Kenza eBookz

Babban gida takun farko - Chapter 5

Babban gida takun farko - Chapter 5

Babban gida takun farko Chapter 5: Babban gida takun farko Chapter 5. “Ammi Ammi Ammi!” “kai Badi'a irin wannan ƙira haka ba ƙaƙƙautawa?” ta faɗa yayin da…

3,224 words

“Ammi Ammi Ammi!” “kai Badi'a irin wannan ƙira haka ba ƙaƙƙautawa?” ta faɗa yayin da take fitowa daga bedroom ɗin ta. “Ammi wallahi amaryar gidan su Zahrah abun tsoro ce, kamar ƙaruwa take. Ammi har tsayar da Ni tayi tana tambaya ta wai wa yake aiko Ni na kawo abinci” “subhanallah sai kika ce mata MEH?” “cewa nayi Ni nake Aiko kaina manah" “yauwah good girl, u're very clever daughter, Allah yayi miki albarka” “Amin ameen Ammi na”

Kawu bai shigo gida ba sai wajen 11:00pm na dare, yana shigowa kuwa ya fara washe baki yana nufar ɗakin amaryar shi. Lokacin tayi shirin ta ta zaba kwalliya tamkar zata fita yawon bariki. Da sauri Kawu ya nufi yadda take. Peck tayi mishi haɗi da hugging nashi “sannu da dawowa mai gida na“ Cike da ɗauki yace “yace sannu amarya ta abar ƙauna ta” Ɗan sake shi tayi, “oyah muje kayi wanka kaji” ba musu Kawu ya biyo ta suka fito da yake toilet ɗin su a waje yake. Cike da ƙwarewa a harƙar barki ta kama hannun shi ta raka shi bayan yayi wanka suka dawo tare ta taya sanya kaya. Abincin da Rubber ta aiko musu da yammah ta zuba mishi, bayan yaci yayi hani'an tukun ya ɗago yana kallon amaryar.

“ko wannan matar ko ta dawo” Cikin halin ko ina kula tace “wace mata kenan?” “ina nufin wannan banzar mai ɗakin can” Ita kuwa jin ya ambaci matar shi da banza farin ciki ya mamaye zuciyar ta, cike da murnar samun nasara a Oman ɗin ta tace “eh toh wata jemammiyar mata da yarinya dai sun shigo lokacin ƙawa ta Asabe tana nan, ai ka santa?” Cike da ƙaguwa yace “eh na san Asabe ƙawar ki” “toh matar tana shigowa ita da yarinyar ta suka yo kan mu suna tambayar wacce ce daga cikin mu amarya. Da Asabe ta nuna musu Ni sai suka kwashe da dariya, duk fushi da rashin mutunci irin namu kasa mata magana nayi ina jin ta riga da ta asirce Ni ne” Ta faɗa tana sakin kukan munafurci. Shi kuma sai lallaɓa ta yake kamar wata uwar sa. “yi haƙuri amarya ta ki faɗa min me ke faruwa manah, tabbas duk wanda ya taɓa min ke zai ga fushi ne” Ɗan guntun hawayen ta ta goge ta ci gaba da fuskantar shi “kawai matar sai ta rufe mu da zagi, a nan ta kora Asabe sannan ta juyo kaina, yarinyar da suka shigo tare ita ma ta ɗaurabkan yadda matar ta tsaya sai zagi na suke wai Ni karuwa ce, abun babu daɗi” ta ci gaba da kukan munafurci nata. “shine na basu haƙuri da ƙyar suka haƙura kuma sun ce idan na faɗa maka sai ta min shegen duka. Daga haka ta juya ta nufi ɗakin gefen can naga ta buɗe, sai a lokacin na gane ita ce matar ka da kuma ƴar ka”

GA FA WANI SALO DA AMARYAR KAWU TA FARA MUJE ZUWA, BA'A FARA WASAN BA. KUYI COMMENTS DA YAWA DON SHINE ƙWARIN GUIWA TA.

