Bakin ruhi complete - Chapter 38
Bakin ruhi complete Chapter 38: Bakin ruhi complete Chapter 38. Siffarsa ta yanzu ta fi ta farkon muni,hankalin kowa ya tashi saboda tiyagas ɗin hucinsa…
3,371 words
Siffarsa ta yanzu ta fi ta farkon muni,hankalin kowa ya tashi saboda tiyagas ɗin hucinsa mai cike da guba da yake furzo mana.Aliya ce kawai mai wata power wannan yasa ta yi yunƙurin shiga gaba domin zama garkuwarmu amma yayi wata hargowa ta yi sama tare da faɗowa ƙasa timmm,daidai wannan lokaci ne ya soma yin magana yana mai kiran sunayen ahalina ɗaya bayan ɗaya.Sai a lokacin ne kuma suka fito suka fuskance mu,iyayenmu maza ne sai Yaya Aliyu wanda ya fito yana yi mini wani irin kallo mai cike da tsana duk uwar soyayyar da ke tsakaninmu ta ƴan uwantaka babu ita.
Kawu Hamza ne ya soma magana,"Ibrahim a fara shirin ƙaddamarwa" shi ne abin da ya furta yana wani irin murmushi.Kawu Laminu,Abbana da kuma Yaya Aliyu suka shiga kunna wasu manyan kyandirori suna yi suna wani waƙe kamar baitin mutuwa.
Mu kuwa dama Aliya ce da Dr Muhamud ne ƙarfinmu,sai Mentor wanda ganin BAƘIN RUHI yasa ya juya mana baya ya ɗaure mana ƙafafuwa ta yadda ko wani motsi mun kasa yi har lokacin da aka soma ƙaddamar da Kawu Hamza matsayin wanda zai yi dakon BAƘIN RUHI.
A gaban idonmu ya sauko daga sama a cikin wata siffa mai kamar hayaƙi ya shiga a gangar jikin Kawu Hamza,ko minti ɗaya bai ƙara ba ya harbo mini wata kibiya ta caki gefen cikina a daidai wurin da baƙin ruhi ya taɓa kai mini suka.
Kibiyar ba ta ida nitsewa cikin jikina ba na ji murya MAHEER na karanto ayar Alkur'ani mai tsarki" Wa Ƙadimna ila ma amilu min amalin faja'alnahu haba'an mansura" kamar yadda ruwa ke kashe wuta haka na ji wani sanyi ya ratsa ni tare da fitar kibiyar ta koma can gaban Kawu Hamza.Yana shirin sake harbo mini wata Aliya ta yi ƙarfin halin tashi tana juya idonta,haske ya turnuƙe wurin ta ce "Dr Mahmud ka yi saurin fitar da su daga wannan daji ka yi amfani da taka power ku fita saboda wannan kalar siddabarun ban taɓa aiki da shi ba sannan kuma bai wani jimawa"
"Ke kuma fa?" ya tambaya.
"Kar ka damu da ni, kai dai ka tabbatar ka fitar da Queen Haulat a nan"
"Avali.."
"Ka tafi please "
Fuskar Dr Muhamud cike da takaici ya fitar da lular da ke cikin tafin hannunsa da niyyar tseratar da mu,yana dab da ya fitar da mu ɗin na yi saurin fita daga cikin hasken na zo gaban Aliya na yi tsaye hakan ya rogaje siddabarun.
"Ba zan taɓa tafiya na bar ki ba Aliya" na furta hawaye na zubo mini,cikin ƙunar rai ta ce "Haule ni fa ba yarinya ba ce,ba tun yau nake cikin duniyar nan ba sam ban tsoron mutuwa me yasa za ki rusa komai?"
Wata irin muguwar dariya ce Kawu Hamza ya gagaɓe da ita kafin ya ce ,"wato in na lura dukkanku nan so kuke ku bai wa Haule kariya? To bari na fara kashe ki kafin ita"yayi furicin tare da wurgo irin kibiyar da ya jefo mini, Dr Muhamud ne ya tare kibiyar ta huda ƙirjinsa yayi wata hargowa yana mai fara yin kalmar shahada hakan ya haifar da rugujewar duk wasu duwatsu da ke cikin jejin hakazalika duk wani mugun abu sai ya fara guduwa ciki kuwa har da Kawu Hamza da maƙarabansa wurin sai ya zamana ƴan tawagarmu kawai.
