Batuol mamman complete novel - Chapter 17
Batuol mamman complete novel Chapter 17: Batuol mamman complete novel Chapter 17. Hadir ya kalla suka hada ido. Anya Mama ce kuwa yace a ransa. Bata taba…
3,374 words
Hadir ya kalla suka hada ido. Anya Mama ce kuwa yace a ransa. Bata taba tambayarsa babansa ba sai su Umma kawai.
Kara kashe shi tayi da wani mamakin ta hanyar cewa ya dora masa wayar a kunne "saura ka sani a speaker"
Bai san lokacin da ya kwashe da dariya ba. Wai dama Mama ta iya wasa haka?
Hankalin Hadir gabadaya yana gare shi sai kawai ya dora masa.
Wani irin sanyi taji ya ratsa zuciyarta da taji sautin numfashinsa. Soyayyar da ta dade tana dannewa ce ta taso mata. Da suna tare yanzu shekararsu goma sha tara da aure.
Cikin wani yanayi na shauki da begen da yake nuna soyayya bata tsufa tace "Hadir"
Allah Sarki rayuwa, yaji sunan har tsakiyar kansa amma bazai iya amsa mata ba.
"ASTAGFIRULLAH" tace da sauri ta katse wayar. Shaf ta manta cewa har yanzu tana karkashin Musa har sai ta gama iddah. Tashi tayi ta bude wardrobe ta dauko akwatunanta.
Da safe Musa da kansa ya sanar da su Aisha cewa mamansu zata dawo sannan Antinsu Zainab zata tafi. Sun saba da ita sosai a hannunta suka girma. Tana kuka suna kuka har airport suka rakata. Motarta Musa yace zai bayar a kawo mata har gida. Tayi ta masa godiya da kyakkyawar addu'a ta shige jirgi zuwa garinsu tana mai fatan samun sauyin rayuwa mai dadi.
**********
A firgice Rtd Major Mustapha ya tashi jike da gumi daga mafarkin da yake yawan yi wanda yake daga masa hankali ya shiga laluben kafar katakonsa. Mafarkin ya tsananta a gareshi tun bayan da suka sanya ranar komawa kasar haihuwarsu. Korido din da zai sada shi da kitchen ya nufa don ya sha ruwa ya hango Mami ta barbaza kaya a gabanta na tsaraba da take ta warewa tana saka sunaye.
Kasa tafiya yayi duk motsinta yake bi da kallo. Wannan kyakkyawar matar kanwarsa ce, matarsa kuma uwar 'ya'yansa. Hakika a kullum baya gajiya da sanya Hassana cikin addu'o'insa domin ta cancanci fiye da haka. Tayi hakuri dashi iyakar hakuri musamman a lokutan da yake ganiyar ciwo har yakan nemi rayuwarta ba a cikin hayyacinsa ba. Tunanin kawai kan sa tsigar jikinsa tashi. Tabo uku ne a jikin Mami wanda suka samu a dalilin PTSD dinsa.
Jikinta ya bata yana kallonta haka kawai, ta daga kai suka hada ido. Murmushi suka yiwa juna ya dawo falon ya zauna.
"Me ya hanaki bacci shabiyu har ta wuce?"
"Aikin nan yaki karewa Daddy. List din mutanen ma kamar bamu yi rabi ba" ta dan bata rai.
"Ku kuma mata da baku da nutsuwa indai akan tsaraba ne ko"
Tattara kayan ta soma yi gefe sannan ta dube shi "me ya tasheka ne?"
Shirunsa ya fahimtar da ita komai. Kusa dashi taje ta zauna "nan da kwanaki goma in sha Allah muna gida. Muna kwana biyu an gama gaisawa da 'yan uwa babu inda zamu je sai wurin Ummin Awwab da Hadir. Lokaci yayi da zaka kore komai daga ranka ka rungumi kaddara."
"Yes Ma" yace yana murmushi.
