Batuol mamman complete novel - Chapter 18
Batuol mamman complete novel Chapter 18: Batuol mamman complete novel Chapter 18. Nazari Innawuro ta soma don abun da yake nema ba karami bane. Mairaman da…
3,354 words
Nazari Innawuro ta soma don abun da yake nema ba karami bane. Mairaman da mahaifinta ya gagara rikewa, dan uwan tsohon mijinta ya tozarta ta yaya zasuyi saurin amincewa bare. Idan a gaba gori ya taso ko wani abu makamancinsa fa. Bafillatani duk talaucinsa akwai pride. Basa son zubar da mutumcinsu gaban kowa saboda babu azo aji dadin takasu.
"To na amince amma Zayyanu kadai zaku dauka. Dalili kuwa kun dai ga irin halin 'Yar Soja wallahi zama da ita akwai dadi akwai wuya. Mairama kuwa bana son nisa da 'yata ko kadan."
Hadir ya kafe Major da ido har ya fahimci so yake ya cigaba da rokonsu. Ai kuwa bai fasa ba yana ta kawo hujjoji.
"Kayi hakuri amma indai ka ga 'Yar soja ta bar garin nan to aure ne ya dauketa" Innawuro tace don ta kawo karshen muhawarar.
"Na ji na amince" Major ya amsa batare da dogon nazari ba.
Baffa Gide ya kalle shi da mamaki "kada kace min aurenta zakayi."
Mafita daya ya hango ya kuwa yi amfani da ita "a'a , akwai babban dana Awwab shine nake son aurawa. Dreban jirgin sama ne yana bakin aiki shiyasa bamu zo tare ba."
"Lallai da gaske kake, amma bana so ka cuci yaronka da auren dole don a baka yarinya. Kasan yanayin zamani"
"Na sani amma ina da yakinin bazai bani kunya ba. Don Allah ku amince. Yanzu ku bari mu tafi dasu har Sakkwato saboda wancan wan Zayyan din. Sai kuma danginsu na uwa dake Nijar su ma ina so na hadasu kafin nan da lokacin bikin"
Tsakaninsu da Allah basu da niyar hana shi yaran ko kadan sai dai magana ta gaskiya sunyi masa haka ne domin kada nan gaba a raina musu. Da mutumcinsu da rufin asirinsu ya nemi daukar yaran ba wai talauci ko maula ya kaisu ba. Sun kara jinjinawa Marigayi Zayyan domin wannan abu halinsa na kwarai ne ya kawo haka. Idan akwai wani abu na bajinta a rayuwar Mairama da Malamijo ya taba yi bai wuce aura mata dan kwarai irin albarka Zayyan Muhammad Tureta ba.
Innawuro da kanta ta fada musu su hada kaya zasu tafi tare suyi musu kwanaki don kowa ya sani hirar jiya da wadda aka sake dorawa yau tayi kadan ta cike gurbin shekarun da suka yi basa tare.
Radhiya sai murna nan da nan ta shiga jibgar kaya. Zainab ta ja ta gefe tace mata ta debi kamar biyar biyar nata da na Mairama.
"Ni fa na zaci kuna sonmu ne sosai baza ku so muyi kwana kadan ba mu dawo"
Tunda suka farka suke cin dariyar Radhiya ashe abin bai kare ba.
"Mu kuwa muke son ku Radhiya, ko nima 'Yar sojan zan fara fada ne"z
Turo baki tayi "to meyasa kika ce na debi kayan 'yan kadan?"
"Kinga muna zuwa zan sa a kaiku wurin tela ayi muku dinkuna masu kyau. Ko da wadannan kayan zaki je bikin Zahra da Fauziyya da za'ayi karshen wata mai zuwa?"
Dariya Radhiya tayi kumatunta na dama ya lotsa.
"To gidan wa zamu fara zuwa?"