ITZ DIAMOND LADY 💎 Oum Zainab

______________★★★_______________ Typing 📲 🏡𝙱𝙰𝙱𝙱𝙰𝙽 𝙶𝙸𝙳𝙰🏡 (𝔗𝔥𝔢 𝔟𝔦𝔤 𝔥𝔬𝔲𝔰𝔢🏠) ★TAKUN FARKO★ [Labari/Rubutawa] 🄳🄸🄰🄼🄾🄽🄳 🄻🄰🄳🅈 𝑂𝑢𝑚 𝑍𝑎𝑖𝑛𝑎𝑏🖊️

PROLOGUE

𝕻𝕬𝕲 0️⃣8️⃣

Bazan manta da ke ba ƙawa ta Murjanatu Abdulwahab Yusuf, ina matuƙar ƙaunar ki saboda Allah. Na gode da ƙaunar ki gare Ni. Ubangiji ya ƙaunace ki.

SHARE AND COMMENT PLEASE! _______________★★★________________

Ran Kawu idan yayi dubu toh duk ya ɓaci a fusace ya fita daga ɗakin amarya yayin da ta daka tsalle saboda murnar cin nasara. Yana isa ko sallama bai yi ba ya fara buga ƙofar ɗakin yayi shaye da mamaki maka ta buɗe Bata aune ba kawai taji sauƙar mari s fuskar ta. Bata tsaya ba kawai ita ma ta rama. Mamaki ne ya kama Kawu wai yau shi Madina ta mara don ya mare ta, gaskiya akwai matsala. A kasalance ya koma ɗakin amarya yana huci..

“mai gida ba dukan ta kayi ba koh, bana so ko kaɗan taji haushi na” Murmushin yaƙe yayi “shikenan mata ta damah warning na kashe mata” “yauwah mai gida ammah gobe ya kamata ace an raba mana girki da kuma kwana ko” Shaye da mamaki yake kallon ta kafin yace “ai nikam kullum ina nan, MEH zanyi da waccar matar kuma” “aahmai gida ba za'a yi haka ba, zata ga kamar ina zaluntar ta ne” nan kuwa cikin ranta daɗi take ji. “aah mu bar zancen nan, Ni anan zan je kwana” “shikenan tunda ka ce haka” ta ɗanyi shiru sannan ta ci gaba. “sai batun girki, ai yanzu tunda ta dawo sai a raba“ “ke dai zan ke baki ki girka, ita dama can ita take ciyar da kan ta da ɗiyar ta” Daga haka ya miƙe zuwa gado, su basabun ba Kawu an samu gadin banza. Ita kuwa amarya farin ciki ne fal ranta.

Mamah kuwa tunda ta rama marin da Kawu yayi mata ta fara jin wani sanyi a ranta, kullin da take yawan ji a ƙirjin ta sai taji kamar ya ragu....ɗaki ta koma tayi alwala sannan ta fara jera nafilfilu daga nan bacci ya ɗauke ta. Washegari da wuri suka tashi, Zahrah ta shirya cikin uniform ɗin ta sannan ta zauna jiran Badi'a, ba'a jima ba ta shigo hannun ta ɗauke da basket, “mamah Ina kwana" “lafiya ƙalau Badi'a ya su Ammi?” “suna lafiya, ga breakfast in ji Ammi Zahrah ki samu ki shirya kafin Abba ya gama breakfast” “toh Allah ya amfana, ki gaishe da Ammi” “toh" sannan ta juya zuwa gida. Chips ta zuba a plate ta fara ci, tana gamawa tayi brush ta fito. Sai da ta shiga ta gaida Ammi suka fito ita da Badi'a don jiran Abba. Abba na fitowa suka gaida shi sannan suka tafi sai school.

Rayuwar school tana yi wa Zahrah daɗi a halin yanzu don kuwa cikin sati da ƴan kwanaki ta fara gane darasi sosai, uncle Hashim na yin iyakar iyawar shi wajen ganin Zahrah ta na koyon abubuwa. Alhamdulillah, da yake ƙwaƙwalwar ta na ja tuni tayi nisa. Ga kuma Badi'a ita ma ba'a barta a baya ba wurin taimaka mata.