Maida masa martanin murmushin tayi ita ma "Tashi muje mu kwanta kasan gobe is a big day"
Suna kwance tuni Mami tayi bacci amma shi ya kasa sai rarraba dayan biyu yake. Ko yaya iyalin Zayyan? Allah Yasa suna cikin mafi kyaun yanayi. Sai kuma ya koma tunanin auren Zahra da Fauziyya da za'ayi nan da wata biyu. Kowaccensu tuni ta hada degree dinta. Hadi ne na gida zasu auri 'ya'yan 'yan uwa kamar yadda ya kusan zamewa danginsu al'ada. Har nan aka turo mazan suka daidaita kawunansu. Bai san lokacin da bacci yayi awon gaba dashi ba.
Washegari kuwa banda shirin tafiyarsu da yaki karewa karfe bakwai na dare suka tasarma gidan da Mami take aiki. Major sanye yake sa suit sky blue da light grey din shirt a ciki. Yayi gyaran fuska yayi kyau yana rike da sandarsa da take taimakawa wurin rage masa rashin jindadin tafiya da kafar katako duk da ya saba yanzu.
Mami, Zahra, Fauziyya da Zayyana duka abaya ne a jikinsu masu kyau kowacce tayi nadi da mayafin da ya dace.
Party ne na bankwana iyalin Herr(Mr) da Frau(Mrs) Schmidt suka shiryawa Mami a matsayinta na shugabar ma'aikatan katon gidan. Sun matukar jindadin zama da ita tun lokacin da suka basu wuri a gidansu kafin daga baya su kama wani mai dan girma a waje. Iyalin babu abinda yasa suka likewa Mami kamar tsantsar tarbiyar da yaransu suke koyi da ita har a makarantunsu. Tarbiya ce irin ta musulunci batare da ta fito zahiri ta tallata musu addinin ba. A fakaice ta rinka kwadaita musu tana fatan wataran idan da rabo su karba. Farkon zuwanta sun so hanata zuwa da lullubi ko karamin hijab. A take tace ta bar aikin. To amma amanar da suke gani daga gareta yasa da kansu suka sake nemota.
Aikin Mami a gidan yana daga cikin abinda Major bazai taba mantawa a rayuwarsa ba. Wai shi Mustapha da ya kai matakin Major a soja shine matarsa take aikatau. Abinda yafi karfi a kasarsu yazo lalura ta cinye komai nasa yafi karfinsa. Bashi da tamkarta a duk duniya. Ya amince samun kamarta sai wata matar sojan. Jarumar mace matar jarumin namiji.
Katuwar harabar gidan tasha gyara da fitilu da flowers ko ina yana kyalli ga kayan abinci a gefe debi wanda kake so. [5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Duk dauriya irin ta Ardo sai da ya matse kwalla ganin yadda hatta mazan kowanne ido yayi jajir.
Mairama ce ta fara magana cikinsu "ina Awwab dan Ummi? Nasan ya girma yanzu? Anyi masa aure ne?"
Zahra tace "Mami ashe da gaske dai Ummin Hamma Awwab mu bata sonmu"
Mairama sai dariya ta kufce mata ta daga hannuwa ta tashi tsaye tana cewa "Zahra, kece ko? Ina Fauziyya da Ibrahim abokin fadan wannan yarinyar?"
Fauziyya da Zahra suka matso suna rike hannuwanta tace "kuji min yara yaushe zan ganeku da hannu kawai, haka ake yi" ta fada tana rungumesu.
Muryar wata shagwababbiya da hausarta ke fita kamar mai waka saboda yadda yaren Germany da turanci ya kama mata baki taji tana cewa "Daddy ni kowa baya sona, she even asked for Hamma that is not here"
Ibrahim kallonta yayi ya tabe baki, yarinya yar shekara sha hudu kamar yadda yaji Mami ta fada sai ta dage tana zuba tabara Daddynta yana biye mata.
Emzee kuwa murmushi yayi bai ce mata komai ba. A gidan Ardo shine karami bai saba ganin haka ba shiyasa yadda tayi ya burge shi.
Mairama sai ta sake dariya ta rasa ina zata kai farincikin da yake cikin zuciyarta.
"Such a sweet voice, wace ce wannan?"
