Bakin ruhi complt by mrs sadauki - Chapter 20
Bakin ruhi complt by mrs sadauki Chapter 20: Bakin ruhi complt by mrs sadauki Chapter 20. "Ki dawo ki zauna ko kuma wallahi...kin san sauran" ya furta…
4,495 words
"Ki dawo ki zauna ko kuma wallahi...kin san sauran" ya furta cikin wata irin murya.Na san halinsa sarai zai iya biyo ni toilet ɗin babu ruwansa da idon mutane.Ina turo baki na dawo na zauna sai a lokacin ya sake cewa "Aliya ɗaure mana ita" "To" ta amsa kafin ta dabaibaye Yasmine da haskenta kawai sai ta farka tana kuka na yi tunanin nan ɗin ma karatun ɓoyayyar duniyar zai karanta ayoyin Alkur'ani inda ake zancen sihiri da kuma wasu Azkhar.
(*- قَالَ مُوسَى مَا جِئْتُم بِهِ السِّحْرُ إِنَّ اللّهَ سَيُبْطِلُهُ إِنَّ اللّهَ لاَ يُصْلِحُ عَمَلَ الْمُفْسِدِينَ* *- وَيُحِقُّ اللّهُ الْحَقَّ بِكَلِمَاتِهِ وَلَوْ كَرِهَ الْمُجْرِمُونَ*
*- وَأَوْحَيْنَا إِلَى مُوسَى أَنْ أَلْقِ عَصَاكَ فَإِذَا هِيَ تَلْقَفُ مَا يَأْفِكُونَ* *- فَوَقَعَ الْحَقُّ وَبَطَلَ مَا كَانُواْ يَعْمَلُونَ* *- فَغُلِبُواْ هُنَالِكَ وَانقَلَبُواْ صَاغِرِينَ* *- وَأُلْقِيَ السَّحَرَةُ سَاجِدِينَ* *- قَالُواْ آمَنَّا بِرِبِّ الْعَالَمِينَ* *- رَبِّ مُوسَى وَهَارُونَ*
*إِنَّمَا صَنَعُوا كَيْدُ سَاحِرٍ وَلَا يُفْلِحُ السَّاحِرُ حَيْثُ أَتَى*
*وَقَدِمْنَا إِلَى مَا عَمِلُوا مِنْ عَمَلٍ فَجَعَلْنَاهُ هَبَاء مَّنثُورًا*
*●اللَّهُمَّ رَبَّ النَّاسِ، أذْهِب البَأسَ، اشْفِ أنْتَ الشَّافِي لاَ شِفَاءَ إِلاَّ شِفاؤكَ، شِفَاءً لاَ يُغَادِرُ سَقما.*
*Allahumma rabbi n-Nâs, adz-hibi-l-Ba's, wa-shfi anta-sh-shafi, lâ shifa'a illâ shifii'uk, shifa'an Lâ yughâdiru saqamâ*
*●بِسْمِ الله أرْقِيكَ، مِنْ كُلِّ شَيْءٍ يُؤْذِيكَ، مِنْ شَرِّ كُلِّ نَفْسٍ أَوْ عَيْنِ حَاسِدٍ، اللهُ يَشْفِيكَ، بِسمِ اللهِ أُرقِيكَ.*
*Bismi-l-Lâhi arqika wa-l-Lâhu yashfika min kulli dâ'in yu'zika, wa min kulli nafsin aw "aynin hâsidin Allâhu yashfik*
*●أعوذ بكلمات الله التامات من شر ما خلق*
*Aûdhu bi kalimâti-l-Lâhi-t-Tâmmâti min shari mâ khalaq*
*●بسم الذي لا يضر مع اسمه شيء في الأرض ولا في السماء وهو السميع العليم*
*Bismni-l-Lâhi-l-Lazî lâ yadur maa-s-mihî shay'un fi-l-'Ardi wa lâ fi-sSamâ', wa huwa-s-Samîu-l-"Alîm*)
Jikin Yasmine ne ya soma rikiɗa zuwa wata halitta marar kyawu sai wani irin juyi take tana mahaukacin ihu wanda iya nan ɗakin kawai ake ji saboda yadda Aliya ta baza basirarta ta yadda ba za a jiyo mu ba.
