Kenza eBookz

Auren huce haushi complete - Chapter 13

Auren huce haushi complete - Chapter 13

Auren huce haushi complete Chapter 13: Auren huce haushi complete Chapter 13. "To magaji babu yanda za'ayi haka Allah ya hukunta sai hakuri". Bayan…

3,639 words

"To magaji babu yanda za'ayi haka Allah ya hukunta sai hakuri". Bayan tafiyarsu da Kamar awa daya Abdul Hakeem ya shigo ya fadawa Ammah tazo Abba Yana kiranta. A bedroom dinsa ta sameshi Yana tsaye ya goya hannunsa a baya Yana Dan Kai kawo a tsakar dakin. Sallam tayi Masa ya amsa sannan ya sauke hannunsa ya nufi gefen gadon inda Ammah ta zauna tana tambayar "Lafiya kuwa Abba meya faru Naganka a haka?" Ajiyar zuciya ya sauke Yana fadin. "Da matsala gaskiya yaron nan ne yazo a rikice yana kuka Kamar yaro karami da kyar muka lallashe shi nida Abdul Hakeem ga mahaifiyarsa da 'yan uwanta kingansu dai nasan mazan ne suka ce ba ruwansu shine ita da kanta ta taso tazo wallahi hawaye bibiyu ta rinka yi min akan na rufa Mata asiri na warware wancan auren a maida kan Musbahu abin har abin tausayin wallahi, shi yasa na turosu cikin Dan ku Basu hakuri tunda wancen zance ya wuce Kuma ji nayi da nauyi na Kira malam wallahi tunda ganin Mahmud nake Kamar Dan cikinsa Kinga na Kira shi akan maganar ai Bai kyautu ba, to bayan sun tafi ne Abdul Hakeem ya Kira Hassan ya fada masa shine ya kirani Yana min magiyar Dan Allah a rakata dakinta yau basai gobe ba da tun farko ma ankaita da hakan Bata faru ba yasan wasu ne daga nan zasu Gaya Masa tunda Yana da mutane sosai suce ai tana gida ma yayi bata tare ba suyi tunanin ko Babu auren ne, Dan haka Nima nayi na'am da maganar tasa, kuje kuyi duk abinda ya kamata da magariba zan mikata dakinta da kaina in Sha Allah, na Kira malam ma na fada masa."

"To hakan yayi duk abinda ka yanke dai dai ne Allah ya nuna Mana lokacin".

"Amin ya amsa".... ✨✨

AUREN HUCE HAUSHI ✨✨ ❤️❤️ ❤️❤️ 💋💋 💋💋

MAMAN FATIMAH.

PAGE SEVENTEEN (17)