Zayyana dadi ya mamayeta ance muryarta da dadi ta tafi da sauri ta ture Fauziyya da Zahra ta shige jikin Mairama tana cewa cikin tsantsar mamakin wannan 'yar kauyen "Daddy she speaks English too"
Ibrahim ya kwalo idanu a hankali yace "ji min rainin wayo."
Sai kuma suka tsinkayi Radhiya muryar tayi kicin-kicin da fuska tana kallon Zayyana "ke yarinya iya bakinki wallahi, Ummina ma 'yar boko ce har secondary ta gama ehe"
"Zaki fara ko?" Mairama tace tana zaunawa har lokacin Zayyana na jikinta ba ta fahimci dogon zancen Radhiyan ba.
"Ai gara na fada mata gaskiya tun wuri kada ganinki a kauye yasa ayi miki kallon wata local"
Haba wuri sai ya kaure da dariya harda Major. Sai lokacin Mairama ta gama gane su waye a wurin kunya ta kamata. Halin Radhiya sai ita.
Zainab tana cewa ta zo Mami ma tana kiranta sai ta rasa wurin wa zata je. Zainab tace "jeki dai dama ita ce mamanki, ni Zayyan zan dauka nafi kama da maman maza"
Rufe fuska tayi da hannuwanta tana kallonsu a fakaice sai wani blushing take "wallahi kun sani jin kunya...duk sona kuke yi"
Wata dariyar ta basu Mami ta janyo hannunta ta zauna a kusa da ita "haka kika koma Alheran din Awwab? Wannan idan na wuni dake cikina sai ya kulle"
"Indai wannan ce baki ga komai ba" cewar Innawuro.
Kowa a cikinsu yana cike da tsananin farinciki. 'Ya'yansu ma ko da basu gama sanin mahimmancin iyayen nasu a wurin juna ba sun amince wannan haduwa ta faranta ran iyayensu su ma dole su ji dadi.
"Idan kun gama kukan da dariyar ya kamata a gaisa kuma haka" Ardo yace dasu don ya dakatar da zubar hawayen matan.
Sai kuma aka soma gaisawa ana tambayar yaya bayan saduwa. Mairama ta fuskanci bangaren da take jin a nan su Major suke ta saki fuska.
"Daddy ina fata duka kuna lafiya"
"Lafiya kalau Ummin Awwab" yace a sanyaye.
Dan bata rai tayi cikin wasa "abokinmu tun shigowarku banji ko tarinka ba, ai shikenan."
Dif taji shiru ya rasa wurin babu mai cewa komai cikinsu. Hantar cikinta ta kada a sanyaye ta rike Zainab "ba dai....Subhanallahi, ba dai shima"
Wani irin kuka Zainab ta saka tana jin ciwon lalurar Hadir har kokon ranta. Jikin Mairama ya gama saki ta sadakar kila shima babu rai.
Radhiya da Emzee sun gane shine akan kujerar amma su din ma basu iya bata amsa ba. Major ne ya danyi gyaran murya ya soma maganar da kafin ya kai karshe wurin ya sake rikicewa.
"Hadir gashi nan muna tare sai dai tsahon shekarun nan da bamu tare ya yi su ne da paralysis sannan baya iya magana."
Sai da ta dan sami nutsuwa daga wannan tashin hankalin abinda yake ci mata rai shekara da shekaru ta kasa daurewa cikin karyewa da dashewar murya tace "uhmmm...uhmm nace babansu Karami. Kuna tare ya rasu ko?"
Major da Hadir da dukkansu da suka san labarin abinda ya sami Zayyan daga bakin shi kowa gabansa ya fadi. Mairama da ba ganin fuskokinsu take yi ba ta cigaba da magana.
"Ko baku san ya rasu ba ma?"
"Mun sani Ummin Awwab, muna tare" Major ya amsa da sauri.