Bakin Dr Muhamud bai gushe yana ambaton kalmar shahada ba yana yi wa kuma Aliya alamu da hannu cewar yana sonta muna ji muna gani ya mutu a gabanmu.
Maheer da kuma Dr Umar ne suka ciciɓe shi,muna tunanin hanyar da za mu bi mu koma kwatsam sai ga wata jibgegiyar halitta ta bayyana a gabanmu tana kuka haɗi da yaƙe haƙora.
"Wannan ba normal dabba ba ce,kowa ya samu sunan Allah ɗaya ya riƙe matsayin madogara " Maheer ya faɗa yana wani ƙara jawo ni bayan sun ajiye gawar Dr Muhamud "
"Ya hayyu! Ya ƙayyum! Ya zul'arshil Majid !" shi ne abin da dukkanmu muke ambato cike da yaƙini,a hankali dabbar ta soma ja da baya kafin ta rugo da gudu ta yi cikin Lubna wacce kana kallonta ka san ba ta wani yi imani da hakan ba kawai faɗa ne take yi.
Ƙafarta ɗaya ta cabko tare da saka manyan haƙoranta ta raba ta da ita, Lubna ta yi wata irin kururuwa kafin kuma ta ɓace ɓat daga jejin gaba ɗaya.
Daidai nan dabbar ta rikiɗe ta zama mutum,ba kowa ba ne sai Yaya Aliyu.Idonsa sai wani haske suke yi kamar wutar murhu,yayin da muryarsa ta shaƙe ta zama kamar ta matattu.
"Har abada ba zan taɓa barin burina ya tashi a banza ba,ki yi haƙuri my little sis amma ni ne nan ajalinki ke da wannan ƙarmasashen mijin naki.Kuma Lubna tawa ce ni ɗaya babu wanda ya isa ya raba mu,yadda na kwaɗaitu a kanta dole ne na same ta.Ke ma kina kan hanya sai kin zo bar kan gadon baccina kin kawo mini kanki "ya ƙarashe furicin yana mai nuna nurse Fatee kafin kuma ya ɓace.
Aliya ta ja wani tsuki kafin ta ce "ina Nadia?"
Sai a lokacin muka farga da ba ta cikinmu,tabbas ta bi Mentor sun zaɓi tawagar baƙin ruhi. Maheer ya ce "duk ba wannan ba mu yi gaggawar komawa duniyarmu domin suturta Dr Muhamud "
Nurse Fatee ta ce "Dr MAHEER duk ina ƙarfin ikonka ya tafi? Me zai hana kai ma ka dawo da taka power?"
"Banda wannan lokacin na bautar abin da ba gaskiya ba ne,duk ƙarfin tsafinsu ai bai kai na Alkur'ani ba don haka da shi za mu yi amfani "
Aliya ta ce "muna iya juya ayoyin mu fitar da layu domin kariyarmu,sannan ya zama dole dai Haule ta nemo wuƙar nan da ta soki baƙin ruhi da ita .Abu na biyu kuma da buƙatar mu je can family house ɗinsu don rayuwar Innarsu na cikin haɗari"
Kasa cewa komai na yi,sai ido da na kafe wuri guda ina kallon abin da su ƙila ba sa ganinsa.Ba komai na ne sai wani kyakkyawan saurayi fari tasss yana tsaye amma ƙafafunsa ba su taɓa ƙasa,fuskarsa cike take da annuri hakan ya ƙara tona tsantsar kyawun nasa.
"Zo! Zo! Zo nan!" shi ne abin da yake furtawa cikin wani irin cool sauti mai kamar yana yi mini raɗa.Ban sani ba ni ce ke tafiya ina tunkararsa ko kuwa ruhina ne,abin da na sani kawai na yi kusa da shi ta yadda numfashinmu yana haɗuwa cikin na juna.Kamar yadda ruwa ke huda ƙasa sun shige ƙarƙashi,haka saurayin ya ratsa ta cikina ya zauna raɗam har ina jin motsinsa.