_________ Karfe biyar mai kyau motar da Alhaji Jafar ya tuko da kansa daga shi sai Zahra a ciki daga bayansa Kuma Abdul Hakeem ne a wata motar ya biyo Abban nasu bisa umarninsa,suka dira kofar gate din gidan Zahra,sau biyu Abban yayi horn Mai gadin ya leko da yaga Alhaji ne da kansa tunda daman ya San Alhajin farin sani yayi sauri ya bude kofar suka shigo gaba daya, da sauri Mai gadin ya karaso Yana budewa Alhajin kofa Yana gaishe shi yayin da Abdul Hakeem ya budewa Zahra ta fito suka zagaya Gurin da Abban yake, Abdul Hakeem suka gaisa da Mai gadin sannan Abban ya Kama hannun Zahrar ya nufi kofar main falon da ita, tasha farar laffaya Mai adon kananan flowers pink, jikinta kamar an Mata barin turare sai tashin kamshi take Mai Dadi. A bakin kofa suka Hadu da Mahmud din ya nufo kofar da sauri Dan Yana bedroom dinsa yaji shigowarsu tun bayan anyi la'asar Baba malam yace Alhajin yace ya same shi a can gidansa da yamma za'a kawo Masa iyalinsa. Matsawa Mahmud din yayi daga bakin kofar Yana yiwa Abban sannu da zuwa sannan ya mikawa Abdul Hakeem hannu suka gaisa, kan kujera Abban ya zaunar da Zahra sannan ya umarci Mahmud daya zauna kusa da ita shi Kuma ya zauna a kujerar dake kallonsu, Abdul Hakeem Shima ya zauna, sai falon ya dauki shiru, gyaran murya Abban yayi kafin yace "Abdul Hakeem yi Mana addu'a' bayan yayi doguwar addu'a sun shafa Abban yace "To Mahmud ga matarka nan na kawo maka bani na baka ita ba Allah ne ya baka ni nawa idawa ce, gata Nan amanace a gurinka kada ka zalunce ta duk inda yanayin rayuwa ya kaiku na baka ita ne saboda na yaba da nagartarka na Dade Ina monitoring dinka ban tabaji ko ganin abun ashsha ba a tare da kai, kullum addu'ata Allah ya bani ikon sauke nauyin marainiyar Allah dake hannuna, kuma Alhamdulillahi na sauke gata nan marainiya ce Bata da uwa Bata da uba ba wa ba kani ita kenan iyayenta duka suka rasu suka barta, kada ka zalunce ta Dan girman Allah ka tausaya Mata saboda Mai rauni ce, ka zamar Mata uwa uba abokin Shawara kuyi dariya tare kuyi kuka tare ka jibinci lamarinta gwargwadon iyawarka. Ina Kuma Kara gode maka bisa share min hawayena da kayi baka watsamin kasa a ido ba lokacin Dana baka aurenta, na gode kwarai Allah ya saka maka da Alkhairi ya yaye maka damuwarka ya kawo maka mafita a bisa lamuranka". Suka amsa da "Amin" Sannan yaci gaba da fadin "ke Kuma Uwata ga mijinki nan kiyi Masa biyayya abisa abinda Bai sabawa Allah ba, ki girmamawa shi ki kiyaye bacin ransa ki kiyayie mutuncinsa da rike Masa sirrinsa kindaraja mas iyayensa da 'yan uwansa lokacin da Allah ya hukunta ku hadu dasu,nkiji tsoron Allah a cikin zamanta kewarku ki saka hannu ki Barbi duk abinda ya biyo bayan aurenki dashi Mai Dadi ko sabanin hakan. Dan Allah ki kwantar da hankalinki kiyi hakuri da abinda Allah ya hukunta a kanki komai Kika gani rubutacce ne daga Allah sai dai mu 'yan adam mu karasa shi, Amma tun ran gini tun ran Zane dama haka kaddarar take, ko shi mijin naki idan yayi nazari zega wata kila wannan kaddarar auren ce ta rabo shi da asalin inda yake, to Dan haka kowa ya rike tasa kaddarar wata Rana sai labari komai na duniya Yana da iyaka ikon Allah ne kawai bashi da karshe, Allah yayi muku Albarka ya kauda fitina a tsakaninku ya tabbatar da Alkhairi a cikin rayuwar aurenku, Mahmud sai anyi hakuri da Mata su masu rauni ne kwarai da gaske". Tunda Abba ya Fara magana yaji kamar ya dauko wani gaigimemen dutse ya Dora Masa aka. Cikin ladabin da baisan Yana dashi ba ya furta "in Sha Allah Abba ba wata damuwa Kuma amana na karba na rike Allah ya bani ikon saukewa nike da godiya Allah ya saka da Alkhairi ya Kara Nissan kwanaki masu Albarka" "To Masha Allah, Abdul kayi Mana addu'a mu tafi kada almuru tayi Mana a nan, Uwata ki daina kukan Nan haka bana sonsa kiyi hakuri kowa da haka ya girma Allah yayi Miki Albarka, ga makullin motarki wadda mukazo da ita takice na sai miki, kudin dayar ta wajen Abbie suna gurin Alhaji muttaka tunda aka sayar da ita nace ya juya Miki kudin zuwa lokacin da za'a bukaci wata motar Dan haka in Sha Allah cikin sati Mai zuwa za'a kawo Miki dayar ma". Suka tashi suka fita Mahmud yayi musu rakiya har gurin mota Saida suka tafi sannan ya dawo ciki, a inda ya bar zahrar anan ya sameta ta kwantar da kanta a kan cinyoyinta tana kuka Mai tsuma zuciya a hankali ya zauna kusa da ita yasa hannu ya dago kanta daga jikin cinyoyinta idanunta a rufe sai tsiyayara da ruwan hawaye suke. Ba zato ba tsammani kawai taji ya sakata a girjinsa ya kwantar da kanta ya saka hankici Yana share Mata hawaye, daya hannun Kuma Yana tapping din bayanta kamar yanda ake yiwa yaro idan ana so yayi shiru Yana kuka, jikinta gaba daya ya dauki rawa ta taso da niyyar zare jikinta Dan wani Abu takeji duk ilahirin jikinta Amma Dan bawan Allan nan yayi kememe yaki sakinta ba arziki ta hadiye kukanta, sai sauke ajiyar zuciya kawai ba kakkautawa saida ya tabbatar ta Samu dan nutsuwa sannan ya saketa Yana fadin " sorry Baby ki daina kuka bana son kuka Sam koda kuwa na karamin yaro ne". Hannunta ya Kama ya mikar da ita ya nufi daya daga cikin bedrooms dinta guda biyu da suke mallakinta, Saida ya zaunar da ita a gefen makeken gadon sannan ya juya ya nufi kofa Yana fadin " it's time for prayer" Ya fice Yana ja mata kofa.