Ajiyar zuciya tayi harda guntun murmushi "Alhamdulillahi, da hankalina ba karamin tashi yake ba da tunanin kila ba'ayi masa sutura kamar kowane Musulmi ba. Nace ko irin mutuwar nan ce ta su da yawa. Ance ramin kawai ake guda daya. "
Major Mustapha shiru yayi ya rasa me zai fadawa wannan baiwar Allah. Allah ne ya cece shi a lokacin aka fara kiran sallar Magariba Ardo yace kowa ya tashi. Mazan waje suka tafi wurin masallacin da yake gefen gidan akwai butoci cike da ruwa.
Ibrahim ya dauko daya ya duka a gaban Hadir zaiyi masa. Emzee yana tsaye a gefe yana ta kallonsa.
"Za kayi masa?" Ibrahim ya tambaye shi yana murmushi.
Murmushi Emzee yayi ya gyada kai.
"Gashi" Ibrahim ya bashi butar.
Emzee ya karba "ka tsaya ka rinka gani kada nayi ba daidai ba"
Da taimakon Ibrahim din Emzee ya yiwa Hadir alwala. Kukan zuci yake yana murmushin zahiri. Yau dan Zayyan dinsa ne yake masa alwala.
Bayan sun gama ya kuma cewa shi zai tura shi cikin masallacin. Dadi ya kama Ibrahim don ba karamin ji da babansa yake ba.
Da suka idar da sallah ma Emzee din ne ya sake turo shi zuwa bakin kofar, Ibrahim sai ya tsaya daga waje ya kama kujerar suka daga shi sannan aka sauketa a kasa saboda tudun da yake wurin shigar.
"Sunana Ibrahim Hadir"
Takalminsa yake lalube wannan ya bawa Hadir damar ganin fuskarsa sosai yana murmushi tamkar an ajiye mahaifinsa a wurin.
"Muhammad Zayyan Tureta"
Wani dagen gira Ibrahim yayi "amma Zeezee naji ana ce maka ko?"
Emzee mai wuyar sabo ya sami kansa da kwashewa da dariya "Zeezee kuma kamar wani mace, Emzee ne."
Ibrahim sai yaji yana son zolayarsa "ni dai kafi min kama da Zeezee haka zan rinka kiranka"
"To Surbajo babu damuwa"
Hadir yana jinsu yana dariya a hankali musamman da ya ga Ibrahim yaji dadi yana cewa zai fadawa Umma kakarsa cewa yazo garin Fulani an saka masa suna irin nasu. Emzee ya gimtse dariyarsa suka koma gidan.
Major ne karshen komawa ya tsaya amsa wayar Awwab da yake ta mita an tafi ba'a jira dawowarsa ba.
"Idan kaso ranar da ka dawo a tare dasu zaka kwana babu mai hanaka"
Daga daya bangaren Awwab yana kwance a dakinsa na hotel a Austria washegari goman dare zai sake wani trip din zuwa Germany ya shafi habarsa.
"Duk dadin ya wuce yanzu. Kun hadu da Ummin?"
"Muna rugarsu a Bauchi"
Tashi yayi zaune da murnarsa "ta tuna ni Daddy?"
"Kai ta fara tambaya"
Wani sanyi yaji a ransa don Allah ne shaida bai taba mantawa dasu ba musamman ita Mairama mamansa ta biyu. Karshen haduwarsu ranar da duka su ukun suke ta kuka daga karshe ya gane halin da nasa mahaifin yake ciki. A wurinsa yaji rasuwar babansa Zayyan mutumin da yake matukar so.
"Daddy Alheran fa?"
"Ita ma baka manta da ita ba?"
Dariya yayi, a shekara goma watanni ne babu tsakaninsu. Babban abinda yafi tunawa da ita shine fada da kuka. Sauran kuwa sai abinda Ummi ta bashi labari. Da kuma hotuna da ta nuna masa nasu lokacin suna tare. Tabon inda ta taba yakushinsa yayi dan siririn layi mai dan duhu daga gefen girarsa ya taba.
"Ban manta ta ba Daddy. Ko za ka bawa Ummin waya?"