"Me kike yi a nan?" muryar MAHEER ta daki kunnena,na ja wani numfashi sai yanzu hankalina ya dawo jikina.Ya ci gaba da cewa "tun ɗazu muke neman ki zo mu je" ya kama hannuna,sai da muka yi ƴar tafiya mai ɗan nisa kafin mu iso inda suke.Kallo ɗaya Aliya ta yi mini sai na ga ta saki murmushi kafin ta yi amfani da ƙarfin ikonta ta fitar da mu .A cikin asibiti muka bayyana,babu jimawa suka kai gawar Dr Muhamud can mutuware kafin a soma shelar mutuwarsa ,iyayensa na riƙo suka ƙaraso abin mamaki babu wanda ya tsaya binciken ta yadda aka yi ya mutu.
Ni da Aliya muka ƙarasa gidan Hajiya nan muka tarar da wani tashin hankalin wai anty Bahijja ba ta nan wani ya zo ya tafi da ita a cikin mota ita da Yasmine. Hajiya kuwa kamar ta goya ni haka ta shiga yin murna,sam ita ba ta ma damu da su Bahijjar ba sai ma waya da ta ɗauka ta shiga kiran dangi tana sanar da su.Dakyar ta iya bari na gusa na shiga wanka,juyin duniya ta hana ni shiga ɓangaren ƴan aiki dole ɗakin Maheer na je.
Bahon wanka na cika da ruwan ɗumi kafin na shiga na kwanta na yi lamo,idona na soma ƙanƙancewa kamar zan rufe su.Nan take aka soma nuna mini abin da ke faruwa a can gidanmu,Kawu Hamza ne a tsaye ƙiƙam yayin da Innarmu ke durƙushe a gabansa tana kuka kamar ranta zai fita.Wani irin ƙuna na ji zuciyata na yi mini,yayin da kuma nake ci gaba da kallon yadda yake yi mata tsawa kan ala dole sai ta basa littafin sirri wanda ya ƙumshi dukkan doddanin ruhaniya farare da kuma baƙaƙe har ma da fatale,yayin da ita kuma take jadadda masa ba ta san inda yake ba.
Abbana ne ya zo ya wanke Innarmu da mari yana mai cewa "saboda ina mugun sonki ne yasa nake ɗaga miki ƙafa,amma ki sani wannan karon ba za mu lamunci shashancinki ba ko ki faɗa mana ko kuma..." Kawu Hamza ne ya katse Abbana da cewa "Ibrahim ku fita" amon muryar tasa kana ji ka san ba shi ɗaya ba ne a cikin gangar jikinsa.
Shi ne shugabansu kuma babba kaf illahirinsu wannan yasa suka bi umarninsa.Suna fita ya soma wani motsa hannuwa daga inda yake tsaye,a hankali luluɓin jikin Innarmu ya soma warwarewa yana bayyanar da surarta.Ba sai an faɗa mini abin da yake son aikatawa ba da kuma dalilin yin haka,yana son yin tarayya da Innarmu ne don tsotse duk wani ƙarfin iko nata wanda ta barsa yana bacci tsawon shekara da shekaru ba tare da ta yi amfani da shi ba in aka cire ranar da ta tseratar da ni daga gidan ba.
Wuƙar da nake son sanin inda take ita ce na hango soke a ƙugun Innarmu,da dukkan alamu tun ranar da na soki Kaka Nalado da ita Innarmu ce ta tsince ta ko kuma wani abu mai kama da haka.
Ban san ta yaya aka yi ba har na soma juya tunanin Innarmu nasa ta soma yin wasu abubuwan jan hankali ba,cike da ƙarfin sarrafa muƙamin iko na yi amfani da wuƙar da ke soke a ƙugunta na caki Kawu Hamza a ƙahon zuciya ta hanyar kallo kawai da furicin bakin da ban ma san ina yinsa ba.