Maheer sai ƙara sautin karatun yake kafin can na ce "ina ga da buƙatar a tofa ayoyin cikin ruwa a bata ta sha kamar yadda Kaka ta sa malam ya yi wa Jafet" Maheer ya ɗan dube ni kafin ya ce "je ki ɗauko kunnuwan magarya a kitchen ki daka su ki kawo" ba tare da na ce komai ba na je na kawo kamar yadda ya ce ya karɓa ya zuba ruwa yayi karatun,bayan yayi sai na karɓi kofin na shiga cikin dunƙulen hasken Yasmine ta yunƙuro za ta kwaɓe kofin amma na yi saurin juya idona na daskarar da ita ,wajen bata ruwan sai da na sha wahala sosai kafin ba ɗura mata su nan take cikinta ya soma girma yayi tsini har sai da cibiyarta ta zazzalo .
Wata ƙara ta yi kafin ta soma yin amai ,a daidai nan kuma Aliya ta kwance ɗaurin da ta yi.Duk baya muka yi muna kallon yadda Yasmine ke aman wani abu mai kumfa kafin can wani ɗan jinjirin maciji baƙi siɗik ya faɗo yana wiƙi-wiƙi da ido.
Cikin sauri Maheer ya fiddo nasa ya haɗiye shi,a duk duniya babu abin da nake tsoro sama da maciji ƙila don ya taɓa sara ta ne wannan yasa na tsorata na ƙanƙame Lubna kasancewar ita ce kusa da ni. "Ga shi nan kusan ƙafafunki" Lubna ta faɗa cikin tsokana na yi ihu tare da soma dire-dire duk suka hau yi mini dariya in aka cire Oga Maheer da ya saki baki yana kallona.Muna haɗa ido na nutsu tare da kawar da kai na je gun Yasmine wacce ta koma so weak duk ta yi laushi.
"Ki biyo ni ki karɓi ruwan da za a yi mata wanka" Oga Maheer ya faɗa yana mai ficewa,na dubi Aliya ita kuwa ta ce "ai kin san dai ba da ni yake ba ko? Sai ki je ki karɓo" shiru na yi ban ce komai ba sai Lubna ta ce "bari na je na karɓo"
"Me yasa kike son matsa kanki ga gini? Yanzu kin ji ya ambaci sunanki?" cewar Aliya. Lubna ta ce "ai bai faɗi sunan kowa ba"
"Eh saboda HAULE kawai yake yi wa haka kuma ita ma ta sani bai taɓa kiran sunanta ba"
"To ai sai ta je ta karɓo" Lubna ta faɗa a ɗan hassale,sai kuma suka soma cacar baki ba su yi shiru ba sai da anty Bahijja ta yi musu magana.
Ni kuwa don su nutsu da kyau sai na ce "anty Bahijja ida bani labarinki mana"
Ta ce "tun daga wannan lokaci na soma karɓar izaya wurin Mr Sahil,yayin da ɓoyayyun halayensa suke ta ƙara bayyana a gare ni.Yana nemana mu yi normal sex,in buƙatar haka ta tashi a can ɗakina yake zuwa in kuma ta haramtacciyar hanya ce to a ɗakinsa za mu yi a gaban wannan halittar da ke cikin mirror.Na gwada tserewa ya fi cikon casbi amma ban ci nasara ba saboda yayi mini mugun kafi.Zancen fatalwar matarsa kuwa da farko sai na ɗauki hakan ba gaskiya ne ba,sai dai yadda nake yawan ganin giftawar mutum yasa na yarda sai kuma farashin tsorona ya sake hauhawa.Ba zan manta ba wata rana na shiga ɗakinsa na soma yin bincike nan na gamu da wata takarda mai ɗauke da hotunan mata kusan su biyar kowacce da sunanta da kuma ranar da ta mutu,tsoro ya kama ni saboda yadda na ga kuma dukkansu Mr Sahil yayi hoto da su da dukkan alamu kuma na ranakun aurensu ne.Nan ne fahimci cewa tushen arzikinsa matansa yake bayarwa matsayin sacrifice,ina nan zaune sai ya shigo na ɗaga kai fuska shaɓe-shaɓe da hawaye ga kuma wani tsoro da ya kama ni.Ba tare da na ce komai ba ya bani amsar tambayar da ke mini yawo a kwanya,"eh abin da kike tunani haka nan ne,sai dai ke ba zan bayar da ke ba za ki zauna tare da ni ki haifa min yarinyar da zan baiwa shugaba domin ci gabana da kuma naki "