"Gidana mana"
Mami da take tahowa daga bayansu ta rike baki "sannu maman yara, ashe wayo kike shirin yi min. To ban yarda ba Katsina zamu wuce"
Zainab ta mairaice "habaaa Mami, mu da zamu zo biki muyi kwanaki. Ki bari a ya da zango a Kano don Allah"
Mairama suka tambaya ina take son fara zuwa tayi murmushi "duk inda mota ta fara tsayawa zan sauka ne."
Ta kashe bakin nasu ta barsu da muhawararsu. Wayar Mami aka kira tana dubawa ta ga Awwab ne. Dariya tayi don jiya yayi ta kira bata sani ba. Tana dagawa a kunnen Mairama ta manna wayar.
Ko gaisuwa baiyi ba ya fara mita "Kai Mami tun jiya nake kira ki bani Ummi mu gaisa kinki dauka."
"To Allah Ya huci zuciyarka dan Ummi"
"La ila ha illallahu Ummi kece?" yace yana mai farincikin sake jin muryarta.
"Nice Awwab, yaya aiki?"
"Lafiya kalau, kinga sun taho sun barni ko"
"Kayi hakuri, kana dawowa zaka ganmu in sha Allah"
"Ummi ina Alheran?"
"Tana can wurinsu Zahra tana damunsu da surutu"
Dariya yayi yana imagining yaya ta koma yanzu "ta dena fada ko?"
"Awwab kenan baka manta halin nata ba ashe. Sai kazo zaka ganewa kanka."
"To Ummi don Allah kice Mami ta turo min numbar da zan rinka samunki. Ki gaishe min da Alheran"
Mami ta bawa wayar ya shiga tambayarta wai yaya girman Alheran yake yanzu don tsaraba yake son yi musu ita da Umminsa, Anti Zainab da Ibrahim.
"Kai kana fa da wani kanin Zayyan sunansa. Dama mun rabu Ummin taka ta kusa haihuwa"
Mamaki da jindadi suka baibaye shi nan yayi musu sallama zai fita. Suma aka gama shiri suka rankaya sai Katsinan Dikko.
**********
Mairama ta rasa wa zata goyi baya tsakanin Mami da Zainab. Gobe su Zainab zasu koma Kano bayan sun zo sunyi kwanaki uku a Katsina. Gidan kullum cikin hayaniya yake sun taru sun gama gyara shi an saka komai a muhallinsa.
"Gaskiya Mami wannan fa amfani da girmanki kike yi kina yi min wayo. Ki bar min 'yan matan nan muje suyi sati. Aure fa zasu yi ina ni ina sake cewa su zo su kwanar min"
"Ai ban hanaki ba, Radhiya ce na hana"
"Ummin Awwab kice wani abu mana"
"Ni ban san yaushe kuka koma haka ba. Ina nan bacci zanyi wadda tayi nasara ta tasheni. Idan zama ne na zauna. Idan kuma Kano ce tayi kira a hada min kaya"
Dariya ta basu daga baya dai an yanke Zainab zata tafi da 'yan mata kuma mazan ma ko don Hadir dole su bita. Mairama ce zata rage tare da Mami.
Taron mata ne a kitchen su Zahra na girki Radhiya na koyo.
"Kunsan nima mai aikacin asibiti zan aura a Bauchi zan zauna. Gara na koya kada aji kunya wata rana"
Emzee da yake shan ruwa sai da ya kware da yaji me take cewa "Adda saurayi gareki bamu sani ba?"
Daure fuska tayi zai bata kunya a gaban mutane "fata nagari lamiri yaro...meye aibu don nayi fatan auren likita?"
Ibrahim ya rinka mata wani kallo kafin yasa dariya "na gama harbo jirgin naki. Wato dai wani ma aikacin asibiti kike so"
"Hhhhhh Adda Kawu Zakari kike so hala? Shi kadai na sani a asibiti"
Yadda tayi da fuska ya karasa fallasata. Suka taru ana tsokanarta, Emzee yace wannan labari duk rugar Barkindo sai ya tona.