"Ka kira ta Mami sai ta hadaku"
**********
Duhun dare ya soma kawo rashin wuta ya sa aka kunna fitilun kwai guda uku aka ajiye a tsakar gidan. Bishiyar tana kada musu iska daidai gwargwado aka zauna mayar da zancen yadda kowa yayi rayuwarsa bayan rabuwa. Wannan karon Innawuro ce ta cewa yaran su tafi gidan Baffa Gide saboda kula da tayi hirar tasu mai taba zuciya ce.
Radhiya tace su taho kowa ya tashi kamar gaske. Suna fita bakin kofar Zayyana tace da Fauziyya "nan gidan basu da wurin da zamu buya"
"A buya kuma, kunyi gamo ne a hanya?" Radhiya ta tambaya tana waige.
Murmushi Zahra tayi yanzu an girma suna jin kunya. Ibrahim kuwa sai yace "kinga magana zasuyi mai mahimmanci idan bamu tsaya munji ba wallahi za'ayi ba mu"
Haba Radhiya ta rike tana jinjina kai "Allah ko? To amma zunubin laben wa za'a rubutawa a cikinmu? Ni dai shekarata goma sha tara da sauran kuruciyata."
Fauziya da Zahra har Ibrahim sai dariya. Emzee da ya saba shi kam bai ga komai ba. Salati suka ji Inmawuro tayi da karfi tana kuka gabadayansu babu babba babu yaro suka dawo suka tsaya a siririyar hanyar karasa shiga cikin gidan. Duhu da girman maganganun suka hana a gano su.
Duk da sun ji yadda iyalin Major da na Hadir suka kare a Kano bai hanasu sake kokawa iyayensu ba. Jin labarin da Mairama ta bayar a karon farko a rayuwarta ta fadi yanayin zaman gidan mahaifinta. Tayi haka ba don ta tona masa asiri ba sai don su Mami su fahimci ainihin yadda al'amura suka kasance mata. Ga wanda bai san Malamijo ba sai a suna bazaka taba hangowa jikokinsa ma talauci da kuncin rayuwa ba. Dabbobinsa tarin arziki ne da shi kansa bai san dashi ba. Ko shanu ashirin ya sayar a yadda suke da girma kosassu zai iya ajiye abincin shekara a gidansa kuma su wadata da abubuwa da dama da bai taba tunanin ya basu ba.
"Abinda ban fahimta ba Ummin Awwab shin gidan da Zayyan ya gina a Kano me ya faru dashi?" Major ya tambayeta
Jan numfashi Hadir yayi da karfi sai da suka kalle shi. Rashin damar bawa Mairama takardun nan kusan shine ya haddasa masa hawan jini. Bai ma san ko Zayyan ya bata na wurinsa ba. Shi dai burinsa wadda aka bashi ajiya ya sadar da ita ga masu hakkinta. Takardun suna cikin wani akwatinsa da yake tunanin babu wanda ya taba bude shi tunda ya koma gida.
A nutse ta warware musu komai da ya wakana tsakaninta da Maikudi. Kunya kuwa ta kama Badaru kamar ya bace daga wurin saboda abinda yayansa ya aikawa matar kaninsu.
Major rai ya kara baci ba don duhu ba sai an ga jijiyoyin kansa da suka dago.
Mami tace "Wallahi mutumin nan sai munyi da gaske. Ta kowace fuska da zai toshe miki jindadi sai da yabi. Mu fa aure yace kinyi kuma baki haifi dan cikinki da rai ba sannan Radhiya tana hannunsa shine muke aikata mata kudin makaranta ta hannunsa"
"Banten uba" Radhiya tace a harzuke tana kumfar baka daga inda suke tsaye. Hanyar shiga ciki tayi Emzee da Zahra suka rikota.
Idanu sun rufe ta shiga kokawar fuzgewa "ku cikani"
Zainab suka gani a gabansu suna sunkuyar da kai kasa tace duk su dawo su zauna tunda annobar labe ta kamasu.
"Ban hanaki wannan zagin ba" Mairama tace da Radhiya cikin fada.