Sai ta dauki kusan minti biyar kafin ta Samu kuzarin warware Laffayar dake nannade a jikinta, doguwar rigar material ce a jikinta anyi Mata dinkin fitted gown tayi Mata kyau sosai kofar data gani ta nufa tasan toilet ne, lokacin data shiga abin ya girgizata irin kayan amfanin data gani a ciki ita ba bakuwar abin bace tasan ba kananan kudin aka narkar ba a cikinsa, abin ya Bata mamaki sosai sai dai wa zata tambaya? ta Jima a ciki kafin ta dauro alwala ta dawo dakin. Ido ta ringa wurgawa ko zata ga sallaya tunda ita dai bakuwa ce a dakin can gefen sofa taga wani stool kamar coffee table da sallayun akai ta shimfida ta Fara sallah. Tana cikin sallah ne taji kamar karar door bell kamar sau biyu, Saida ta idar ta tashi ta fito har lokacin tana share hawaye jefi- jefi, gurin kofar ta karasa ta bude Sajida da Hameeda da Mujiba ta gani ai batasa lokacin data fada jikin Sajida ba tana dakin kuka Mai tsuma zuciya. Ciki suka shigo Sajida na fadin "haba bestie wallahi Dana San har yanzu baki daina kukan Nan ba da bazamu biyo bayanki ba, haba Ashe bazaki karbi kaddara yanda tazo Miki ba? ki Kuma godewa Allah a kowane Hali Kika Samu kanki, bake Kika halicci kanki ba ballantana ki tsarawa kanki yanda Zaki rayu, kin taho kina kuka duk kin dagawa Ammah hankali itama, kin kyau kenan? haba kiyi hakuri Dan Allah ki share hawayenki wallahi nasan yanzu zuciyar masu binki da mugun nufi tana can kamar zata fashe Dan ba haka suka soba duk da bansa daga Ina matsalarki take ba, ai kodan makiya kin kwantar da hankalinki ki rungumi mijinki ki ba mara d'a kunya, Amma kin tsaya kina wani Abu kamar wata karamar yarinya" Tayi tsaki tana kallon zahrar da tayi kozai kozai ido ya kode Mata abinka da farin mutum. Suma su Hameedar ban baki suka dunga yi Mata, da kyar ta hadiye kukan ta kallesu tana fadin "wallahi bazaku Gane bane ni kadai nasan me nakeji, komai ya kwance min Sam duniyar bata mun dadi". "Hakurin dai zakiyi ki Kuma yawaita addu'a in sha Allah komai ze wuce kamar ba'ayi ba, muda muke son next year by now mu dawo suna". Sajida ta fada tana murmushi. Wani kallo zahrar tayi Mata ta juya kanta gefe tana fadar "Allah ya kiyaye min wata haihuwa can". Mujiba ce ta kwashe da dariya tana fadar "A'a Banda cika Baki dai 'yan Mata Nan da labari yasha banban zamu tsinceki kina faman 'yan amaye amaye, lokacin ne Zaki gane Baki da wayo ko ba wata haihuwa can ba?". Zumburo Baki tayi tana fadin "sai kiyi Kuma haka kawai Zaki jaza min, wani ciki ko dadin fada ma Babu". Saima zahrar ta zame ta kwanta, tana jinsu suna ta faman zolayar ta har aka Kira sallar insha'i a Nan sukayi sallah kafin su shiga Kara gyara Mata Fallon da Kara masa freshner da turaren wuta Hameeda ta Kara karfin A C a falon ta gyara cutains din, bedroom din data fito suka shiga Mujiba bakinta ya kasa shiru tunda dai suka Samu zahrar ta daina 'yan koke koken sai ta balle da santin gidan Dan bayan sun idar da sallar ba inda Bata shiga ba ta leka can ta shiga can bedroom din Mahmud ne kawai Bata shiga ba tunda a rufe yake, fada take "wallahi zahra ki Kara godewa Allah, irin wannan haduwa haka wallahi ko makiyi Saida yaki fada Amma dai duk wani gata kin same shi sai dai fatan zaman lafiya kawai". Ita dai Zahra ba baka sai kunne.Dan ita kadai tasan abinda ke Kai komo a zuciyar ta, su inda suka dosa daban ita inda ta dosa daban, ko tayi musu bayani ba ganewa zasuyi ba, domin su duka ba wadda ta tab'a shiga irin gararin data shiga, rayuwa