Tun tana da bakin ramawa ta gaji ta watsar ta fita ta koma daki. Zayyana ta samu tana busar da gashinta da ta wanke da hand dryer. Sai ta dena fushin hankalinta yayi gaba.
"Shi kuma wannan ya sunansa Zayyana?"
"Hand dryer, kema ki wanke kanki sai na busar miki. Mai kitso zata zo an turota daga gidan Alh Baba"
Tsit Radhiya tayi kamar ruwa ya cinyeta. Zayyana tayi tayi tace bazata wanke ba kanta babu datti.
Da su Fauziyya suka shigo Zayyana ta fada musu. Radhiya ta galla mata harara "kinga ki fita idona, ina ruwanki don naki wankewa ba kaina bane?"
Zayyana ta mike a fusace ta fita "kuma sai na fadaki da Daddy"
"Sannu shasshaka uwar narkewa, shagwabar nan nima na iya. Kuma bazan wanke kan ba"
"Dama masu gashi bakwa son bude kai fa. Shiyasa kullum kina cikin hijabi" inji Fauziyya.
Zayyana kuwa tana kai karar Radhiya wurin Daddy ashe Mairama ta jiyo yana cewa a fada mata yace ta wanke shi zai bada kudin kitson. Idan kuma taki wankewa a gida zai bada kudin salon.
"Daddy fada fa zaka yi mata, kara na kawo"
"Yi hakuri Zayyana ai ko ni bazan taba Alheran ba."
Harda guntun hawayenta tace "kafi sonta akaina"
Ibrahim yana gefensu yace "Daddy ka barni na dan saita yarinyar nan mana."
"Taron dangi zaku yiwa auta. To a kira min Alheran yau sai an wanke kan nan"
Mairama tana ji ta tabo Mami "taimaka ki hana wankin kan nan wallahi idan suka bude mata kai gidan nan yau ba lafiya"
Mami ta tashi da sauri duk da bata san ko meye matsalar ba. Tana zuwa Zayyana ta kai rahoton Daddy. Dama su Zahra sun matsu su ga gashinta saboda na Mairama da suke gani mai tsaho sosai.
Duk sun dauki abin nata wasa suka danneta aka cire dankwalin suna cewa yau sai sun ga gashin da take boyewa.
**********
Shiri Awwab yake da sauri sauri yau kadai yake da damar fita yayi sayayyar da zaiyi gobe ya taho Nigeria. Tun dare yake tunanin me zai saya ya kai musu ya rasa. Ba sabawa yayi da irin wannan abubuwan na mata yayi ba. Dan tunani yayi ya dauki waya ya kira wadda yasan za ta bashi shawara mai kyau. Ringing biyu ta dauka kamar jira take dama. A shagwabe ta soma magana tana korafin rashin kiranta da yayi har na kwana biyu.
"Sorry my G aiki ne"
"Lokacin aiki daban nawa ma daban" Ghazalatu ta sake narke masa.
"Naji nayi laifi shiyasa ma ticket din Abuja na saya don na fara ganinki kafin na wuce gida"
Ihun da tayi sai da ya cire wayar daga kunnensa yana dariya. Yana matukar son Ghazalatu. Ita ta nemi su boye soyayyarsu ma sai ta gama degree dinta idan ba haka ba aure za'ayi mata a gida ta sani. Yanzu wata biyu da yin final exam bautar kasa take jira. Sun gama tsarinsu idan Awwab ya dawo zasu gabatarwa da iyayensu da abinda ke tsakaninsu.
Sun taba hira don ta dena fushin tunda taji zai taho washegari.
"G albishirinki"
"Goro kyakkyawa kamar Yayana"
"Su Mami sun je gidan Ummin nan nawa da nake baki labari"
Yadda taji yana murna dole ta taya shi ba don ta damu ba. Yayi ta fada mata ashe harda kani an yiwa Alheran.