Kururuwarsa ita ce ta jawo hankulan sauran iyayenmu maza har suka shigo ɗakin suka tarar da Kawu Hamza kwance cikin jini amma babu wuƙa ko ɗaya a ƙirjinsa.Yaya Aliyu ne ya shigo daga baya ya ja ya tsaya bakin ƙofa yana mai furta "Innarmu ce ta kashe shi" wanda hakan yayi daidai da zuwan iyayenmu mata har da sauran ma ƴaƴa ciki kuwa har da anty Mardiyya wacce ba ta yi jinkirin kai wa Innarmu bugu ba wanda kuma shi ne babban kuskuren da ta aikata a rayuwarta.
Tsabar yadda wani ɓacin rai ya luluɓe ni yasa na yi wata hargowa ina fitar da wani huci mai zafi tare da ware idona duka,nan komai ya ɓace mini.A gaggauce na yi wankan na fito,ina tambayar kaina abin da ke faruwa da ni don ji nake kamar tunanina ne kawai ko kuma mafarki.
Gaban madubi na ja na yi tsaye,cike da nutsuwa na soma nazarin inuwata da ke cikin madubi wacce ke nuna mini layi biyu na siffa.Fuskar tawa ma gizo ta fara yi mini kamar ta mace kamar ta namiji,a hankali na kai hannu na ɗauko wani turare da niyyar fesawa sai kuma na kasa sakamakon ganin sam inuwata da ke cikin madubi a tsaye cak sam ba ta nuna alamun na motsa ba kamar yadda in mutum na tsaye a gaban madubi duk motsinsa yana tafiya daidai da inuwarsa ta cikin madubi.
Mamaki bai gama rufe ni ba sai da na motsa na gusa daga saitin madubin amma da na juya haka na ga wata irina a tsaye a cikin madubin kafin kuma na ƙyafta ido komai ya dawo normal.
Na ja ajiyar zuciya ina ji a raina kawai tunanina ne ke bani haka amma ba gaskiya ne ba.Ina saukowa ƙasa na tarar da wani ɗan ƙaramin shagali wanda ahalina suka shirya mini,duk da ina cikin jimamin mutuwar Dr Muhamud bai hana ni ɗan sakin raina ba suka gudanar da shagalin yadda suke so kafin Hajiya ta ɗauko sarƙar nan ta saka mini a wuyana.
Zaman sarƙar yayi daidai da hasko mini Innarmu da aka yi wacce ke tsakiyar ƴan sanda suna jaye da ita,amma a hakan murmushi ne kan fuskarta tana kallon tsakiyar idona da dukkan alamu ita ma tana ganina hakan kuma nada alaƙa ne da sarƙar wuyana.
"Haulatu? Ya dai?" Hajiya ta furta tana mai taɓa kafaɗata,na ɗan zabura kafin na yi murmushin yaƙe na ce "na'am Hajiya "
"A'a daga yau Mama za ki dinga kirana " ta faɗa tana wani rungume ni,haka su ma dangi Mama suka dinga yi mini.A tare muka ci abinci muka yi salloli suna ta yi mini hira da kuma bani labarin yadda Maitama ya ƙware wurin farautar mayu.
Sai bayan sallar isha'i MAHEER ya shigo gidan, lokacin tuni na gyara ɗakinsa na saka turare na mayar da shi tsaf sai ƙamshi ke tashi.Ni ma na yi wanka na saka sabbin kayan da Hajiya ta bani.
A falo ya tarar da mu,bayan ya gaishe su ya haura sama cikin wani irin yanayi.Ina son bin bayansa amma ina jin kunyar haka,can Aliya ta fito daga kitchen hannunta riƙe da madaidaicin faranti ta zo ta miƙo mini tana mai cewa "abincin Oga Maheer "
Hajiya ta yi murmushi mai sauti kafin ta ce "ai kuwa Aliya kin kyauta,tashi ki kai masa kina dai ganin yadda ya shigo fuska a murtuƙe da dukkan alamu ma bai lura da ke ba"
Ban ce komai ba sai farantin da na karɓa na je na fara hawan step ina jin ƙafafuwana na yin wata irin rawa.Ina tsayuwa bakin ƙofar ta buɗe da kanta,da na shiga ban tarar da shi ba sai motsin ruwa da na dinga ji a toilet.Drower na buɗe na fitar masa da kayan da zai saka,bai wani jima ba ya fito ƙugunsa ɗaure da towel.A hankali na ɗaga kai na kalle shi,har zuwa yanzu fuskarsa na yadda take babu walwala.Jiki a sanyaye na ɗauki ƙaramin towel na je gabansa na soma tsane masa jiki,can ƙasan maƙoshi na furta "sai haƙuri! Allah dai ya jiƙansa"
"Amen!" ya amsa mini kafin ya riƙe towel ɗin,na ɗaga kai na saka idona cikin nasa kafin kuma da sauri na lumshe su jin tafin hannunsa mai sanyi kan fuskata yana shafawa.
"Don Allah ki samar mini nutsuwa,raina duk a dagule yake" ya furta ƙasan maƙoshi yana mai ɗora laɓansa kan nawa.A tare muka ja ajiyar zuciya,na yi tunanin iya sumba ce kawai amma sai da na ga ya soma yin nisa sannan na dakatar da shi.Muryata na ɗan rawa na soma magana a rarrabe "am...ka manta an yi mutuwa n..e sam bai kamata a ce mun shhhi..." sauran maganar tawa ce ta maƙale ganin irin kallon da yake jefo mini mai cike da tsantsar kishi da kuma zargi.
"Dama har yanzu da nake matsayin mijinki kina son Dr Muhamud ?" ya furta cikin ɗacin rai,cike da mamaki na dube shi na ce "so? So dai? Ni zan so Dr Muhamud ɗin? Ka manta har lokacin da ya bar duniyar nan yana mai nuni da Aliya ce mafarkinsa?"
"To me yasa za ki hana mini haƙina in ba sonsa kike yi ba? Kin fi ni sanin ya mutu ne? A tunaninki ban damu da mutuwarsa ba ne shi yasa na zo gare ki ? In ban zo wurinki ba H.lat wajen wacce mace kike so na je na samu sa'idar azalzalar da ruhina yake yi?" yana gama faɗa kawai ya shige toilet tare da banko ƙofa.Jikina ne yayi sanyi,sama da minti goma ina jiran fitowarsa amma kamar an aiki bawa garinsu ya ƙi fitowa.Dakyar na ja ƙafafuwana na taɓa ƙofar sai na ji yasa key ya rufe ta,da ido na kalli ƙofar nan take ta buɗe.Cikin bahon wanka na hango shi yana zaune yayin da kuma wani ruhi ke ƙoƙarin ganin sun kusanci juna,iskan bakina na hura sai kuwa ya fito ya daki ƙirjin MAHEER sautin ƙarar mace ya fito tana ƙoƙarin ƙara nitsewa cikin gangar jikinsa na yi saurin cabko ta tare da zuwa gaban madubin da ke cikin toilet na ɗaure ta.
Ta bayana na ji an rungumo ni,na ja ajiyar zuciya kafin na juyo muna fuskantar juna.A hankali na soma shafar sajensa kafin na yi tsaye kan yatsun ƙafafuna don ƙara tsayi amma duk da haka ban kai tsawonsa ba sai da na jawo wuyansa,muna yi wa juna murmushi mai sauti kafin na soma sumbatarsa.
Cike da hikima na tura shi ƙarƙashin shower kafin na sakar mana ruwan su soma zuba a kanmu.Tsawon lokaci muna a haka kafin na yi dubara ɗora idona kan madubi inda na ɗaure ruhin Siren ɗin da tun kallon farko na samu labarinta da kuma inda suka haɗu da MAHEER.Ina juya ido madubin ya tarwatse wanda hakan na nufin na cilla ta can duniyar da ta fi dacewa da ita,cikin kunne na yi masa raɗa "ka goya ni mijina!" ya saɓe ni kafin ya fito da mu yayi mini masauki kan lafiyayyen gadonsa,ido na lumshe ina karɓar salon soyayyarsa a wannan lokacin muka ƙara buɗe sabon babin rayuwar ma'aurata. Bayan mun samu nutsuwa ya je ya ɗauko wasu duwatsu ya saka mini a ƙugu,cike da shagwaɓa na shige ƙirjinsa ina cewa "wurin wa ka sayi jigidar nan? Ba dai mace ba?"
"Ni ne da kaina na yi fa,tana burge ni sosai"
"Kenan ka taɓa ganin wata mace da ita?" na faɗa cike da kishi,yayi murmushi mai sauti yana shafar cikina ya ce "lokacin da kike zuwar mini a mafarki iya ita kaɗai nake gani kin ɓoye fuskarki ta wannan abin ne da ke kusan cibiyarki na gane ke ce dai mai zuwar mini a mafarki"
Hannunsa na janye na ɗora nawa daidai baƙin tabon haihuwar da ke ga cikina,na ce "an ce wai idan mahaifa ta shafi jariri ne yake fito masa" bai ce komai ba sai bakinsa da ya kai daidai wurin ya sumbata sannan ya ce "ni dai ina sonsa"
Zan yi magana kenan na ji idona na ƙanƙancewa da kansu, numfashina ya soma gudu a slow yayin da kuma laɓana suka soma motsa kansu suna furicin da ban san mene ne ba kawai dai na hango mutuware a maduban idona kafin kuma na ga gawar Dr Muhamud zaune kan gado tana kalle-kalle.
"Bai mutu ba!" na furta cikin hankalina . "Wane ne?" na ji MAHEER ya tambaye ni. Na basa amsa da " Dr Muhamud!" sai kuma na dawo hayyacina ina wani jan numfashi kamar raina zai fita.... [5
My book is only 500 via
2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank
DM +22795045822.
🔞In kin san ba ki biya ba kar ki karanta min book,yin haka babban kuskure ne don cin haƙin da ba naki ba ne.Kuma Allah ba yafe haƙin wani akan na wani,don haka kar ki raina girman haƙi komai ƙanƙantarsa.
__________________________________________________ *PAID PAGE*
45
Da sauri na dire daga bed ina ƙoƙarin saka sutura domin isa can,amma MAHEER ya tsayar da ni sai da muka yi wanka sannan muka fita tare. Daidai bakin get muka hangi Aliya tana zaune ta ɗaga kai sama kamar mai lissafin taurari.Na je gare ta ina mai rungume ta,a tare muka sauke ajiyar zuciya kafin ta miƙe ba tare da mun cewa juna komai ba.Asibitin muka wuce,ni duk a zatona ma tuni an yi jana'izarsa kamar yadda na ga danginsa sun iso.
Mu uku muka nufi mutuware,wurin tsit yake kamar masaukin mutuwa ita da kanta.Ina taɓa ƙofar ta buɗe,ɗakin sanyin ac ne kawai ke motsi amma kaf gawarwaki ne suna kwance shanɗal.
Kusan a tare muka je muka yi tsaye kai ga gawar Dr Muhamud,Aliya ta yaye zanen da aka rufe shi daidai nan wani iska mai kashe jiki ya soma wucewa kamar wata mota kafin kuma ya tsaya cak ya soma yin wani kuka kamar jiniyar asibiti.
"Ruhinsa bai yi nisa ba yana cikin garin nan,amma da dukkan alamu so suke su fitar da shi can ƙasar waje domin mallakawa wani power da ke tattare da shi" na yi furicin ina mai ƙanƙance ido.
Aliya ta ce "ta ya za a yi mu dakatar da su?"
"Da farko dai sai mun gano wane ne ke riƙe da ruhin,abu na biyu kuma dole ne mu san yadda za mu yi mu maido mutumin a tsagenmu "
Aliya ta matso ta buɗe idon Dr Muhamud kafin ta ce "Oga Maheer ka yi zama da power na maciji zo ka duba mana cikin ƙwayar idon nan hoton wa ka gani?"