Rumi rumi saika Gama sakankancewa da mutum Rana tsaka Abu ya lalace, uwa uba ganin da tayiwa Musbahu ba karamin famu yayi Mata ba, saboda da ta cire shi daga ranta kwata kwata ta hakura, Amma tana ganinsa komai ya rikice Mata da tana zargin kamar da niyya mamansa tayi haka saboda ya taba fada mata Maman nasa taso ya auri 'yar Yayarta shi Kuma ya ringa sharewa ana haka ne Allah ya had'a shi da zahrar abinda ya kawo karshen wancan dambarwar kenan. Amman tasowar mamansa da 'yan uwanta dashi kanshi takanas ta kano har Azaren don bada hakuri da neman gyara idan lamarin Mai gyaruwa ne, sosai abin ya tashi hankalinta, wata sabuwar soyayyar sa ce ta sake bijiro Mata idan tana tuna yanda yaci buri a irin wannan ranar da za'a kawo Masa ita a matsayin matarsa ta sunna halalinsa, irin abinda yake fadin ya tanadar Mata ita a wancen lokacin idan Yana fada kamar zata nitse kasa dan kunya Amma shi ko a jikinsa. Wasu sabbin hawayene suka zubo Mata masu zafi tana ayyana shike nan komai ta Zama tarihi, ga inda kaddara ta kawo ta gurin da ba'asan darajarta ba ko alama sai aukin taba Mata jiki da yake Wanda ta fashimci hakan tun haduwarsu ta farko, ba kunya ya wani saka hannu ya rungumota Wama ya sani ko Dan duniya ne aka hadata dashi, tunda ance ba Wanda yasan asalin sa kuma tasan yanda yake din nan ko bashi da sisi mata zasu ringa kawo Masa rida tunda sun ganshi smart dashi. Wani tsaki tayi tana ayyana to Ina ruwanki da wani smartness dinsa. Mahmud Bai dawo gidan ba sai bayan sallar insha'i ganin takalma yasan akwai baki cikin gidan baya raba daya biyu 'yan uwanta ne ko kawaye, dakinsa ya wuce yayi wanka ya canza kaya ya fito falo, bai shiga dakinta ba daga inda yake yana jiyo mganganun bak'in, ita dai baiji tata maganarta ba Sam Zama yayi yana daddana wayar hannunsa. Acan Kuma dakin Zahra Ya Abdul Hakeem ne ya Kira wayar Sajida Yana fada Mata su fito su tafi ya dawo daman lokacin daya basu kenan bayan sallar insha'i lokacin daya kawo su. Sun fito falone suna zolayar Zahra Basu kula da mutum ba sai da suka sauko daga steps din da ze sada ka da corridor din bedrooms din suka ganshi a zaune Yana ta faman Danna waya, kallo daya Zahra tayi Masa ta kauda Kai haka kawai taji gabanta ya fadi, ta rasa wace irin masiface wannan. Kansa ya dago yana amsa gaisuwar su Sajidar Yana fadin "har zaku koma ne?". Hameeda ce tayi farat tace "To ba dole mu tafi ba yallabai tunda angon yaki zuwa ya sayi bakin amaryarsa ba Yana ganin Mai araha ce bai Sha wahalar komai ba aka bashi ita". Ba Zahra da aka ciwa fuska a fakaice ba hatta Sajida da Mujiba Saida sukaji kamar kasa ta nutsa dasu a gurin Dan kunya, gaba daya suka zubawa Hameeda ido har shi uban gayyar, wani abune Wanda Zahra Bata taba tunanin Hameeda zatayi Mata ba, dan wannan cin fuska ne qarara bako kawaici a cikin maganar ko kad'an. Zahra kasa gaba ko baya tayi ta tsaya a gurin kawai, su sajida ma rasa ta cewa sukayi shi kuwa uban gayyar wayar dake hannunsa ya aje Yana kallon Hameeda direct kafin yace " waya fada Miki Mai araha ce bakiji sunanta ba? Zahra fa kinsa ma'anar sunan kuwa? tauraruwa fa a cikin taurari a gurinki take Mai araha Amma ni a gurina tafi zinari daraja, bari na baku indai abin sayen Baki ne in dai shi ne abinda ke shaida Kima da darajar mace a irin wannan ranar gurin kawayenta, ina zuwa". Ya fada Yana mikiwa ya nufi hanyar bedrooms dinsu, tunda ya wuce zahra ta juya da sauri ta nufi daki Bata yi musu ko sallama ba.