"Na tayaka murna, zan so ganinta gaskiya"
"Ki bini Katsina mana idan na zo"
Dadi taji tayi saurin amincewa. Awwab bai kyaleta ba yace "kune sarakan tsaraba, me kike ganin zai dace da yarinya about 18 to 19 years"
"Friend kayi mace har kake fada min za kayi mata siyayya?" Tace cikin fushi da kishi.
"Nope, Alheran nake son sayawa wani abu"
Duk da haka ranta baiyi mata dadi ba amma bata son bata masa rai yanzu sai yace ya fasa tsayawa a Abujan.
"Ka saya mata takalmi, jaka, turare, kayan kwalliya da jewelleries"
Yaji kayan da yawa to amma so yake ya yi musu abin bajinta "thanks dear" yace da Ghazalatu kafin ya ajiye wayar. [5/22, 10:51 PM] Sis Ruky: Iyakar karfinta tasa suna jan hijabin nata su ma suna ja. Mami na isowa tace su dagata amma an makara don Zahra tayi nasarar cire dankwalin.
Emzee da Ibrahim suna bakin kofa don sun jiyo hayaniya daga dakin. Rasa me bakin magana akayi harda Mami kuwa. Zainab ce ta kawo Mairama dakin, tunda taji shiru tasan aikin gama ya gama.
Zayyana ce ta fara dariya gashi ya soma lekowa amma saboda makero baifi a kirga ba sai wani uban fari fari kamar amosani kamar kora. Kullum tana shafa mai idan tayi wanka amma yau saboda da mutane a dakin ta hakura ta daure kayanta.
Kowa ta kalla gimtse dariya yake ta harzuka sosai tayi kan Zahra tana ihu "wallahi sai na rama"
"KE! Samu wuri ki zauna kada naji kinyi fada da kowa."
Kuka ta fashe dashi da karfi "wallahi Ummi kada ki cuceni ki barni na rama."
"Zahra bata dankwalinta kafin na saba muku. Wane irin abu ne haka da girmanku saboda Allah." Mami ta soma fada.
Jefa mata dankwalin Zahra tayi don yadda take kallonta kamar kura ta ga nama bazata so hannunsu ya gogi na juna ba.
Jikinsu sai yayi sanyi saboda kukan da take yi ta dauki dankwalinta ta kulle kan sannan ta mayar da hijabinta. Zainab da Mami na bata hakuri taki kula kowa sai sautin kuka da take karawa. Mairama tace su kyaleta ba shiru zata yi ba. Kowa ya fita daga dakin tana zaune tana kukanta dole Mami taje ta fadawa Major.
"A kirawo min ita"
Zahra ta kalli Fauziyya, a tsorace tace "ba dai ni ba, kece babba kuma ke kika bude mata kan"
"Zayyana...." Zahra ta soma kira ta bari saboda kyabe fuskar da ta ga tayi ta koma gefen Major tana cewa
"Daddy kace bazani ba"
"Mazaje waye zai kira min 'yata?" Yace da Ibrahim da Emzee kamar yana rokonsu.
Ibrahim ne ya tashi, Emzee kamar ruwa ya cinye shi. Yana zuwa ya sameta ta gama hada kayanta a cikin jakar da tazo da ita tana bakin kofa zata fito.
"Dariya ka dawo yi?"
"Daddy ne yake kiranki"
Gani tayi ya tsaya kallonta yaki tafiya ta zaro masa idanu "in sake bude maka ka gani da kyau ne?"
Murmushi yayi mata kawai don idan ya sake ya bude baki sai ta saka shi dariyar da baiyi niyya ba. Sai yanzu ya gane meyasa kan nata yake kullum a daure kamar mai tallan magani.
Da jakarta a hannu ta shiga su Zahra suka fara kuskus. Daddy ya gani sai ya shareta "waye ya saka ki kuka?"
Rage tsayi tayi bakin nan a gaba kowa ya ganta yasan an tabota karshe "Daddy na san komai fa, kaine da kanka ka turo Zayyana su gane min aski na"
Kafin su shigo sai da Mami ta roke shi akan ya taimaka kada yayi dariya. An san soja da dakiya, amma a cikin iyalansu, iyalan ma na Zayyanunsa mantawa yake ya taba zama soja. Ya fi fahimtar ya sake tare dasu ya nuna musu shi uba ne a garesu domin kada a sami wani shamaki tsakaninsu.