"A'a ni ba zan zauna a gidanka ba,za ka sawwaƙe min na koma gidan iyayena " na faɗa amma sai ya ƙyalƙyace da dariya kafin ya ce "wane iyayen ? Can lahira za ki tarar da su? To tsaya ki ji Bahijja na kashe iyayenki ,ba za ki sake ganinsu ba.Kwaɗayinsu ya ja musu suka aura mini ke ba tare da wani bincike ba yanzu ai sun ga ribar haka" tun daga wannan lokaci na riƙi kuka matsayin aboki,na rame sosai na rasa abin da ke yi mini daɗi.Ga azabar Mr Sahil ga kuma yadda fatalen matansa ke yi min yawo a cikin gida,sai ina zaune in ji suna magana cikin raha "ita wannan sai yaushe za ta buyo layinmu?" "hahha! Wa'adinta bai yi ba ita ma za ta mutu ta dawo tsagenmu " ire-iren waɗannan maganganu su suke sa na ƙumshe kaina a ɗaki na toshe kunnuwana.Ban samu kaina ba sai ranar da Mr Sahil ya bani wasu ruwa ya ce maganin da zai sa na bar jin maganarsu ne,eh na bar ji sai kuma na manta duk wata izaya da yake yi min a haka har na raini cikin Yasmine na haife ta.Tun daga ranar da ta zo duniya sai ya bar nemana kwata-kwata a cewarsa shi ne sharaɗin da aka yi masa sai dai fa yana neman matan banza,ga kuma Yasmine da ke yin abu duk dare kamar tana yin sex da na yi masa magana sai ya ce duk yara na yin haka ai da wannan ya ɗaure bakina har ta girma .A satin da ya gabata kafin na haɗu da ku ne yake shaida mini jagabansu zai zo gidanmu,wai za mu yi sex mu uku in kuma na ƙi sai ya yi da Yasmine in ta cika shekaru sha takwas" tana kawo wa nan ta yi shiru tana mai yin kuka mai taɓa rai.
Ina shirin soma rarrashinta Hajiya ta ƙwala kirana daga can falo,da sauri na miƙe na fita. "Hajiya ga ni " na furta . "Ki ɗauki bokiti ki cika da ruwa ki kaiwa Maheer " ta faɗa tana gyara kwanci,na so na tambaye ta ina baƙin suke ganin sai ita ɗaya amma na yi shiru na je na cika bokiti da ruwan na hau sama ina tsayuwa ƙofar ta buɗe da kanta na shiga ciki kafin kuma ta rufe kanta .Na ajiye bokitin da sauri ina kawar da kai ganin daga shi sai gajeren wando ya tsaya yana wani danna remote yana canza channel.
"Sai yanzu kika ga damar zuwa?" ya tambaye ni,sai na juya na ɗan saci kallonsa hankalinsa na kan tv amma da yake har a ƙeya ido ne da shi sai da ya ga na kalle shi.
"Ki ci gaba da satar kallon kyakkyawan jikin da ya saka kika suma ɗazu" "Ka buɗe mini ƙofa zan fita" na faɗa cikin dakiya. Sai a lokacin ya ajiye remote ɗin ya tako kusa da ni har da wani riƙe ƙugu kamar mace ya ce "ba ki shigo don ki fita ba,ina son jin labarinki ne zo mu je" ya faɗa tare da kamo hannuna na fizge na ce "mu je ina? Shi labarin ba a iya saurarensa a nan sai mun shiga bedroom?"