Bai jima da shiga ba ya fito da wata katuwar leda da Kuma envelope guda uku a hannunsa. Yana zuwa directly Hameeda ya nufa ya Mika Mata ledar da envelope daya sannan ya baiwa Sajida da Mujiba Suma dai dai Yana fadar "ga kayan sayen bakin Nan a cikin wannan envelope din Kuma kunsha ruwa a hanya". Ba kunya Hameeda tace yanzu naji magana ai shi tuwon girma miyarsa Nama mun gode". Taja katuwar ledar tayi gaba abinta mujiba ma tabi bayanta har suka fita Sajida Bata motsa ba ita kollon ikon Allah take akan Mahmud Wai wannan shine Almajirin da ake ta yayatawa a aurawa Zahra har Hajiya Mama na yiwa Abba magiyar kada ya Fara wanna danyan aikin tab wallahi da sake ita tafa abinda ta gani ga tare dashi ai da hasashe ne take yanzu be taga zahiri. Ganin sun fita yasa sajidar aje Masa envelope dinsa a gefen shi tana fadin "kabar abinka na gode, ni fatana ka rike min bestie da mutunci da amana yafi ka bani duk abinda ka mallaka, bansan Kai ko waye ba Amma jikina Yana bani kana boye wani Abu tun lokacin Danazo gidan nan da Kuma irin kayan danaga an kawowa bestie nasan Kai ba kaskantanccen mutum bane, Ina hadaka da girman Allah kada ka bautulcewa Iyayenta da suka baka ita kaji tausayinta marainiya ce, Dan Allah nasan duk inda ka fito ba karamin guri bane ka Zama garkuwarta ka zamar Mata bangon da zata jingina taji dadi duk rintsi. Dan Allah ka Bata kulawa Zahra 'yar gata ce kaddara ce ta zaunar da ita a kasar nan da Kuma kawaicin kakanninta suka hakura suka barwa Ammah ita, Dan Allah ga amana Nima na baka kamar yanda iyayenta suka baka kaji tsoron Allah a cikin zamantakewar ka da ita na San Nan gaba zaka samu zabinka ko Kuma tuntuni kana dashi Dan Allah kada ka wulakanta ta.. na rokeka ka Zama adalin shugaba a gurinta idan kaji yanda rayuwa ta dunga jujjuyata zaka tausaya Mata matuka, Dan Allah badan niba...." Da tayi gaba ta nufi kofa Bata taji me ze fada ba domin hawayene suka ciko Mata idonta idan tace zataci gaba da magana kuka zata fasa masa ne. A bakin kofa sukayi kicibus da Mujiba wadda ta dawo kiranta ganin shirun ya yi yawa.