"Cewa nayi ace ki wanke kanki fa 'Yar soja uwar sojoji"
Sai da tayi murmushin jindadin kirarin ta sake daurewa "a bani kudin mota in tafi gida ko kuma a barni na rama"
"Radhiya kiyi hakuri da kaina zanyi punishing dinsu. Amma ki bar zancen ramuwa ko tafiya gida" Mami tace tana hararar bangaren da su Zahra suke.
Kumbura baki tayi "ni dai wallahi sai dai a zabi daya"
Mairama taji kunyar kada a fara ganin ko harda sakacin tarbiya a halayen Radhiya. Fada ta soma yi mata tace ta tashi ta koma ciki ta zauna.
"Allah Yasa naji kinyi fada da wani, zaki ga yadda zanyi dake. Ana lallabaki kina wani botsarewa mutane"
"Laifinsu ne fa ki kyaleta, zo nan kinji Radhiya"
Kin tashi tayi tana kallon Zainab din tace "kema Mama na ga kamar kin danyi dariya da aka bude kan"
Mairama ta sake fusata Daddy yace duk suyi hakuri laifinsa ne amma tayi hakuri.
"Ku kuma manyan ku daku kuna tsokanarta na kusa bata kambun girma a gidan nan. Kwanannan zata zama yayar kowa da kowa a cikinku sai na ga wanda zai sake gane mata askinta" murmushi yayi amma bata ji haushi ba tunda ya yi mata alkawarin zata zama yayar kowa.
Da yake ba riko gareta ba sai ta saki fuska ta harari wannan ta harari wancan "kun dai ji me Daddy yace, kuma daga nan ma soja zai kaini abuna. Hahaha idan na dawo gidan nan za'a ga kawuna"
Zayyana sai tasa hannu ta rike nata kan tana kallonta a tsorace "yanke mana kai zaki yi?"
"Inaaa yarinya kan Balotelli zanyi muku in huce haushin yau"
Ibrahim ya tuntsire da dariya harda fadowa daga kan kujera. Zainab ta daka masa duka a baya ko a jikinsa sai dariya yake "zan rike miki su 'yar uwa, ai dai baki ganni ina dariya ba"
Major ma dariyar yake yadda ta hakikance abinta. Sauran matan babu wadda ta damu da ball ko 'yan ball balle su fahimci me take nufi da Balotelli din. Hakuri dai yayi ta bata tana kara jaddada masa burinta na zama soja tunda ta ga yana lallabata.
"Soja mai babban mukami zanyi miki amma ta cikin gida, yanzu dai ku tashi amma idan kun shiga ciki kada ki kula kowa"
"Daddy gaba fa kenan?" Tace tana ware idanunta ta rike haba.
Su Zainab sai dariya, Major ya dage yana ta bayanin cewa ba gaba yake nufi ba. Kada ta kula su dai azo ana rigima.
"Au ho...ai na hakura tunda idan na dawo daga soja zan dauki mataki. Baba zanyi kyau da soja ko?" Tace tana kallon Hadir.
Kai ya gyada mata yana murmushi. Hannunsa taje ta rike tana durkushe a gabansa ita dai tana son sa sosai, sai da Daddy yace ta bi bayan 'yan uwanta zaiyi magana da iyayenta ta fita. Da taje dakin daga bakin kofa ta wulla jakarta ciki sai gasu suna darewa da sauri don ba karamin tsoro ta basu ba. Wata shu'umar dariya tayi wani abu ma sai an dawo daga makarantar sojoji. Babu wadda ta tanka mata ta shigo ta haye gado ta kwanta. Wayar Zahra aka kira ashe Awwab ne ya ya tambayeta size din takalmin Radhiya saboda yasan suna gidan. Kintata kawai tayi ta fada masa saboda ita dai bazata tambayeta ba a yau dai sannan a gabanta bazata taba mata takalmi ba don tsoron me zai faru take ji.