"Ai wallahi Ummi sai dai fa kiyi hakuri yau daya dai. Hmmm gaya miki ne banyi ba da idan munje hutu fa duk inda ya ganni sai ya rankwasheni ko ya makeni. Inata hakuri, inata hakuri. Wata rana yana rankwashina na tafi a gabansa na dauki Bushira lokacin tana karama na maka ta da kasa. Shine fa ya dena dukana. Yo ashe harda ke bai kyale ba"
"Ya isa haka Radhiya kiyi hakuri tunda magana ta fito ba zamu bar masa hakkin marayu ba" Mami tace da sigar lallashi.
"Uhmhum" kawai ta amsa ba don ta hakura ba.
Badaru ya ari baki ya basu hakuri sannan ya kara da cewa "dole ne na sake neman su mutanen Nijar din. Bana yi musu zaton wadanda rasuwar Zayyan zata sanya su watsar da iyalinsa. Allah Yasa su din ma ba wani abin yaje ya fada musu ba. Don ni yanzu lamarin nasa ya fara bani tsoro kuma."
Sunje sunyi sallar isha sun dawo sai ga yara biyar suka shigo gidan a tare rike da kwanukan abinci. Biyu yaran babban dan Innawuro ne sauran ukun kuma na mai binsa mace. Tun a masallaci lokacin Magariba Ardo ya sanar da dan nasa da kuma mijin 'yar suna da baki ayi abinci na gani na fada.
Farantai da cokula Radhiya ta dauko sai ruwan sanyi da aka aiki Emzee ya siyo a wani shago daga bakin titi Ibrahim ya bishi.
Anci an sha hira taki karewa Innawuro ta sa Radhiya da Emzee tayata gyaran dakunan saukar baki. Su Mami da ko baa fada ba da Mairama zasu kwana. Badaru, Major da Hadir Baffa Gide yazo ya tafi dasu gidansa. Ibrahim da Emzee a dakin Emzee din da yake daga hanyar waje. Sai 'yan matan su hudu a dakin Innawuro. Dreban da ya kawo su shima an sama masa masauki.
Da asuba kaji goma aka yanka domin yi musu abincin safe. A gaban Hadir Major ya fadawa su Baffa da Ardo cewar auren su Zahra ya matsu suna neman izini su tafi da su Mairama zuwa bayan biki. Radhiya da Zayyan kuma a bar masa su zai nema musu makaranta su fara jami'a a.
"A yi haka kuwa?" Baffa Gide yace yana kallon Ardo "a son ranmu dai suyi zamansu da yaran a tare damu har Allah Yasa duka suyi aure."
"Abinda baffanta Gide ya fada gaskiya ne. Ita ga matsalar idanu ga marayunta gara suna tare damu. Lokaci lokaci idan kun bukaci su zo su kwanan muku biyu sai a turo su"
Ransa dama ya bashi da wahala kai tsaye su bari ya daukesu. Sai dai kam yaci alwashin bazai yarda alkawarin da ya daukarwa kansa na cigaba da kula da bayan Zayyan ya tashi ba.
Sauran labarin da ya kasa bayyanawa jiya na ainihin yadda Zayyan ya rasu ya fada musu. Baffa Habubakari sai da yayi kuka don tausayi.
Cikin damuwa da fami ga gyambon zuciyarsa yace "Bazan taba iya kallon idanun matarsa in bata wannan mummunan labari ba. Tana da hakuri amma ina ganin sai ta tsaneni da iyalina. Yau da nake raye ku ke ganina Allah ne Yayi da sauran kwana na amma Zayyan shine sila."
Ya nuna Hadir "wannan bawan Allah da lafiya kalau yake wallahi kunji na rantse zaiyi komai don ganin 'ya'yan Zayyan sun koma karkashin kulawarsa. Sai dai shima lalura ta same shi ne da ya cigaba da kokarin kare rayuwata kamar yadda dan uwansa ya fara. Ku taimaka ku barni na kyautatawa bayan Zayyan sannan kuma na saukewa Hadir nauyin da nasan da yana da lafiya bazai taba bari na dauka ba"
Jikkunansu sunyi sanyi da maganganun Major. Ardo ya kira Innawuro yace "kece uwar Mairama kakar 'ya'yanta me zaki ce game da batun da bawan Allahn nan yazo dashi?"