Ya ƙanƙance ido yana mai cewa " yaushe na faɗi cewa mu shiga bedroom? Oh! Abin ne bai ishe ki ba? Oyaaa zo mu je to na sake lugwigwita ki" hannunsa na buge ina harararsa kafin na turo baki gaba,yayi dariyar shaƙiyanci kafin ya ce "don Allah H.lat me kike so da ni ne? Ke ko tausayina ba ki ji sai wahalar da ni kike?"
Hanci da baki na saki ina kallonsa jin wani zance,ƙila ya fahimci haka sai ya ce "je ki zauna kan kujera don Allah " saboda yanayin yadda yayi magana yasa na ja ƙafafuna na je na yi zaune. Bokitin ruwan ya kawo a gabana kafin ya zube kan gwiwansa, hannuwana ya kamo ya jimƙe su sosai kafin ya tsunduma su cikin ruwan."Tofa yawunki" ya faɗa ,na dube shi cikin ido ya ce "eh tofa" kamar ba zan yi ba sai kuma na tofa shi ma ya zuba nasa a gaban idona na kowanne suka ware kansu tare da soma tafasa,nawa suka fitar da color ɗin baƙi yayin da nasa kuma suka fitar da wani irin fari suna ƙyalli kamar farar azurfa.
"A shekarun baya irin haka ta taɓa kasancewa a tsakanin wasu aminai biyu maza.Dukkansu ƴan ƙauye ne,in na ce miki ƙauye ina nufin irin hatsabibin ƙauyen nan mai ɗauke da abubuwan almara,ban tsoro da kuma firgici.Abubuwan da suka yi wannan ƙauye ado da ƙawa su ne baƙin tsafi,Maita da kuma alƙawari a tsakaninsu da duniyar ruhani.A cikin aminnan nan biyu ɗaya shi ne kakanki Nalado,ɗayan kuma shi ne Kakana Maitama.Su biyun ba iya abokaina ba ne, a'a ƴan uwa ne na jinin maƙwabtaka iyayensu ma suna yin wannan zumuncin kafin ra'ayoyi biyu mabanbanta su raba su .Kamar yadda na faɗa miki cewa ƙauyen sun ƙware a harakar baƙin tsafi to haka Nalado da kuma Maitama suka laƙance shi.A wani bincike nasu ne nasu na matsafa suka gano akwai wata keɓaɓiyar duniya wacce ta kasance ta hatsabibai,fatale da kuma aljanu.Yarda da ƙarfin tsafinsu ne yasa suka ratsa dajin AOKIGAHARA,wanda shi kuma a cikinsa tsagi biyu ne .Yankin duhu da kuma yankin haske,da zuwansu sai suka rasa ta ina za su bi Nalado ne ya fara cewa abokinsa "mu shiga inda ke da hatsabin duhun can mu gano mene ne ya harzuƙa wurin har yayi baƙi haka kamar zunubi" amma sai shi abokin nasa Maitama ya ce "a'a Nalado me zai hana mu shiga dai inda ke da hasken ka sani ko can ɗin aljanna ce can kuma hanyar wuta ce?"
"Kana nufin nan ne lahirar da muka ji Musulmin cikinmu na faɗa?"
"Eh to kusan hakan ne nake gani,in ba haka ba a ina ne ke da hanyoyi biyu mabanbanta?" cewar Maitama. Sai Nalado ya ce "in kuwa haka na zaɓi na shiga ɓangaren da ke da duhun ko ba komai na san zan tarar da tsofaffin bokaye da matsafa da aljanun da suka bijire suka saukar da fasadi a cikin doron duniya,ka ga sai na roƙi su bani ƙarfin ikonsu ta yadda in mun koma duniyarmu zan baza mulki na kuma mulki kowa "
Maitama ya ce "ni kuma na zaɓi bangaren haske ta yadda zan hana ka cika baƙin nufinka na mulkar duniya,zan tabbatar kuma duk inda ka ɗiga ɗigon baƙin kalarka ni kuma zan bi ko ina ina jefa ƙwayar haske a ciki" bayan kowa ya faɗi furicin bakinsa kamar da wasa sai kowa ya kama hanyar da ya zaɓa tare da kutsa kai a ciki" Maheer na kawowa nan da zancensa na yi saurin ƙwace hannuna ina zarar ido yayin da zuciyata ke matsananci bugawa kamar za ta faso allon ƙirjina ta faɗo. Dakyar na iya haɗa yawu murya na ɗan rawa ina kuma nuna shi da yatsa,"kenan...kenan ka san Kakana Nalado? Kenan ni..ni.Ni da kai.." sai kuma na yi shiru.
Maheer ya lumshe ido tare kuma da buɗe su kafin ya ce "yes mu ƴan uwan juna ne,Innarku ƙanwar mahaifina ce shi ya aurar da ita kuma ga mahaifinki Ibrahim saboda ya cika burin mahaifinsa Maitama wanda ya kasance Kakana"
Hawaye ne suka soma yi min zuba,yayin da Maheer ya ci gaba da cewa "na soma baki labarin nan ne saboda babu wata sauran mafita,tun da kika yi tozali da ƴan uwan Daddy masu kama da Innarki na san dole ki bi didigi ta ya haka za ta kasance"
Na ce "amma a can garinmu Innarmu nada wasu iyayen har da ma ƴan uwa"
"Na bogi ne,amma na asalin sun rasu ko kuma na ce miki suna can a ɓoye in ba ki manta ba kuma kin ganni a tsaye tare da wani mutum mai shafafar fuska to wannan shi ne Kakana Maitama mahaifin Daddyna da kuma Innarki ya zo gare ni ne don sanar da ni an ɗaura mana aure ni da ke"
Zumbur na tashi tsaye kamar wacce aka tsikara,shi ma Maheer ya tashi tsaye yana mai ci gaba da cewa "wallahi tallahi a gaske nake Haulat an ɗaura aurenmu in kuma ba ki yarda ba za mu je ni da ke can wurin Papy ya faɗa miki da bakinsa ke ɗin matata ce"
Ba wai ban yarda da furucinsa ba,a'a yadda ya ce wai shi mijina ne ya saka ni cikin tsananin shock da na kasa controling kaina.Wani irin jiri nake ji na yi luuu zan faɗi yayi saurin taro ni na faɗa kan ƙirjinsa.Ƙanƙame shi na yi gam ina mai lumshe ido haɗi da soma sauke numfashi da sauri-sauri ko Allah zai sa na ji sassaucin abin da nake ji.Ina jin lokacin da Maheer ya zagaye ƙuguna da hannunsa ya gyra mini tsayuwata a ƙirjinsa kafin ya ɓalle maɓallan rigar sanyin jikina wacce dama can shi ne ya saka mini ita.Hullar ya ture ta yi baya,sai a lokacin na ɗaga kai na dube shi muna kallon juna cikin ido.So nake na furta masa kalmar so ko zan samu sukunin abin da nake ji,amma kuma ba zan iya ba na ci alwashin shi ne zai fara faɗa mini ita sannan kuma sai na gwara kansa sannan ya ji kalmar a bakina.A hankali ya zare mini rigar ta faɗi ƙasa,sai yanzu ne kuma na ga ashe riga da wando ne a jikina na Adidas waɗanda suke mallakinsa.Da sauri na lumshe idona ban shirya ba ganin ya soma matso fuskarsa kusan tawa,murya can ƙasan maƙoshi ya ce "ina son mu haɗe tunaninmu wuri guda Please Queen" sai ya sauke lips ɗin nasa kan nawa,yayin da ni kuma na aiwatar da abin da ya ce ɗin.Sosai nake jin daɗin yadda yake min sumba,na shagala sosai a cikin shauƙin kafin na ji wata muryar na cewa "to ni dai ya isa haka ka sakar mini jika haka" da wani mugun sauri na fizge bakina daga cikin na Maheer sai na ga sam ba a ɗakinsa muke ba muna cikin wani ɗan ɗaki ne na kara,gefe kuwa wannan mutumin ne a zaune kan gadon itace. Maheer ya saki murmushi kafin ya ƙara jawo ni ya manna a ƙirji sannan ya ce "Papy na cika alƙwarin da na ɗaukar maka,na furtawa fitinaniyar jikarka komai ka ganta da rawar kai take ƙila kuma tun yau ita ce za ta fara ƙoƙarin cika burinka"
Wanda ya kira da Papy ya ɗauki wani abu ya wanke fuskarsa da shi sai ga shi ya dawo normal mutum ana ganin dukkan gaɓoɓin fuskarsa,sannan kamanninsa da Innarmu ne na gani jere ras a tattare da shi.