✨✨ ✨✨ AUREN HUCE HAUSHI

✨✨ ✨✨

💎PAGE EIGHTEEN💎

STORY

AND

WRITTEN

BY

MAMAN FATIMAH.

_________ Bayan wucewar Sajida Mahmud ya Dade Bai tashi ba, kwarai yarinyar ta burge shi matuka, da gaske take son Zahra domin furucin da yarinyar can tayi yayi touching dinta sosai, lallai ya tabbatar son da take yiwa Zahra bana Wasa bane shi tun lokacin da Magaji ya fada masa ta baro syprus Dan kawai ta halarci bikin zahrar ya jinjina Mata duk da suna hutu Amma yasan irin wadannan daliban ba kowane hutu suke zuwa gida ba sai dai idan iyayen sun sunci sun tada Kai. Envelope din data aje masa ya kalla yayi wani killer smile ya zurata a aljihun Wando Yana Kara wani murmushin Wanda shi kadai ya barwa kansa sani. Yaso ya shiga dakinta sai ya share kawai Dan yasa baya raba daya biyu kuka take Dan da gaske koshi baiji dadin furucin da akayi Mata ba Kai tsaye bako rusunawa a ciki. Lokacin da Abdul Hakeem ya Parker motar a parking lot na gidan Sajida ce ta farkon ficewa daga motar zuciyar ta na Mata wani zafi Dan da gaske idan ta tsaya zata shatawa Hameeda rashin mutunci ne na karshe Wanda zata Dade Bata manta ba, dan da gaske an shirya ne kawai dan a tozarta Zahra a gabanta mijinta, shi yasa kenan lokacin da zasu ltafi ta shiga part din Mama Kiran Hameedar akan ta fito suje, taji Salma na fadin saura Kuma ki kasa fada ki dawo Mama ta tumurmushi banza, ita Sam Bata kawo komai ba kawai dai ta dauka wani abune can tsakaninsu saida hakan ta faru ta Gane me ake nufi da waceccen maganar. Tana jin Mujiba na kwala mata Kira lokacin data nufi karamin gate wanda ze sada ta da cikin gidan, batabi ta Kanta ba tayi wucewarta ciki ta kyalesu. Koda ta shigo part din Ammah directly bedroom din da suka kwana ta wuce tana yiwa su Aunty Hasana sannu har ta shiga ta fito tana fadin "Aunty Dan Allah idan su Hameeda sun shigo kice su raba kayan su biyu kwai Banda ni". Ta koma da sauri Dan tana jiyo maganar su a kusa alamar Nan suka nufo.

Tun shigar Zahra bedroom din Nan ta kwanta rub da ciki take risgar kuka Kamar ba gobe, Hameeda ta Bata mamaki Bata taba zaton irin wannan ranar ba a tsaknainta da Hameeda cewa take ko kowa ya nuna Mata naqi a bangaren Mama ita kadai zata tsaya a bayanta duk runtsi duk wuya saboda a baya ba Mai cin fuskar ta a dakin Mama makukar tana gurin Koda kuwa mamar ce, Amma yau Hameeda da bakinta Kuma a gaban idonta take fadar magana irin wannan, to meya canzata daga Hameedar data sani Mai sonta da kaunar ta da Bata kariya da kulawa a kowane janibi. Saida tayi Mai isarta har ta baiwa uku lada, sannan ta hakurkurta da Kanta ta tashi zaune. Kanta taji ya Sara Mata a hankali ta furta "Alhamdulillahi ala kulli halin. Allah na gode Maka duk abinda kayi nufi a gareni na karba ka bani ikon cinye jarabawar Nan dan isar Annabi Muhammad s.a.w.w". Hannu tasa ta dafe Kanta dake matukar Sara Mata, wannan wace irin rana ce a gareta? ranar da duk wasu masoya keda tarin burika a Kanta Amma ita ranar ta ta farko ta kasance ranar cin fuska daga inda Bata taba zato ba, ba tarairaya duk burin da suka dade sunaci na irin wanna ranar ya tashi a banza. "Astagafirullah Ubangiji ka yafe min zunubina daya janyo min irin wannan rayuwar Mai tarin qalubale a cikinta". Ajiyar zuciya ta sauke tana Kara dafe Kanta da gaske jinsa take Kamar ze rabe gida biyu, ba zato ba tsammani taji an bude kofa Bata daga Kai taga ko waye ba dan kamshinsa kadai ya Isa ya fada Mata Mai shigowar, Kuma ma waye ze shigo haka Kai tsaye a irin wannan lokacin, sallama yayi Mata Amma Allah baisa ta amsa Masa a fill ba ta dai amsa a zuciyar ta.

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull