh yana mugun burgeni yasin, kaga mutum kaman shi yay kansa.....",

" ai in dae da irin wad'annan a gari to fa mu munshiga ukku wllh don mata ko kallon irinmu bazasu rink'a yi ba" wani da ya katse waccan ya fad'a aikuwa gaba daya suka kwashe da dariya suna fad'in shi damuwarshi kenan yace to ai gaskiya ya fada suna jin har maza yana burgewa inaga matan kuma, haka suka ci gaba da hiransu suna yin d'inki shi kam Kb fiddo kayan Fatun ma yay yace bari ma ya yanka su tun yanzu.

A daidai kopar gidansu ya parker Motar lokacin anata yin sallar Azahar a Masallacin gidan Hajiya, batare daya fita ba ya mik'a hannu baya ya janyo babbar ledar sauran kayan yace ta fita sai ta d'auka, bayan ta fitan ta saukko ledan k'asa wasu guda biyu marasa girma ya sake daukkowa a bayan ya mik'a mata mai d'auke da atampopi guda biyu yace taba Friend dinta da Mom nata sai mai guda d'ayan yace taba Grandma dinta, gyad'a mashi kai tayi alamar to tana ta bin shi da ido kaman akwae abunda take son fad'a, kallonta yay ya dan kwantar da kanshi ganin tayi mashi tsaye ya furta "any problem" kaman wadda aka zarewa lakka ta girgiza mashi kai alamar ba komae, tana niyyar rufe kopar Motar taji yace "check inside suna nan" da sauri ta juya ta kalleshi shima ita d'in yake kallo fuskanshi a sake kaman zaiyi Murmushi, turo baki tay tace "nifa ban tambayesu ba ai ko", " kinji nace wani abu ne?" ya d'age mata gira, a hankali ta girgiza mashi kai alamar a'a,

"Owk kije" ya fad'a bayan ya d'ago yana k'okarin jan Motar,

"Ya Handsome" yaji ta kirashi a sanyaye, dakatawa yay ya kalleta ba tare daya amsa ba, "Nagode, Allah ya saka da Alkhairi ya saka ka a Aljanna" ,"Ameen yar fillo" ya fad'a da dan Murmushi, har ta juya ta sake juyowa, "Allah ya baka mata ta gari ta haifa maka yara masu kyau in rinka yi masu wasa ina kuma goya su" bud'a ido yay alamar mamaki hakan yasa ta kyalkyace da dariya ta rufo mashi kopar, baija Motar ba har saida ta kinkimi kayan ta shige sannan ya nufi gida,

Lokacin data shiga cikin gidan d'akin gwaggo ta nufa ta taras ta gama salla tana zaune kan darduma tana lazimi, cike da zumud'i ta nufeta ko sallama bata yi ba ta zauna agabanta bayan ta ajiye kayan a gefe, hannu ta kai ta cire gyalen kanta ta juya ma gwaggo k'eya yadda zata ga gashin sosae, shafa Addu'a ta fara yi kafin ta kai hannu ta shafi gashin da fara'a tace "inyee, Fatuuta ce ta zama yar India haka" juyowa tayi tana ta dariyar farinciki ta hau bata labarin yadda aka gyara gashin tiryan tirya, "Yar kauye kawae" gwaggon ta fad'a bayan ta gama fad'i mata, ita dae sai faman tik'ar dariya take, hannu ta kai ta janyo ledar kayan ta fara curo wanda ya bata daga baya ta mik'a ma gwaggon tata "gashi nan yace in baki" jinjina kai tay ta ciro atamfar mai kyaun gaske tana ta Murmushi don al'amarin Haisam ya daina bata mamaki sai dae in yayi abu tayi godiya tasa mashi Albarka, fiddo na cikin d'ayar ledar Fatuu tayi wanda guda biyu ne daya mai Golden daya Normal Chiganvy irin ta cotonou mai laushin gaske itama ta gwaggon irin tace amman design ba daya ba, Fatuu na gani tace "lahh gwaggo wannan shigen irin tawa ce da aka kai dinki wllh, kinsan na waye?" girgiza mata kai tayi alamar a'a, "Haulat yace in kai mawa ita da innarta fa" bud'a ido gwaggo tayi sai kuma ta shiga yin godiya, jawo sauran kayan dake acikin babbar ledar tayi anan kuma tai kacibus da yan bras dinta tana ganinsu tai saurin d'agowa ta kalli gwaggo suka had'a ido don ita take kallo tana jiran ganin abunda zata fiddo a ciki, ganin ta k'ame yasa gwaggon tambayarta "lafiya" shiru tayi tana ta d'age baki hadi da dan sosa kai, ganin taki cewa komae ne kuma ga alamun rashin gaskia atattare da ita yasa gwaggo ta kai hannu ta jawo ledar ta lek'a ciki, da mamaki ta d'ago ta kalleta "wannan kuma na waye?" ta tambaya yayin da ta kai hannu ta fiddo da bras d'in, mar mar ta fara yi da ido kaman zata yi kuka cikin in ina ta fara magana "W..wa..wai mai shagon da akai siyayyar ce tace ina bukatarta...." katseta gwaggo tayi "ita ya akai tasan kina buk'atar tatan?"