Yau suna da English, uncle Hashim ya shigo yayi delivering class ɗin shi kuma kowa ya gane daidai gwargwado. Bayan ya fita aka yi sauran three classes ɗin daga nan aka tashe su. Kamar kullum.ya Abba ne ya zo ɗaukar su, suka gaida shi. Bayan su isa gida kowa ta wuce gidan su. Zahrah na shiga taci karo da amaryar Kawu na girki, ɗauke kanta tayi don ita ba mai shiga abun da ba'a sanya ta baneh. Kamar daga sama taji Muryar matar “ƴata babu gaisawa ne?” Harara Zahrah ta cilla mata tare da nufar hanyar ɗakin Mamah. Murmushin mugunta amaryar Kawu tayi sannan ta ci gaba da girkin ta.

Wanka tayi sannan ta ɗauko uniform ɗin ta na islamiyya ta zura..Mamah na fitowa daga bayi daidai isowar Badi'a da abinci ita ma cikin shirin ta na islamiyya. Sannu Mamah tayi mata ta amshi abincin.

Zahrah na gama ci ta ɗauki jakar ta ta fice, da yake islamiyya ba wani nisa sosai daga gidan su yasa suka taka da ƙafa. An samu sauyi sosai don yanzu Zahrah tana maida hankalin ta ga karatun ta na islamiyya, kuma hadda sosai take bayar wa.

Bayan sun dawo daga islamiyya wanka kwai tayi ta sauya kaya sannan tayi wanki. Tana gamawa ta fice zuwa kasuwa wurin Mamah. Sai bayan maghrib suka dawo. A daren suka wanke kayayyakin amfanin su kafin suyi dinner da aka aiko daga gidan Ammi.

Haka rayuwa ta ci gaba a gidan Kawu, babu abun da ya taɓa haɗa Baba Amarya da Mamah har suka shafe watanni uku a gidan sai dai a ɓangaren baba amarya kullum akwai abun da take ƙunsawa kuma har yanzu Kawu baya ciyar da Mamah da Zahrah. A irin wannan lokacin ne su Zahrah suka fara exams, Alhamdulillah an gama kuma sakamako yayi kyau, Badi'ah Kabir Umar ita ce first sai Umar Yusuf sai kuma Zahrah Abdulkarim Kuru. Farin ciki kamar suyi yaya Abba yayi musu kyauta ta Musamman kuma lokacin Hutu Badi'a da Zahrah suka tafi Jos gidan yayar Ammi.

Hajiya Barira yayar Ammi ce, uwar su ɗaya uban su ɗaya. Tana da yara huɗu, yaya Affan, Aunty Fadila, Aunty Aisha sai ƙaramar su Khady.. sun samu tarba ta musamman daga wurin Hajiya da kuma yaranta..

Yaya Affan baya nan yana Cyprus, a can yake karatu, Aunty Fadila da Aunty Aisha su kuma sun gama secondary sun fara karatu a ATBU ammah an saka auren su tare. Khady kuwa sa'ar su ce, yarinya mai ɗan karen kinibibi da rashin ji, rayuwar su a Jos tayi musu daɗi, sai da suka shafe sati biyu suka dawo Bauchi. Abun mamaki duk budurin nan Kawu bai san Zahrah baya nan ba, abinci kuwa kullum sai Ammi ta shigo da kanta ta kawo.

Baba Amarya abun na ci mata tuwo a ƙwarya saboda haka tun da Kawu ya dawo take mishi kuka wai ita ta gaji. “nikam na ganiii zan bar gidan nan don har ga Allah bazan iya rayuwa cikin sa ba” “yi haƙuri amarya ta meh aka yi miki har kika gaji da gidan” Share ƙwallar idon ta tayi tace “Wannan matar taka bata son zaman lafiya, haka kawai sai ta turo yarinyar ta mai zubin Mayun nan tayi ta zagi na, yarinyar nan har da zubar min girkin da nayi maka wai kowa ya rasa tunda su baka basu, nikam tsiro nake kada wata rana baka nan su yanka Ni" Rungume ta yayi jikin shi “aah ki bar Ni da su, zan hukunta su kuma ba zasu ƙara shiga rayuwar ki ba, ke da gidan ki ai ina kin ce na kora su sai na kaɗa su. “uhm uhm ka bar su zasu ce nayi musu munafurci an kore su, Ni ina son zaman lafiya tare da su, suna bani tausayi” “shikenan zan bar su ammah zan gargaɗe su akan ki don baza su takura miki ba a Cikin gidan ki, Yanzu dai zubo min abinci naci”