Wani ƙyalle ya miƙo min na karɓa,ya ce "idanun Hassana ne,Kakarki ce ta kawo min su ajiya ta ce duk ranar da kika zo na baki su domin mayarwa da ƴar uwarki kayanta" Yana gama furta hakan sai na buɗe ƙyallen,ƙwayar ido biyu ce a ciki sai motsi suke kai kace yanzu ne aka cire su har da kumfan jini.Murya na ɗan rawa na ce "wacce ta je gidanmu? Mai ganin nan ita ɗin Kakata ce?" ya jinjina kai yana murmushi kafin ya ce "ku zauna ,ni nan zan baki dukkan tarihinki da kuma abin da ya shafi ahalinmu.Labarin da King Maheer ya baki wannan shimfiɗa ce,zan sanar da ke komai kafin na roƙi alfarma a wurinki ki yarda ki amince da da King a yau a matsayin mijinki"......
*Intermission/tsakiya*🌚
Sai kuma ranar asabar in sha Allah za mu ɗora daga inda muka tsaya,nan ne labarin ya zo a tsakiya zan je hutun kwana biyu .
Ga waɗanda ke karanta mini book ba tare da sun biya kuɗin karatu ba ku sani ban yafe muku ba,duk wacce ta ji haushi kuma ta biya ni😝
My book is only 500 via
2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank
DM +22795045822.
🔞In kin san ba ki biya ba kar ki karanta min book,yin haka babban kuskure ne don cin haƙin da ba naki ba ne.Kuma Allah ba yafe haƙin wani akan na wani,don haka kar ki raina girman haƙi komai ƙanƙantarsa.
__________________________________________________ My book is only 500 via
2670215530 ZULFAU YAHAYA Ecobank
DM +22795045822.
🔞In kin san ba ki biya ba kar ki karanta min book,yin haka babban kuskure ne don cin haƙin da ba naki ba ne.Kuma Allah ba yafe haƙin wani akan na wani,don haka kar ki raina girman haƙi komai ƙanƙantarsa.
__________________________________________________ *PAID PAGE*
31
"Kamar yadda Maheer ya faɗa miki sunana Maitama,banda babban aboki kamar Nalado.Tun ƙurciyarmu mun taso muna ganin kakanni da iyaye ana tsafi da kuma maita,sai dai ba mu taɓa ɗaukar haka wata illa ba sai ma bazama da muka yi wurin koyo.Da farko dai kamar ba za mu iya ba sai ga shi mun koyi siddabaru,duk ranakun kasuwa haka muke bin gari-gari muna wasar tsibo ta rufa ido.Na san za ki so sanin ta ya muke yin haka? To hanya mai sauƙi ce,muna aiki ne da aljanu saboda in ka kafircewa Allah ka yi kuma duk abin da aljani ya sharanɗa maka to shi kuma zai zamo yaronka.Da wannan muka soma cin abinci,yin siddabaru za mu rufe kwano babu komai amma da zarar mun buɗe shi sai lafiyayyen abinci ya bayyana a ciki wanda ba kowa ya kawo shi ba sai aljanin da ke yi mana aiki.A cikin irin wannan ikon ne muka haɗu da wata bafulatana,a kallon farko da Nalado yayi mata ya ji yana son ta maimakon ya je ya sanar da ita sai yayi amfani da tsafinsa ta zo gare shi ta ce tana sonsa.Wannan abu da ya faru sai na ji ni ma da buƙatar na samo tawa bafulatanar,sai dai abin da ban sani ashe Nalado da yake abokina yayi min sihiri ta yadda ba zan taɓa yin aure ba.Dalilinsa na yin haka ba komai ba ne saboda yayi bincike ya gano cewa duk ranar da na samu macen aure to za ta yi silar raba mu .Da haka na gaji da neman aure har na haƙura,kafin Allah ya haɗa ni da matar mafarkina wacce ta kasance Siren .Ba zan manta ba,a wani yammacin Laraba ne mun je kamo kifi ni da Nalado sai dare yayi mana a can ga shi kuma ba mu kama sosai ba.
"Maitama ya kamata mu koma gida ka sani sarai muna da matsala da esprit ɗin ruwa a matsayinmu na matsafan baƙin tsafi " Nalado ya faɗa yana mai ɗaukar kifinsa da ya kama.
Sai na ce masa "a'a sai dai ka tafi ni kam sai na kamo mai ɗan yawa kafin na koma gida,ko ka manta gobe ne ranar gasa?"
"Hahaha! Dama akwai wani tsafi da ake yi da kifi wanda ban sani ba? Ka ga sam ba zan shiga wannan gasar ba saboda na san ba zan ci ba.Ko ka san da cewa manyan matsafa daga ɓangarorin duniya ne za su halarci wannan gagarumar gasar?"
Na ce "ni kam zan shiga kuma ina nan da kai sai na shigo layin zakaru uku" Nalado yana yi mini dariyar shaƙiyanci ya tafi,yayin da ni kuma na ci gaba da jefa ragata a cikin kogin da hasken faɗuwar rana ya haska shi. Kamar da wasa na soma jin ragata ta ɗau nauyi,da sauri na soma jawo ta ina murna cewa na kamo babban kifi kafin kuma murnar ta koma ciki a daidai lokacin na yi tozali da wata halitta rabi mutum rabi kifi sai juya idonta take suna kawo haske.Ko babu tsafi dama can ni ba ma'abocin tsoro ne ba hakan yasa na mazge duk da kuwa na yi mamakin ganin irin halittarta.
"Ke kuma wace ce ke?" na samu na jefo mata tambayar .Da idonta masu ƙyallin haske ta dube ni kafin ta ce "ni ce matarka wacce ƙaddararka ta haɗa ma da ita,ka sani samuna a matsayin matarka shi ne mafita a gare ka"
Baki da hanci na saki ina kallonta,ina jin maganarta tamkar gatanar gizo da ƙoki.To ta ina ma bil'adama zai auri aljana? Don kuwa marabarta da aljana ƴar kaɗance.
Ba tare da na tanka ta ba na ɗauki tarkacena zan yi tafiyata amma ta tsayar da ni ta hanyar cewa,"gasar da za a yi gobe kai ne za ka zamo Zakara,muddin za ka ɗaura wannan abin a ƙugunka" sai ta miƙo min wata aba kamar laya.Saƙo na yi ina kallonta kafin na karɓa ina mai ci gaba da kallonta can na ce "in zancenki ya zama gaskiya mene ne farashin abin da zan baki?"
"Aurena za ka yi shi ne farashin"ta bani amsa,ba tare da wani tunani ba na ce "na yarda" sai ta yi suka ta koma cikin ruwa yayin da ni kuma na tafi gida na kaiwa Innarmu ɗan kifin da na kamo don ta sarrafa shi mu ci da dare.
Bayan ta zuba shi tukunya sai kuwa ya ƙara auki,"Maitama zo ka ga yadda kifin nan ya cika tukunya" shine abin da ta faɗa ,na je na leƙa na gansa mai yawa a nan take na ji a raina aikin Siren ɗin nan ce wacce ban ma san sunanta ba.
Bayan an gama girki muna ci sai mahaifina yake cewa "Maitama ban san a cikin me ka tsoma hannunka ba,amma ina ji a jikina tamkar za a canza maka alƙibila daga tsafin da muka gada zuwa wani tsafin na zamani"
Murmushi kawai na yi,don ko na ce na yi magana ba zan faɗi gaskiya ba in kuma na yi ƙarya mahaifina babban matsafi ne zai gano hakan.Bayan mun gama sharɓar romon kifi sai na kimtsa na je gidan Nalado domin basa labarin abin da ya faru da ni bayan ya tafi. Na nemi izini har babu iyaka amma bai fito ba,cikin rashin jin daɗi na koma gida ina ji a raina ƙila matarsa ce ta hana shi fitowa tun da na fahimci ta tsane ni kawai haka don ina abota da mijinta.
Da na koma gida haka na yi ta juya wannan igiya da kifin ruwa ta bani,kafin kuma na mayar da ita ma'ajiyarta. Washegari tun safe bayan mun yi sallah na yi wanka da ruwan magunguna na asirai da tsafi,ban ɗaura laya ko ɗaya ba illa igiyar nan kawai sannan kuma na saka yaƙinina a kanta.
Gidan Maigari na yi tsinke inda gangunan tsafi ke ta kaɗa kansu yayin da kuma dakaru waɗanda za su yi gasar tsafi kowanne ya samu wuri ya zauna.Ni ma sai na bi ayari ina ta duba inda zan ga Nalado amma ban gansa ba har sai da aka soma gudanar da gasa wacce ba gasar komai ce ba sai ta ɗaukar wani rawani wanda ya kasance na wani tsohon matsafi da yayi mulki kusan ƙarni uku baya.Haka mutane suke ta gwada sa'arsu sai dai wasu da zarar sun taɓa rawanin suke faɗuwa a mace,wasu tunkararsa ma kawai suke yi sai su faɗi a some ganin haka yasa duk sauran da muka yi saura suka ji tsoro suka janye suka fasa shiga sai yayi saura ni ɗaya tal.
Na soma takawa kenan don ɗauko rawanin sai ji na yi an jawo ni baya,Nalado ne har ƙasa ya zube yana roƙona "a'a Maitama kar ka yi wannan kuskuren,wallahi in ka tafi mutuwa za ka yi .Dubi gabanka gawarwakin mutane ne a zube kamar ƴan tsaki, waɗanda a harakar tsafi sun dame ka sun shanye amma ka ga duk sun mutu masu damar ne suka some dubi wasu ga su can sun haukace" na saki murmushi tare da miƙar da shi tsaye,akwai wani kallo da nake yi wa Nalado don basa tabbacin zan kai labari akan abin da na sa gaba.Yanzu ma shi na yi masa,sai ya ɗan waro ido kafin yayi ƙasa da murya "ka tabbata?" na jinjina masa kai kafin na sake shi na je na hau kan dandamalin da aka ajiye rawanin wanda ashe manyan sheɗanu ne ke a tsaye kansa suna gadinsa.Ba tare da tsoro ko ɗarrr ba na kai hannu na ɗauki rawanin tare da ɗora shi a kai sannan na juyo na fuskanci al'umma waɗanda suke cike da mamakin ta yadda aka yi na haye.
Kiɗa aka soma yi ana yin duk wani abu da ya shafi tsafi,yayin da ni kuma a inda nake tsaye nake iya hango Mayu daga cikinmu ,sannan da waɗanda aka haramtawa yin tsafin zamani.Daga inda nake ina hango wuraren da ke ɗauke da wasu tsoffin asirai ,wasu abubuwan ma ban san da su ba.
Bayan kyaututtukan da na samu sai duk aka soma wa watsewa,sai a lokacin dangina na kusa suka fara zuwar min yi mini barka a haka har na samu keɓewa da Nalado.
"Aboki mene ne sirri?"ita ce tambayar da ya fara yi min . Na ce "za ka gani,amma ka bari sai dab da magarib " duk yadda Nalado ya so na faɗa masa sirrin a lokacin sai na ƙi,a haka muka rabu maraice na yi kuma ya zo har nan gida ya same ni sai muka kama hanyar tabki.Kan hanyar ma sai da ya sha min kai da tambayoyi amma ban basa amsa ba,har muka isa muka yi tsaye muna kallon ruwan.Ba a ɗauki lokaci ba kusa ruwan suka soma yin motsi kafin ta fito tana kaɗan bindin,Nalado ya ja da baya da sauri yayin da ni kuma na ƙure ta da ido ina kallo ina jin wani sonta na fizgata saboda silarta ne martabata ta yi sama.