"Ai dayake shagon biyu ne,to da aka gama zabar lace da atamfar nawa sai Ya Handsome d'in yace mu shiga ciki a idasa daukko sauran abubuwa...." nan ta kwashe komae yadda Zee ta bata bras d'in ta fada mata, shiru gwaggo tayi had'i da sunkuyar da kai, tunani ta shiga yi dama can tayi tunanin yakamata ta siya mata bra din don irin breasts din nan masu nipples gareta koya tasa riga mara nauyi sai an gansu sosae, to ganin ba wani girma garesu bane yasa ta kyaleta don sam itama ba irin jikin ainihin yan Matan fulani ne da ita ba, su kansu breasts din nata da gani ba irin masu yin girman nan bane sosae wanda suke zubewa, jin gwaggon tayi shiru kuma ta duk'ar da kai ne yasa gabanta ya fara fad'uwa murya na rawa tace " Gwaggo in baki so dama nace mata zansa Ya Handsome ya kaini a maida mata su", d'agowa tay ta kalleta, nannauyar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta fara magana " tunda ta baki taga ya dace ki rinka sawa ne, ki yi amfani dasu....,amman don Allah Fateema ki natsu kisan kin girma duk wani sakarci da wauta ki ajesu agefe, kada ki fara amfani dasu kice zaki bi mutane kina yamadidi kina nuna masu ko fadi masu, sam hakan bai dace ba don rashin kunya ne, ina son ki kama kanki mace da kunya aka santa ba kaman ke da kike bafullatana wadanda aka sani da tsananin kunya, idan naga kina rawar kai don kin fara saka su to kuwa tabbas zan hana ki amfani dasu ne, kinji ni da kyau?" da sauri ta d'aga mata kai alamar eh, duba sauran kayan tayi tasa albarka yayin da farinciki ya lullu6eta saidae sam bata bayyana a fuskarta ba dalilin Maganar da suka gama da Fatun, umarnin kai kayan d'aki ta bata bayan ta mik'e tace in an sha ruwa sai taje ta kaima su Haulatun tace ai ba azumi take yi ba bari taje yanzu ta kai masu gwaggon tace to ta fara yin salla ta amsa da to daga haka ta fice gwaggon ta bita da ido, girgiza kanta tayi lokaci guda kuma idonta suka ciko da kwalla don tunawa da yadda tai fama da Mahaifiyar Fatun kan saka bireziya sam bata so saboda tsananin kunya dake gareta sam ba halinsu d'aya da Fatuu ba duk da tasan dalilin dayasa wasu halayen nata take yinsu haka, d'aga hannu tayi ta shiga yi masu Addu'a gaba daya.

Tana gama yin sallar ta nufi gidansu Haulatun, lokacin da ta kai masu kayan Golden d'in tace ta haulatu ce dayar kuma ta innar tasu, Murna sosae sukai dama rannan Hajiyar Sanata ta aiko masu da turmi ukku su dinka harda kannanta kaman yadda ta saba yi duk salla tana rarraba atampopin salla ga marasa k'arfi, har tukuici Innar tasu taba Fatun amman tak'i amsa Haulat tace bayan sallar asham zata rakata tayi mashi godiya, labarin irin kayan da ya siya mata ta shiga ba haulatun amman abun mamaki sam bata yi mata zancen bras din ba da alama taji fad'an gwaggo, sosae haulat ta tayata murna tana ce mata ita yanzu ai tazama yar lelen Ya Handsome, sai la'asar Fatuu ta koma gida, da dare bayan an gama sallar asham tare suka iske shi a part d'inshi don sun duba part d'in Hajiya bai je can ba, karo na farko da Haulat ta shiga part d'inshi sosae ta jinjina had'uwar falon acikin ranta, yana kishingide akan kujera yana lallatsa waya suka iskeshi Haulat d'in na k'okarin duk'awa kan Carpet yace ta zauna kan kujera lokacin ita Fatuu tuni ta haye, sosae tayi mashi godiya yace mata ba wani abu daga haka Haulat ta mik'e tace ma Fatuu tazo su tafi, sanin dama da angama sallar yake rakata gida yasa ta mik'e suka mashi sai da safe tana ta fama yi mashi Murmushi harda yi mashi bye bye shima ya d'an d'aga mata hannu suka fice.

Washe gari ya rage saura kwana shidda salla da daddare bayan angama asham taje part d'in hajiya, lokacin da zata tafi ta bata wata babbar leda mai dauke da kaya tace ta kai ma Dije, cike da zumudi ta nufi gida don tasan bai wuce kayan sallar data saba yi masu, lokacin da ta isa gidan gwaggo na kan darduma a tsakar gidan bata dade da gama sallar asham din tata ba tana zaune ga haske ya haske tsakar gidan don tana cikin yin sallar aka maido da wuta, gabanta Fatuu ta nufa da sauri ta aje ledan tana fad'in "gashi Hajiya tace in kawo maki" saida ta shafa Addu'a sannan taja ledan ta bud'e, fiddo kayan ciki tayi gaba daya sannan ta fara daddaga su Fatuu na ganin hakan itama tasa hannu tana tayata d'agawar, d'inkakkun kaya ne d'aya Voile material ne bak'i mai d'auke da manyan fulawowi kala kala ya matukar yin kyau anyi dinkin doguwar riga wadda da gani ta fatuu ce gaban rigar sai sakin kyallin stones da akai ado dasu cikin flowers d'in Material yake, sauran kuma brown shadda ce aka dinka masu gaba daya, gwaggo riga da zani rigar umbrella ce tasha aiki sai ta Fatuu itama shaddar doguwar riga akai mata sai na kawu Amadu dogayen riga da wando ne akai mashi, dama ko sallar data wuce haka tay masu d'inkakkun kaya saidae wanccan karon atamfa tayo masu Amadu kuma yadi ne mai kyau kuma dama ko ba salla ba tana yi ma Fatuu d'inki lokaci zuwa lokaci, wata k'arar murna Fatun ta saki tana fad'in tafi kowa kayan salla wannan sallar gwaggo dai nata faman dariya, lissafi ta shiga yi Ya Handsome yayi mata kala hudu ga bakar doguwar rigar data aje kala biyar kenan sai ga biyu hajiya tayi mata bakwai kenan sai kuma baffanta da yazo ya kawo masu atamfofi ita da gwaggon anyi mata dinki kala biyu Amadu kuma ya kawu masa yadi mai kyau mai matsakaicin kudi dama ita gwaggo bata da niyyar yi mata d'inki wannan sallar tunda baffanta ya kawo mata kuma tasan hajiya dama zata yi mata ga kuma jallabiyar da ta aje, sam bata ma sa ran na Haisam ba iyaka dae ta siya mata gyale da takalma dasu sarka harda sabbin pants da undi da vest sai gashi kuma Haisam din shima ya siya mata, lallae da alama su Fatuu canjin wardrobe za'ai, cike da murna ta ruga waje ta fad'o ma Kawu Amadu suka dawo tare, sosae yay farinciki da ganin kayan, koda lokacin kwanciya yayi Fatuu tasa dukkan kayan tayi gabanta ahaka tai bacci..........

ALBISHIRUNKU MATAN AFRICA DA KEWAYE SHAHARARRAR MAISAIDA KAYAN MATAN NAN WADDA KUKAFI SANI DA MAMAN HAIDAR TANA YIMAKU ALBISHIR DA CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE AFADIN NIGERIA DA NIJAR, KARKU MANTA MACE MAI GYARA BATA BORANCI💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃08040448621 Akwai zafafan kayan mata masu matukar kyau da arha cikin sauki zamu aika miki da kayanki cikin aminci da yardar Allah su isa har inda kike ba cuta ba cutarwa karku bari abaku labari. Muna kawo kalolin ingantattun kaya kamar haka 💥💫💥💫👇👇👇👇 1-Maganin sanyi 2-Maganin gyaran nono 3-Maganin hips 4-Akwai gumba kala kala 5-Maganin matsi masu ciko da gaba ki koma kamar budurwa 6-Kalolin garirrika masu bawa mace ni'ima da jimawa ajiki yana aiki 7-Akwai tsumi sha yanxu magani yanzu 8-Akwai jigidar sirri kala kala Sannan kuma muna dahuwa kamar haka 💥💫💥💫👇👇👇👇 1-dahuwar kaza 2-yan shila 3-ciccibi Dadai sauran su.Abubuwa dayawa gaskiya bazasu lissafu bah saboda lokaci maiso ta bini PC don ganin Kalolin kayan da muke dasu 08040448621, ALLAH YAYI MAKI KIMA DA DARAJA AMATSAYINKI NA MACE👰,KADA KI WOFINTAR DA KANKI A WURIN MIJI SABODA RASHIN GYARA KAI, BURIN MAMAN HAIDAR KO WACE MACE TA ZAMA TAURARUWA⭐YAR LELE AGUN MIJINTA😍 SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI🤝

*💖A SANADIN MAKWABTAKA💖*

_A heart touching story of Love and Destiny_ 💔

*Mallakin* ⬇️ *🌹ZAINAB LALUH*📲✍ _~(Oummu imam)~_

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*

6️⃣0️⃣

Washe gari da Safe suka d'unguma gaba d'aya suka tafi yin godiya, ana saura kwana ukku salla bayan la'asar lokacin gwaggo da Fatuu suna cikin aikin kayan shan ruwa Amadu ya shigo cikin gidan da sallama, nufar Fatuu yay dake jajjagen kayan miya aturmi ga kuma dankali na soyuwa kan gas agefenta, "Gashi nan in ji Ya Haisam" ya fad'a yayin da ya aje babbar ledar da ya shigo da ita daga haka kuma ya juya don ya baro Mutane a shago, cike da zumud'i ta janyo ledan ta bud'e, koda ta yi arba da kayanta da aka kai d'inki sai ta saki dariyar farinciki ta fara kwala ma gwaggo kira tana fad'in tazo taga dinkinta gasu an kawo, fiddo kayan ta fara yi tana dubawa nan take tsananin farinciki ya lullu6eta ganin yadda dinkin sukai bala'en kyau, a atamfar akai mata fitted gown d'in lace din kuma sai akai mata riga da skirt, sunkutar gown d'in tayi ta nufi d'aki don ta gwada, bayan shigarta da d'an lokaci gwaggo ta fito daga cikin kitchen tana fad'in taga dinkin, ganin ba Fatun a wurin yasa takai hannu cikin ledar ta fiddo rigar lace d'in ta d'aga sama, waro ido gwaggo tayi gannin dinkin rigar ba arziki ta d'aurata a saman kafadarta ta curo skirt d'in shima ta d'aga tana k'are mashi kallo bata gama al'ajabin d'inkin da akai masun ba sai ga Fatuu ta fito cikin fitted gown d'in ta kamata tayi mata d'as ajiki daga k'asa ta bud'e sosae yayin da hannuwan ma suka wani kumbura anyi masu wani kalan design d'in dinki da wani abun kwalliya mai kyau, nufo gwaggo tayi tana faman washe baki tana fad'in bari tazo ta idasa zuge mata zip d'in, cakk taja ta tsaya sakamakon jin salatin da gwaggon ke rafkawa hannu a baki, tsaye tayi ta kwalalo ma gwaggo ido,