Bayan yaci abinci yayi wanka ya nufi ɗakin mamah. Ta idar da Sallah a lokacin tana tasbihi ya shigo bata ko kalle shi ba ta ci gaba da tasbihin ta. “keeee Madina, kwana biyu ina ɗaga miki ƙafa daga ke har shegiyar ƴar ki zaku takura wa amarya ta. Kar ki ga nayi sanyi kiyi tunanin tsoron ki nake ji, wallahi daga ke har ita Zahrah zan azabtar da kuma fiye da tunanin ku akan mata ta” Daga haka ya fice a fusace, a tsanake Mamah ta bishi da ido har ya fice. Ta girgiza kanta sannan ta maida hankalin ta kan karatun Alkur'ani da ta fara.

Ranar da su Zahrah suka dawo sun dawo da goma sha tara ta arziƙi daga Jos.... kayayyakin sawa da makamantansu duk sun samu ga kuɗin da aka basu. Mamah tayi farin cikin dawowar Zahrah gida don kuwa kullum sai tayi kuka ina ta tuna ta.

Sun koma makaranta lafiya tare da ƙara maida hankalin su a karatun su both ALMUNAUWARA da kuma IMAM MAKIK. Zahrah ta zamo zakara don yanzu ana matuƙar ji da ita cikin school ɗin su. Sam bata shiga sabgar kowa in ba ƙawar ta Badi'a ba, ammah duk wanda ya shiga sabgar ta toh ya shiga sabgar ta bata ƙyale wa.

Ɓangaren Mamah ta ci gaba da suyar Masar ta a kasuwa, kuɗin kuwa tana adana shi saboda gaba, don a halin yanzu babu abunda ta nema ta rasa, abinci za'a kawo tun daga breakfast, lunch har dinner daga gidan Ammi. Sun ɗauke su tamkar jinin su hakan yasa damuwar Mamah ta ragu uwa uba yanzu babu wata alaƙa tsakanin ta da Kawu, sai ya share watanni biyu basu haɗu ba hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba lokaci ɗaya daga ita har Zahrah suka murmure jiki ya ƙara kyau. Bana amarya ma dai bata shiga sabgar su saboda bata samu damar hakan ba ammah ƙudurin ta yana nan dangane da su.

Tufafi ma dai basu rasa ba saboda Abban Badi'a yana siya musu, school fees kuwa already Yaya Ishaq ya biya mata har kammala junior studies nata.

Wasu lokutan in ta zauna ita kaɗai babu abun da ke faɗo mata sai yaya Ishaq wanda a halin yanzu bata san ya yake ba, ko yana lafiya ko akasin haka. Takan yi mishi fatan alkhairi domin kasancewar shi haske cikin rayuwar ta, sanadiyar shi yanzu ta samu wayewa fiye da da, addu'a kuwa kullum cikin sallolin ta bata mantawa da yaya Ishaq tare da fatan Allah ya dawo da shi lafiya.

Bahaushe yace sannu sannu asarar mai rai yanzu haka Zahrah sun kammala jss 1 ɗin su, sakamako mai kyau mai haskaka wa kowa mamaki yake yadda Zahrah Kuru ta zama popular cikin school ɗin duk da cewa lokacin da tazo makarantar she's nothing but a stupid girl. An now she shines everywhere gata dai yarinya ce ammah akwai ƙwaƙwalwar manya. Hakan yasa ta samu farin jini da ɗaukaka kama daga ƴaƴan uwanta students, seniors ɗin ta, teachers na baa barsu baya ba hakan duk da taimakon uncle Hashim da kuma Aminiyar ta Badi'a.

WANNAN KENAN TEAM ZAHRAH KUYI FARIN CIKI MUTUNIYAR KU TA DAGE FAH KO INA YAYA ISHAQ HAR YAU BAI NEMI CUTIEN SHI BA? HAJIYA BABS AMARYA FA TANA NAN TANA SHIRI, KO ZATA CI NASARA.

KU BIYO NI TARE DA ALƘALAMI NA DON JIN YADDA ZATA KAYA. BA'A FARA WASAN BA HAR YANZU.

DIAMOND LADY 💎🤟 CE (Oum Zainab)

______________★★★_______________ Typing 📲 🏡𝙱𝙰𝙱𝙱𝙰𝙽 𝙶𝙸𝙳𝙰🏡 (𝔗𝔥𝔢 𝔟𝔦𝔤 𝔥𝔬𝔲𝔰𝔢🏠) ★TAKUN FARKO★ [Labari/Rubutawa] 🄳🄸🄰🄼🄾🄽🄳 🄻🄰🄳🅈 𝑂𝑢𝑚 𝑍𝑎𝑖𝑛𝑎𝑏🖊️

PROLOGUE

𝕻𝕬𝕲𝕰 0️⃣9️⃣

Wannan shafi naku ne masoya littafin babban gida. Ku ci gaba da bibiyar alƙalamin DIAMOND LADY. Much ƙauna🤩😘

SHARE AND COMMENT PLEASE! _______________★★★________________

Yau rana ce ta musamman da aka ware a cikin makarantar ALMUNAUWARA ACADEMY kamar yadda ya kasance cikin tarihin makarantar duk shekara akan gudanar da bikin yaye ɗalibai -speech and prize giving day-.

Ko ina na makarantar ya ƙawatu kasancewar makarantar ta ƴaƴan masu hannu da shuni ne. A nan aka fara gabatar da programs da ke a agenda na taron.

Cikin programs ɗin akwai drama show da wasu students zasu gabatar. Drama ɗin an shirya ta ne only to motivate the students. Cikin lokaci MC ya sanar da agenda na gaba, wanda shine drama show.

Wani curtain da ya kasance tamkar decoration naga an yaye. Babu abun da ya bayyana sai herarrun seats da aƙalla zasu kai 30 daga can baya. Ta gaba ɓangaren hagu akwai evidence box sai kuma ta can tsakiya kujeru biyu da kuma tables biyu. Ɗaya ɓangaren by the right hand side wasu kujeru ne dake facing waɗannan seats sai kuma can jikin bango babban table da wata lallausar kujera.

Haka wajen ya tsaru, babu ɓata lokaci jama'a suka fara shigowa suna zama a waɗannan seats ɗin. Badi'a ce da kuma khalid suka shigo cikin kayan lawyers ɗauke da files a hannun su. Suna zama sai ga Umar ya shigo ya tsaya near the evidence box.

Maryam kuma ta zauna a seat ɗin dake facing mutanen by the right hand side. Onportunately sai ga Zahrah well dressed in judge's dress, ga kuma wasu sanye da kayan police na biye da ita.

A hankali ta ke takowa har ta iso seat ɗin da aka tanada domin ta. Kowa a lokacin ya miƙe har sai da ta zauna sannan ɗaya daga cikin police ɗin ya miƙa mata files da sauran abubuwa gaban ta.

Ba tare da ɓata lokaci ba ta ciro glasses 👓 ɗin ta ta sanya, nace MASHA ARRAHMAN, Files ɗin ta fara buɗe wa sannan ta umarci Muhammad da ya karanto cases da suke da shi. Cikin harshen turanci ya fara magana a nutse..