A falon Daddy kuwa bayan fitarsu Mairama ta shiga basu hakurin halayyar Radhiya. Gani take kamar laifinta ne ko sakacin tarbiya ne ya kawo hakan.
"Kowane da da irin halayensa da dabi'u da ake haihuwarsa dashi. Kuma yadda take dinnan Allah kadai Yasan wace irin tarin baiwa Yayi mata. Ki dena damun kaki watarana zaki ga kamar ba'ayi ba"
Mami ce da wannan dogon jawabi sauran suna gyada kai. Daddy ya bijoro musu da zancen da sukayi da su Ardo.
"Hada Awwab da kanwarsa abu ne da na kudurta tun ranar da na dora ido a kanta. Hadir ya amince ina fata Allah Yasa ku ma ku bani goyon baya"
Gabadaya matan nan uku bakunansu murmushin jindadi suke nunawa. Mami tana maraba da wannan hadin domin bazata taba kyamar tsatson Mairama da Zayyan ba. Tafi kowa sanin mahimmancin yin hakan a wurin mijinta. Zai kara sakawa yaji a ransa cewa bai ya da iyalan Zayyan din ba. Ya so Zayyan tun basu saba ba duk ranar da suka je training zata kwana yana bata labarin fitinannen basakkwacen nan. Lokaci kalilan ne Radhiya zata waye tayi zarra cikin sa'anni. Zainab ma taji dadi don burinta su hadu su baiwa Mairama da 'ya'yanta dukkan farincikin da suka rasa. Allah Ya sani ba don sa'anni suke da Ibrahim har ta bashi watanni ba itama da zata so hadasu ne.
Farincikin Mairama yafi na kowa. Wadannan mutane masu dimbin karamci a gareta ace babu kyamar yadda su suka kara wayewa ita da 'ya'yanta suka sake ci baya ta fannin wayewa da sanin ababen rayuwa amma su nemi hada Radhiya da Awwab, Awwab dinta dai wanda ya mayar da ita da mijinta iyaye tun farkon haduwarsu. Hawaye ta shiga yi tana mika godiya garesu.
"Bani da bakin godiya, Zainab kunji wani karamcin kuma?"
"Idan kina haka sai mu ga kamar a wurinka Radhiya da Zayyan ba namu bane Ummin Awwab"
"Haba Mami kada kice haka mana, farinciki ne kawai yayi min yawa"
Mami ta tambayi Major "yaushe kake tunanin auren?"
"Kuna ganin zamu iya hadawa da na su Zahra? Idan hakan yayi in sha Allahu karshen sati Alh Baba zai dawo daga Umara sai na fada masa"
To waye ma zaice baiyi na'am da wannan hadi ba. Bakinsu duk yazo daya, abu guda ya rage a sanar da Alh Baba sai ayi shiri aje a nemi aurenta wurin wadanda ya dace wato dangin mahaifinta na Sakkwato da kuma marikanta ta bangaren uwa su Ardo Barkindo.
**********
"Banza jaka bace min da gani ko inyi kwallo dake. Har yau ina tsananin mamakin yadda akayi na kwaso ki Salame"
Janye tsumman jikinta tayi da ya gama karewa ya tsotse babu wani tudu a jikinta bayan cikin jikinta na wata shida. Gabadaya ta mokade baka ce Salame bace da tauraruwarta ta taba haskawa a gidan Salisu. Aure dududu bai wuce shekara takwas ba amma haihuwarta biyar ga cikin na shida. Da kyar take tafiya yunwa ta yiwa hanjinta mugun lahani ga yara tun asuba suke kira mata yunwa suna kuka.
Ba ta daddara ba ta sake hada hannuwa a gaban Alh Indararo "Alhaji ko naira hamsin ce ka bani don Allah, bani da karfin karbo wankau da bazan tambayeka ba"