"Yanzu Fatuu wannan d'inkin akai maki sai kace wata kifi, waye yace ai maki shi ne?" ta tambaya rai a 6ace, shiru tayi tana ta zare ido ganin yanayin fuskar gwaggon, har saida ta kwatsa mata tsawa sannan cikin en ina tace "n..nice na za6a" cike da takaici gwaggo ta maimaita abunda ta fad'an kafin tace "saboda baki da hankali ko shine bazaki za6i d'inkin arziki ba sai wannan duk da irin fad'an da nike maki akan matsatstsun kaya shine don kin raina ni baki jin maganata kika za6i wannan dinkin na rashin arziki duk an matse halitta ta bayyana, to naga yadda za'ai ki saka su da sallar in Allah ya kaimu sai dae ki kallesu kuwa", yamutsa fuska ta fara tana jujjuya kai kaman zatai kuka tace " ni dae don Allah ki barni nasa abuna ai dae ajikin Mutane naga anyi nima na za6a ko" "To ni bazan bari kisa ba sai in ga ta tsiya" bubbuga kafafu ta fara tana k'unk'uni tana fad'in " Wllh nidae sai nasa abuna tunda ai bake kika siya man ba ko kuma....." cakk ta tsaya da yin Maganar ganin gwaggon na dube duben k'asa da alama abun bugu take nema, hannu takai cikin robar da fatun ta yanka dankali ta curo wuka, a rud'e Fatuu ta zaro ido tace "Gwaggo wuk'a ne fa!" "Wukan ne don kazan ki, in na illata ki ba sai inga yadda za'ai kisa su da Sallar ba" ta bata amsa lokacin da take d'agowa hannunta ruke da wuk'ar aikuwa Fatuu na ganin haka ta juya fatal fatal don ta kasa yin gudu sosae, maimakon ta jefa wukar saitinta sai ta jefata can gefe guda kafin ta duk'a da sauri ta curo slipper d'in kafarta ta jefa mata daidai fatun ta shige ya d'an sameta a gefen jikinta, tana shigewa d'akin ta rufo kopar, ita kuwa gwaggon cigaba da d'aga riga da skirt d'in tayi tana ta zabga uban tsoki don da gani suma kayan matseta zasuyi sosae gashi lace d'in ya Matuk'ar burge Gwaggo don ya had'u sosae kuma ko ba'a fad'a ba da an kalleshi an san mai kudine sosae, k'arshe dae da takaicin ya isheta sai ta jawo ledar kayan ta cusa su ciki ta ajeta can gefe taci gaba da aikinta cikin ranta kuwa takaicin Fatuu ne k'unshe,

(Gwaggo ai ba laifin Fatuu bane ita kadai, harda haisam da ya goya bayan ayi mata shima yakamata kije ki hukunta shi gaskia🤣)

A ranar bayan gama sallar asham atare da haisam suka nufi falon hajiya kamar dae kusan ko yaushe, basu dad'e da shiga ba itama Hajiyar ta fito jikinta sanye da hijab ta zauna suka ci gaba da yin fira sai dae tafi yi da Fatun, suna cikin yin firar ne Hajiyan ta juya tana ma Haisam zancen tafiyarsu Abuja jibi wato daren salla, har saida gaban Fatuu ya fad'i duk da tasan dama indae Hajiyan bata je Umrah ba to k'aramar sallah a Abuja take yinta babbar salla ce take yi anan, gaba d'aya jikinta yay sanyi jin harda Ya Handsome d'in za'a tafi lokaci guda walwalarta ta dushe, koda ya rakota lokacin zata tafi gida shiru tay mashi sa6anin yadda ta saba suna tafe tana mashi surutu, daren ranar dae cike da kunci ta kwanta har bacci ya kwasheta ba kuma komae yaja hakan ba sai don tunda tasan Haisam bai ta6a tafiya ba, ko lokacin baya kafin azumi daya tafi lagos shida Abbas sam bata san bai gari ba don in taje bata iske shi ba sai tai tunanin ya fita ne saida ya dawo ranar Monday da yamma taje bayan an taso su daga islamiyya ya bata tsaraba anan ne tasan tafiya yayi yanzu kuma tasan in suka tafi sai sun dade don in hajiya taje sallar tana dadewa bata dawo ba,

Readers Also Read