"Case na farko: Ana zargin Mallam Uba Idi da safarar ƴan mata da kuma miyagun ƙwayoyi tare da lalata wata ƴarinya da tazo Companyn shi neman aiki wacce a halin yanzu ta mutu. Case na biyu: Ɓarayi guda uku, Dauda, Muhammadu, Idris da shiga gidan wani attajiri don satar daga ƙarshe har ta kai ga kashe mutumin da ahalin sa"

Daga haka ya ɗan rusuna sannan ya zauna. Zahrah da ta make ta ce “su waye lauyoyi” Badi'a ce ta fara tashi haɗe da rusunawa “Suna na Barr.. Badi'a Kabir, nice lauyan Wanda yayi ƙara” sannan ta rusuna ta zauna. Khalid ma ya miƙe “I'm Barr. Khalid Umar, I'm for defense counsel" daga haka ya rusuna.

Cike da ƙwarewa suka yi zaman nan tamkar dai a court ɗin gaske suke gudanar da shari'ar sannan aka yanke wa masu laifi hukunci daidai da laifin su. Daga nan aka sauƙe curtain.

Manyan baƙin mu appreciated the drama sannan sun bada kyaututtuka da dama wa waɗanda suka yi wasan, yayin da wasu suka ware kyauta ta Musamman ga Justice Zahrah Kuru wacce ta matuƙar burge mutane da damah.

Haka aka ci gaba da gabatar da programs har aka kammala. Daga nan aka fara raba prizes. Zahrah ta karɓi prizes sosai ita da Badi'a. Irin prizes ɗin da ta karɓa yasa a wajen wakili Governor ya Bata kyautar garin kuɗi har 100k haka sauran jama'ah suka yi ta mata kyaututtuka na ban mamaki. Anyi taro lafiya an gama lafiya. Lokacin tashi Abba yazo ya ɗauke su sai gida. Mamah da Ammi sun yi matukar alfahari da ƴaƴan nasu ammah duk wannan sha'ani da ake yi Kawu da amarya babu wanda ya sani. Shaye shayen Kawu kuwa sai abunda ya ƙaru...dabar su ma ta dawo tamkar dai da yanzu kuwa har shiga cikin gidan suke yi saboda samun dama daga Bana amarya.

Ranar Monday suka je makaranta. Principal ne ya aiko a ƙira mishi Zahrah Kuru. A tsorace ta fito daga class ɗin su ta nufi office ɗin principal da sallama ɗauke a bakin ta ta shiga bayan ya bata umarnin hakan

“good morning sir" “morning Zahrah, how's studies?” “Alhamdulillah sir. I was informed that u want to see me”

Ba tare da ya bata amsa ba ya ɗaya phone ɗin shi ya kara a kunne, bayan few seconds aka yi picking. “Assalamu Alykum" baa jin meh ake cewa daga ɗaya ɓangaren daga bisani ya miƙa mata wayar. Ba tare da ta san wanene ba cikin Muryar ta mai daɗin sauraro tayi sallama. A lokacin kuma principal ya fita daga office ɗin.

Jin Muryar cutien shi ya sake wani murmushi mai ɗan sauti “wa alykumussalam cutien yaya” Bata san lokacin da ta cilla wani ihu ba saboda farin ciki sai kuma hawaye sharrrr “aah cutien yaya kuka kike yi? Toh shikenan lemme hang off the call and I won't call again” Da sauri ta share hawayen ta kamar tana gaban shi “i'm sorry yaya Ishaq, kukan farin ciki ne, ina kwana ya karatun" “Alhamdulillah cutie, ya Mamah?” “lafiyae ta ƙalau, kusan kullum sai tayi jajen ka” “Ayyah ki gaishe ta zan aiko muku saƙo in Sha Allah” “toh Yaya mun gode, i thought har ka manta da mu" “ni ina na isa na manta da ƙanwa ta!, Rufa min asiri kullum cikin kewar ku nake" Murmushi mai ɗan sauti tayi daga ɗaya ɓangaren yace “ba wannan ba dai cutie, jiya naji abun alkhairi da kika yi, kuma na gani. Ina alfahari da ke ƙanwa ta, ki ƙara dagewa Please” “in sha Allah yaya” “shikenan sai anjima, damah I called only to complement on your performance and I'm proud of you zahrah" “thank you yayah, bye”

Readers Also Read

More by Bilyn Abdull